Showing 45001 words to 48000 words out of 70663 words

Chapter 16 - WACECE NI BOOK COMPLETE BY UMMUH HAIRAN.txt

kada ku kasheni..." rufe Mata baki yayi yace “sanin zamu fuskanci wannan qalubalen ne yasa nace kibani hadinkai wajen tabbatuwar kasancewar mu tare kada kisa haukannan a ranki aurena dake mutuwa ce kawai zata raba kuma wlh everlasting bazan taba rabaki da danki ba duk duniya wa kike dashi bayanni dashi meyasa saboda farin cikin wata zan rabaki da naki? Adalci kenan Marwah? Hmmm! Uhmmm!! Sadaukarwarki gareni tafi gaban wannan butulcin Marwah zanyi komai don farin cikinku dake da Ra'isah amma bazan taba tauye haqqin wani saboda farin cikin wani ba" karbar yaron yayi yace “banso ya farajin kowacce kalma ba a duniya naso ace kalimatusshihada itace ta fara ratsa kunnenka Mu'azzam" shiru yayi yana yiwa yaron huduba a kunnensa.
Gefe kuma Ra'isah tanata haukanta na cewa dole sai an bude Mata ta shigo bayan ya gamane ya dago yace “daga yau na koma Abu Mu'azzam na tashi daga Colonel" lumshe idonta tayi ya sake dora matashi a cinyarta ya miqe ya matso ruwan zafi a dispenser ya fara hada mata tea me kauri ya dawo ya fara bata tanasha saboda ji take cikinta kamar anyi mata sata tasha tea din sosai, ajiye cup din yayi ya sanya hanunsa ya zuge mata zip din rigarta ya zare mata ita ya gyara mata riqon yaron a hannunta ya sanya masa nonon a saitin bakinsa aikuwa ya kama, sosai taji wata a azaba ta ziyarceta tayi wata qaramar qara ya kalleta yayi mata ni'imtaccen murmushi yana shafa dayan nonon nata tare da sawa a bakinsa shima yana taya dan nasa zuqowa saida yaji wani ruwa me maiqo ya fara zuwa a bakinsa sannan ya cire ya juyo da yaron yasa masa wannan din a bakinsa yakuwa fara zuqo ruwan nonon tanajin kamar Mu'azzam din na zuqowa da ranta saboda zafi.





Cigaba yayi da matsa dayan breast din nata na hagu da hannunsa yanata zuba mata sannu har saida yaga ta daina ciccijewar sannan ya miqe ya nufi wajen asibitin lkcn Ra'isah ta gaji da haukanta ta fice daga asibitin,
Office din likitan ya koma tayi discharge nasu suka dawo tare yana riqe da ita ita kuma likitan tana rungume da kyakkyawan yaron tanajin kamar tace subata shi yaron balarabe sak.
Kai tsaye wani hotel ya nufa ya fita ya barta a mota bai jima ba ya dawo ya karbi yaron itama ya rungumota jikinsa suka hau hawan farko ya bude wani daki suka shiga ya zaunar da ita ya cire mata mayafinta ya fita bai jimaba ya dawo dauke da kayan abinci ya baje mata a gabanta gasasshen nama ne daya hadu da wata saup sai wani shayi me kauri batajin dadin komai a bakinta haka ya rinqa matsa mata saida taci har saida ya tabbatar ta qoshi sannan ya qyaleta kasancewar dare yayi a lkcn ma bakwai da rabi na dare yasashi gyarawa Babyn kwanciya ya dagata ya dorata a gadon yaja mata blanket ya rufeta yace.





“Kiyi bacci zanje yanzu na tura kayanmu 9ja nanda awa goma sha biyar zasu sauka so zanje na siyo wanda zakuyi amfani dasu zuwa gobe da zamu tafi banason komawa gdan can nasan Ra'isah tanacan tana jirana"
Batayi masa mgn ba ya juya ya fita bayan ya miqa mata wayarta qurawa yaron ido tayi tana kallonsa yanata baccinsa cikin kwanciyar hankali mamaki takeyi wai ta jikinta yaron ya fito, ajiyar zuciya tayi tare da riqe goshinsa tayi masa addu'o'in da suka sawwaqa, wayarta tayi qara ta kai hanunta ta dauka a hankali “Ummuh" taga an rubuta ta kara a kunnenta da sauri kafin tayi mgn tace “barka da arziqi Bintun yanzu Bunayyah yakiramu yake fada mana kin haihu Masha Allah Masha Allah nayi murna da wannan haihuwa Allah ya raya mana Mu'azzam gobe muna jiranku kinji ki shafa min kan dana Allah yayi muku albarka wannan aure shine aure me albarka"




Ajiyar zuciya tayi cike da kunya tace “na gde Ummuh Allah ya qara girma" murmushi tayi ta rinqa fada mata yanda zata kula da kanta sosai sannan sukayi sallama tana ajiye wayar Kiran Helin ya shigo tayi kamar karta dauka sai kuma ta canza shawara ta dauka.
Guda ta rangada tace “am very happy My Marwah kinyi farar haihuwa sai maqiya shabune wannan shine matakin nasararmu ta farko kin haifa ya hana matar gold akwai rikici a gaba amma shima zaizo ya wucce da qafarta saita gudu tabar maki mijinki, inanan Ina jiran dawowarku kada ki yarda ya raba muku gda ya hadaku guri daya tanan ne kawai zata gane kema mace ce kinfi wata macenma ta nanne zata gane yanzu Marwan ba nata bane nakine keda danki tanan ne zata gane tayi wauta kuskure me girma da bazata iya gyarawa ba, mu hadu a next level Marwah Ra'isah kin gama yawo qaramar yar bariki ce ke maci amanar miji...........





~_Rikitata rikita wannan rikicin cikin gida shi ake kira turnuqu fadan ibilisai, ko waye da nasara a hargitsin oho._~





More comments😍
More typing😍





*Mrs Dr M.A...✍🏻*
[3/6, 1:09 PM] MRS M.K.D: https://www.facebook.com/Freedom-Writers-Association-110039363936693/



https://www.facebook.com/Freedom-Writers-Association-110039363936693/


*FREEDOM WRITTER'S ASSOCIATION.* 📕🖊️
( _Y'anci don cigaban Mata, y'an ci ya d'ara bauta, freedom writters._ )

*( F.W.A)🖌*



*WACECE NI?*
*(SANADIN KUKANA!)*



_typing✍🏻_



*Mrs Dr M.A...*



*28 to 29*







Ajiye wayar tayi cike da tsoron abinda zaije ya dawo “wanne rikici ne wannan?" ta tambayi kanta tare da sake jan danta a jikinta tana karanto masa addu'ar neman tsari da haka har bacci ya dauketa.
Shikuwa goga kasan hanyar yana fita wani qaton shopping Mall ya shiga ya lodo musu kaya musamman na baby aka zuba masaa but ya wucce wani gurin saida gwala-gwalai ya siya mata wani arnen set na sarqa dankunne banguls and rings harda agogo set din sunyi masifar kyau tsadarsu abar jinjinaw ce.




Fitowa yayi ya shiga mota ya nufi airport ya qarasa yimusu abinda zaiyi na tafiya sannan ya koma hotel din, lkcn daya shiga sunyi bacci ya zuba masa ido sunyi kyau sosai sun qawatar da idanunsa gani, qaunarsu na ratsa zuciyarsa ya sunkuya yayi kissing din yaron ya sakeyin kissing dinta ta bude manyan fararen idanunta da suke cike da bacci ta dorasu akansa, murmushi yayi ya lakace mata hanci ya juya ya shiga bathroom yayi wanka ya fito ya hau gadon ya kwanta tare da daukan dansa ya rungume a jikinsa ya matsa ya shige jikinta yace “yau zanyi kwanan maraici babu service everlasting Bunayyah yayimin bazata"
Ajiyar zuciya tayi tace “ai garama hakan" kallonta yayi yayi dariya yace “zakiyi bayani ne duk ranar da kikazo hanuna" bata kuma cewa dashi komai ba ta lumshe idonta ya sanya hanunsa saman boobs dinta ya rinqa shafawa a haka har bacci ya daukesu.





Da asuba ya tashi ya fita yayo sallah ya dawo lkcn itama ta tashi duk jikinta ciwo yakeyi ta shiga bathroom ta gyara jikinta tayi wanka da ruwa me zafi sosai ta gasa cikinta da yake a shafe kamar ba itace ta haihu ba sannan ta zuwa wani ruwan magani da aka bata a asibiti tayi qarfin halin cijewa ta shiga cikin ruwan tana kuka tana hawaye mahaifiyarta da bata saniba tana dawo mata a ranta yanzun da ace itadin me cikakken gatace da tasamu wanda zai kula da ita amma yanzu komai saidai tayiwa kanta shidin da zai taimaka mata shima ba iyawa yayi ba.
Da wannan tunanin ta gama gasa jikin nata ta miqe ta fita tasa kayanta ta bude kayan da yazo dasu ta dauki wani bathtub na wankan jarirai me masifar kyau ta zubo ruwan zafi ta hadashi daidai wankan baby ta cire masa kayansa ta zauna ta fara yi masa wankan yana kuka tanayi saboda ba wani iya wankan babyn tayi ba kawai dai tana ganin yanda su Nanny Indo sukeyiwa jarirai idan an tsintosu an kawosu gdan marayu ne shiyasa hartayi karabbanin yiwa dan nata ta gama masa wankan ta sashi a towel ta rungumeshi tana kuka me tsuma zuciya tana qara qanqame yaron ta bude bakinta tace “Allah nasani kowacce qaddara me kyau ko akasinta daga gareka take ubangiji na roqeka ka rayani da dana kada ka jarabceshi da irin qaddarar daka jarabceni"
A haka ya turo qofar ya shigo ya tarar da ita rungume da yaron tana kuka gabansa ya fadi hankalinsa yayi mugun tashi ya qarasa da sauri yace “meye kuma ya faru everlasting?" Kamo hanunsa tayi cikin kuka tace “na roqeka da girman Allah Colonel duk juyin da zamani zaiyi kada kace zaka rabani da dana bana fatan ya dandana zafi da radadin maraici me ciwo mara magani a rayuwarsa radadin da duk dadin da dunayi zata baka idan ka tunashi saika zubar da hawaye zuciya bata iya mantawa dashi Marwan kayimin wannan alfarmar koda kuwa itace alfarma ta qarshe da zaka yimin a rayuwarka"




Wani irin hawaye ne suka zubo masa yace “insha Allahu zan kasance me cika alqawari a gareki everlasting da izinin Allah danmu zai girma tare damu cikin aminci da qauna kinji" lumshe idonta tayi tayi murmushi ta qara rungume yaron tace “bansan so ba bantabajin inason wani abu a duniya kamar Mu'azzam ba saboda banida wani makusanci a duniya daya fishi a yanzu bansani ba ko nan gaba zan samu"
Wani kallo yayi mata na tsoro da mamaki yace “meyasa duk mgnr da tazo bakinki kikeson fada mani Marwah kina nufin haukana kawai nakeyi duk soyayyar da nake nuna miki baki tabajin kinaso naba Marwah tabbas da sauran aiki a gabana tunda har yanzu nakasa samun zuciyarki"
Yunqurawa yayi ya miqe ya fara safa da marwa a tsakiyar dakin yana mamakin taurin zuciyar Marwah tunda yake baitaba son mace tace bata sonsa ba sai ita baitaba jin kalma mai muni irin tataba to meye ma amfanin zama da abinda baya sonka ya tambayi kansa, sunkuyowa yayi ya dago fuskarta hawayensa suka diga akan hancinta ta lumshe idonta saboda bazata iya jure kallonsa a haka ba yanda jikinsa yake rawa yasa gaba daya ta tsorata yace.





“Sau daya tak kika taba fadamin kina sona shima nasan takura miki nayi Marwah ki cire tausayi da tunanin ni uban danki ne ki fadamin matsayina a gurinki kice bakya sona bakya raayin zama dani Marwatuh kinada yanci bazan taba tursasaki ki soni ki zauna dani ba duk da yake cewa nayiwa kaina alqawarin babu saki a aurena dake amma zan nisanta kaina dake har zuwa lkcn da sona zai shiga zuciyarki Marwah baa tursasa zuciya taso abu da kanta takeson abinda taga ya dace da ita, yau na gane kuma na fahimci matsayina a gurinki Marwah danda muka haifa jiya wanda baki Isa ki samar dashi ba dole saida gudunmawata da ace hakanan kike zaune batare dana kusanceki ba da har yanzu baki sameshi ba bare kisoshi amma kin fadamin cewa yafini matsayi kina sonsa baki tabason wani abu ba sai a kansa kayy! kayyy!! Kalmar nan tayi tsauri a kunnena wlh da nasan abinda zaki fadamin kenan da dana fita masallaci ban dawo ba"




Miqewa ya kumayi ta ruqoshi da sauri tace “ba nufina kenan ba Colonel wlh ba abinda ka dauka nake nufi ba idan nace banasonka na yaudari kaina inasonka so na mata da mijinta inasonka so na mai jibantar lamurana ina nufin so na jini shine son da nake yiwa Mu'azzam so na tsakanin uwar da bata da kowa sai dannan guda daya a duniya Colonel kayimin adalci kada kayi kishi da danka na cikinka akaina, ka duba ka gani banida wani abu a duniya da yake ikona mallakina ni kadai wanda zaa dangantashi dani kai tsaye sai dana Mu'azzam kaidin da kake fadin haka mutum nawane suke da haqqi akanka bayanni mutum nawa ne zaa dangantaka dasu bayanni Ummuh tafini haqqi akanka saboda ita ta haifeka Abuh yafini haqqi akanka Colonel sannan ga matarka da nasani har abada bazan kama qafarta a zuciyarka ba saboda ita tanada asali tanada nasaba me kyau nifa banida ita Marwan banida ita banida itahhh!"
Kukane yacinye sautinta ta sake qanqame yaronta a jikinta tace “Allah na roqeka ka albarkaci rayuwar dana ya zamemin haske kuma mabudin cikon farin cikina na duniya..."




Rungumesu yayi a jikinsa yana bubbuga bayanta yana sauke ajiyar zuciya yace “sh...shikenan ya isa na fahimceki everlasting kiyi hqr inaji a jikina zaki hadu da cikon farin cikinki insha Allahu kin kusa ganinsu kinji wlh Marwah bana fatan nayi kaffara sanyin yanayinki yana nuna kedin daga asali me kyau kika fito"
Qara shigewa jikinsa tayi tace “inasonka mijina don Allah kada ka barni kaji" hade bakinsa yayi da nata yace “nafi so sonki matata" sun jima a haka kafin ya janye jikinsa ya dauko shirgin kayan kwalliyar yaron suka rinqa shirya abinsu a tare har suna musu kowa yana cewa dashi yaron yake kama tayi dariya tace “yarona baya kama dakai dani yake kama akwai wani hotona lkcn inada shekara uku da yake a gdan marayu wanda duk bayan wata daya Nanny Indo take nunamin takan cemin a lkcn nafi kama da larabawan Misrah amma yanzu na koma baqa saboda baqin hali da nasa araina Allah Colonel idan kaga hoton zakace fuskar Mu'azzam ce a yanzu amma kana wani liqa masa kama dakai da wata Baby Zahran ka farar fatar ce kawai taka sai yatsunsa da sumarsa"






Dariya yayi sosai yace “ashe dai yana kama dani din dai ni bansan ya akayi ma yarinyar nan kika fini qarfin jini har haka" hakadai sukaci gaba da hirarsu har suka gama shirinsu tsaf suka fito ya bawa wani yaronsa motar yakaisu airport suka shiga jirgi sai qasa 9ja.
Suna fitowa daga jirgin suka hangi Abuh da Ummuh da sauri suka nufosu abin mamaki daga Abuh har Ummuh rungume Marwah sukayi Abuh ya karbi takwaransa ita kuma Ummuh ta qara rungume Marwah a jikinta tanata zuba mata sannu tana dubata sosai gabanta na faduwa ta rasa meyasa ko muryar yarinyar taji sai qirjinta ya buga haka dai suka rankaya suka shiga motar Abuh ne yakeja Marwan na gefensa Ummuh da Marwah suna baya tanata satar kallon Marwah hanunta dauke da Mu'azzam tayi ajiyar zuciya ta kasa hadiye mgnr dake bakinta tace “Bunayyah kullum na kalli fuskar matarka sai naji gabana yana faduwa bansan meye yasa ba inajin qaunar yarinyar a cikin jinina"





Murmushi yayi yace “hakan yafi komai yimin dadi da Allah ya nufeni da kawo wacce kikeso amma Ummuh wani musu mukeyi da everlasting tace “Junior da ita yake kama nikuma nace da Baby Zahrah yake kama taqi yarda tace wai da ita yake kama lkcn tana qarama" Ummuh tayi murmushi tace “tunda na dauki yaron nan nake ganin hoton fuskar Bintu Zahrah haskene kawai ba irin nata ba ita ba fara bace tas"
Wani ihu yayi da yasa Abuh saurin cin birki yayi dariya yace “Allah Abuh tunda aka haifeshi nace da Baby Zahrah yake kama taqi yarda to dai yanzu gashi kinji ko?" Ya juyo yayi mata gwalo takai masa duka ya goce ta turo baki kawai sai hawaye ya zubo mata, da sauri Ummuh tace “Subhanallahi meye kuma na kukan?"
Qara turo baki gaba tayi tace “ba kune kukace baya kama dani ba" dariya sukayi dukkansu ya juyo yace “yarinyar nan kishine zai kasheki ke kishin naki harda wadda bata raye ma yi kikeyi kinga fa Ummuh yar mitsitiyar yarinyar nan saida ta mayar dani kamar wani danta ko waya ban isa nayi da Ra'isah a gabanta ba yanzu saita barni na kwana gwauro"
Tsuke fuska Ummuh tayi saboda sako Ra'isah da yayi a mgnr, da sauri ya saita nutsuwarsa Abuh yace ai muna murna da zuwanta cikin rayuwarka" sake kwanciya tayi a jikin Ummuh hakanan takejin qaunar surukar tata tana ratsa jininta tace “Allah Ummuh dani yaron nan yake kama idan na nutsu zan nuna miki wani hotona da wani mutum da bansan waye ba ance wai a aljihun wandon jikina aka ganshi lkcn da aka tsinceni ina tunanin shine babana"





Ajiyar numfashi Ummuh tayi tace “karki takurawa kanki ki bari a hankali idan kin samu lfyrki kya nunamin ai muna tare Marwah kinji takwarar mijinta" zaro ido yayi ya sake juyowa ya mintsineta yace “Au hakane fa saboda gasa sunan ma irin nawa aka saka miki" murmushi tayi hawaye ya cika idonta tace “Nanny indo tace lkcn da aka kawoni gdan banida baki abu daya na riqe kawai sunan Malwal da aka tambayeni sunana sai nace Malwal komai aka tambayeni sai nace Malwal shiyasa kawai su sanyamin Marwanatuh"
Daga Ummuh har Colonel Marwan babu wanda qirjinsa be buga ba a fili yace “Malwal everlasting shi kadai kika iya kema? Itama Baby Zahrah ta harta mutu bata iya cewa Marwan ba saidai tace Malwal"...........





More comments😍
More typing😍





*Mrs Dr M.A...✍🏻*
[3/7, 8:57 AM] MRS M.K.D: https://www.facebook.com/Freedom-Writers-Association-110039363936693/



https://www.facebook.com/Freedom-Writers-Association-110039363936693/


*FREEDOM WRITTER'S ASSOCIATION.* 📕🖊️
( _Y'anci don cigaban Mata, y'an ci ya d'ara bauta, freedom writters._ )

*( F.W.A)🖌*



*WACECE NI?*
*(SANADIN KUKANA!)*



_typing✍🏻_



*Mrs Dr M.A...*



*30-31*




Ajiyar zuciya tayi daidai lkcn da Abuh yayi parking cikin gdan nashi kallonsa Marwan yayi yace “Abuh na dauka gda zaka saukemu" murmushi yayi yace “kada ka damu Bunayyah haihuwar fari mace tana buqatar kulawa ta musamman saboda jikinta danye ne tana buqatar hutu sosai, idan tayi qwari zamu baka matarka"
Bai iya cewa da mahaifin nasa komai ba amma har cikin ransa wannan hukunci baiyi masa dadi ba, Ummuh ce ke riqe da dan suna tafe tana riqe da Marwah har suka shiga ciki shima yana riqe da ita.
Wani daki suka shiga an qawatashi da komai na buqatun rayuwa, zaunar da ita sukayi ya zauna a kusa da ita yanata zuba masa sannu fita Ummuh tayi ta shiga dakinta.





Riqota yayi ya sauke numfashi yace “meyasa su Ummuh zasuyimin haka me suke nufi da daukoki su kawoki nan nifa banason irin haka everlasting yanzu nikadai sukeso na rayu kenan" kallonsa tayi cike da mamaki ya daga mata gira yace “ko kadan banason nesa dake wlh dumin jikinki ya ratsa nawa babu abinda nakeso kamar kasancewa dake" qasa tayi da kanta ya sake dora hannunsa saman kanta yace “dare yayi yanzu..."
Shigowar Ummuh ne yasashi hadiye mgnrsa ta harareshi tace “ka tashi kaje

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login