Showing 12001 words to 15000 words out of 60852 words

Chapter 5 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt

08 Dec 2024

3774

mai amsa sallamar d'ansa. Cike da girmamawa ya russuna ya gaida Daddy. Daddy ya amsa fuska a sake kafin yace


"Gaisuwarka bata k'arewa Harisu,ayi ta gida ayi ta ofis ko?"


Haris yayi murmushi mai bayyana hak'ora,baice komai ba ya zauna saman kujera bayan yayi kokarin d'an rage tsawo duk da hakan. Daddy yayi gyaran murya ya soma magana


"Haris,kwanaki sun shude sun zama watanni,ga watannin sun koma shekaru. Dan uwanka gashinan zaune da iyalinsa,a dukkan tsawon watannin nan mun barka ne akan ka nemi zab'inka gudun shiga rayuwarka. Saidai har kawo yanzu,shiru Harisu."


Daddy ya k'arashe cikin rarrauniyar murya mai russunar da zuciyar wanda ake yiwa. Haris baice komai ba yayi shiru yana sauraron Daddy


"Ga iyayenka nan girma yana k'ara hawan kanmu,wannan ya sanya naga tunda abun ya zama haka na baka zab'in zuwa can Kazaure,ka duba cikin 'yan uwanka dake can ko Allah zaisa ka sami wata cikinsu da zakaji nutsuwar zuciya akanta. Nidai fatana Allah Ya baka mace ta gari."


Haris yayi murmushi kad'an jin wannan batu da Daddy,a gefe kuma ya gama gaskata cewa ba k'aramin so Daddy da Hajiya sukeyi mishi ba,tamkar daga cikinsu ya fito. Ya tabbata gudun abunda zai b'ata ransa ne yasa Daddy b'ullowa ta wannan hanyar.


"Tashi ka koma ga aikinka Harisu,zan jiraka daga nan zuwa gobe duk abunda ka yanke toh,idan ma akwai wacce ka gani kake so toh Alhamdulillah. Wannan ma shi muka fi muradi. Allah Yayi jagora. Tashi ka tafi, ka turomin sakatare."


Cike da jin nauyi Haris ya mike yana mai amsawa da toh,ya fice jiki a sanyaye. Ya isar ga sak'on Daddy ga sakatare kafin ya koma ofis.


Kasa nutsuwa yayi,zancen Daddy yake ta juyawa. Toh wai ko zai koma ya sanar dashi cewar ya bashi zab'ine? Su zab'a mishi kawai mace tagari? Idan ba hakan ba ya zaiyi toh? Shi kam bai taba budurwa ba,a takaice ma basa gabansa. Allah Ya yishi mutum ba mai son magana sosai ba,baisan ta inda zai soma zuwa ga mace da zummar soyayya ba. Toh yace mata me? Ai shi kam matan ma bakin jini yake a gurinsu,bai mantawa dai da wata abokiyar karatunsa a Malaysia,Rahima. Babu irin bibiyar da batayi ba akan ya amince da soyayyarta amma sam bata samu fuska ba.
Bai mance ranar da Kb ya tursasashi akan sai ya saurareta ba. Suka shirya suka fita wajen shak'atawa inda tuni Kb ya yiwa Rahima maganar ta isa wajen zasu zo. Koda sukaje,nan suka hangeta zaune a kujera bakin swimmingpool na wajen. Kb ya daki kafadarsa yana dariyar mugunta


"Oya jeka,sannan don Allah kada ka bani kunya. Nasan wannan ne farkon tsayuwarka gaban mace a matsayin saurayinta,be a man!"


Harararsa yayi kafin yayi gaba cikin takunsa na nutsuwa,tana ganinshi ta mike tsaye domin girmamawa gareshi tana dariyar farin ciki.


"Sannu da zuwa Haris na."


Yayi dan murmushi kafin ya amsa ya zauna,hakan ya sanyata zama itama. Shiru ya ratso,ya zamana hirar ita keyi yayinda shi ya zama macen. Daga um,sai um um,ga murmushi da yakeyi baya ko dariya. Tun yana burge Rahima,har ya daina cikin yanayin damuwa tace


"Haris na yadai? Ko ka gaji da ganina ne? Na dameka?"


Ya duba agogo kafin ya kalleta yana murmushi


"No,ba haka bane saidai akwai wani uzuri dake gabana yanzu. Kiyi hakuri dai sai mun hadu a makaranta."


Daga haka ya mike da niyyar tafiya,tayi azamar dakatar dashi ta hanyar cewa


"Ya makomar soyayyarmu? Ka amince dani ne ko kuwa..."


"Yanzu kam karatu ne a gabana ba soyayya ba. Kiyi hakuri "


Yayi gaba,yayin da ya barta cike da bakin ciki da dana sanin zuwanta. Yana haduwa da kb wanda yake dubansu. Ya shiga dariyar mugunta har yana kwarewa. Daman yasan amininsa ba iya zancen yayi ba,saidai ta duri haushi. Abun ma bai bashi dariya ba saida Haris ya labarta mishi yanda sukayi shima yana dariyar. Kb ya bugi sitiyari


"Amma kai kam anyi d'an iska,wato baka soyayya sai karatu. Kalaman yayi yanayi dana mace."

Tun daga wannan ranar Rahima bata k'ara neman shiga harkarsa ba. Hakan ma sai yayi mishi dadi domin sam ba sonta yakeyi ba.


****
Haris yana kaiwa nan a tunaninsa yayi murmushi kafin ya watsar da komai ya cigaba da aikinsa.


****


Dalal,Manal da kuma Hibba,sai Baby. Zaune a falon.
Baby sanye da wando three quarter sai 'yar shimi,kwance take akan two sitter ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya tana (game) da iPad dinta,tana yi tana taunar cingam. Hankalinta kwance,jifa jifa take sanya baki a hirarsu na duniya. Manal ta dubesu tana murmushi


"Albishirinku."


Suka amsa da goro banda Baby dake sha'aninta saidai kuma hankalinta yana ga sauraron abunda zai fito daga bakin Manal.


"Zanje zaman wata uku gidan Alhaji Ubale Kwangila."


Cikin rashin fahimta Dalal da Hibba suka yamutse fuska


"Bamu fahimceki ba."


Kafin ta basu amsa,Baby tayi dariya ba tare data dubesu ba


"Kudai kam baku saurin fahimtar mutum,kasuwanci na wata uku zataje yi gidan Alhaji Ubale. Don wannan baikai kimar da za'a kirashi da aure ba."


Dalal da Hibba suka buga shewa,Manal tana dariya tace


"Dad'ina dake saurin fahimta Baby,toh kun fahimta inace?"


Hibba tace


"Kwarai kuwa,amma fa yana da mata ko?"


Ta rausaya idanu


"Taci kaza kazanta(ashar),ke aure ne fa tun ana fama da shan miyar kuka a kauye. Babu abunda zata hanani,wai kin manta nafi kunama radadi?"


Ta buga hannuwanta


"Wata uku kacal,nayi na gama dashi na fito. Batun da nakeyi maku wahalallen ya kammala yimin gyaran gidansa na Abuja. Can zan lula mubar shegiyar a Kaduna. Magana ma ta isa kunnen Momi,aure nan da wata d'aya sai a soma shiri."


Sukayi dariya gaba daya har Baby,domin yanayin da Manal tayi furucin duka ya basu dariya.


"Kidai shiga da shirinki,kada a samu matsala ya gark'ameki. Me akeyi da aure?" Cewar Hibba.


Dalal tayi dariya


"Shegiya,kada ki manta shine ya haifeki,ko kin mance gyatumarki Sarai mai kosai na tuna maki?"


Dam! Kirjin Baby ya buga,jin furucin daya fito daga bakin Dalal......!
















'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)


(18)


Shewarsu ta katse mata tunani,hibba tace


"Allah Sarki uwata,hauka nakeyi zan mance da ita? Karki ganni anan, duk wata saina tura mata kud'i ta account kawata Balaraba. Ba don wannan mugun uban nawa ba ai da wataran saidai ta ganni naje ziyara. Kunsan dai duk iskancina bana manta MAHAIFIYA."


Baby tayi shiru,jikinta a sanyaye. Ita kam yaushe rabonta da tata uwar? Shekaru biyu kenan,gwara ma mahaifinta,tana da masaniya akansa,ta tsaneshi shima ya tsaneta,wannan dalilin ne yasa babu wanda ya taba yunkurin neman wani a cikinsu. Amma mahaifiyarta fa?


Dalal tace "Ai gwara a dungayi ana tuna asali,nikam saidai nace Allah Ya jik'an nawa iyayen. Ita kuwa Gwaggona da ita muke ci da sha. Ina yawan zuwa gidanta a Kano,kuma kun sani."


Ga mamaki sai sukaga Manal na hawaye tace


"Gwara ku, kuna da iyayen. Nikam idan baku manta ba tsintata akayi a bola,sai ya zamana wanda ya daukeni ya rikeni har girmana,shine mutumin farko daya soma aikata masha'a dani."


Tayi shiru tana sharar kwallah,kowannensu jiki yayi sanyi na tuno abubuwan daya shud'e a rayuwarsu. Baby daga kwance itama hankalinta taji ya tashi,babu wacce ta tsaya a ranta kamar mahaifiyarta. Taji gaba daya tanason taje duba lafiyarta. Manal ta share hawaye ta mike


"Yan iska zaku tunomin bakin labarin rayuwata,ku tashi muje shan ice cream. Yau jakata a cike take."


Sukayi murmushi don babu wacce keda kuzarin dariya,Manal ta dubi Baby.


"Zakije ne?"


Baby ta girgiza kai


"Banajin fita ne."


Sun lura jikinta yayi sanyi, tausayinta ya mamayesu musamman ma Manal wacce anan duniya ita kadai tasan wacece Baby Tasneem. Ita kadai tasan tarihin rayuwarta. Don kafin ta hadu da kowacce cikinsu,Baby tasleem ta soma haduwa da ita harma ta sauketa a gidanta. Haka suka fice suka barta a gidan. A ranar Baby taci kuka sosai,ba don komai ba sai don rashin sanin halin da mahaifiyarta ke ciki. Karshe ta mike ta shiga daki ta kwanta ba don tanajin bacci ba. Sai don kawai tunanin rayuwarta.


*****
KWANA HUDU BAYAN HAKA
Tafiya takeyi da baya da baya tana kallonta,yayinda ita kuwa ke kwance duk fuskarta ya baci da kuraje,hannu take miko mata alamun tsayar da ita tana ihun kuka


"Ya d'iyata,kada ki gujeni! Karki barni cikin wannan halin! Ki dawo gareni!"


Maimakon ta dawo,sai ta juya a guje zata tafi, karar da taji uwar tayi ya sanyata itama kwala ihu kafin tayi wuf ta fada wata rijiya a wajen."


A tsananin firgici Baby ta tashi sakamakon wannan mafarki mai rud'arwa,gumi ya wanke fuskarta duk da Ac dake a kunne. Sai haki takeyi tamkar wacce tayi gudu. Ta sanya hannu ta dafe kirjinta dake dukan uku uku. Can kuma tayi wuf ta sauko daga gadon. Wani d'an karamin akwati ta dauko ta bud'e. Hoto ne a cikin (envelope),nan da nan ta zaro tana duba. Dattijuwa ce tare da yarinya mai shekaru uku,sai dan saurayi mai kimanin shekaru goma sha daya a hoton. Dukkansu suna dariya.


Ta rungume hoton a kirjinta yayinda hawayenta suka karu. Tausayin kanta ya dabaibayeta,taji nan duniya bata sha'awar komai daya wuce na zuwa kauye ganin Mahaifiyarta. Tun hirar da sukayi tare dasu Manal,hankalinta yake a tashe. Ta amince bazata taba samun nutsuwa ba har sai ta dangana ga duba lafiyar mahaifiyarta.


******
Karfe goma na safiyar Asabar,ya shirya tsaf cikin kananun kaya ya feshe jikinsa da turaruka. Bai dauki komai ba sai karamin trolley dinsa inda ya shirya kayan sawarsa. Saida ya soma zuwa gidansu yayi sallama da Daddy,kafin yaje gidan Abba. Nan ma yayi musu sallama,mahaifiyarsa ta bashi sako a kaiwa uwarta,wato kakarsa. Daga haka ya kama hanya.


******
Zaune suke suna karyawa,basu ankara ba suka ganta ta fito tana jan akwati. Ba jan akwatin ne yafi basu mamaki ba,tunda sun saba tafiye tafiyensu. Shigar dake jikinta ne ya burgesu kuma ya basu mamaki. Doguwar rigar atamfa ce, anyi mata dogon hannu three quarter,maimakon ta dora dankwalin saita yafa karamin mayafin (pashmina) a kanta. Saida tazo kusa dasu sannan ta dubesu fuskarta babu wata kwalliya ta daukar ido sai hoda da jan baki mai kalar ruwan hoda(pink).


"Zanyi 'yar tafiya ne,amma in sha Allah bazata wuce kwana uku ba. Amanar gidana yana hannunki sister."


Ta dubi Manal. Murmushi manal tayi kafin tace


"Karki samu damuwa baby,shigarki tayi mana kyau,tamkar bake ba."


Tayi murmushi batace komai ba ta nufi waje. Babu wata wata,ta fada motarta ta shiga. Duk da dai bata taba karambanin tuk'i mai nisa ba,yau kam tanason yi. Dole taje ga mahaifiyarta ta duba lafiyarta. Tsananin kewarta yana neman hanata sukuni,ga fargabar abunda zata tarar sskamakon mafarkin da tayi a daren jiya......!







'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)


(19)


Tafe take kawai saidai dukkan hankali da tunaninta yana ga zantukan karshe da tayi da mahaifiyarta kafin su rabu.


"Na sanki,yarinya kike mai basira da kula dakai. Kada ki sake ki bari shaidan yayi maki hud'uba Tasleem. Kibi matar ubanki sau da k'afa,kiyi biyayya ga mahaifinki kada ki sanya damuwar komai a ranki. Allah Yana tare dake."


Hawayenta suka k'aru,yayin data k'ara karfin gudunta.


"Fitarmin daga gida,yar iskar yarinya! Kin bata wayonki! Bazaki zo ki b'atamin tarbiyyar yarana ba! Shegiya! Kedai kam ina kwakwanto akanki! Anya nine ubanki?!"


A zuciye ta kuma k'ara karfin speed dinta,hawaye bai bar kwaranyo mata ba.


"Kin bani mamaki kanwata,kin bata wayonki. Har da kanki ki dunga kai kanki dakin namiji?!! Tirr da wannan d'abi'a taki. Toh wallahi ki barmin gidana,kuma kika kuskura kikaje ga mahaifiyarmu kika kashe aurenta,wallahi saikin raina kanki! Kije duniya ce! Daidai take da kowa!"


A fusace take tafiya,bata ankara ba,motar ta kufce mata, ta rasa yanda zatayi ta tsayar da ita. Taka burki takeyi saidai batasan dalilin cijewar burkin ba,haka tayita wala wala har ta k'umu da bishiya. Bata k'ara sanin duniyar da take ba.


******
Farkawa tayi ta ganta kwance a gadon da yafi kama dana asibiti,ta tsurawa rub'abb'en kwanon silin din ido tana duba,hannunta tayi kokarin d'agawa da niyyar tab'a goshinta wanda ke sarawa tamkar zai fad'o saidai wani irin azaba da hannunta yayi ya sanyata cije lebbanta tana 'yar k'ara kad'an.


Wannan ya jawo hankalinsa,yana zaune saman gadon dake fuskantarta yana danne wayarsa a kokarinsa na kiran gida domin kada a jishi shiru ayi tsammanin ko babu lafiya. Ya dubeta,nan da nan zuciyarsa tayi sanyi ya mike ya karaso wajen kanta


"Sannu,ya jikin?"


Ta waiwayo dakyar sakamakon ciwon kan da takeji ya addabeta,ido kawai ta zuba mishi ba tare da tace komai ba. A zuciyarta mamaki kawai takeyi,meyasa Allah Yake yawan kawo mata shi aduk lokacin da take da buk'atar taimako? Abun tambayar ma shine,ya akayi yazo nan?


Kafin ta kammala tunaninta tuni ya juya ya fita. Minti daya sai gashi da likita,likitan ya karaso yayi mata gwaje gwaje kafin ya dubeta yana murmushi


"Sannu fa madam,yanzu meke damunki bayan hannunki? Kina jin wani ciwo daban ne?"


Baby ta k'ak'alo murmushi kafin ta d'aga hannu ta dafe kanta.


"Oh sorry,bari na sanya nos ta k'ara baki magungunanki. A sannu zai daina. Saidai kafin nan..."


Ya juya yana dubansa


"A samo mata abunda zata ci don bana zaton taci wani abu a yau."


Ya dubi Baby wacce tayi tsai da ido tana kallonsa,fuskarta babu yabo ba fallasa kamar dai wani tunanin na daban takeyi. Ya dauke kansa ya maida ga likita yana mai gyada mishi kai.


Likitan yana fita yabi bayanshi ba tare da yace mata uffan ba. Ta bishi da kallo sannan ta kauda kanta tana tuna abunda ya janyo mata hatsarin. Hawaye suka gangaro saman kuncinta,ko kusa batayi yunkurin sharesu ba,saima ta barsu suka cigaba da shatata.



'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)


(20)


Haka har ya dawo ya sameta cikin wannan yanayin. Shigowar baisa ta sharesu ba,a zahiri ma sam batasan da wanzuwarsa ba. Lura da cewar ko kusa batasan da shigowarsa bane da kuma sallamarsa,yasa shi yin magana


"Tasleem."


Batasan lokacin data dubeshi ba,haka kawai sanyi ya ratsa zuciyarta domin tunda take bata tab'a jin wanda ya iya kiran sunanta ba kamarsa. Ya kauda kansa yana mai bude ledojin,fuskarsa a daure


"Tashi ki d'an ci wannan."


Ta mike dakyar ta zauna bayan ta sauke kafafuwanta dake ciwo kadan kadan a k'asa. Batace dashi komai ba ta mike tana dafe gado,band'aki ta zagaya. Can kuma sai gata ta fito.


"Ko zaka taimakamin da brush da maclean please?"


Ya mike ya fita, sai gashi ya dawo dauke dasu sabbi. Saida ta tabbatar da tsaftar bakinta sannan ta fito. Maimakon ta iskeshi saita iske nos. Da taimakonta ta ci abincin kadan ta sha yoghurt din da yawa kafin daga bisani tasha magungunan. Bayan nan tayi mata godiya,nos din tana shirin fita ta tsaidata


"Don Allah karfe nawa ne? Inason gabatar da sallar dake kaina."


Ta bata amsa


"Ai Hajiya yanzu haka ma isha'i ta kusa."


Cikin mamaki Baby ta mike tayo alwala ta fito, rarraba idanuwa ta tsaya yi ganin babu wani darduma ko abunda zata rufe jikinta dashi. Turo k'ofar da akayi ta sanyata waigawa. Sukayi ido hud'u dashi,ta sakar mishi murmushi ya kauda kai.


"Sannu HARIS,don Allah inason yin sallah ne."


Wani irin kallo yayi mata,ta kauda kanta. Ya jinjina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login