Showing 15001 words to 18000 words out of 38502 words

Chapter 6 - BAWAN ALLAH COMPLETE DOCUMENT BY Maman Muhammad .txt

20 Dec 2024

2526

ba kowa , daga gefen kujera yata an shimfid'a mishi sallaya , nan ya hau ya gabatar da sallah




*Waye DR AHMAD*




Dr Ahmad bakano ne ciki da bai awata k'aramar hukuma da ake cema Rano , *Ahmad Abdallah* shine cikakken sunan shi su biyu ne awajen iyayen su shi da k'anwar shi *Fiddausi* Alhaji Abdallah d'an kasuwa ne yana da rufin asirin shi dai dai na Alhajin k'auye, matar sa d'aya ce *Maimuna* kuma ita ta Haifa masa yaran sa biyu da yake matuk'ar so da k'auna,






Tun asalin Ahmad mutum ne me son taimakon jama'a hakan ya sanyan ya sanar mawa mahaifin shi yana son zama likita , mahaifin shi ya bashi kulawa ta musamman har ya kammala karatun shi, nan mahaifin shi yayi mishi aure da wata 'yar abokin shi *RAMLA*


Bayan bikin shi da kimanin wata uku ya samu aiki a asibitin Aminu kano , bayan shekara d'aya Ramla ta sunkuto d'anta namiji yaci suna *Abdallah* suna kiran shi da Abba,


Dr Ahmad ya samu nasarori masu d'imbin yawa ciki harda bud'e asibiti nashi mai zaman kanshi wato private sai da Abdallah ya shekara goma sannan Ramla ta sake haifo wani namijin yaci sunan Babanta *Abubakar*


Abdallah yana da shekara ashirin da bakwai ya gama karatun shi na law a k'asar England saurayi ne ajin farko kamili, alokacin da ya dawo aka fara batun auran shi da wata yarinya *Aisha* amma kuma cikin ikon Allah bikin shi saura wata d'aya ciwan ciki ya murd'e shi ya rasu ,


K'ololuwar tashin hankali Dr Ahmad da Hajiya Ramla sunshige shi amma da suka sa tawwakalli sai suka hak'ura , ,


Masu karatu idan kuka ga *Abdallah Ahmad Abdallah* ba zaku banban tashi da *Abdallah Abdallah* ba




Wannan ne mafarin taimakon da Dr Ahmad yake shirin yima Abdallah
[12/29/2017, 7:53 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






🌹 *ZURI'A D'AYA*🌹




*BY UMMU BASHEER*


🌹 *Congratulation sister for successful completing your amazing book ZURI'A D'AYA more grace to your powerful elbow*🌹


🌹 *KEEP SHINING DEAR*🌹








® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




#PMLWRITERS@GMAIL.COM
# WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com




2⃣3⃣ 2⃣4⃣






Akwana bakwan nan kuwa babu abinda su Ummi suke sai addu'a , Malam sai da yaje kano sau uku amma duk bawani cigaba




Wata safiya ce Malam ya yi sallama gidan su Abdallah aka bashi izinin Shiga , bayan 'yan gaishe-gaishe da k'ara jajanta ma juna , sai ya k'ara da cewa




"Nayi istihara akan b'atan yaron nan alamu sun nuna yana nan da rai kuma cikin kyakyawan masauki sai dai akwai k'unci a tattare da shi"




Mama ta share k'walla ta ce " to Malam yanzun ya za'ayi?"




"Addu'a , Addu'a ita ce kad'ai mafita"




Nan dai suka cigaba da tattaunawa , Ummi kam tana d'aki duk tunani ya gama addabar ta shi yasa ma bata ji zuwan Malam d'in ba ,




*KANO*




Dr Ahmad ne zaune a office d'in shi tunani duk ya da meshi ya kasa samun solution akan damuwar shi,




Nan ya d'aga waya ya kira Dr Usman ba b'ata lokaci sai gashi ya iso ,




Bayan ya zauna ne Dr Ahmad ya fara,


"Dama akan maganar patient d'in nan ne yaron mak'oci na , ina so zan maida shi zuwa k'asar London domin duba lafiyar shi"




Ido Dr Usman ya zaro" you just say London?"


"Yeah ,any think?"


"No sir"


"OK yanzun ina son kuyi discharging d'in shi domin in samu gudanar da shirye shirye na cikin sauki ?"


"Ok sir insha Allah ba damu wa"




Nan suka yi sallama ya tafi ,




Kamar yadda Dr Ahmad ya buk'ata haka aka sallami Abdallah alokacin da ya tashi aiki ya shiga d'akin shi domin tafiya dashi




Yauma kamar kullum azaune ya same shi yayi shiru ba tunani yake ba domin ba shida abinda zai tuna




Da sallama ya shigo d'akin , Abdallah ya amsa mai sannan ya k'arasa shiga d'akin d'auke da murmushi a fuskar shi ,




"Abdallah tashi mu tafi gida "




Sunan da yaji an kirashi da shi sai da ya razana ya kasa tuna inda ya San sunan amma tabbas sunan yana da muhimmaci a wajen shi ,




Dr ne ya katse mai shirun shi da cewa "ko kafi so ka CI gaba da zama a nan ne kayi ta barci?"


Kai ya girgiza alamar baya so


"To tashi mu tafi"


Cikin natsuwa ya mik'e ya bi bayan shi ,


Suna fita daga d'akin suka CI karo da Dr Usman rik'e da wani file a hannun shi , yace


.
"Yawwa sir ga records din "


Nan ya karb'a tare da godiya nan Dr Usman ya raka su har bakin mota sannan ya juyo , shikuwa ya tada motar shi ya d'au hanya , hanyar gidan shi ya d'auka da ke cikin G R A gidan Babban gida ne kuma da kagani Kasan Wanda ya mallaki wannan gidan ba k'aramar dukiya gareshi ba ,




Flat ne guda biyu a gidan tangama tangama , bayan yayi parking motarsa ya fito Abdallah ma ya mik'e ya fito d'aya daga cikin flat d'in suka nufa shi dai Abdallah tafiya kawai yake batare Da yasan inda aka dosa ba, ,


Key yasa ya bud'e k'ofar d'akin sannan ya ba Abdallah izinin shiga , tun da Abdallah ya d'aga kai bai sauke ba har sai da yaci tuntub'e da center table , shiko Dr murmushi kawai yake sannan yace ,




"Nan d'akin ka ne akwai duk wani abun buk'ata aciki bari nasa akawo maka abinci"


Kai kawai ya gyad'a tare da zama acikin d'aya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun d'akin,


Tunani da yawa yake acikin ransa , wane ne shi?, waye kuma wannan mutumin? Waye Abdallah , sunan da yafi d'aga masa hankali kenan idan ya tuna,


Yana nan zaune Dr ya shigo shi da wani matashi d'auke da tire a hannu ,


Cike da mamaki matashin ya tsaya yana kallon Abdallah , sai da Dr ya daka masa tsawa sannan ya aje kayan abincin ya fita ,




Kusa dashi Dr ya ya zauna sannan ya dafa kafad'ar shi yace"Babana tashi muje na nuna maka d'akin ka kayi wanka lokacin magrib yayi "


Jin maganar sallah ya sashi saurin mik'e wa , wata k'ofa ya bud'e suka kutsa , bedroom ne na gani na fad'a tamkar a k'asar turai , duk kayan more rayuwa akwai gidan , directtoilet ya wuce da shi ya nuna masa yadda zaiyi amfani da komai sannan ya kullo masa k'ofar ya fita,


Cikin tsoro Abdallah ke wanka har ya gama ya fito kayan da ya cire ne ajikin shi ganin wasu kaya yayi an aje mai su akan bed nan ya cire na jikin shi ya sasu , k'ananan kaya ne sunyi matuk'ar yi mishi kyau asalin kyanshi da talauci ya b'oye duk sun bayyana, masu karatu zanso kuga *Bawan Allah*




Ko da ya fito pallor ba kowa , daga gefen kujera yata an shimfid'a mishi sallaya , nan ya hau ya gabatar da sallah




*Waye DR AHMAD*




Dr Ahmad bakano ne ciki da bai awata k'aramar hukuma da ake cema Rano , *Ahmad Abdallah* shine cikakken sunan shi su biyu ne awajen iyayen su shi da k'anwar shi *Fiddausi* Alhaji Abdallah d'an kasuwa ne yana da rufin asirin shi dai dai na Alhajin k'auye, matar sa d'aya ce *Maimuna* kuma ita ta Haifa masa yaran sa biyu da yake matuk'ar so da k'auna,






Tun asalin Ahmad mutum ne me son taimakon jama'a hakan ya sanyan ya sanar mawa mahaifin shi yana son zama likita , mahaifin shi ya bashi kulawa ta musamman har ya kammala karatun shi, nan mahaifin shi yayi mishi aure da wata 'yar abokin shi *RAMLA*


Bayan bikin shi da kimanin wata uku ya samu aiki a asibitin Aminu kano , bayan shekara d'aya Ramla ta sunkuto d'anta namiji yaci suna *Abdallah* suna kiran shi da Abba,


Dr Ahmad ya samu nasarori masu d'imbin yawa ciki harda bud'e asibiti nashi mai zaman kanshi wato private sai da Abdallah ya shekara goma sannan Ramla ta sake haifo wani namijin yaci sunan Babanta *Abubakar*


Abdallah yana da shekara ashirin da bakwai ya gama karatun shi na law a k'asar England saurayi ne ajin farko kamili, alokacin da ya dawo aka fara batun auran shi da wata yarinya *Aisha* amma kuma cikin ikon Allah bikin shi saura wata d'aya ciwan ciki ya murd'e shi ya rasu ,


K'ololuwar tashin hankali Dr Ahmad da Hajiya Ramla sunshige shi amma da suka sa tawwakalli sai suka hak'ura , ,


Masu karatu idan kuka ga *Abdallah Ahmad Abdallah* ba zaku banban tashi da *Abdallah Abdallah* ba




Wannan ne mafarin taimakon da Dr Ahmad yake shirin yima Abdallah
[12/29/2017, 7:56 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*


*To readers ina Wanda ya shirya zuwa kano Neman bawan Allah Sadiya neman bawan wa Allah Wanda rashinsa Sam baiyi mata d@d'i ba cikin sa'a ko ta samu abokan tafiya Maman sa'a tace ba'a barta a baya ba dole su nema wa Ummi farincikin ta , aceeya kuwa cewa tayi jirgin ya tsaya ajigawa ya d'auke , Amne kuwa da yake 'yar black stormach ce 🤪cewa ta ba inda za'a je saboda man fuel yayi tsada , Aunty axland ma tace ba'a barta a baya ba*🤣🤣🤣






❤ *Gaisuwar fatan alkhair agareku masoya masu bibiyar littafin bawan Allah sakon ku na fatan alkhairi yana isowa agarene nagode agaskiya bansan da bakin da zan gode muku ba amma kusa ni har cikin raina inajin dad'in yadda kuka amshi wannan litttafin nagode sosai Allah ya had'a fuskokin mu a aljannatul firdaus Amin ya Allah*❤❤❤. *one luv*😘




*Ameenart Nd fatima (MAMAN Sadeeq) wannan page d'in naku ne dama d'aukacin yan Bawan Allah fans , I really like your comments❤*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com






Page 21----22






Haka nan su Malam suka tattara suka koma Zaria ba tare Abdallah ba zuciyoyin su cike da zullumin me zasu gaya ma mahaifiyar shi da kuma matar shi , ahaka suka sauka a tasha suka hau napep , direct gidan su Umar suka wuce ,




Aiko Maman Umar na ganin shi sai kuka domin yadda ta Ganshi ba k'aramin firgita tayi ba nan k'annen shi suka hau ihu " yaya Umar oyoyo !"




D'an autan su ne ya fita da gudu yaje gidan su Abdallah Ummi na alwalar la'asar Mama na kofar d'aki Hafsa kuma tafito daga bayan gida ,




Yaron ya k'arasa kusa da Mama cikin zumud'i yake ce mata "Mama yaya Umar ya dawo "


Cikin zafin nama Ummi ta waigo tana kallon shi




Mama ko cewa tayi "da gaske ?!"


"Eh Mama amma ya dawo kanshi a d'aure da wani Abu"


AI nan Ummi ta yarda butar hannun da dama already akwai hijab ajikin ta AI sai ta nufi k'ofar gida ,




"Ke Ummi ina zaki je ?" Mama ta fad'i yadda taga Ummi zata fita kamar zautacciya




"Ina zuwa Mama "kawai Ummi tace tasa kai




Hafsa da sai yanzun ta k'araso waje sai k'wala kira tayi "Aunty Ummi jira ni"


AI ina AUNTY Ummi gudu-gudu sauri-sauri ta runk'a had'a wa ,




💔💔💔💔💔💔💔💔




*Kano*


Yau kwana bakwai kenan ana fama da Abdallah amma Sam be san ana yi ba gashi zuciyar shi tana aiki amma kuma gangar jikin shi bata motsi , duk sun sare da al-amarin shi,




Yauma kamar kullum likitoci ne zaune awani k'awataccen office suna tattaunawa akan Abdallah , wata nurse ta shigo cikin sauri ta fara gaya musu patient din room no 18 ya farka kamar jira suke nan suka mik'e cikin sauri suka k'ara k'ofar d'akin ,




A zaune suka same shi akan gadon ya sakko da k'afafun shi k'asa , ya rik'e kanshi dake tsananin Sara masa ,


Koda suka bud'e k'ofar suka shigo kallo kawai ya bisu dashi domin be tab'a ganin su ba ,


Doctor d'in nan ne da ya ce ya sanshi ya matsa kusa da shi ya fara magana




"Ni sunana Dr Ahmad , zan iya sanin naka sunan?"


Shiru yayi bece komai ba , Dr Ahmad ya sake cewa "ko zan iya sanin naka sunan?"


"Ban sani ba" ita ce amsar da ta fito daga bakin Abdallah


Dukkan su likitocin suka kalli junan su


Dr Ahmad ya sake jefa mashi wata tambayar "ya sunan garin ku?".




Girgiza kai yayi nan ma alamar be sani ba


Nan likitoci suka sake firgita wani likita ne ya ce mai "nan ina ne ?" K'are ma d'akin kallo yayi tas sannan ya runtse idon shi gami da matse hannun shi kamar zai kai naushi




Dr Ahmad ne yace su k'yale shi ya huta , nan suka yi mai allurar barci ya koma




💔
[12/30/2017, 10:59 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com






2⃣5⃣






*Cigaban labari*




A b'angaren Dr Ahmad kuwa be b'oye ma iyalin shi komai game da Abdallah ba ,




Hajiya Ramla tayi farin ciki sosai har ta k'osa safiya tayi taga me kama da d'anta,






*Zaria*




Yau kusan sati uku kenen ba labarin Abdallah hakan bai sauya akalar damuwa acikin zuciyoyin dangin sa ba musamman ma mahaifiyar shi da matar shi ,




Ummi kuwa yanzun wani irin tsantsar son Abdallah ne ke damun ta gashi yayi mata nisa , Dan yanzun gani take bayan iyayen ta babu Wanda take ma so da k'auna tare da mararin gani irin Abdallah,




Malam kuwa ya duk'ufa addu'oi ba dare ba rana ,




Umar kuwa Alhamdulillah ya ji sauk'i sai dai damuwar rashin d'anuwan shi amininshi, shi kad'ai ke tayar mai da hankali akoda yaushe






Hafsa ce keta fama da Ummi akan taci abinci " haba Aunty Ummi yanzun ke kullum sai an ta fama da ke wajen cin abinci kamar k'aramar yarinya ?"


Ummi dai bata ce komai ba iya kacin k'walla da keta gudu a kan kumatunta ,




Hafsa ta sake cewa , " ayyah k'awata Dan Allah ciki kinga rabon Ki da abinci tun jiya da rana gashi yanzun Kusan k'arfe uku"




Kallon Hafsa tayi tace "zanci amma sai in zaki bani a baki " ta k'arasa maganar cikin shagwab'a




"Naji duk wannan me sauk'i ne "


Nan Hafsa tayi ta ba Ummi abincin tana ci , haka Mama ta fito ta samesu duk sai suka bata tausayi,






*Kanon Dabo*




Kamar yadda Dr Ahmad ya tsara acikin sati uku ya samar masu *Visa* shida D'an mak'ocin sa kamar yadda yake fad'i , basu bar garin ba sai da yasan yadda yayi ya masamar ma Abdallah takaddun makaranta sannan suka d'aga birnin *London*






Sosai Abdallah yayi k'auyanci Kasan cewar bai tab'a sanin wani Abu makamancin k'asar ba ,




A wani hotel suka sauka , bayan sun D'an huta sannan Dr ya nema masa Wanda zai runk'a koya mai turanci




Ba da jimawa ba ya saman mai admission a London university , inda zai karanci medicine,




Sosai Abdallah ya maida hankali wurin karatun shi saboda bashida damuwar kowa acikin k'wak'walwar shi,




Sai da Dr ya tabbar da Abdallah ba shida matsalar komai sai nan ya dawo Nigeria tare da barin shin amanar shi awajen wani Bature




💟💟💟💟💟💟💟




Wasa-wasa dai yanzun wata takwas da b'atan Abdallah ko wanda yaga me kama da shi basu gani ba,




Abun da yake k'ara d'aga ma Ummi da Mama hankali bai wuce duk in sunyi istikhara suna samun natsuwa ba hakan ke nuna musu Abdallah yana cikin kwanciyar hankali, to amma yana ina ne? Mai ya sa yayi nesa da su? Shin baya tunanin halin da zasu shiga ne? Wad'an nan tambayoyi su suke ta yawo a k'ak'walen su amma kuma kaf babu mai amsa masu su,




Wata rana Mama tashir ya taje gidan su Ummi domin su tattauna da mahaifiyar ta akan makomar auren Ummi da Abdallah,




Bayan sun gaggaisa tace " Dama nazo ne akan maganar wad'an nan yaran , kinga yanzun wata takwas amma bawan Allah shiru , shine nace ko za'a raba auren Ummi idan ta samu wani mijin tayi aure"




Maman Ummi tace " amma Maman Hafsa sai naga kamar yayi wuri afara wannan maganar balle ma muna sa ran insha Allah ba da jimawa ba zai dawo"




Ajiyar zuciya Mama tayi sannan tace " to AI shikenan ni dama naga k'a'idar musulunci wata shida ne shiya sa kuma da naga babu rabo a tsakanin su"




"Hakane Maman Hafsa my dai k'ara hak'uri"




Nan dai suka gama maganar su ta tafi ,




Ummi na kwance a d'aki tunani duk ya isheta Mama ta d'aga labulen d'akin ta shigo da sallama amma Ummi Sam bata ma anayi ba ,




Sai da Mama ta dafa ta sannan ta waigo a firgice ta kalleta "yanzun Ummi ba zaki cire wannan yawan tunanin a ranki ba ,? Shi wanda kike yi Dan shi d'in yana chan hankalin shi kwance bema San kina yi ba , Dan Allah Ki rage tunanin nan kar ya haifar miki da wata matsalar kuma"




Cikin jin kunya Ummi tace "to Mama"




💟💟💟💟💟💟💟




*BAYAN SHEKARA D'AYA DA RABI*


*London*


Wa ni had'add'en guy ne na gani na fad'a zaune a cikin library yana karatu fuskarsa d'auke da wani farin glass , kamar daga sama , yaji an ce mai


"Hi"


D'agowa yayi yakalli wanda yayi maganar shima matashi shi ne kyakyawa , "hi"kawai yace masa ya maida hankalin shi zuwa littafin da yake dubawa




Matashin ya sake cewa " please can I have a sit?"


D'aga mishi kai kawai yayi , ,


Shi kuma wancan ya zauna yana murmushi, mik'amai hannu yayi yace " I'm saifullah from Nigeria "


Sai alokacin mai karatun ya aje littafin tare da cire glass d'in idonshi sannan ya mik'a masa hannu sai ya ce " Abdallah also from Nigeria"


*Nikam nace lallai ma lallai Ashe Abdallah ne gaskiya ya k'aro wulak'anci*




Cike da murmushi Saifullah ya ce "Ashe dai nasamu D'an uwa"


Murmushi kawai Abdallah ya mai ,


Saifullah irin mutanan nan ne masu shegen surutu ba irin su Abdallah ba miskilai,




Ba jimawa suka saba sosai har suka k'ulla abota
[1/1, 6:56 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login