Showing 9001 words to 12000 words out of 38502 words
Chapter 4 - BAWAN ALLAH COMPLETE DOCUMENT BY Maman Muhammad .txt
lallab'a ya kwanta kusa da Ummi ya D'an janyo ta jikin shi kad'an , ita ko mage Sarkin son jiki ai sai ta k'ara shige masa ,
Can acikin baccin ta take jin wani Abu yana ratsa ta , tadai ji kamar ana mata waiwayi , har wani D'an zillo take , bata k'ara dawo wa hayyacin ta ba sai da taji yana k'ara mulmula ta, cikin fargaba ta cire hanunshi da ke kan k'irjin ta ,
Shi kuma kunya ce ta kama shi yaji kamar k'asa ta tsaye ya shige , kawai sai ya juya mata baya ,
Ummi ta kira shi a hankali " yaya?"
Da k'yar ya iya cewa "uhum"
"Dan Allah kada kayi fushi dani da gaske tsoro nake ji"
Abdallah najin ta ce haka a zuciyar shi sai yayi hamdala yace "bari na buga sabon wasa" ya k'arike da murmushi
Juyo wa yayi ya kalle ta sannan ya ce "idan bakya so nayi fushi da ke to Ki barni na gama abinda na fara"
"Yaya da zafi fa"
"Karki damu zanyi miki a hankali ba zaki ji zafi ba "
Da haka ta yarda yana ta wasa da ita a hankali har bacci yayi awon gaba dasu ,
Da safiya tayi Ummi kunya Abdallah kunya , shi atunanin shi zata gaya ma Hafsa abinda yayi mata shi yasa yak'i sake wa ,
❤❤❤❤❤❤❤❤
Lokaci yana ta tafiya yanzun auran Abdallah da Ummi ana Neman wata biyu , kullum zaiyi 'yan wasanninshi da ita domin wai a cewar shi tausayi take bashi k'aramar yarinya ce ,
Ummi ce kwance akan cinyar Abdallah yana yi mata tsifa duk da ba iyawa yayi ba amma tasa daru ita sai ya mata ,
Bayan ya gama na ta ce "yaya juya bayan ka kaga wani Abu "
Shi ko yace "a ina?"
"D'an duk'awa za kayi wani Abu zan cire maka"
Juya wa yayi yace" gani cire min"
AI sai ta d'are bayan shi tana fad'in "na mishi wayau" harda gwalon ta
Murmushi yayi yace "sauka min abaya ke kullum ba kya girma"
Nok'e kafad'ar ta tayi a lamar A'ah
"Ummi kin cika rigima kamar wata 'yar yaye"
Dariya tayi tace "ka manta yaye na aka kawo maka"
Juyo da ita yayi yace "yarinya karki damu naku sa yaye Ki" ya k'arike yana kashe mata ido d'aya
Duka ta kai mai abaya tana fad'in" wallahi ni bana so"
Dire ta yayi yana dariya yace "wannan kuma ke kika sani ni na tafi masallaci"
Cikin dare suna cikin barci manne da juna kamar tip da tyre sai Abdallah yaji motsin Ummi yayi yawa , janyo ta yayi ya sake k'ank'ame ta yana fad'in "Ummi Ki natsu mana"
Sai da tayi wani D'an k'ara tace "wayyo yaya cikina zan mutu"
Zumbur ya mike ko da ya duba ta Ashe ta galabaita sai murk'usu take yarik'e ta yana fad'in "ina ne " amma ta kasa magana , kwantar da ita yayi sannan ya hau Neman maganin ta cikin kaya be sha wahala ba ya gansu cikin hanzari ya d'ebo ruwa ya d'aga ta ya na bata yana shafa bayan ta ahaka har ta shanye ,
Ahankali taji ciwon na sauka tare da wani bacci , a haka ya k'arasa baccin da ita a nannad'e ajikin shi,
Da safiya tayi ya je ya gaida Mama ya ke gaya mata ciwon Ummi ya tashi Dan haka zai je kasuwa ko zai samu dako , ya kaita k'aramin asibiti ,
Mama tayi mishi fatan alkhairi ya fita a hanya ya gamu da Umar shima kasuwar ya nufa bayan sun gaisa Umar ya D'an tab'a shakk'iyyancin shi sannan yace "ustaz sai ina haka"
Nan Abdallah ya gaya mishi dalilin fitowar shi gida Dama inda ya yanufa
"Allah Sarki Allah ya bata lafiya"
"Amin "Abdallah ya amsa
"Dama yau za'a sauke ma Alhaji Bello kaya a store d'in shi , yanzun ya kirani kayan sun iso muje mu rok'e shi ya bamu kayan mu sauke sai ya biya mu"
"To" kawai Abdallah yace Dan shi mafita kawai yake nema
Da suka je suka samu Alhaji Bello be hana su ba ya ce suyi domin shi mutum ne tausayi
Suna cikin kwashe kayan ne , wayar Abdallah ta hau ruri , bak'uwar number da ya gani sai da gaban shi ya fad'i
Yana d'aga wa muryar Mama tayi mai sallama tana fad'in " Abdallah ka dawo gida Ummi ba lafiya" Mama tayi maganar cikin muryar kuka sannan ta katse wayar
Juyawa yayi a dabur ce yace "Umar jikin Ummi ya tashi" AI sai ya kwasa a guje
Shima Umar ya runtuma ya bishi
🙆♀🙆♀🙆♀🙆♀🙆♀🙆♀🙆♀🙆♀
[12/21/2017, 1:12 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*Dedicated to Bawan Allah fans , kusani ina sonku ina k'aunar kuma saboda ku nake rubuta wannan labarin , Allah ya bar zumunci ya k'ara mana dank'on soyayyah❤🏹 one luv*🏌com
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
15+++16
Koda suka k'ara sa gida Ummi a sume take bata San ma inda kanta yake ba , Mama na rik'e da ita ita kuma hafsa tana duk'e gaban Ummi tana kuka tana fad'in "Dan Allah Aunty Ummi kar Ki tafi Ki barni inkika mutu bansan yadda zanyi ba "
Hankalin Abdallah yayi k'ololuwa gurin tashi , kasa yin komai yayi , Umar ne yayi k'arfin halin fita waje a guje cikin sa'a kuwa yaci karo da me Napep nan ya tsayar da shi ya gaya mishi asibitin da zai kaisu sannan ya juya dashi suka koma , inda Umar ya bar Abdallah nan ya dawo ya same shi , dafa kafad'ar shi yayi yace "aboki ga me Napep can na samo a waje ku kama ta ku saka"
Haka nan jiki ba k'awari suka saka ta a napep suka nafi wani primary health care da yake kusa da su ,
Suna zuwa wani likita ya duba ta yace musu ba zasu iya yi mata komai anan ba saboda ba suda kayan aiki , nan likitan ya rubuta ta musu transfer zuwa A B U teaching hospital dake tudun wada , hakalin kowa ya k'ara tashi sai alokacin ne Umar ya d'aga waya ya sanar ma Malam abinda yake faruwa yace gashinan zuwa shiko Abdallah ya zama kamar photo domin D'an zaman da yayi da Ummi ta riga ta zama wani jigo na rayuwar shi, tunanin shi d'aya idan ya rasa Ummi ba Wanda zai k'ara bashi 'yarshi ya aura , shi yasa kullum idan ya tuna da Ummi yake k'ara sonta gashi ita kuma halin da take ciki ,
Dai-dai nan Mama tazo ta tab'ashi tare da cewa " kamata muje"
Kasan cewar wurin ba'a rasa abin hawa yasa suna fita suka samu napep sai tudun wada ,
Suna zuwa akayi emergency da ita nan ma likitoci suka shiga aikin su , bayan awa biyu wani likita yazo ya tambayesu sune 'yan uwan Zainab Kabir? Suka amsa masa yace su biyo shi office d'inshi
Bayan suje office d'inne ya basu izinin zama sannan ya fara bayani cewar "wani k'ari ne ya fito mata a gefen k'odar ta kuma yayi girma Dan haka dole ayanke , amma kuma ba zamu iya yi mata aikin nan ba dole zamu tura ta Babban asibitin mu dake *Shika* Dan haka ku shirya"
Tunda doctor ya fara maganar Abdallah ke karanto "Inalillahi wa inna ilaihirraji'un"
Bayan fitowar su daga office d'in Mama tace suje suyi sallah , Hafsa kuma ta koma gida tunda sun bar gidan ba kowa ,
Bayan Abdallah da Umar sunyi sallah ne sai Umar yace "ustaz bari naje gida na dawo ba jimawa zanyi ba"
Kai kawai Abdallah ya d'aga masa , sannan Umar ya tafi ,
Yana zuwa gida ya fasa asusun da yake Tara kud'in auren shi duk da dai beda budur war🤪🤪
Ya fito kenan zai fita sai Maman su ta kirashi "ina zaka je ne haka?"
.
Nan ya Sanar da ita meke faruwa , ita tace bata ga ta zama ba,
Ko da suka koma asibiti sun tarar da Malam da uwar gidan shi can Wanda har yanzun ba'a basu ikon ganin Ummin ba
Daf da la'asar wani likita yazo yace ga Ambulance cen suje su shiga za'a wuce da Ummi Shika , Umar ne yaje yayi clearing komai ba tare da sun sani ba ,nan suka d'unguma suka wuce asibitin
Nan ma wani gwajin aka sake yi likitoci suka tabbatar da lallai saidai ayima Ummi surgery gobe domin abin yana gab da fashe wa kuma idan ya fashe mutuwa zatayi ,
Abdallah najin hakan yayi sauri yace "likita kuyi duk abinda ya kamata ni zan biya kud'in"
Kowa ya juya ya kalleshi tare da mamakin abin yace
Doctor yace shikenan ba damuwa ,
Abdallah ya sake cewa "kud'in zasu kai kamar nawa ?"
"Zaku iya kashe kamar dubu d'ari da goma "
"Shi kenan doctor kuyi duk yadda ya kamata"
Mama dai suman tsaye tayi da jin kalaman D'an nata ,
Umar kuwa cewa yayi "Allah yasa abokina ba haukace wa kayi ba"
Juyawa yayi ya kalli Umar yayi masa wani murmushi me wuyan fassara
Malam ne yayi k'arfin halin cemai "Bawan Allah Kasan me kake fad'a kuwa ?"
D'aga kanshi yayi alamar "Eh"
"To ina zaka samo wannan mak'udan kud'in"
Cikin sanyin murya yace"wallah nima bansan inda zan samu ba amma ina rok'on Allah ya bud'a min hanyar alkhairi kafin safiyar gobe"
Malam ya jinjina kai
Tunda Abdallah ya shiga masallaci sallar magrib ya duk'ufa sallah da addu'ar Allah ya kawo masa mafita dashi da Umar kwanan tsaye suka yi ,
Bayan sun idar da sallar asuba ne Abdallah ya tuna da wani Abu bashiri ya mik'e kamar an tsikare shi yace ma Umar bari yaje ya dawo
🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔
[12/22/2017, 12:23 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJI'UN*
*KULLU NAFSIN ZA'IK'ATUL MAUT ( dukkan wata rai sai ta d'and'ani mutuwa)*
*AMADADINA DA SAURAURAN 'YAN UWANA WRITERS NA PURE MOMENT OF LIFE WRITERS MUNA MIK'A SAK'ON TA'AZIYYAR MU GA 'YAN UWAN ZAINAB MUHAMMAD (ZEE SOBA) ALLAH YAJIK'ANTA YAYI MATA RAHMA ALLAH KA GAFARTA MATA ALLAH KA KYUTATA MAKWANCIN TA ALLAH KA WANKE TA DA RUWA MAI SANYI DA K'ANK'ARA ALLAH KA GOGE MATA ZUNUBAN TA KAMAR YADDA KAKE GOGE FARIN TUFA DAGA DATTI , KA MUSANYA MATA GIDA MAFI ALKHAIRIN GIDAN TA , DA IYALAI MAFI ALKHAIRIN IYALAN TA ALLAH KASHIGAR DA ITA CIKIN AJANNAR KA , KAKARETA DAGA AZABAR WUTA . AMIN YA ARHAMARRAHIM*😰
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
17++++18
Abdallah na fita be zame ko ina ba sai tasha cikin sa'a saura mutum biyu motar ta cika , wata mace ce tazo ta shiga sannan driver ya ja suka wuce k'auyen su Abdallah,
Yana sauka gidan Baban Hafsa ya wuce yana zuwa yayi sa'a ko ya sameshi a gida bayan gaishe-gaishe ya gaya masa abun da ke damun sa sannan ya ce yazo ne ya bada jinginar gonar mahaifiyar su ta gado domin su samu kud'in da zasu biya ama Ummi aiki ,
Bamusu kawun nashi ya amince sukaje wurin me gari aka samu Wanda zai amshi gonar aka buk'aci Abdallah ya fad'i ko nawa yake so abashi , yace dubu d'ari uku nan akayi yarjejeniya aka mik'a mai kud'i daganan yayi godiya ya kamo hanyar zaria ,
Ya shigo Zaria bayan la'asar gida ya wuce Hafsat kad'ai ya tarar a gidan tana ganinshi ta taso "yaya ya jikin Aunty Ummi?"
"Da sauk'i "kawai ya iya ce mata ya karb'i mukullin d'akin su ya shiga, dubu d'ari da hamsin ya d'auka sannan yayi sallolinshi a gida ya kulle d'akin ya tafi da mukullin , yana fita mashin ya hau har k'ofar asibitin ya k'arasa shiga ciki ,
Umar ne ya hango shi yayi sauri ya k'araso yana fad'in "ustaz ina kaje ne har yi ma Ummi aiki baka nan"
Murmushi yayi yace "naje Neman kud'i ne "
"Abdallah Dan Allah karka je ka sama kanka damuwar da ta fi k'arfin ka , kaga yadda ka koma kuwa daga jiya zuwa yau?"
"Umar damuwa dole ce agareni , kanaganin 'yar mutane zata mutu ta dalilin gazawa ta dole na shiga tashin hankali "
"Hakane amma Kasan rayuwa da mutuwa duk na Allah ne idan kwanan mutum ya k'are ba tsumi ba dabara dole sai ya tafi"
"Allah kasa mudace " Cewar Abdallah yana rik'e hannun Umar suka k'arasa ciki
Har a lokacin bacci take yi Mama ce kad'ai AD'akin ta zabga uban tagumi ga carbi tana ja , har suka shigo ma bata sani ba ,
Sai da yace "sannu Mama "
Da sauri ta d'ago kanta tana fad'in "Bawan Allah ina ka jene?"
"Mama naje Neman kud'i ne kuma Alhamdulillah na samu"
"Ina ka samo kud'i?" Cewar Mama tana zare ido
"Bashi na samo kuma Dan Allah karki d'aga hankalin Ki nan bada jimawa ba zan mayar musu da kud'in su"
Shiru Mama tayi tana tunanin ina d'anta zai samo wad'annan kud'in harya ya biya , azahiri kuma saita bishi da fatan alkhairi,
Mik'e wa yayi yace ma Umar suzo suje su biya kud'in su dawo dayake akwai receipt a hannun su direct bank din cikin asibitin suka je suka biya kud'in , tare da siyan magunguna suka dawo ,
Satin su d'aya a asibitin aka sallame su duk wannan lokacin Abdallah be gayama mahaifiyar shi cewar gonar ta ya siyar Dan ya sama matar shi lafiya ba ,
Ummi kuwa kyakyawan kulawa take samu awaurin mijinta da Mama Hafsa ma ba'a barta a baya ba domin kullum ita ke kai mata ruwan wanka , bayan sati biyu da sallamo Ummi Abdallah yaje ya samu mahaifiyar shi ya sanar mata da gaskiyar inda ya samu kud'i , amadadin ya tayi fushi sai yaga murmushi a fuskarta tace " Abdallah banida wani magaji aduniyar nan sai kai duk abinda na mallaka halalin ka ne , Allah yayi maka albarka , ita kuma Allah ya bata lafiya , "
"Amin Mama na gode"
"Yanzun ina sauran kud'in suke?"
"Suna d'aki"
"To Sana'a ya kamata ka fara"
"Eh hakane Mama ni anawa tunanin me zai hana inrunk'a zuwa kano ina saro kayan provision "
"Hakane amma shago fa ?"
"Insha Allah ba matsala zan ma hadi me shago magana naji yace zai saida nashi zai koma k'auyen su".
"To shikenan Allah ya bada sa'a "
"Amin , bari naje na nemi Umar naji ya tafiyar zata Kasan ce mana"
"To adawo lafiya "
"Allah yasa" nan ya fita ,
Ya samu Umar yana shirin fita kasuwa inda yake tsaron shago,
Nan suka sauna suka tattauna suka tsaida ranar laraba zasuje kano , danan suka wuce gurin me shago suka fara ciniki Wanda da k'yar ya karb'i dubu ashirin ,
*LARABA*
Da safe bayan sun gama karyawa ,Abdallah yayi wanka , Dan sunyi da Umar karfe goma zasu bar gida , Abdallah ne ya d'aga waya ya kira Umar yake sanar masa da ya shirya Dan haka yafito su tafi ,
Bayan ya aje wayar ne Ummi dake kwance jikin Abdallah tace"yaya ji nake kamar karka tafi"
Murmushi yayi yace"bakiso naje Neman kud'i ko?"
"A 'ah ba haka bane kawai dai..."sai kuma tayi shiru
"Kawai mene ? K'arasa mana"
"Kawai inajin jikina ba dad'i ne?
Cikin sauri yace"bakida lafiya ne?"
"Lafiya ta k'alau yaya kawai dai tafiyar taku ce bana jin dad'in ta a raina"
"Kiyi hak'uri Ummi na nima yau tunda na tashi nake jin jikina duk ba k'wari kiyi min addu'a"
Wata k'walla ta share idon ta sannan tayi masa addu'ar fatan alkhairi , suna fitowa d'aki Umar yana shigowa gidan , yana ganin su ya saki wani murmushi, nan suka gaisa da Ummi sannan suka lek'a d'akin Mama fatan alkhairi tayi musu sannan suka fita Ummi sai da ta raka su k'ofar gida sannan Abdallah yace mata ta koma amma ta nok'e kafad'a ita baza ta koma ba
Azaure ta tsaya tana hangen su har sai da suka b'ace ma ganin ta sannan ta koma gida jiki a sanyaye , bata tsaya fira ba ta wuce d'akin ta tana ta juyi a gado irin wasan da suka yi jiya da Abdallah ne ya ke ta mata yawo a k'wak'walwa sai murmushi take tana dad'a matse pillown data rungumo
Abdallah da Umar kuwa bayan sun rabu da Ummi Umar yace ma Abdallah akwai mutumin da Alhaji Bello yake siyan kaya awajen shi a kantin kwari Dan haka suje chan d'in ,
Sun isa kano azahar tayi kawai sai suka tsaya wani masallaci suka yi sallah sannan suka k'arasa cikin kasuwa dayake Umar yasan shagon kai tsaye chan suka nufa,
Alokacin da suka isa ana sauk'e ma Alhaji Mati kaya Dan haka ya rok'esu da sujira agama Dan kar lissafi ya kwace masa ,
Bayan ya gama ya hau sallamar mutane sannan ya waiwayo kan su Abdallah lokacin had la'asar ta wuce , siyayyan kayan ciyaciye na yara su suka fi yawa sannan su omo da sabulai kaya dai sosai ya had'o , ko kafin su gama magrib tayi Umar ya kalli Abdallah ya ce "ustaz dare fa yayi mu kwana a garin nan da safe sai muyi sammako"
"Gaskiya bazan iya ba yau duk dare gida zan kwana "
Umar yayi dariya yace " kafiso kullum ka jika gaka ga 'yar k'anwar ka"
"To ya San ranka , dalla Malam wuce muje"
'Yan dako biyu suka samu suka d'aukan musu kayan sannan suka fita kasuwa suka hau adaidaita suka nufi tasha suna shiga wata motar Zaria tana tashi Dan haka dole sujira ayi sabon Lodi ,
Sai k'arfe Tara sannan motar ta cika akayi duk abinda ya dace mota ta tashi bayan sunyi kamar tafiyar awa d'aya kawai sai motar ta mutu da kanta , nan fa driver yayi duk iya dabarun shi tak'i tashi gashi sunyi nisa da gari gasu a k'ungurmin daji,
Sunan nan tsaye masu salati nayi masu zagin driver nayi wai lefinshi ne da bai duba mota ba ya kwaso su ,
Abdallah kuwa shiru yayi kamar ruwa ya cishi,
Kwai sai suka ga ana ta kashe musu ido da wani haske me shiga k'wak'walwa , wata razananniyar murya suka tsinkaya ana ce musu "sit on your kneels!"
AI sai kowa ya hau salati Ashe 'yan fashi ne,
Haka suka ruk'a rashin mutumci harzuwa wannan lokacin Abdallah yana cikin motar be fito ba sai da wani yazo ta jikin window ya hasko ko shi yace "oga kaga wani D'an iska ana magana ya zaune ,