Showing 18001 words to 21000 words out of 60852 words
Chapter 7 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
"Kada kayi mamaki idan kaji cewar mahaifina sananne ne a fad'in jahar Kano ba b'oyayye ba."
Ai sai ya kasa dauke ido a kanta,yayinda ta cigaba da yi mishi murmushin nan wanda ke k'ona zuciyarta. Haris ya numfasa
"Idan kinga babu damuwa,ko zaki iya bayyanamin labarinki Tasleem?"
Ta d'anyi shiru tamkar bazatace komai ba,can kuma ta karkato jikinta sosai tana mai lankwasar da kafafuwanta a saman kujera. Idanuwanta suna duban na Haris, yayin da fuskarta ta chanja kala zuwa ja. Murmushi ta k'ak'alo ta jefamishi
"Zakaji tarihina,zakaji wacece ni Haris. Na yarda dakai dari bisa dari."
Ta jingina kanta jikin kujera ta tsurawa sitiyari ido kafin ta bud'i bakinta ta soma magana...
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(23)
"Mahaifina Doctor Abba Waziri,d'a a wajen marigayi Wazirin Kano,Alhaji Ma'aruf Waziri.(ahuwan kanawa..lol)."
Haris ya fiddo ido kadan yana dubanta cikin razana,Doctor Abba Waziri? Shi kuwa ya za'ayi ya kasa saninsa? Babban likita kuma kwararre a fannin k'ashi. Dukkan fad'in garin kano harma da yawa daga sauran garuruwa ansan da zamansa. Ko marigayi mahaifinsa,Alhaji Ma'aruf Wazirin kano,baiyi sunan da d'an nasa yayi ba. Wajen taimakon mutane da kiyaye lafiyarsu.
Baby ta cigaba da zancenta bata ko damu da razanar data sauka a saman fuskarsa ba.
"Mahaifiyata kuwa,Hajiya Maryam Abdulmalik,haifaffiyar Kazaure ce. D'iya a wajen babban limamin masallacin juma'a na Kazaure,Malam Abdulmalik Hussein."
Ai sai Haris ya k'ara sarewa,Malam Abdulmalik Hussein,babban aminin kakansa ne na wajen uba. A iyakar saninsa,gidansa ya zamto na mahaddata Al-k'ur'ani. Suna da nutsuwa yaransa hakanan kowannensu suna zaune ne a gabansa. Duk shine ya aurar da yaransa. Kenan Gwaggo Maryama itace mahaifiyar Tasleem? Unbelievable!
Sai lokacin ne ma idanuwansa suka soma hasko masa kamannin Gwaggo maryama a fuskar Tasleem.
Hawaye akan fuskarta
"Wad'annan bayin Allah biyun,sune sukayi silar samuwata a duniya da ikon Allah.
Mahaifana sunyi rayuwa cike da jin dadi a matsayinsu na ma'aurata kafin Allah Ya albarkacesu da samun d'a namiji,Abdullah. Yaya abdullah yana da shekara d'aya a duniya,kakanmu Alhaji Ma'aruf ya rasu aka nad'a Yayan mahaifina,Alhaji Nasir akan karagar mulki.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(25)
Mamma tana nan zaune har na kusan mintuna sai gasu sun fito suna dariya. Abba yayi shirinsa na tafiya asibiti yayinda briefcase dinsa ke a hannun Raliya tana takowa da murmushi dauke saman fuskarta. Mamma duk da haushinta da takeji ta kasa cewa uffan akan wannan al'amari,saidai ta daure fuska. Wai ma duk a banza,Abba baisan tana yi ba. Har ya nufo teburin sai Raliya tayi saurin magana,wai me yake nufi ne? Bazaici wainar da tayi mishi ba? Ga mamakin Mamma sai ya juya ya dubeta ya bata hakuri cewar zaije yaci wainar Raliya kada tayi fushi. Mamma kai kawai ta gyada mishi,ta kasa cewa uffan har suka fice.
A ranar kuma,da daddare tana zaune a falonta,Abba yayi kiran wayarta yana nemanta. Ba musu ta tafi da tsohon ciki,ta nufi sashensa. Turus tayi ganin matasan da basu wuce ashirin da wani abu ba,zaune saman kujera tare dasu Abba da Raliya sai hira akeyi da dariya. Abba ya ankara da shigowarta,ya dubeta kafin yayi mata iznin shigowa. Ta karasa ta zauna a gefensa. Abba ya dubi samarin
"Banji kun gaisheta ba?"
Sai lokacin dukkansu suka hau kwasar gaisuwa,Mamma ta amsa. Bayan ya kira sunanta,ya shaida mata yaran Raliya ne,da Hamza,Nura da kuma Usman. Anan gidan zasu cigaba da rayuwarsu kasancewarsu marayun da ubansu ya rasu. Zai dauki nauyin karatunsu da komai ma na rayuwarsu. Maganar ta daki Mamma,sai lokacin ta k'ara gaskata magana gwaggo sarai. Ta boye mamakinta tayi mishi fatan alheri akan niyyarsa sannan tayi mishi alk'awarin itama zata daukesu tamkar Abdullah d'anta. Bazata bambantasu ba kamar yanda ya nema. Abba yaji dadi,yace su bata girmanta a matsayinta na matarsa. Suma kamar gaske sukayi na'am. Daga haka ta tashi ta koma.
Zamanta da Raliya kuwa zama ne ba yabo ba fallasa,Raliya aikinta bai wuce jaye jayen fad'a ba duk da ba sashe d'aya suke ba. Tsakaninta da Abba ma ya chanja,ya zamana mukullan motar gidan a hannunta suke,acewarsa itace babba don ta girmeta. Mamma batace komai ba ta bisu hakanan.
Babbar matsalar data soma tayarwa Mamma hankali,bai wuce kwananta da yake kaiwa ga Raliya ba. Ya chanja mata kullum cikin daure dauren fuska. Abdullah bashi da damar sakewa da Abba kamar a baya,ya zamana bai fiye janshi da wasa ba.
Cikin wannan yanayin na rashin samun kulawar miji,abunda bai kai ya kawo ba zai hau ta da fad'a marar dalili koda a gaban 'yan aiki ne. Nakuda ya kamata,gatanan ita d'aya a d'aki. Da abun yaci tura ta lalubo wayarta ta kira Abba. Cikin magagin bacci ya amsa,jin cewar tana nakuda ne ya wartsakar dashi domin har lokacin akwai burbushin sonta a ransa. Haka ya taso Raliya na biye dashi."
Baby ta dakata tayi dariyar takaici gami da kwafa
"Ta hana akai uwata asibiti,shegiyar taso ta kasheni Allah Yayi zan fito duniya na zame mata annoba."
Haris dai kallon Baby yakeyi,murmushi kawai yayi jin abunda ta fad'a kafin ta cigaba.....
Sorinku...bana gida ne...sai zuwa dare in sha Allah.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(24)
"Mamma,wato mahaifiyata. Sunan da muke kiranta dashi kenan,tana dauke da cikina ne babu zato Abba ya soma shirye shiryen aure. Sam,Mamma bata tayar da hankalinta ba kasancewarta mace tagari,wacce take da ilimin addini kuma take aiki dashi. Ta bashi goyon baya sosai har kuma a yanda ta labartamin yazo yana jin kunyarta ba kuma ya fasa batun auren nasa ba.
Hankalin Mamma bai tashi ba har saida labari ya risketa ta hanyar kanwar Abba,Gwaggo Sarai akan wacce Abba zai aura ba yarinya bace. Asalima a girme ta girmeshi nesa ba kusa ba sannan tana da manyan 'ya'ya maza har su uku sai kuma mace d'aya dake gidan mijinta. A yanda Gwaggo Sarai ta ji harda yaran Abba yayi na'am zai rike mata su tunda dai marayune mahaifinsu ya rasu gashinan su d'in basu kasance masu kudi ba. Wannan babban taimako ne zaiyi. Tun alokacin ma ya zamana shine komai na karatunsu,domin kuwa sun kusan yin watanni uku suna tare da Abba kafin ya sanarwa Mamma halin da suke ciki. Wannan shine ya d'agawa Mamma hankali saidai ta nunawa Gwaggo Sarai hakan ba damuwa bace tunda a irin girma na gidan Abba da kuma tazara dake tsakanin sasunan guda uku sai mutum yayi abunda zaiyi babu wanda yaga wani tsakaninsu. Sai bayan tafiyar Gwaggo Sarai ne hankalin Mamma ya tashi,ta nemi yin shawara da aminiyarta wacce bani da masaniyar ko har yanzu suna tare,wato Hajiya Aisha,itama 'yar Kazaure ce kamar yanda Mamma ta gayamin. Ta sanar da ita halin da take ciki,Hajiya Aisha ta bata shawara akan ta dage da addu'a domin dai idan ta d'aga hankalinta babu ribar da zata tsinta a ciki. Haka dai Mamma ta nutsu ta zubawa sarautar Allah ido. Lokacin kuwa Abdullah babu inda baya yawonsa ya soma wayo.
Akayi shagalin biki tamkar na wata budurwa da saurayi harda dinnerparty. Koda Mamma ta nunawa Abba rashin alfanu ayin wani party sai ya hau fad'a acewarsa tunda ita Hajiya Raliya haka tafiso toh bazai hanata ba,idan Mamma taga zata amsa gayyatarta toh,idan kuwa bazata je ba nanma matsalarta.
Tun lokacin Mamma ta soma shan jinin jikinta,ace tun kafin ta Raliya ta shigo har ta soma ganin chanji daga Abba?"
Baby ta dakata da tabe baki tana girgiza kai cikin tsana
"Hum,Haris yawancinku maza baku da kunya. Baku kunyar nuna rashin adalci k'arara a bayyane."
Ta numfasa kafin ta d'ora
"Saida Mamma ta toshe kunnuwanta ta kauda kanta. Ga tsohon ciki da take fama dashi ga kuma wannan damuwa na auren da Abba zaiyi data sanya a ranta. Ta gwammace ace Abba ya samu matashiya daidai ita ya aura akan dai ya auro mata babbar mace wacce ta doshi arba'in. Don alokacin Mamma bata wuce talatin ba,gwara ma Abba ya girmeta don zai kai talatin da takwas. Haka Mamma ta rame,ta zamana Abba hankalinsa kacokam ya koma ga Raliya tamkar wanda ya auri budurwa,kai a yanda Mamma ta misaltamin cewa tayi koda budurwar ya aura sai haka.
Bayan Raliya ta tare ne,Abba ya sami Mamma a daki a niyyarsa ta wucewa dakin Raliya. Anan ya tambayeta game da kwana nawa ta bashi,takaici ya sanya tace mishi sati biyu. Ta dauka zai nuna wata alama ta damuwa saidai walwala data k'aru a fuskarsa,yayi mata godiya ya ajiye mata leda ya fice.
A wannan sati biyun kuwa,Mamma sai ta wuni cur bata sanya Abba a idanunta ba duk da tasan yanayin aikin likitanci,wani sa'in da daddare yake fita amma abun yayi mata ciwo. Ko irin ma a kawo maka amarya ku gaisa baiyi ba.
Saida yayi kwana uku kafin ya lekota,anan ne tayi mishi tambayar ko bazai kawo mata matarsa su gaisa bane. Sai cewa yayi,a girme fa Raliya ta girme mata don haka ita ya dace ta taka taje su gaisa. Domin shi kanshi yana bata girma a matsayinta na wacce ta fishi shekaru. Mamma shiru kawai tayi don mamaki,don alokacin idan Abba yana wani furucin saika rantse baida ilimin addini. Ta rasa dalilin juyamata baya da yayi. Abun sai ya kasance tun tana ganinsa da wasa har dai ta daina,don koda girki ya dawo hannun Mamma sai ya chanja mata. Komai tayi na burgewa sai ya gwatsale yace baiyi mishi ba. Batun Raliya kuwa,Mamma bata ganta ba sai a safiyar da take da girki. Tana cikin shiryawa Abba kayan karin kumallo akan tebur,Raliya ta shigo. Mamma ta kalleta a d'an firgice saboda rashin jin sallamar da batayi ba. Kyakkyawan harara ta watsawa Mamma tana yiwa cingam wani d'an iskan tauna.
Raliya gajeriyar mace ce,mai k'iba. Fuskarta sai godiyar Allah,domin kuwa bata daga layin kyawawa da kuma tsaka tsaki. Kallo d'aya zakayi mata kasan an gwabza a duniya. Ta k'araso ta watsawa Mamma duba na raini a karo na biyu,gaban Mamma ya bada sautin dam! Haka kawai taji matar tana bata tsoro,tayi saurin sunkuyar da kanta ba tare da tasan dalilin dayasa take tsoron Raliya ba daga haduwa da ita a farko.
"Mijina na biyo."
Ga mamaki sai ga Mamma ta d'aga yatsa tana nuna mata hanyar d'akin Abba,muryarta na rawa tace
"Yana ciki,ki shiga."
Malalacin murmushi Raliya ta sakar mata sannan ta karasa ciki. Sai fa a lokacin ne Mamma taji tamkar ta jawota ta shak'eta alhalin a farko bata iya tab'uka komai ba....
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(26)
"Ta sanya Abba ya fice daga dakin tace mishi babu komai ai ta iya karb'ar haihuwa. Abba ya fita. A haka Raliya ta zauna tana duban Mamma tana faman salati. Bata yi wani yunkurin komai ba,cikin ikon Ubangiji kuma ta haifeni,jin nayi kuka Abba yana shirin fadowa dakin tayi azamar mikewa ta isa ga Mamma. Anan ta tambayeta inda ta ajiye kayan haihuwar,Mamma tayi mata nuni da hannu,nan ta sami reza ta yanke cibiyar domin dai ta iya d'in tsabagen mugunta ce ya hanata taimakawa Mamma koda da sannu ne. Daga haka ta wanke hannunta ta fito ta dubi Abba tace yayi kiran yar aikin mamma. Yaje ya kira kulu,itama tayi mamakin nakudar da Mamma tayi a daren kuma sam bataji ba. Nan ta shiga ta tsaftacemu ta gyara wajen.
Haka washegari mutane sukayita tururuwar zuwa ganina. Ranar suna aka sanyamin Tasleem.
Rayuwa tana tafiya har nayi shekaru biyu a duniya da dadi da rashinsa babu kalar wanda Mammana da yayana Abdullah basu gani. Daidai da 'ya'yan Raliya basu kyaleta ba,sun raina Mamma,rashin kunya babu irin wacce basuyi mata. Wani sa'in idan suka fita yawon darensu basu shigowa gidan sai washegari. Mamma tana lura da komai nasu, har dai rannan ta kasa daurewa a matsayinta na matar gida mai kokari wajen kiyaye dokokin Allah,ta yiwa Abba maganar akan ya dunga sanya ido kan 'ya'yan daya kira amana gareshi. Ta fada mishi yanda suke tafiyar da rayuwarsu wannan ya sanya Abba zuwa sashen Raliya ya tarar dasu yayi musu tambaya game da hakan. Nan suka k'aryata,sukace su kam idan sunyi dare toh basu wuce majalisarsu. Raliya tayita bambamin fad'a har da tashi taje sashen Mamma wai don ba yaranta bane shiyasa takeyi musu sharri da yawon banza. Haka dai tayi ta fada mamma mai hakuri batace komai ba. A karshe ta fice, shima Abba ya bawa Raliya hakuri,ita kuwa ta tubure wai idan har ya kasance mai daukar magana ba tare da bincike ba toh lallai bazasu daidaita dashi ba zata dauki mataki kan hakan. Abba ya lallab'ata kafin ya juya ga Mamma ya hau yi mata fad'a akan tana neman shiga tsakaninsa da matarsa.
Tun daga wannan ranar ne kuma,yaran Raliya suka daina ganin girman Mamma,acewarsu ta sanya musu ido. Sai ta wuce su wuce amma ko gaisheta basuyi.
Shekara biyu ne tsakani da Yaya Abdullah,shekara kuwa na zagayowa,aka sanyashi a makaranta yana da shekaru uku a duniya. Duk da alokacin yayana baida wani girma saidai Allah Ya bashi baiwa ta hankali ga wayo. Yakan zauna ya fashe da kuka idan yaga Mamma ta zauna tana yi,hakan ne ya janyo tabar yin kuka a gabansa saidai ta kulle kanta a d'aki idan abun yayi mata yawa tasha kukanta ta share hawayenta. Ita kadai tasan wuyar da Abba ya gasa mata kafin na girma nayi hankalin sanin abunda ke wakana.
Duk fa wani arziki da mace zata rayu cikinsa idan har mijinta bai bata kulawar daya sabar mata dashi ko kuma ma ace baya bata gaba d'aya,toh fa bata da wani jin dadi a rayuwa idan har tasan ciwon kanta. Menene amfanin rayuwa namiji yana wulakantaka alhalin karkashinsa kake?
Ko Hajiya Aisha bata da masaniyar halin da Mamma ke ciki don macece mai zurfin ciki,ni kaina sai bayan dana ziyarceta bayan mutuwar aurenta nakejin wannan d'an labarin daban sani ba a bakinta duk da a rufe ta bani ba komai take bud'emin ba.
Raliya bata rufa shekaru biyu ba a gidan,Allah Ya azurtata da haihuwa 'yan biyu,mace da namiji. Kar kaso kaga dukiyar da aka kashe,Abba kuwa sai kace ba'a tab'a yi mishi haihuwa ba. Haka ran suna sai gidan Waziri akaje akayi taro. Nan ma anyi shagali,Mamma ko a kanta saidai fa tayi mamaki kwarai na yanda wasu cikin yan uwan Abba suka bar shiga sha'aninta saima suyi zuwa biyu gidan Abba amma saidai ya samu labarin ko daga yar aikinta kulu na ta ga fitarsu ko sunce a gaisheta. Aka sanyawa yara suna,Hamid da Hamida.
Rayuwa ta cigaba da tafiya a haka,'yan biyu suna da shekara daya ta kara haihuwar mace aka sanya mata Hindatu. Mamma kuwa tun daga kaina sai cikin ikon Allah haihuwarta ya tsaya abun yana damunta saidai hakanan ta barwa Allah.
Yan biyu suna da shekaru shida a duniya,hakanan suna aji daya a primary,yayinda Hindatu ke a Nursery 2. Yaya Abdullah kuwa lokacin yana (primary 6) ne,akayi auren Hamza,ni kuwa lokacin shekaruna takwas a duniya ina aji na uku a firamare. Ranar da Yaya hamza ya tare a gidan aurensa,har 'yar walima nayi da k'awayena a ajinmu bayan mun fito break saboda tsabar murna. Na wahala sosai a zaman Yaya hamza a gidan nan duk da cewar banda wani wayo amma alkawari ne duk sadda muka hadu sai ya murdemin kunnena. Gashi sam bashi da fara'a,akwai sadda ya aikeni nak'i zuwa domin mamma ta hanani shiga b'angarensu shi kuwa yace naje na dauko masa canvas dinsa,ba tsoro nace mishi ban zuwa Mamma ta hanani shiga dakinsu. Ranar saida na gwammace kid'a da karatu. Haka ya kamani ya zaro belt ya jibga tamkar ya samu wata babbar mace. Saboda azaba ko tashi ban iya yi daga wajen ba saida Maigadi ya daukeni cak ya kaiwa Mamma. A can ma mamma saida ta bubbuge bakin nawa sakamakon Allah Ya isan da nayita jero mishi. Tun daga ranar ko yaya na yiwa Hamza laifi,kai koda ace banyi bama toh fa sai ya kamani ya mora da duka. A lokacin kuma,Nura da Usman basu k'asar,Abba ya biyamusu sun fita London karatu. Tun ina Nursery,amma har nayi wayo na shiga Primary basu dawo ba. Allah kadai yasan abunda suke shukawa. Koda ace twins sunyimin laifi,nakan kamasu na jibga a hanyar zuwa makarantarmu domin makaranta daya ake kaimu. Haka zan horasu a mota,koda Malam Nasir yayimin magana saidai na zumbura baki nace ya rabu dani tunda baisan abunda sukeyimin ba. Haka kuwa idan muka dawo zasu sanar da uwarsu,har nan gaban Mamma take zuwa koda ina kuryar daki,shiga takeyi ta jawoni ta jibga wataran kuwa Yaya hamza take sanyawa ya kamani ya jibga.
Yaya abdullah ya tsani wannan rashin ji nawa,domin haka Allah Ya yini,bani