Showing 30001 words to 33000 words out of 38502 words

Chapter 11 - BAWAN ALLAH COMPLETE DOCUMENT BY Maman Muhammad .txt

20 Dec 2024

2527

asibitin amma tunda muka Shiga d'akin duk ta birkice kuma ni bata cemin komai ba shine na kwaso ta na dawo da ita"




Malam ya kalli Ummi cikin takaici zai magana tayi sauri ta ce "wallahi tallahi Baba naga yayan Hafsa indan kuma baka yarda ba kuje dashi ka gani idan bashi ba wallahi na yarda daga yau na zama bazawara" ta k'arike maganar da wani kuka me tsuma zuciyar me saurare.




Kowa awurin sai da ta bashi tausayi , Mama da k'ar ta tattaro natsuwar ta tace " Malam aje a duba ko Allah yasa za'a dace"


"To"kawai yace ya fice Aminullah ya bi bayan shi , suna fita ya juyo ya kalli Aminullah yace " ka tsaya muyi sallar magrib anan sai muje ka kaini" jiki a sanyaye yace "to"




Shikam Bawan Allah duk wainar da ake toyawa bai sani ba sharar baccin shi kawai yake yi sabo allurar da aka mai




Saifullah kuwa tun da su Aminullah suka fita yabi bayan su amma cikin rashin sa'a ya sa bai gansu ba , tun lokacin ya ke kiran wayar Aminullah amma bai d'aga ba hankalishi duk ya tashi gashi shi kad'ai ne awajen Abdallah ballantana yabi bayan su .




Sai 7:30 sannan Dr Ahmad ya dawo ganin Saifullah cikin rud'ani yasa shi tambayar meke damunshi amma ya rasa amsar da zai bashi kawai sai yace mai "ba komai "




Bayan minti goma Abdallah ya farka gami da mik'a da salati , duk suka yi mishi sannu jiki a mace yakalli agogon da ke mak'ale a bangon d'akin zumbur ya mik'e ya fad'a toilet domin d'auro alwala , shigarsa bayin kenan Aminullah ya bud'e k'ofar d'akin tare da sallama suka shigo da Malam


Cike da girma-mawa suka gaggaisa Malam yayi musu ya mai jiki , Saifullah ya kalli Aminullah domin Neman k'arin bayani suna had'a ido yayi sauri yuyar da kanshi ,




Murfin k'ofar bayin aka bud'in tun da Malam yayi arba da wannan fuskar gaban shi yayi mummunan fad'uwa ya tabbatar da ba'a zaune yake ba da sai ya fad'i k'asa warwars lallai Ummi tayi namijin k'ok'ari


😂😂😂😂😂😂😂😂






Da k'ar Malam ya had'o miyon bakin shi yace " *BAWAN ALLAH?*"




Sosai sunan ya daki k'ok'on zuciyar Abdallah amma Sam Brain d'in shi ta kasa functioning ,


D'aga idanun shi yayi ya d'orasu kan Malam take tsigar jikin shi ya tashi , brain d'in d'in shi ta fara mishi flash back nan take ya runtse ido , Dr Ahmad na ganin haka ya danna k'ararrawar kiran likita zame wa yayi zai fad'i sukayi sauri suka tare shi.










*sorry for this one wayata tana hucking*🤪👈
.
[1/21, 12:18 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com


*This page dedicated to you Bawan Allah fans , nagode da addu'oin fatan alkhairi da kuke agareni lallai Ku k'awayen arzik'i ne nagode Allah ya barmu tare ya sadamu aljannatul firdau*❤


*k'awa*🤪




3⃣7⃣






Gaba d'aya Abdallah ya birkice wasu irin hotuna yake gani black and white wa D'an da bai San inda suka samo asali ba .




Ko da likita yazo tambayoyi ya runk'a mai amma yace bai San komai ba , haka suka sake masa allurar bacci ya koma .




Har zuwa wannan lokacin Malam yana asibin mamaki duk ya cika shi .
.


Dr Ahmad ya maida duban shi ga Malam yace " Malam dama ka sanshi ne?"




Murmushin takaici Malam yayi yace "Abdallah haihuwar shi ce kawai banyi ba , kuma har yau bana bamban tashi da 'ya'yan da na Haifa da ciki na"




Shiru d'akin yayi Malam ne kawai da Dr Ahmad suka san mai suke cewa amma Saifullah da Aminullah gaba d'aya Kansu s juye yake .




Malam ya kalli Aminullah tare da nuna Abdallah dake kwance yace "wannan shine mijin Ummi da ya b'ata shekara biyar da suka wuce "




Wayyo Allah zo kuga tashin Hankali a idon Saifullah gaba d'aya yaji maganar ne tamkar saukar aradu , tabbas da za'a gwada jininshi alokacin da ansha mamaki , domin bai taba zato ba balle tsammani,




Cikin murya mai cike da firgici yace " Malam mai kake nufi ne wai ?"


Malam bai ce komai ba domin baisan kuma ya zaiyi ya fahimtar dashi ba .




Dr Ahmad yace "Saifullah ka kwantar da hankalinkA gobe insha Allah za kaji komai yanzun dare yayi "


Sannan ya juya ya ce "Aminullah ka maida Malam gida gobe zamu je gidan dukan mu in Allah ya kaimu"


Nan suka mik'e Malam yaje wajen kan Abdallah ya tofa masa addu'oi sananan sukayi sallama amota kuwa Aminullah ne ya damu Malam da tambayoyi domin shi duk ya k'agu yaji gaskiyar al'amari, amma Malam yak'i Sam suyi magana .






A can gida kuwa su Ummi sun kasa sun tsare , har da Umar ma da ya shigo gidan bayan fitar su Aminullah da Malam , tun suna tsaye har suka gaji suka zauna amma babu su babu labarin su, har 10:30am .




Mama ta kalli Umar tace "Umar kaje gida mana kaga dare yayi "


" Mama ko naje gida bazan iya yin bacci ba"




Mama zatayi magana kenan sai sukaji k'arar tsayuwar mota , Umar yace "Mama Bari na duba nagani"




Ummi kuwa zuciyarta sai k'ara bugu takeyi.




Umar na fita Aminullah har ya ta tada motar shi yayi gaba Malam kuma ya d'auki hanyar k'ofar gidan shi, cikin sassarfa Umar ya k'arasa gurin Malam yana fad'in "sannu Malam"




"Yauwa Umar "


"Malam Abdallah ne kuka gani ko?"


Murmushi Malam yayi sannan ya dafa kafad'ar Umar yace " ka kwantar da hankalinka gobe insha Allah zasu zo sai muji koma wane ne"


Ajiyar zuciya ya sauke sannan sukayi sallama , shikuma Umar ya koma gidan su Hafsa dan sanar dasu yadda sukayi da Malam,




Ranar dai kowa kwanan zullumi yayi musamman ma Ummi da take ganin ga k'oshi ga kwanan yunwa.






*Da safe*




Misalin k'arfe Tara na safe Abdallah ya fito wanka ya shirya cikin shigarshi ta k'ananan kaya maroon din T-shirt ce ajikinshi sa navy blue d'in jeans kalar yayi matuk'ar amsar jikinshi Kasan cewar shi faran saurayi kan kujerar robar da aka tanada dan masu dubiya ya zauna tare d'aukar wayarshi ya fara dannawa .




Aminullah ne ya bud'e k'ofa ya Shiga tare da sallama , batare da ya juyo ba ya amsa sallamar ,




"Bros Dr yace mu same shi awaje " cewar Aminullah yana kallon Abdallah da ya kyab'e fuska




"Ina zamu je ne?"


Aminullah zai yi magana kenan wayar Abdallah ta fara ringing , cikin sanyi ya d'aga wayar gami da sallama , bayan D'an shiru kuma sai ya mik'e ya kashe wayar ba tare da yace komai ba , Aminullah ne ya d'auki wata 'yar k'aramar traveling bag dake gefen gadon suka fita




A parking space na cikin asibitin suka tarar da Dr Ahmad da Saifullah suna jiran su Saifullah ya Shiga mazaunin driver , Abdallah ya Shiga b'arayin me zaman banza , yayin da Dr da Aminullah suka Shiga baya .




Tunda suka d'auki hanya Abdallah ya tattare hankalin shi da natsuwar shi yaba titi amana, runtse idanun shi yake yi yayinda wasu hotuna keta masa yawo a kwanyar shi wasu kalamai suna ta mashi yawo a dodon kunan shi , hannu ya sa ya toshe kunan shi idon shi kuwa runtse shi yayi kamar k'aramin yaro , duk suna lura dashi amma Sam Dr ya hana su tab'a shi sai dai suka bishi da fuskar tausayi , har suka iso k'ofar gidan bai ma San sunzo ba , sai da Saifullah yayi mishi magana sannan d'ago jajayen idanuwan shi ya kalle shi




"Mun iso fa" cewar sai ya bud'e murfin motar zai fita , shima murfin ya bud'e ya fita k'ofar gidan su ya ci karo dashi take wasu abubuwa daban daban suka runk'a yi mishi yawa akai gaba d'aya ya daina ganin zahiri sai bad'ini




Malam dake ta karatu da almajirai ba shiri ya sallame su suka tafi sannan ya k'araso fuska d'auke da farinciki




Umar ya fito daga cikin gidan su Hafsa sakamakon tsayiwar motar da yaji yana fitowa yayi arba da Abdallah jingine jikin mota aiko da gudu yaje ya k'wak'wu-meshi , shi dai Abdallah ji kawai yayi an rungume shi , shikam Umar ji yake kamar in yasaki Abdallah bazai sake ganinshi ba , rungumar da Umar ya ma Abdallah sai da yajiyo bugun zuciyar shi domin yi take zamar zata fasa k'irjin ta fito




Cikin dauriya Abdallah ya b'amb'are Umar daga jikinshi , kallon juna suke ido cikin ido , da k'yar Abdallah ya k'ak'alo wani murmushi ya jefa asaman fuskarshi , Umar ya kalli Abdallah cikin kewa yace "nayi kewarka aboki na , kai kam ko nema na baka yi "


Shikam Abdallah bubbuga kafad'ar Umar kawai yayi amma Sam bai ma San koshi waye be .




Malam ne ya katsesu da cewa " mu Shiga daga ciki ".




Hafsa da tafito ta basu izinin Shiga sai kallon Abdallah take kamar taga sabon hallita , suna had'a ido dashi ya balla mata harara azuciyar ta tace"bari na kama kaina tun kafin ya jizga ni dan naga ya k'aro wulak'anci"




Juyawa tayi sukuma suna binta abaya tana tafe tana tuntub'e , shiko Aminullah sai dariya yake kwasa aranshi yace ya samu na tsokana
[1/22, 5:11 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com






38




Hafsa na k'arasa Shiga gida ta runtuma aguje sai d'akin Ummi ko sallama bata tsaya yi ba ta yaye labule ta afka , Ummi dake ta cikiniyar sa kaya Wanda da alama yanzun ta fito wanka ta kalli Hafsa tace "ke dai banga ranar da zaki girma ba ke kullum aguje kamar y'ar gudun hijira "


Hafsa ta had'a girar sama da ta k'asa tafara magana cikin hasala "ke fa gaba d'aya ba'a miki gwaninta daga zuwa yi miki albishir sai Ki hau gwasale mutum , to ni kinga tafiya ta nama fasa fad'a " ashagwab'e ta k'arasa maganar




Cikin marai-raice murya Ummi tace "ayya *k'walli* ta yi hak'uri zo Ki fad'a min "


Hafsa ta had'e rai tace " a nawa ?,"


Ummi tayi dariyar mugunta tace "a arba'in"


Du Kansu suka kwashe da dariya .




*Bawan Allah* kuwa tunda suka shigo gidan ya k'ara birkicewa musamman ma da yayi arba da Mama tana shimfid'a tabarma k'uri ya k'ura mata ido tamkar mai son ya fahimci wani Abu amma Sam ya kasa




Saifullah ne ya jashi ya zaunar dashi, har wannan lokacin idonshi yana kan Mama , ko da Mama ta juyo suka had'a ido sai da taji gaban ta ya fad'i , azuciyarta tace "tabbas wannan bawan Allah ne"




Bayan 'yan gaishe-gaishe Mama ta mik'e taje ta kira su Ummi domin ayi komai a gaban su ,




Ummi ce agaba Hafsa tana binta a baya ahankali take takun ta kamar me tsoron kar ta taka wani abun , dai dai lokacin Abdallah ya juyar da fuskarsa b'angaren , tundaga k'afafuwan ta yake kallon ta har sai da ya dire idanuwan shi cikin Nata Sam yakasa daina kallon ta wani Abu yake ji tamkar magnet yana fizgarshi zuwa gareta badan ya danne zuciyarshi ba to tabbas zai iya mik'e wa zuwa gareta , cikin natsuwa tagaishe sannan ta nemi wuri chan gefe ta rakub'e




Malam ya kalli Aminullah da yayi shiru amma idanuwan shi k'yar akan Ummi yayi murmushi kawai ya maida duban shi ga Saifullah da kawai pretending yayi amma zuciyar shi Sam bata mishi dad'i ,




Malam ya Kali Dr Ahmad yace " Alhaji zamuso muji ya akayi ka had'u da Abdallah?"




Cike da fahinta Dr Ahmad yafara magana sai alokacin Abdallah ya maida dubanshi wurin, Dr yace" akwai wata rana ina hanyata ta dawowa kano daga Kaduna Kasan cewar tafiyar asuba nayi k'arfe shida da Rabi nakusa Shiga kano ina daf da shiga gari sai naga cincirundon jama'a a gefen titi har zan wuce kuma sai naji zuciyata tana fizgata akan naje wajen koda na fita nayi parking mota ta a gefen titi na tsallaka abunda nagani ba k'aramin tayar min da hakali yayi mutane ne kwance kamar matattu cikin gaggawa na kira motar asibitin my nan da nan sai gasu sunzo akwashe su sai asibitin aminu kano , to nikam tunda na mik'asu cikin saurin likitoci ban k'ara bi ta Kansu ba domin ba b'arayi na bane , bayan yan kwanaki sai aka kirani ake sanar dani cewar mutanen nan duk 'yan uwansu sun gansu amma banda mutum biyu dan d'ayan ma bai farfad'oba likitoce nata aiki akanshi shikam d'ayan ya farka , tunda naji hakan na garzayo nazo asibitin , abunda na gani ba k'aramin rud'ani nashiga ba amma na dake duk dan kar agane , fuskar Abdallah iri d'ayace da fuskar d'ana Abdallah da yarasu shekara bakwai kenan da ace yana Raye to tabbas za'a kirasu da identical twince wannan dalilin ne yasa naji ina son taimaka masa"


Tunda ga nan Dr Ahmad ya cigaba da bada labari har yau da suke tare .




Malam yayi ajiyar zuciya yace "lallai Allah mai girma wato Abdallah Allah bainifi zakayi ilimi har ka zama wani abuba sai da basirarka ta gushi lallai Allah mai girma ne , Alhaji babu abunda zamu ce maka sai dai mu bika da godiya gami da fatan alkhairi Allah yasaka maka da mafificin alkhairi , Allah ya jik'an Abdallah"


Nan dai Malam yayita kwararo addu'oi suna amsawa da Amin,




Daganan Dr Ahmad ya buk'aci yasan wane ne Abdallah , tiryan tiryan Malam ya runk'a bashi labarin tundaga haihuwar Abdallah har zuwa ranar da suka rabu dashi da sunan zuwa kano saro kaya , maikaratu idan ya had'a da labarin Dr zai bashi cikkaken taruhin Abdallah,




Ko da Malam ya gama bada labari gaba d'ayan su kowa da hawaye a idonshi musamman ma Saifullah da baitab'a tsamanin Abdallah zaiyi irin wannan rayuwar ba tsantsar tausayin abokinshi ne ya kamashi matuk'a .




Shikam Abdallah kuka yake kamar yaro dan sai yau duk abubuwan da yake gani suka fayyace mishi gaba d'aya ya rasa bakin magana sai hawaye dayake ta faman yi .




Ummi kuwa abad'aya farinciki ne ya mamaye mata zuciyarta Rana ji kamar taje ta rungume mijinta dan murna da jin dad'i .




Duk dauriyar da Mama taso yi amma hakan ya gagara sai hawaye ya sub'uce mata .




Umar , Saifullah tare da Aminullah su kaita rarrashin Abdallah




*gareku readers shin me kuke tunanin dai Kasan ce bayan nan ? Shin Dr zai bar Abdallah hakanan duk da cewar ya taka muhimmiyar rawa a rayuwar shi ? Shin ya alak'arshi da Ummi zata kasance , maiye makomar soyayyar Saifullah ga Ummi? Wannan da ma sauran wasu tambayoyi suna cikin page na gaba*


Taku ce Maman Muhammad💓


@08165728746
[1/24, 4:46 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com






*Wannan page d'in na sadaukar da shi ga dukkanin masoya labarin bawan Allah , tare da duk mai suna Zainab*💓




*Fatan alkhairi*❤


*Edited by Mum Mussadiq*😁






3⃣9⃣






Bayan natsuwa gami da gamsuwa ta ratsa zukatan su sannan Malam ya maida hankalinshi kan Abdallah yace " to Abdallah yanzun ka gane ko kai waye ko ?"




Sai da ya ajiye wata nan nauyar ajiyar zuciya sannan yace "na gane Malam"




Murmushi Malam yayi sannan yace " to wace ce waccen?" Ya nuna Mama




Kallonta yayi tana ta sharar k'walla yaja gwuiwoyin shi ya tafi kusa da ita tare da rik'e hannuwan ta yana fad'in " Ki yafe min Mamana na saki kuka insha Allah ba zaki k'ara kuka ba daga yau"




Dafa kanshi tayi tana Sosa gashin kanshi da ya kwanta yayi luf tamkar D'an India tama kasa magana tsabar farinciki ,




Dr Ahmad yayi gyaran murya yace " Allah ne k'addara zumunci tsakanin mu shiya sa bai bani ikon Neman danginka ba tunda farko kuma zumuncin mu ba zai tsaya anan ba "


Rarrafawa ya sake yi yakoma gaban Dr Ahmad yana mai share k'walla yace " thank you soo much Dad bansan da bakin da zan godemaka ba hak'ika kai wani haske ne acikin rayuwata, ka bani ilimin da ina rayuwar zahiri banyishi ba sai gashi na samu alokacin da iyayena da dangi na suka cire tsammani da rayuwata, nagode Allah ya saka maka da mafificin alkhairi Allah ya jik'an d'an uwana Abdallah yayi mishi Rahama"


Duka suka amsa da "Amin"


Kusa da Umar ya koma tare da rik'e hannun shi yace "ina cikin kewar d'an uwana wani lokacin nakanji zuciyata tayi min baki Ashe rashin abokin arzik'i ine irin ka"


Murmushi kawai Umar yayi


Dai dai kusa da Aminullah ya koma ya saiti kunnanshi yace " thanks for taking care of my wife I really appreciate you are indeed a real hero"




Aminullah yace " you deserve it"




Banza yayi da Saifullah kamar bai ganshi ba , Ashe shikuma abin ya bashi haushi sai ya mik'e afusace zai bar gurin , cikin sauri Abdallah ya rik'o hannunshi " where do you think you're going? ka kwantar da hankalinka ba sai na ambace ka ba you're always and ever in my heart"




Nan duk suka kwashe da dariya haka sukayita hira har lokacin azahar yayi ,




Awaje haka mutane keta tururuwar zuwa ganin D'an gayu Abdallah wasu ma sai sun tab'a shi sunji .




Mama kuwa haka mak'ota suka ta zuwa mata barka da taya murnar dawowar tilon d'anta cikin lafiya da aminci




Bayan tafiyar su massalaci sai ga yara daga gidan su ummi d'aya Leda ce ahanunshi bak'a d'ayan kuma d'irkeken zakara ne anyanka shi an fige sukace gashi inji Malam , nan da nan suka fara aikin su ,




K'arfe 2:30 suka dawo massalaci , suko su Ummi har sun gama dafa jalof d'in shinkafa da wake ga naman k'aza k'amshi sai tashi yake , su jera kan tabarma .






Bayan sun ci abinci sun k'oshi Dr Ahmad yace musu dama yau yake San komawa kano , Abdallah yaso ya bishi amma k'emadagas Dr yak'i yace ya zauna sai ya huta agida sunaji suna gani yayi musu sallama yatafi bayan ya yima Mama da Malam alkhair




Nan fa suka zauna shida abokanshi suna ta hira Mama na gefe yana kallon D'an

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login