Showing 30001 words to 33000 words out of 60852 words

Chapter 11 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt

08 Dec 2024

3780

zata dunga yi musu wanka
sai Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan."
Raliya bata musa ba domin duk yanda zan
kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace
"Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro
kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa
ta gama wanka sannan zaki dawo."
Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata
ta kammala aikin na mike na shiga daki. Haka
na tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba
da ita ta tuntsire da dariya gami da yimin
gwalo"Haka zaki k'are." Kamar nace mata wani
abu saidai na fasa nayi gaba,Raliya har lokacin
tana falon banko kalleta ba nayi gaba abina a
fusace.
Saida nazo daidai garden na zube anan na
fashe da kuka,wai haka rayuwata zata k'are?
Wane irin uba gareni da bai daukeni komai ba?
Ya manta da ya haifeni ne har ya banzatar dani
a gidansa ya maidani wofi? Ace yan aiki ma
sun fini daraja da kima a gidannan? Na daga
kaina nakai duba da d'an lilon da muka saba
wasa da Yayana. Haka zaiyita cillani yana
goyani muna zagaye garden dinnan muna
dariya. Ba zato naji an dafani ta baya,nayi
azamar juyowa ganin Usman bansan lokacin
da naja tsaki ba nayi kokarin mikewa yayi
saurin dawowa ta gabana.
"Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har
takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna
kina kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki
bayan ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi."
Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban
kyauta ba,nace
"Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin
wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan
ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma
me na tsarewa mutane ba."
Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo
hannu zai dora kan lebbana nayi azamar ja da
baya,cikin tsoron yanayin kallon da yakemin
"Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi.
Ni bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa
dani shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar
zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika
kware a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA
ce, banason ganin gidan nan da kazanta. Don
Allah kanwata wallahi tana yin arba'in I
promise you zaki komo gida."
Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi
gaba yana magana ko juyowa banyi,menene
saukin da nan da can din?
****
Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana
bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief)
dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da
niyyar share hawayen. Ta dubi Haris wanda
shima ya gaji da waigenta ya karkato gaba
daya yana duban fuskarta don jin dadin hirar.
"Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman
komai na rayuwata ya soma tabarbarewa.
Yanda akayi kuwa shine......."
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)


(34)


"Usman ya dunga jana a jiki da wasa da dariya musamman idan ba idon matarsa a wajen. Tun ina daure masa har dai na hakikance dagaske tausayina yakeji kuma kauna ta don Allah yakemin. Hakan ya zamana na amince cewar bashi da wata manufa akaina. Yaya Abdullah kuwa munfi sati lokacin bamuyi magana dashi ba don bana samun kudin da zan sayi data,hakanan shima bansan meya hanashi kirana ba.


Wahala iri iri babu banayi a hannu meena,ni ce kula da jaririyarta da taci sunan uwar meena wato Sadiya suke kiranta da Ummi. A farko Usman so yayi ya sanya sunan mahaifiyarsa saidai ta murje idanunta tace sam bazata amince ba,UWA TAFI UWA don haka saidai a sanya sunan nata uwar. Haka dai Usman ya goyi bayanta,dayake itama Raliyar irin dukiyar da ake kawowa Meena daga gidansu a matsayinta na wacce ta haifi jikar fari ya hargitsa mata kai tace bakomai abi tsarin da Meena da takeso.


Wanki kuwa babu ranar da hannuna baya taba ruwa,hakanan daidai da undies din Meena ni nake aikin wanke mata su. Sau daya na taba gigin yi mata musu akan wankin ta jibgeni ba tare da kowa yayi yunkurin cetona ba. Hakanan nayi jinyata na warke domin alokacin Usman baya garin yaje daurin auren abokinsa a Zaria kamar yanda ya shaidamin.


Bakar ranar da bazan mance ba itace ranar da babu kowa a sashen usman sai ni. Gwaggo ta raka meena asibiti don allurar da zata kai Ummi,ina zaune a falo zaune kan kujera ina hutawa sanin da nayi matar gidan batanan balle kuma ta gani tunda dai ta rigaya ta sanyamin dokar hawa kujerunta nikam gajiya da aikin dana kammala yasa na shimfide saman kujerar ina kallon tashar Zeeworld da suke hasko series dinnan na Destiny wanda an riga anyimin nisa sakamakon jimawa da nayi ban kalla ba. Yawo naji wani abu kamar hannu yana yimin a kunnena nayi azamar mikewa zaune don ba karamin firgita nayi ba. Ganin Usman yasa nayi murmushi kadan ban kawo komai a raina ba na gaisheshi hade da tambayar
"Yaushe ka shigo?"


Wani kallo yake watsomin,hakan yasa cike da mamaki na dubi shigar dake jikina naga babu inda na kuskuro da shigar banza. Na kara dubansa "Lafiya dai baban ummi?"


Ya basar yana mai mikewa tsaye da dariya


"Lafiyar kenan Kanwata,kallonki nakeyi ina tausayawa rayuwarki. Ace ke kam baki da wani hutu sai masu gidan basunan kike da yancin sakewa tamkar ba gidan mahaifinki ba?"


Nayi murmushi ina mai jin dadin yanda Usman ke nuna damuwarsa akaina,alokacin na ayyana cewar ko na manta kowa bazan mance kaunar da Usman ya nunamin ba alokacin da dukkan gidan suka juyamin baya.


"Ayya,bakomai Baban ummi wataran sai labari fa."


Yayi dariya yace "Hakane kanwata,kiyi kallo abinki domin kuwa ina maki albishir cewar matar gidan bazata shigo yanzu ba don zata biya ta gidansu." Naji wani sanyin dadi shi kuwa yayo hanyar dakinsa na maida kaina ga kallo. Jimawa kadan ya fito ya shiga kicin bayan ya chanja suturar jikinsa zuwa doguwar jallabiya. Ban damu da sanin abunda zai aikata a kicin ba,a cewata ma,ai gwara kada ya matsamin ya barni na dan huta kafin hakimar tasa ta dawo. Hankalina ya nutsa sosai ga kallo saidai naji alamar ajiye kwalin a kusa dani. Hakan yasa na juyo na dubeshi,murmushi ya sakarmin yana kurbar lemon kwalin na Chi exotic dake hamnunsa,yayimin nuni da ido ga lemon da yake ajiye akan tebur kusa dani.


"Bismillah kina kallona,nasan rowa irin ta Meena bazaisa ta baki damar daukar abun sha ba. Bari na dan kwanta kafin nan da la'asar." Ya mike ya shige daki,nayi murmushi don nasan gaskiya ya fada. Meena rowan tsiya ne da ita,koda bak'i tayi sai sun nemi ruwa sannan ake basu balle akaima ga lemo. Na dubi kwalin lemun ina tunanin yaushe ma rabona dana samu yancin shan lemun kwali duk da a baya katon katon babu irin wanda Abba baya ajiyewa Mamma. Na dauka na bude na sha sosai,inayi ina kallo. Tsayawa nayi cak yayinda kaina yayimin nauyi,na ajiye kwalin lemun na dafe kaina ina mai runtse ido. A hankali na soma fita hayyacina,tun ina jiyo muryoyin dake fitowa a tv har dai na daina ji da ganin komai."


*****
Baby ta dakata tana mai sheshshekar kuka sosai,Haris cike da tausayawa ya daure yace


"Kiyi hakuri Tasleem."


Kamar bazatayi shiru ba,har ta soma rikita mishi tunani don hakikanin gaskiya ya tsani kukan mace. Dakyar ta nutsu ta goge fuskarta da (handkerchief) din daya bata. Kafin ta zubamishi jajayen idanunta wadanda sukayi kusan kwana uku suna zubar da ruwan hawaye.[2/3, 21:29] Rufy: 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(35) "Haris a wannan ranar Usman ya ketamin haddina.
Yayi amfani dani ba a hayyacina ba." Ta numfasa kafin
ta cigaba "Baccin nan bai sakeni ba sai wajen magriba.
Nayi mamakin irin radadin da naji a gabana. Na yunkura
da zummar mikewa daga shimfidar da nake kwana na
katifa a karamin dakin yar aikin meena wacce zuwana
yasa ta koma sashen raliya da aiki,saidai ko kalilan ban
iya motsawa ba. Kawai sai na fashe da matsanancin
kuka,a hankali kuma tunanina ya dawo da lemun dana
sha hakanan cikin magagin bacci na hango fuskar
Usman lokacin daya kwasheni zuwa dakina. Nayi
azamar duba pant dina,jinin dana gani ba karamin
dagamin hankali yayi ba. Ihu nasa hadi da fashewa da
kuka. Yayi daidai da shigowar Meena da Gwaggonta,wuf
suka fado dakin. Meena na fadin "Wane irin iskancin
banza ne zaki...." Sauran maganarta ta makale ganin
halin da nake ciki,gwaggo ta matso tana buga salati
"Mun shiga uku,Aminatu kinga abunda nake gani? Yau
tsinanniyar nan ta janyo mana abun magana." Meena ta
dubi Gwaggo tace"Wa?! Wallahi badai dani ba! Kanta ta
janyowa,karuwae banza da wofi. Bazaki janyomin zagin
mutane ba." Daga haka ta hau buguna kamar Allah Ya
aikota. Ihu nakeyi ina kuka kakkarfa saboda radadin
daya hademin biyu. Ta sakeni tayi wuf ta fita ina nan
zaune ina jan jikina zan shiga bandaki ta dawo rike da
bokiti,kafin na ankara ta gwalemin kafafuna ta
watsamin. Ai bansan sadda na saki razananniyar k'ara
ba saboda azabar ruwan zafin nan,daga haka na sume.
Ban farka ba sai a gadon asibiti. Nayi mamakin ganin
har da Abba cikin wadanda ke tsaye a kaina,sai Raliya
da kuma Gwaggon Meena. Na dubesu daya daya kafin
na maida dubana ga Abba cikin matsanancin tsanarsa.
Dukkansu babu masoyina ciki,makiyana ne. Bansan me
suka kawoni ayimin ba bayan sun rigaya sun gama da
rayuwata,inama ace sun barni na karasa rayuwata
anan. Na kauda kaina ina mai jin saukin radadin azabar
da nakeji a gabana bansani ba ashe wai har dinki
akayimin. "Munafuka,ke juya keyarki mana kin jawo
mana zagin mutanen gari. Haba Tasleem,me muka
rageki dashi da har sai kinje ga bibiyar yan iskan gari?
Har nawa suka baki kika basu kanki? Tir!" Cewar Raliya
tana matsar kwallar munafunci. Bance uffan ba,jira
nake naji abunda zai fito daga bakin Abba saidai baice
komai ba fuskarsa cike da bacin rai ya nufi hanyar
ficewa. "A'a Doctor ina zakaje kuma?" Cikin takaici ya
fice baiko k'ara kallonmu ba. Yana fita itama Gwaggon
Meena tace zata koma gida don ba aikin kula dani ya
kawota gidan ba. Bayan fitarta Raliya ta tuntsire da
dariya harda hawaye,idona na runtse inaji kamar na
mike na janyota na d'irka. Naji maganarta daf dani
"Usman ya biyani! Da ace tun farko nasan kudurin nan
yayi a kanki da tuni na bashi goyon baya hakanan da
banji bacin ran kulaki da ya dungayi ba. Ki godewa
Allah ma da abun ya tsaya a iya nan. Na tsaneki! Na
tsani uwarki da dukkan tsatsonta! Nafison ganina da ya
yana kadai a gidan ubanki.! Sai kiyi jinyar kanki!" Ta
kara tuntsirewa da dariya ta juya zata fita, wallahi
bansan lokacin dana fisgota ba na janyo almakashin
dake ajiye cikin tasa a gefen kaina. Saitin wuyanta na
sanya kafin na soma magana a fusace "Kina zaton kinci
galabar abunda kikayimin ko? Toh wallahi ki ajiye a
ranki saina dauki fansa akan Usman! Sai ya gane shayi
ma ruwa ne RALIYA! Don ina shanye dukkan wahalhalun
da kuke sanyani ba wai hakan yana nufin tsoronku
nakeji ba! Kawai dai biyayya nakeyi ga MAHAIFIYATA!
Wallahi ko ba dade ko ba jima sai na dauki FANSA.!" Na
wuncikalar da ita,na ajiye almakashin,a fusace tayo
kaina wanda hakan yayi daidai da shigowar nos. Ba don
taso ba ta bini da mugun kallo,na tabbata tayi mamakin
karfin hali irin nawa,da shekarunta da komai nayi mata
haka? Hum, bari dai akai mutum bango Haris, wani
abun da bai taba zaton zai aikata ba sai ya aikatashi.
Kwanana uku a asibitin Abba,wata nos me mutunci ke
kula da lafiyata bansani ba ko bisa umarnin Abban ne
kodai a'a. Ni nake lallabawa nayi wankana nasa sutura.
A rana ta hud'u ne ina zaune ina shan lemun b'awo naji
sallamar wanda banyi tsammanin ganinsa nan kusa ba.
YAYA ABDULLAH. Gaba daya ya chanja yayi
haske,saidai fa ya rame akan yanda naga hotonsa
kwanakin baya. Sanye yake da shirt da wandon jeans
bak'i ya dora brown jacket a samanta. Farin cikin
ganinsa ya koma ciki sakamakon yanayin dana gani a
fuskarsa. Kallon da yakeyimin ba karamin kad'amin 'yan
hanji sukayi ba. Salati na shigayi a zuci kafin na
russunar da kaina sai hawaye.......


'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(36)
Karasowa yayi ya durkusa a gabana,hannuna ya
riko na hagu kafin ya fashe da kuka. Hankalina ya
tashi ainun ganin kukan Yaya abdullah tamkar na
wani karamin yaro. Saidai ban iya cewa uffan ba
nima sai karfin kukana daya k'aru. Na ajiye
lemun b'awon dake hannuna. Ya dawo ya dubeni
cikin rawar murya yace
"Why Tasleem? Why?! Meyasa kika bari rayuwarki
ta lalace har haka? Wane irin halin rashi kike ciki
da har zaki bawa wani kanki? Meyasa Tasleem?
Akan wane dalili kika boyemin rashin Mamma a
gidan nan?"
Ya karashe cikin sheshahekar kuka. Na tsayar da
idanuna bana ko iya kiftasu a kansa, bakina a
bude na kasa cewa komai. Tsananin mamakin
yanda akayi yayana jinina ya yarda da wannan
kazafin da akayimin nakeyi. Ashe Yaya abdullah
shima zai amince da wannan zancen nasu?
Ya mike tsaye ya zauna gefen gadon,na cigaba da
bin fuskarsa da kallo yayinda ya dauke kansa
yana mai kara tamkemin fuska. Murmushin bakin
ciki nayi,tabbas an rabani da yayana kuma dan
uwana. Babu sauran wata magana,banga amfanin
sanar dashi komai dangane da lamarina ba. Babu
wani amfani a yin hakan. Zuciya irin tawa tasa
nak'i bayyanawa Yayana gaskiyar abunda na
sani. Maganarsa ta katseni
"Nayi bakin cikin jin rabuwar Abba da Mamma.
Kodayake naga alamar akwai wata a kasa tun
rayuwar da nayi a abroad. Wallahi Abba baida
masaniyar a yanda na kammala karatuna na
dawo. Duk a zatona Mamma tana tare da
Abbana,wannan yasa nayi kiranta na shaida mata
dukkan halin da nake ciki,bani da komai sannan
na tabbatar idan a wannan gab'ar nace zan ajiye
karatuna na dawo toh fa nan ma wata matsalarce
don bani da kudin jirgi. Mamma hankalinta ya
tashi tace kada na sake nayi kokarin tahowa na
bata nan da kwana uku. Haka na cigaba da zama
a gidan yayan abokina,Rilwan da muke makaranta
tare. Har saida ya zamana inajin nauyinsu,gani
nakeyi kamar ina matsa musu. Rilwan ya fahimci
halin da nake ciki domin ya lura har lokacin bani
da niyyar biyan kudin makaranta. Bansan ya
akayi ba sai ji nayi yace na shirya na rakashi
wani waje. Ban kawo komai ba nayi shirina tsaf
muka tafi. Nayi mamakin ganin Rilwan ya
biyamin kudaden nan,bawai ina mamakin ko a ina
ya samu kudaden nan bane,ko kadan saboda
nasan waye mahaifin Rilwan. Babban ma'aikaci
ne a 9ja garin Abuja. Mamakin da nakeyi har
wane matsayi Rilwan ya bani da sai biyamin
kudin shekara biyun daya ragemin. Na rasa
kalmar daya kamata na godemishi. Har hawayen
farin ciki nayi,ya nunamin babu komai domin shi
don Allah yake sona. A haka bayan kwana uku sai
gashi Mamma ta turomin kudi har dubu dari uku.
Nayi mamaki sosai,a karshe nayi kiranta na
shaida mata yanda akayi,kusan ta fini murna tace
na tattala wadannan zasuyimin amfani kada na
damu Abba ayyuka sukayimishi yawa shiyasa naji
shiru. Na bita a haka. Kinji yanda na kammala
karatuna,da taimakon Rilwan da Mamma sai
matar da nake niyyar aura, Hasinat kamar yanda
kika san tsakanina da ita. Ita kam dukkan wani
abu daya danganci sutura da kayan kamshi ita ke
siyamin batare dana sanyata ba. Tun bana shiga
harkarta har nazo ina shiga,iyayenta sun sani
hakanan mamanta na yawan waya da Mamma.
Itama hasinat tasan mamma sosai."
Yaya abdullah ya numfasa ya share hawayensa
yana dubana cikin mugun takaici
"Na kammala na dawo saina riski labari marar
dadin ji daga bakin Maman twins(Raliya),wai
Tasleem kin siyar da mutuncinki saboda abun
duniya?!! Wane irin kunci kika shiga?!! Abba ya
cucemu daya dauke mana mahaifiyarmu daga
gidansa!"
Zuwa lokacin hawayena sun gaji da zuba sun
dauke,murmushi kawai nakeyi wanda yafi kuka
ciwo
"Kaddarata ce mai yiwuwa! Haka nawa..."
"Ba kaddara bace!!"
Ya katseni a tsawance har na firgita ina dubansa
yanda ya mike cikin fusata.
"Son zuciyarki kika bi tasleem! Kin manta
tarbiyyar da Mamma ta jima tana iyakar kokarinta
wajen baki? Meyasa zaki lalata rayuwarki har
haka? Nayi bakin ciki marar iyaka jin wannan
batu! Nayi danasanin tafiyata na barki,wallahi da
nasan Abba zai rabu da Mamma da ban amince
na ketara ko nan da can ba!"
Ya dakata yana mai hade kansa da bango kafin
yayi wuf ya fice, ina kiransa saidai ko waigowa
baiyiba.
Kaina na cusa cikin filo ina kuka mai karfi. Gaba
daya zaman asibitin ya isheni hakan yasa na
sauko na dauki hijabin da bansan ko na waye
ba,dashi dai nakeyin salla,ban iske takalmi ba
hakanan na fice.
Ban tsaya ko'ina ba sai kofar gidanmu,na nemi
rance wajen baba Maigadi don bawa mai
adaidaita,baba maigadi yace babu komai naje zai
sallameshi. Yayimin sannu banko tsaya amsawa
ba nayi ciki. Tsayawa nayi cak ina duban ko'ina
na gidan,ina ya dace na nufa? Wajen wa zanje?
Waye zai saurareni? Na kara taku daya biyu,na
daga da niyyar yin na uku mukayi ido hudu
dashi,cikin sanyin jiki na maida kafar baya na
dukar da kaina. Ya k'araso a fusace
"Me kika dawo kiyimin?!!!"
Na dago kaina murya na rawa na soma magana
"Abb..." Marin daya saukemin a fuskata ya
dakatar dani daga karasawa
"Fitarmin daga gida,yar iskar yarinya! Kin bata
wayonki! Bazaki zo ki b'atamin tarbiyyar yarana
ba! Shegiya! Kedai kam ina kwakwanto akanki!
Anya nine ubanki?!!!"
"Wannan shine furuci na biyu cikin ukun da bazan
taba daina tuna su ba,hakanan tunaninsu ya
sanyani yin mummunan hatsarin da har ka kaini
asibiti Haris." Cewar Baby tana duban
Haris,sannan ta cigaba.
Kalaman Abba yayi daidai da fitowar yayana
Abdullah a guje daga sashen Mamma.
Gwuiwoyinsa a k'asa ya shiga rokon Abba akan
yayimin afuwa ya barni na rayu koda a sashen
'yan aiki ne. Abba ya hankad'ashi
"Gidana ne! Ina ajiye wanda naso a ciki amma
banda yan iska! Kaima kuma idan bakayi wasa ba
yanzun nan zaka bita ku tafi."
Maganar da Abba keyi da karfi ce ta janyo
hankulan yan aiki. Zuciya ta kwasheni cikin kuka
da daga murya nace
"Naji gidanka ne! Zan fita na barshi,zan barshi
har abada!! Kai uba ne ga wasu amma ba ni ba!
Na amince idan har ka manta hakkina dake
kanka ka manta akwai hisabi a tsakaninmu! Toh
hakika zan bar gidanka yanzu ba anjima ba. Ko a
kiyama bana fatan Allah Ya kara hadani da
azzalumin uba..."
Mari Yaya abdullah ya daukeni dashi,
"Kina hayyacinki kuwa? Kin manta waye
agareki?!!"
Cikin kuka da daga murya nace
"Ban manta ba yaya abdullah! Amma shi ya
mance diya nake awajensa. Abba ina kake sadda
nake rayuwar garari acikin gidan ka?! Ina kake
sadda abincin yan aiki ma yafi nawa mutunci da
dadi a harshe? Ina kake sadda na kammala
karatu?!! Ka taba zaunar dani kaji damuwata?! Ka
taba yimin nasiha koda sau daya akan rike
addinina?! Ka taba damuwa da ni?! Wallahi na
tabbatar ko sunana bazaka iya tunawa ba saboda
baka sona! Ka tsaneni! Har gashi ayau kana
kokwanto ko kaine ubana!!! Shikenan gaka ga
gidan naka! Allah zai mana sakayya!!"
Daga haka nayi waje a guje,Yaya abdullah yana
kirana amma ko juyowa banyiba. Nayi nisa sosai
da gidanmu kafin na samu kasan bishiya na zube
ina kuka da numfarfashi. Kaicona!!!!


'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)


(37)


Taku naji da sauri sauri kafin aci burki a gabana. Na dago kaina,Yaya abdullah ne. Kaina na cusa cikin cinyoyina,dagomin kai yayi kafin ya rungumeni shi kansa hawayen yake. Ganin mutane sun soma taruwa ne yasa ya mikar dani tsaye yaja hannuna. Na turje na tsaya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login