Showing 36001 words to 38502 words out of 38502 words

Chapter 13 - BAWAN ALLAH COMPLETE DOCUMENT BY Maman Muhammad .txt

20 Dec 2024

2534

nan d'aki na mana "


"To ai kaji matsalar guy haya zaka nema idan ba haka ba ina mai tabbatar maka ba zaka mori amarcin ka ba"




Umar ya kalleshi ya kwashe da dariya yace "ahankali dai abokina yanzun kam dole mu zauna a nan dan duk basira ta ta k'are Mama kanta bataso mu zauna wuri d'aya amma insha Allah ba da jimawa ba zan nemi hayar"




"Tashi muje Umar "


"Ina zamu? nifa kasuwa zanje "


"Shikenan kaje amma kasani gobe ba inda zaka je "


"Allah ya kaimu"


Nan sukayi sallama
[2/6, 10:54 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com






*dedicated to you readers ina alfahari daku*




*BAwan Allah fans much luv dearies Allah ya barmu tare*❤






Page4⃣2⃣






Su Abdallah anata shirye shiryen bikin Babban aboki , acikin kwana uku ya Samar ma Umar gidan haya me dan sauk'in kud'i .






Alokacin da biki ya rage saura sati d'iya sai Mama ta kira Abdallah tana masa fad'a , ranar ba kowa agidan su Ummi duk sun tafi makaranta ,




"Kai ma ai ya kamata ka d'auki taka matar kusan inda dare yayi muku "


Shiru yayi yana Sosa k'eya sannan yace "to Mama ina zamuje?"




"Kai ma hayar zaka nema kuje can Ku bani guri in sarara"






Sai da yad'anyi nazari sannan Yace " ni da Mama na bari ne idan na fara aiki na samu kud'i sai in siyan mana wadataccen gida sai mu koma gaba d'aya"




"Eh tunanin ka yayi kyau amma dai yanzun kafin wannan lokacin ka nemam muku wani gurin da zaku D'an zauna"




"Shikenan nan Mama bari a gama bikin Umar sai na fara Neman gidan"




"A'ah *BAWAN ALLAH* ni so samu ma Ku tare rana d'aya da abokin naka"




Kunya ce ta kamashi ya mik'e yana Sosa k'eya yace " to Mama sai anjima"


"Mu juma da yawa" ta fad'i tana murmushi .




Bayan ya dawo da daddare ya samu Malam ya fad'a masa yadda sukayi da Mama fatan alkhairi ya bisu dashi Sannan suka k'ara tattaunawa daga nan ya rok'i alfarmar kar asanar da Ummi komai har sai ta tare Malam dai murmushi kawai yayi,




Daga nan ya koma gida bayan yayi wanka yayi shirin baccin shi tsaf sannan ya kira Dr Ahmad shima cikin jin kunya ya sanar masa , cike da jin dad'i da murna yayi masa fatan alkhairi Sannan sukayi sallama,




Ajiyar zuciya Abdallah ya sauke sannan ya furta a fili "komai ya kusa zuwa k'arshe" murmushi yayi tare da jero addu'oi sannan yayi bacci,






Washe gari da safe Umar yazo gidan dama sunyi da Abdallah zasu je funtua gidan Amaryar Umar d'in, bayan sun gama shirya wa tsaf suka fito. Abdallah ya sha kwalliya kamar wani sabon ango sai fara'a yake , Ummi dake zaune d'akin Hafsa tunda ta k'yallara ido ta ganshi sam ta kasa kauda idonta ba dan k'yafta ido dole bane to da Ummi bata yiba tasan Abdallah kyakkyawa ne amma bata tab'a ganin asalin kyanshi ba sai yau .




Shikam tunda ya juya suka had'a ido sau d'aya bai k'ara waiwayar inda take ba , ya nufi k'ofar Mama , yana shirin yin sallama ita kuma tana fitowa, hakan yasa duk suka zauna a k'ofar d'akin kan tsaftacecciyar tabarmar dake gurin ,


Bayan sun gaisa Mama tace "Umar ina zuwa haka wannan shiri kamar yaune za'a kawo mana suruka "




Caraf Abdallah ya amshe da " wata surukar za'a je nemo miki"




Cike da mamaki Mama tace"wata suruka kuma AI ni na gama aurar da yarana maza sai dai na jira suruki kuma"




Dariya Abdallah yayi sannan yace " to Mama suruka ta biyu za'aje ne mammiki" ya k'arishe maganar yana langab'ar da kanshi tare da had'e hannunshi guri d'aya alamar pleading ,




Mama ta gane zolaya yake ji sai tai murmushi ta ce "Hakan yana da kyau AI Allah ya sanya alkhairi "


Duk suka amsa da "amin"




Umar yace " Mama AI yarinyar ma k'awar Maryam ce "




"Masha Allah Abu yayi kyau" nan dai sukayi ta barkwancin su sannan suka fita .




Ummi kuwa tunda suka fara maganar take jin zuciyar ta kamar zata tarwatse , mekunanta ya ke jiye mata ne ?tun kafin ta tare Abdallah zai mata kishiya ? , wani kuka ta fashe dashi , Hafsa kam ya kwance a d'aki tana sharar baccin ta har Ummi taci kukanta ta gaji , har tayi shiru






Shikam Abdallah ko ajikin shi fita ma yayi harkarta duk da hakan bai mishi dad'i shirye shiryen kawai yasa agaba






A b'angaren Dr Ahmad kuwa zuzurutun kud'i ya turama Abdallah yace su sha shagali shida aminin shi




Abdallah kuwa wani gidan haya ya samu unguwar me kyau gashi babu hayaniya




Plat uku ne agidan da ya wadatu da manya manyan dakuna 2 bedrooms ne sai Babban parlor mai tare da dining area gefe kuma kitchen ne da madai daicin store aciki balaifi gidan yana da tsari mai kyau






Wajen Ummi Mama da ummanta gyara suke mata sosai da tambayi dalili duk amsa d'aya suka bata suna so 'yarsu tafi ta kowa kyau , Babban abinda abinda ke damun ta kuwa shine yadda Abdallah ya d'auke k'afa agidan sai ya kwana bai shigo ba bata San yana can ya k'ok'arin karb'ar Amarya ba ,






Akwana a tashi ba wuya agurin mai rai yau ta kasance juma'a, Wanda gobe asabar za'a sha shagalin biki,




Ummi na zaune ita da Hafsa ad'aki yayin da Mama tana tsakar gida tana Taryar bak'i daga danginta zuwa dangin Baban Abdallah , wata daga cikin k'annen MAMAN Ummi tashigo d'akin da sallama bayan sun amsa mata tace "Ummi yaya tace maza Ki tashi muje gidan su Habiba mai kotso da k'unshi ayi miki"




Shiru tayi kamar bata jita ba da yake ba wani girman Ummin sosai tayi ba.




Hafsa tace" ummi dake fa ake magana ,"




Azuciye ta juyo dan bak'in ciki duk ya gama cikata tace " naji sai mene ? Ni ku k'yaleni da kinibibin kU ba inda zanje"


Zuwaira k'anwar Umma taji haushi ta fita kai tsaye Mama ta sanar ma duk yadda sukayi da Ummi , murmushi Mama tayi tace "muje gurin Ummin "




Ummi najin sallamar Mama sai ta hau kuka ita bazata ba da k'yar da sid'in goshi Mama ta lallab'a ta ta tafi ,




Daren ranar kuka ta kwana yi sai ta d'aga waya zata kira Abdallah dan ta gaya mai irin dumbin k'aunarshi da take yi sai kuma ta kasa domin zuciyar ke gargad'in ta muddin tayi hakan to zaiga zak'ewar ta bare ma yanzun da yake rawar jiki za'a kawo mai sabuwar Amarya zai yi auren soyayyah acewar Ummi fa kenan🤣
[2/7, 10:12 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com




_Assalamu_ _alaikum_ _readers anan Zan tsaya da littafin*bawan Allah*sakamakon wasu dalilai ina fata zaku yi min uzuri🙏sai mun had'u a sabon novel dina mesuna RAYUWA TA ina fatan shima zai nishad'antar damu ngd_




*GODIYA*


_Godiya ta musamman ga k'ungiyar REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS,like I said b4"sisters we are the best ever so let's keep shining like a stars in the sky🌠🌠_📚✏


*jinjina gareku readers*


*Bawan Allah fans bansan ta inda zan fara ba duk fad'in social media bani tamkarku ina yinku irin sossai d'in nan Allah ya bar zumun ci*




*my bestie I miss you (Ummu Sadeeq)*


*Ameenert*


*Rahma Ismail*
*Sadiya illa*
*acceya*
*Maman hanan*
*Ummu adil*
*fareeda*
*nafi khan*
*matar me kake*
*sadeeya*
*MAMAN sa'a*
*Binta mala*
*aisha saleh idrees*


*Kai aradun Allah kuna da yawa ba zaku lissafu ba Kawai Kudai Ku sani kuna mak'ale azuciyata*🤞🤸‍♀




*miss husnah*no more hawan water yanzun agayama likita bawan Allah yazo k'arshe dan haka ya ajiye ya ajiye makaman aikinsa agefe wannan ba fanni shi bane Maman Muhammad ce zata yi aikin ta🤣




*Maman Mimi*
*MAMAN Abdul*
*ummul khairi Gj*
*ummul khairi Jibril*
*hussaina sanee*
*Rabi'atu paki*
Love you guys😍






Kuyi hakuri readers idan nace zan lissafoku to kunfi k'arfin fige d'aya mai d'auke da read more goma fatan kun gane






🤣🤣🤣🤣🤣🤣






🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚




Page 4⃣3⃣




Washe gari da safe haka ta tashi kamar an zare mata laka ajikinta komai cikin sanyin jiki take yinshi .




Tana kwance a d'aki har 11:00am batayi wanka ba Sai ga Mama tashigo d'akin ta kalli Ummi da kwaNce tamkar mai bacci , gefen katifar Mama ta zauna sannan ta dafa kafad'ar Ummi dake kwance tace "kiyi hak'uri Ummi nasan dukkan kowace Mace dole tayi kishin mijinta bai kamata Ki nuna damuwar Ki acikin mutane ba aro juriya zakiyi Ki sanya ma zuciyarki , sannan kada Ki kuskura Ki nuna ma kishiyar kin damuwar ki domin idan tasan lagwan Ki ta runk'a k'untata miki kenan , Ki zama mai juriya ta fannin kishi, Ummi ?" Mama ta k'arishe da kiran sunan Ummi wadda tuni idonta yake ambaliya da ruwan hawaye




Cikin sanyi Ummi ta d'ago ta kalli Mama tacw "na'am"




"Kiyi hak'uri da duk wacce zaki gani amatsayin abokiyar zamanki ba bak'uwar Ki bace kin Santa farin sani dan na tabbata zakuji dad'in zama"




Tunda Mama take maganar k'irjin Ummi ke dukan uku uku , kanta be k'ara kullewa ba sai da Mama tace mata tasan wadda Abdallah zai aure , mamaki take ita dai tasan bata San kowa Funtua ba to me hakan yake nufi?




Haka dai Mama tayita mata nasihohi sannan ta lallab'a ta taje tayi wanka ,




Da daddare Hafsa tashigo d'akin ta samu Ummi na zaune ta zabga tagumi, cikin tausayin k'awarta ta , zama tayi kusa da ita sannan ta fara magana


"Kiyi hak'uri Ummi nasan yaya bai kyauta miki ba , kin jajirce kinyi zaman jiran shi na shekara biyar duk da cewar bakida tabbacin cewar yana Raye ko akasin hakan amma kika jure, sai gashi da ya dawo babu abinda ya saka miki dashi sai kishiya, kiyi hak'uri Ummi wannan wata jarabawa ce daga ubangiji ya gwada kine don ya gane k'arfin imaninki, kuma nan gaba kad'an zaki samu *CHANJIN RAYUWA* tare da *RIBAR BIYAYYA* Kinji k'awata?"




Cikin sanyi Ummi ta d'aga kanta alamar "eh"




Hak'ik'a nasihar Mama da Hafsa ba k'aramar tasiri sukayi ba azuciyar Ummi har taji damuwarta ya fara raguwa.




"Yauwa k'awata to tashi muje ance Amarya na hanya muje mu tarbeta"




Harara ta juya ta watsa ma Hafsa sannan ta ce"to meye nawa kuma aciki?"




"Haba Ummi ba yanzun muka gama magana ba?"




"Eh amma Ki sani ba inda zani"




"To shikenan dama Malam ne yace lallai muje Dake tunda kince bazaki ba bari naje na gaya mai"




Bashiri Ummi ta mik'e ta sanya hijab d'inta tare da fad'in "Hafsa bomb "




Koda suka firo k'ofar gida motoci biyu ne dalla dalla sai d'aukan idanuwa suke ,




Abinda yaba Ummi mamaki bewuce ganin yayyen mamanta biyu da k'annin Malam biyu tana cikin Mamaki taji anjata zuwa jikin d'ayar motar da Babu kowa aciki , itadai Ummi haka ta zama rak'umi da akala, har suka isa gidan ,








"Masha Allah gida yayi kyau " haka mutane keta fad'i lokacin da suka gama zaga Gidan,




Hafsa da Ummi kuwa suna parlor Kamar suyi kuka dan takaici dan gidan ya tsaru komai ansa dadai na k'aramin mekud'e ,




Suna zaune su kad'ai a parlorn sai Ummi tace "ke nifa naji gidan shiru "


Hafsa tace "nima haka"


AI duk sai sukayi waje abin mamaki babu motocin da sukazo dasu babu Kuma matan da suka zo tare , nanfa suka fara salati kowa na bazai zauna ba ,




Suna zuwa bakin gate megadin ya taso yace "kuyi hak'uri 'yanMata an bani umarnin kar na bar kowa ya fita daga wancan b'arayin " ya k'arike yana nuna inda suka fito




Nan suka hau magiya da bashi hak'uri amma Sam yak'i hakanan suka koma ,




Hafsa Ce tace "yauwa bari na kira Aminullah ya zo ya maida mu gida ,"


Ummi tace" dad'ina na da ke akwai basira wani lokacin"


Alokacin da Hafsa ta kira Aminullah yace mata gasu nan a Hanya shida angon ,




Suna zaune tsumu kowa da abinda yake sak'awa azuciyar shi , suka jiyo k'arar tsayuwar mota,




Nan da nan zuciyoyinsu ya tsananta bugawa ,


Hannun k'ofar aka murd'a tare da turo k'ofar gami da sallama ,


Nan take numfashin Ummi yayi sizing na wucin gadi sakamakon idanuwanta da sukayi tozali da kyakkyawan angon ta ahankali ta furta "Subhannallahil khalk'il azim"




Abdallah ne a gaba sannan Saifullah sai Aminullah dake take masu baya ,


Abdallah kuwa direct kusa da Ummi yAje ya zauna yana fad'in "uwar gida sarautar mata"


Ta kaici ne ya kama Ummi ta yunk'ura zata mike kawai sai taji an jawota , unexpected taJi ta fad'o ajikin shi ,


Dariya Saifullah yayi yace "au tun bamu je ko ina ba?, ke Hafsa tashi mu tafi",




Shi dai bai ce komai ba harsuka kai bakin k'ofa , Ummi ko sai kick kici take tana son k'wacewa amma ta kasa Da dai taga dagaske tafiya zasuyi AI sai tace "ni ka k'yaleni zasu tafi subaRni,"


Ahankali ya rad'a mata. Dai dai saitin kunnanan Ta," ina zakije ne baby?"


"Gida" ta bashi amsa a tak'aice




Kallon yayi sannan yace " Ummi kina tunanin zanyi miki *Butulci* bayan *Hallacin so* da kikamin idan na miki haka banzama adali ba , Ummi kisani har *ABADAN* bani da tamkarki ke kad'ai ce Mata




AI mutumiyar taku duk ya kashe mata jiki da k'yar ta iya cewa "Amaryar taka fa?"


"It's just a plan"ya fad'i yana dariya


Cizo ta daddage ta ganna Mishi a k'irji saida yayi 'yar k'ara ita ko mik'e wa tayi taruga bed room aguje ya bita yana fad'in " saina rama"




Haka dai sukayita guje guje daga K'arshe dai sukayi abinda ya zamar musu wajibi bayan sunyi sunnoni sannan suka fuskanci junansu cikin soyayya da k'aunar juna ,




Tun daga wannan rana Ummi take samu kulawa ta musamman gami da soyayya




*Bayan sati biyu*




Saifullah ya aika aka nema masa auren Hafsa Kasan cewar da sannayya nan take aka bashi tareDa sa rana wata d'aya aiko Saifullah ya daka tsalle yace yayi yawa ina laifin sati biyu nan dai Aka sha kan Baban Hafsa ya hak'ura




An ragargaji biki Ummi itace Babban k'awar Amarya Sosai akasha shagali ,


Bayan biki Dr Ahmad yakira Abdallah ya sanar masa ranar ranar wata litinin asibitin shi bashiri ranar Sunday ya wuce Kano ,






Aiki yake sosai , ,sai ya kasance shi da Zaria sai dai week end ,





Allah Sarki Abdallah bai manta hallaci ba mak'udan kud'i ya d'auka yA ba Umar domin YakAfa kanshi
,


Bayan shekara d'aya Da Rabi




Tunda Nesa na hango shi yana Ta sunturi k'ofar labour room ya had'a zufa,


Bud'e k'ofar da akayo ne ya sashi saurin matsawa Dr da ya bud'e k'ofar D'auke da murmushi afuskarshi yace"congratulation Dr Abdallah your wife delivered healthy Nd safely "


Murnar Abdallah Sam tak'i b'oyuwa jiYake duk duniya ba Wanda ya kAI shi Sa'a, yana cikin murna sai ga Saifullah da Hafsa itama DA tik'ek'en cikinta, tare suka Shiga dakin saibarcin ta take ,


FArincikinSu bai Kara bayyanu wa ba sai da suka ga yara biyu kyawa wa Wayyo zokuga godiya ga ubangiji wajen Abdallah. Ranar suna yara Ahmad da kabir .


Bayan wata uku Hafsa ta Haifo sankaceceyar yarta taci sunan Hindatu (Mama)




Aminuallah kam yana chaina yana masters dinshi akan bussines




*ALHAMDULLIH*

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login