Showing 60001 words to 60852 words out of 60852 words
Chapter 21 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
in sha Allah kin shiryu kenan,bana fiddaki a addu'ata."
Farin ciki yasa Tasleem dariya. Mamma ta kara dubanta bayan ta saketa
"Kabiru da Harisu sun taba ganinki cikin waccan rayuwar,hakan yasa Harisu rokona akan kada na bari ki hadu dashi."
Ranta idan yayi dubu ya baci,Haris yafison kare sirrin abokinsa akan nata??
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(65)
Bata cewa Mamma komai ba banda toh.
******
Yaran gida sai ihun murna sukeyi da ganin Kabir. Hajiya Atine ce a
tsakar gidan zaune kan tabarma suna hira da mai musu hidimar
girki yayinda take kwasar tuwo. Ganin dagaske jikan nasu ne ta
hangame baki tana dariya
"Ashe da gaskiyar yaran nan. Lale marhabin da mijin."
Kabir yayi dariya suka gaisa suka taba barkwanci kafin ya shige
wajen kakarsa Hajiya Badi'at. Itama karatun Kur'ani takeyi,sanye da
gilashinta na ciwon ido,ganin Kabir ta karashe aya tayi addu'a kafin
ta shafa.
"Ashe zakazo nan kusa? Ai da bamu ganka tare dasu Harisu ba nayi
zaton kaida zuwa nan sai biki kuma?"
Ya kai hannu ya bude firij ya dauki robar ruwan Faro,yana kokarin
budewa yayi dariya
"Haba dai? Ai dole nazo ganin amaren namu. Ko Haris din baisan da
zuwana ba so nakeyi dai na bashi mamaki. Wai ma naga kokarin
Haris,naji don karfin hali mata biyu ya aura? Yayi kokari."
Ya karashe yana mai daga robar ruwan ya soma kwankwada. Hajiya
badi'at tayi dariya
"Kai don bakaga zuk'ak'an matan da ya zab'a ba. Zahra da
Tasleem,....."
Tuni ya maido ruwan bakinsa ya fesar har yana b'ata jikin Hajiya
Badi'at. Ya cigana da tari saboda ba karamin kwarewa yayi ba.
"Baka da hankali ne? Kana shan ruwa kamar wani karamin yaro? Ji
yanda ka b'atamu?"
Hankalinsa baya tattare da ita,gabansa na bugu da sauri da sauri.
Ganin yanda gaba daya ya chanja yasa Hajiya Badi'at dakatawa
tana k'ara cillaro mishi idanuwanta wadanda tsufa ya soma
tab'awa.
"Kai Kabiru lafiya kake?"
"Hajiya wacece Tasleem da Haris ya aure ne?"
Ta d'an tabe baki
"Kai amma Allah Ya kyauta,ai na dauka wani abun ne wallahi. 'Yar
wajen maryama ce ta gidan Liman."
"What?!!"
Ya fada cikin tsawa wanda ya tsorata 'yar tsohuwa Hajiya. Ya mike
tsaye,duk jikinsa rawa yake. Nan da nan idanunsa suka kad'a wai
kodai wata ce daban?
Da sauri ya fito daga dakin ya zura takalmansa,yana ji Hajiya na
kwala mishi kira amma baijin yana cikin hayyacin da zai samu ya
tsaya. Bai dire ko'ina ba sai gidan Liman. Tsayawa yayi ya rasa ya
zaiyi,gashi ba wani sabo yayi da mutanen gidan ba saidai ko ta halin
k'ak'a yau sai yaga Tasleem matar Haris. Yana nan tsaye yana
shawarar shiga ko tsayawa anan,saiga Baharu ya sauka saman
mashin dinsa yana kokarin tsayar dashi. Kb ya karasa wajenshi
sukayi musabaha,cikin sakin fuska kasancewar Baharu yasan Kb.
"Yaya kabir saukar yaushe?"
Kabir yayi murmushi wanda iyakarsa lebbansa
"Dazun nan na sauka. Ina amaryarmu?"
Baharu ya washe baki yana dariya
"Anti Tasleem tana nan mun b'oye maku ita har sai ranar."
Kb ya share wannan don ba shine a gabansa ba.
"Kana iya yimin magana da ita? Sak'o angon nata ya bani."
"Kash,ai kuwa tana gidan Mammanta."
"Ko zan samu rakiyarka gidan?"
Ba musu suka hau mashin din Baharu suka tafi. KB burinsa yaga
wacece Tasleem matar Haris,baya fatan ta kasance bebinsa.
Haka har suka iso kofar tangameman gidan. Kb yabi gidan da kallo
kafin ya tabe baki
"Not bad." Ya fadi a zuci.
"Bismillah shigo."
Ya bi bayan Baharu suka shiga. A nan tsakar gidan suka iske
Humaira gwaggo mai aikin Mamma tana turata a saman kekenta.
Kuri KB yayi mata da ido yana karajin gaskiyar zatonsa tana
bayyana. Wannan inda ace Baby bata wuce sa'arta ba sai yace itace
saboda matukar kamar da sukayi da juna.
"No Haris! Kada kayimin haka."
Ya fadi a fili kasa kasa,zuciyarsa na tafasa sosai. Suka shige ciki ba
tare daya amsa koda gaisuwar da gwaggo keyi mishi ba. Sukaci
karo da Mamma ta fito daga kicin. Ta amsa sallamarsu cikin jin
dadin rashin ganin Tasleem a falon kamar yanda ta haneta fitowa
daga daki har zuwa sadda Kabir zai ba Kzu.
"Mahaifiyar Baby kenan." Ya fada a ransa.
"A'a yau kuma wa muka samu haka kamar ma ba bakuwar fuska ba
a wajena?"
Ta fara maganar da duban KB,yayin data karashe tana kallon
Baharu.
Baharu yayi dariya
"Yaya Kabiru ne da,jikan Hajiya kuma aminin surukinki."
Magana ta fito! Tasleem da Haris! Wai wanene maci amanata a
cikinsu ne?
Dakyar suka gaisa da Mamma,baharu ya tambayi Tasleem Mamma
kuwa tace bacci takeyi. Kabir murmushi kawai yayi kafin a karshe
ya mike yace zai wuce.
"Haba dai ko ruwa baka sha ba?"
"Bama wannan ba,yace sak'o aka bashi ya bata fa."
Cewar Mamma da Baharu. Kabir tuni yayi kofa,ganin haka Baharu
ya mara mishi baya. Tuni yakai gate wajen mashin din. Baharu yana
zuwa yayi azamar fiddo wayarsa ya bud'o bangaren hotunan
tasleem wadanda ma'adanarsu daban ce a wayarsa,dakyar ya
lalubo wanda take zaune a falo sanye da doguwar rigar abaya tana
dariya ya dauketa domin shi kadai ne mai mutuncin a ciki.
Kafadar Baharu ya rike cikin dusashshiyar murya yace
"Duba dakyau,itace wannan?"
Baharu wanda ya tsorata da yanayin KB yayi saurin duba hoton.
"Itace ai amaryar taku."
Ya watsawa Baharu mahaukacin kallo kafin ya maida jajayen
idanunsa ga gidan. Ashe Tasleem da Haris zasu iya cin amanarsa?
Bar maganar Tasleem,yafi mamakin yanda Haris ya munafunceshi
ya auri wacce yafi so cikin mata. Ya rantse sai ya dauki mataki koda
hakan zaikai ga rabuwarsa da Yasmeen,rabuwar zumuncin iyayensu
hakanan da rabuwar wannan amintar tasu da Haris na shekara da
shekaru,duk akan 'YAR BARIKI.......!!!!!
KARSHEN NA DAYA....!