Showing 54001 words to 57000 words out of 60852 words
Chapter 19 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
batun
aurensa har haka? Inda aminci kamata yayi ma
ace a bakina Princess(yasmeen) zata soma ji ba
bakinka ba. Haba Haris,abun har yakai haka?
Allah ma munayin laifi gareShi ya gafarta mana
ballantana dan adam?"
Ya karashe a sanyaye gwanin tausayi domin
hakikanin gaskiya KB yana kaunar Haris kwarai
dagaske,kauna ce mai tsafta tun suna yara suke
yiwa juna. Jin yanda ya narke murya yasa Haris
sauka daga fushinsa,shima cikin sanyin murya
yace
"Dan uwan nawa ne ya kasa saita rayuwarsa,ya
kasa fahimtar hatsarurrukan dake cikin sab'awa
Ubangiji. Banda wannan babu wani abu dake
had'ani dashi."
"Oh come on my friend,tuni na watsar da wannan
hanyar wallahi. Just ita ke wahaldani ga kuma
fama da rashin sanin inda take amma daman
banda ita komai na watsar. Ka tayani addu'a."
Murmushi Haris yayi na mugunta
"Bakomai,itama zaka mantata har abada in sha
Allah. Zan tayaka addu'a. Barni hakanan,Daddy
suna jirana."
"Toh ango,yaya sunan matar.."
Kafin ya karasa Haris ya katse kiran yana
murmushi
"Da sauran lokaci Kb,bazan amince ka rusamin
komai ba."
Daganan yayi ribas ya fita kasancewar tun
shigarsa mota isah ya wangale gate din.
*****
Rashin samun wadataccen bacci da kuma
matsanancin kukan da baby tasha a daren ya
janyo mata ciwon kai matsananci da zazzabi
wanda ya sanyata lafkewa saman darduma tun
bayan sallatar Asubahi da tayi. Gwaggo Hajara
tayi shigowa dakin wajen sau biyar amma bata
tashi na gashi har rana tayi sosai domin lokacin
wajejan karfe sha daya na rana. Ganin bata da
niyyar motsawa ne,yasa Gwaggo tashinta
"Wai lafiyarki kuwa 'yar nan? Wane irin bacci
kikeyi hakane?"
Jin muryar Gwaggo yasa baby bude ido kadan,
ganin yanayin baby yasa ta taba wuyanta
"Ikon Allah wannan bandejin kuma fa na kanki?
Jiya dankwalin kanki bai barni na lura ba,ga
jikinki da zafi ashe masassara kikeyi baki fada an
nema maki magani ba? Bari na aika kemis din
Abdulaziz a amso maki magani. Kokarta ki tashi
ki sanya ko kunu a cikin naki."
Ta karashe tana kokarin mik'ar da Tasleem
zaune,dakyar ta mike tayi azamar rike kanta
sakamakon sarawar da yakeyi.
Ta daure ta wanko bakinta ta dawo tasha kunun
kadan,saidai fa tuni cikinta ya hau murd'awa
saida ta ruga bandaki ta amayar dashi tas!
Gwaggo na mata sannu. Bayan ta kamota sun
fito take fadin
"Haba jama'a,ana kokarin yi maki gata amma
kina facali da damarki? Harisu yaron arziki ai ba
abun gudu bane."
Ita dai tasleem batace uffan ba,da gwaggo zata ji
labarinta da bata amince da aurawa namiji irin
Haris 'Yar Bariki ba. Dakyae ta iya hadiyar
magungunan ta sha ruwa sai kuma bacci ya
dauketa a saman gadon bayan ta ja bargo ta
kudundune jikinta saboda sanyin da takeji yana
damunta duk da kasancewar rana ake kwalawa.
******
"Kace ashe harisun sun iso kenan?"
Tambayar da taji Gwaggo na yiwa wanda batasan
ko wanene ba. Tashinta daga bacci kenan,ba laifi
zazzabin ya d'an sauka saidai ciwon kan.
Batasam takamaiman karfe nawa ba saida taji
muryar Baharu na fadin
"Ya iso gwaggo,shiyasa Baffa yace nazo nayi
kiranta su gaisa."
"Toh ai shikenan,bari na gani ko jikin nata yayi
sauki."
Jin gwaggo na kokarin shigowa tayi saurin
mayarda idanunta ta rufe gabanta na bugu fat
fat......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(58)
Ta taba goshinta taji sanyi radau wanda ya
tabbatar mata da saukar zazzab'in. A nutse
gwaggo ta hau bubbuga kafarta
"Tasleem,tasleem."
Ta bude ido sannu sannu kamar mai baccin
gaske.
"Na'am gwaggo."
"Sannu ko? Ya jikin naki?"
"Alhamdulillah."
"Haka nakeson ji,maza daure ki tashi,Baffa ya
aiko kiranki ku gaisa da bak'i."
Kamar zatayi kuka tace
"Banjin dadi fa gwaggo."
Gwaggo ta hau lallab'ata
"Haba d'iyata,meyasa bazaki kasance mai hakuri
a rayuwa ba? Babu amfanin bijirewa maganar
manya. Ki tashi kije ai ba auren kikaga anyi ba.
Mu dage da addu'ar zab'in Allah."
Haka tayita kashe mata jiki da maganganu,Baby
ta mike ba don taso ba.
"Toh nidai ki sanya a daukomin akwatina sai nayi
wanka."
Gwaggo tayi dariya
"Ai shikenan babu komai d'iyata ta kaina. Shiga
kiyi abinki don ma kayana bazasuyi maki ba ai da
shi zan baki."
Murmushi baby tayi kafin ta soma kwab'e kayan
jikinta.
****
Ta fito wanka sai kuma ta rasa suturar sanyawa.
Manyan kayan daman kala biyar ne. Uku
atamfa,biyu kuma shaddoji suma kyautarsu akayi
mata. A karshe dole ta dauki daya cikin shaddojin
nan ta sanya ba don taso ba. Shaddar brown
ce,tasha surfani anyi mata riga fitet hakanan skirt
din yayi d'as a jikinta saidai hakan bai boye 'yar
ramar da tayi ba. Ta sanya dankwalinta tayi
dauri wanda ya rufe bandejin kanta,ta kudurta
suna tafiya zataje kemis a fidda mata.
Kai kuzo kuga baby acikin hadaddiyar shaddar
nan. Batayi kwalliya ba kwata kwata,toh auren da
bata murna da yinsa kuma ma me zata nunawa
Haris bayan shi d'in daban ne a komai. Ta fesa
turaruka masu fisgar hankali wanda har gwaggo
dake waje saida tayi mata magana
"Kai tasleem,turaren nan kodai na maza ne? Kibar
amfani da turare mai k'arfi haka kina mace."
Batace komai ba ta maida ta ajiye,ita kam anya
zata iya daina shafa turare? Da kamar wuya don
ma'abociyar son kamshi ce. Ta zura takalminta
sai kuma ta rasa mayafi. Kawai saita janyo na
mamma da tun zuwanta take yafawa ta yafashi.
Gwaggo Hajara ta dubeta tana zabga murmushi
sadda ta fito
"Ko babu kwalliya kina da kyawunki diyata ta
kaina saidai muje na baki wani mayafi ki sanya
wannan ya tsufa da yawa."
Murmushi kawai baby tayi gabanta bai bar bugu
ba,taji kwallah ta taho mata saidai tayi azamar
maidasu. Baharu ya shigo karo na biyu yana
sallama ta amsa. Baki ya washe
"Antina wallahi kamar bake ba. Kullum k'ara kyau
kike."
Ta d'an harareshi ya kyalkyale da dariya
"Kamar kinsan kuwa surukan naki ne ya
tambayeki shine nace bari na turo masa ke."
Surukanta? Ta nanata a ranta,ita fa jikinta yana
k'ara yin sanyi. Mamaki takeyi ace wai Haris ke
sonta,haka kawai tsoronsa yayi mata dirar
mikiya. Tunaninta ya katse sa'ilin da gwaggo ta
fito rike da wani mayafi kalar ruwan madara(wato
surfanin dake jikin shaddar)
"Fiddo wannan ki yafa wannan."
"Kai gwaggo ashe kinsan kalar gayu." Cewar
Baharu. Baby dai kamar kurma ko don bata fiye
son yawan magana bane? Oho. Amma batace
musu uffan sai murmushi na dole.
Suka jera Baharu yana bata labarin yanda
surukan suka yaba da wannan auren ji sukeyi
tamkar a daura auren ma a yau.
"Wallahi anti angon nan naki burgeni yakeyi kana
ganinsa kaga dan boko kuma wayayye amma ko
kusa bashi da wulakanci ko girman kai. Kunyi
bala'in dacewa dashi wallahi."
Ta dubi Baharu zatayi magana ta fasa
sakamakon ido hudu da sukayi da Haris ya fito
yana amsa waya. Sanye da manyan kaya amma
babu babbar riga, kansa sanye da hula. Sai taga
yayi mata kyau da kwarjini sosai,shi kansa
Baharu saida yaga yayi mishi kwarjinin. Ya daure
fuska yana mai kauda kansa yana mai juya musu
baya ya cigaba da wayarsa da alama dai da
kanwarsa yakeyi. Ta sunkuyar da kanta yayinda
kwallah suka cika mata idanuwa. Daman tasan
ba sonta yakeyi ba. Har suka is a daf dashi bai
bar wayar ba hakan yasa tayi cikin gidan,zata
karasa can wajensu inna,Baharu ya dakatar da ita
da cewa
"Ki soma shiga suna nan d'akin fa anti."
Ta gyada kai kawai,gabanta na faduwa tayi
sallama. Dukkansu suka amsa kafin ta shiga
kanta yana k'asa. Su kuwa su Abba ganin
surukar tasu nan da nan fara'arsu ta k'aru bare
ma Malam Hussein wanda yaji tamkar diyarsa ce.
Ta gaishesu a ladabce,suka amsa kafin ta
tambayesu hanya. A karshe Malam Hussein ya
kara jin ta bakinta sannan yazo mata da batun
cewar ba ita kadai Harisu zai aura ba(kamar
yanda suka zauna sukayi zancen da yaransa
abba da daddy da hajja kubra,Haris ya amince da
hakan ga mamakinsu. Itama Zahra tayi na'am
tana mai farinciki saboda son da takeyiwa Haris
mai girma ne.),hankalinta ya tashi jin wannan
zancen. Saidai ta daure tunawa da nasihar
gwaggo tace ta amince da bakinta. A karshe suka
sanya mata albarka ta mike ta fito kanta na
k'asa suna zubar hawaye. Jikinta kuwa rawa
yakeyi gabanta na dukan tara tara sakamakon
tunanin daya darsu a zuciyarta na cewar lallai
d'osanawa Haris ita akayi,daman Zahra yakeso.
Tana kokarin sanya takalminta amma jikinta rawa
yakeyi,ta dunguro zata fad'i tayi azamar kai
hannu da niyyar dafe bango saidai taji ta dafa
hannun mutum. Da sauri ta dago idanunta ya
sauka akan kyakkyawar fuskarsa,taja baya bayan
ta sakeshi.
"Sorry." Ta furta murya na rawa,ya matso saitin
kunnenta ya soma magana
"Kina tsammanin sonki yasa na amince zan
aureki ne Tasleem? No! Lik'amin ke akayi,ni
kuma babu yanda na iya na kaucewa maganar
magabatana. Zahra itace zab'ina! Abar kaunata!
Zan aureki bisa kaddara kawai!"
Ta juyo da sauri, ganin numfashinsu na gogar
juna tayi azamar ja da baya tana kallon
fuskarsa,murmushin mugunta kawai yakeyi mata
a zahirin gaskiya kuwa daurewa kawai yayi domin
cin zarafin dan adam baya daga d'abi'arsa. Ya
daga mata gira yana murmushi
"Idan kinga zaki iya,muje zuwa toh..."
Daga haka ya wuceta ya fita ya fasa shiga dakin
ma. Kawai tayi ciki a guje takalmin da bata
sanyaba kenan...!!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(60)
Takai mintuna biyar kafin ta kammala saidai kuma jin yanda hayaniya da shewar murna ta cika dakin inna ya hana Tasleem fitowa yayin data kifa goshinta jikin kofar bandakin tana rusar kuka. Ta tabbata an daura aurenta da Haris akan sadaki dubu hamsin. Shikenan Haris ya samu damar wulakantata da cin zarafinta. Yan uwanta sun kasa fahimtar Haris ba kaunarta yakeyi ba. Ta bandakin tana jiyo muryar Baharu yana labarta musu cewar ai Haris ne ya nemi a daura auren a yanzu,Abba(alhaji Aliyu,mahaifinsa) yana fadan wane irin gaggawa ne haka? Liman yace hakan shine daidai tunda gashi an hadu domin har mijin Mamma,Dad yana wajen wanda shine ya zama wakilin tasleem aka daura auren kawai. Zahra ma an daura saidai an bar tarewar sai nan da wata daya bayan an kammala shirye shirye. Nan dakin ya dauki kabbara cike da sowar farin cikin jin wannan labari. Tana jin sadda d'iyar Dada(dada matar kanin Liman daya rasu take zaune gidan) wacce take zawarci sakamakon mijinta daya rasu da jimawa,wato Hafsa ta tahowa tana buga kofar tana fadin
"Fito kin kunshe kanki a bandaki,komin abunki fa sai mun murjeki da lalle." Aka kwashe da dariya kafin dai kowa ya tattara ya fice. Saida taji shiru sannan ta fito, ji tayi an rukunkumeta ana dariya
"Ja'ira,ai daman nace sai na ga fuskarki." Cewar Hafsat. Tasleem tana kuka tace
"Anti Hafsa kina kallo aka auramin wanda baya kaunata baya sona? Anya ba'a kwareni ba?"
Jikin Hafsa yayi sanyi,ta ja hannunta suka zauna bakin gado
"Haba Tasleem,kinga yanda yake rawar kafa da wasa da dariya kuwa? Anya zan amince baya sonki? Kodai kece bakya sonshi ne?"
Tasleem tayi shiru da kukan,toh tana da bakin cewa batason mutumin da tun zuwanta Kazaure dashi take kwana take tashi a zuciyarta? Tabbas tana son Haris. Banda Rilwan bata taba son wani d'a namiji ba da zuciya daya sai shi.
"Kinyi shiru?"
Inna dake jinsu tace
"Ki rabu da wannan sakaryar wacce batasan abunda ya dace gareta ba. Nikam takaicinta ma yana sanyani jin kamar na kwasheta da mari."
Hafsa taja hannun Tasleem sukayi hanyar fita zuwa dakinta tana fadin
"Ayi hakuri innarmu,kinsan sabon shiga."
Inna ta tabe baki suka nufi dakin Hafsat. Ita dinma rarrashi da ban baki gami da gwada mata hanyoyin kissosi da zata bi domin mallakar zuciyar Haris cikin sauki. Tasleem dai sauraronta kawai takeyi,wannan ba matsalarta bace,babu wani abu na fannin kissa da bata kware dashi ba saidai Hafsa ta gaza fahimtar matsalarta. Ita fa kalaman da Haris keyi mata ne yake daukar hankalinta.
"Nan zuwa sati biyu za'a kawo lefenku. Aurensa dake aka soma d'aurawa sannan kuma da Zahra. Kinga kenan matsayinki ta babba dole saikinyi hakuri kin rike girmanki koda dai Zahra bata da raini yarinyar akwai hankali da nutsuwa ba kamar su Atika ba. Duk da haka sai kin dage."
Haka dai sukayita hirarsu har Hafsat take bata labarin zaman hakurin da tayi da facalolinta wanda yasa Tasleem sakewa sosai. Sallamar Musty ta katsesu. Ya shigo suka hada ido da Tasleem yayi mata murmushi a sanyaye
"Babana ya akayi?" Cewar anti Hafsa kasancewar sunan kanin Liman yaci kuma mahaifi gareta. Hakanan mustapha jikan Dada ne mahaifiyarta sannan shi din maraya ne gaba da baya a hannun Dada ya girma har zuwa aurensa da Farida.
Ya zauna saman hannun kujera yana yamutsa fuska
"Ina fa lafiya kuna ji kuna gani an kwacemin matata." Duk suka dubeshi Tasleem kuwa saita dauki abun wasa ashe Antin ma wasa ta dauka jin tayi dariya tace
"Me zatayi dakai yarinya yar birni.?"
Ta fice daga dakin,Tasleem ta gaidashi yak'i amsawa
"Small ashe zaki iya auren wani ba ni ba?"
A mamakince ta yamutsa fuska kadan kamar bazatayi magana ba sai kuma tayita tamkar bataso
"Wai daman kana sona ne yaya?"
Musty ya ciji lebbansa cike da takaici
"Tun kina secondary nake dawainiya da sonki. Allah bai kaddaro ke zam fara aure ba sai Farida. Yanzu kuma gashi ina murnar dama tazo min sai kawai na tsinci labarin aurenki da wannan gayen."
Ya danyi shiru itama tausayinsa takeji,
"Haka Allah Ya kaddaromin. Allah Ya baki zaman lafiya da mijinki. Saidai ina fushi har yau gashi satinki daya cif a garin nan baki tako kinga matata ba shiyasa nima duk da dokin ganinki da takeyi domin ina yawan bata labarin sister dita mai sona amma na hanata zuwa."
Ya karashe a wasance,itama ta share wancan zancen watakila dai ya tuna a yanzun matar aure ce,
"Kayi hakuri dai yaya mustyna,zan shigo."
"Ai na mantaa yanzun saida iznin oganki ko?"
Gabanta ya fadi,ashe yanzu komai zatayi saida iznin Haris? Tab ai kuwa ta gwammace tayi ta zaman gidan gashi tana matukar son komawa wajen mahaifiyarta domin ta kara neman afuwarta.
"Bari na wuce."
Ya maidota daga kogin tunanin data shiga,ta dubeshi har yakai kofa
"Toh yaya saida safe." Itama ta mike ta koma dakin inna. Sallar isha'i kawai tayi kafin tayi zaman hira da inna. Sai ga Liman ya aiko kiranta. Ta iskeshi babu kowa a dakin sai shi. Nan yayi mata doguwar nasiha akan aure da nuna mata ita din yanzu fa karkashin ikon Haris take sannan ya gargadeta data dunga mutunta shigarta. A karshe ya damka mata sadakinta tace ita yanzu bata da abunda zatayi dashi,ya adana mata. Yace shikenan. Ta mike ta fita, zatayi ciki taji muryar Baharu a bayanta yana kiranta dole ta tsaya ta dubeshi ta lura dai d'asawa yakeyi da Haris sosai. Leda ya mik'omata yana dariya
"Gashi inji maigidanki."
Ita kam duk sadda aka dangantata da Haris sai gabanta ya fadi,tasa hannu ta karba babu ko godiya tayi ciki.
Waya ce da chajinta da komai,sai kwalinta da alama harda sim. Blackberry ce. Sai kayan ciye ciye, nan inna ta hau duddubasu tana fadin oh,abun dadi basu karewa a duniya. Wayar tayi k'arar shigowar sak'o. Ta bude ganin lamba.
"Ga waya nan,ban amince ki bawa kowane namiji damar mallakarta ba ke daidai da dan uwanki banda Abdullah banason ganin lambar kowaye!
"Harith"
Ta tabe baki ai shi d'inma bazaici darajar saving number nasa ba a wayar. Ta ajiye wayar ta mike domin watsawa kanta ruwa haka dai inna ta dauka tayita kalle kallenta tana fadin yanda wayar ta burgeta kwarai.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(59)
Cikin fushi inna ta ture tasleem daga jikinta
"Ke ni matsamin kibani wuri shashashar banza kawai! Aure hauka ne? Don za'ayi maki gata ke kuma kin kasa fahimta? Toh wallahi ba baki zanyi maki ba Tasleem,amma matukar kika bari batun auren nan naku ya rushe da yaron nan zaiyi wuya ki samu madadinsa. Ke kamar wata yarinya karama,a hakan ake cewa kinyi degree? Amma tabbas bakiyi kama da matan jami'a ba sam sam baki da wayewa. Mts. (Hhhh kuji fa! Baby ake fadawa duniya..cewar Rufaidarh)
Ta dago ta dubi inna dake faman zazzaga masifa
"Shi da bakinsa fa yace baya sona lik'a mi.."
"Kina nufin Liman k'arya yayi maki?"
Ita dai batace uffan ba,ai sai fadan inna ya k'aru karshe tace bazata iya ba saita had'ata da mamma. Sai kuma tayi shiru kafin ta kara cewa
"Allah Ya kyauta,namanta ashe ita dinma daren jiya tazo tana surutanta wai don me za'a yiwa Harisu haka? Saida na zageta tsaf na nuna mata kurenta sannan tace shikenan. Haka kawai kunbi kun tsani yaro na arziki ma."
Haka dai inna ta mike ta fice bayan ta dauki furar data kammala damunsa zata bayar a mik'awa bak'i.
Baby ringingine ta kwanta ta lumshe ido yayinda kwakwalwarta ke k'ara tunano mata bakaken maganganun Haris daya jefa mata. Zarginta ya tabbata kenan ba sonta yakeyi ba? Zahra,Zahra? Wacece ma hakan?
'Yar farar yarinyar nan dai siririya mai siririyar fuska. Kallo daya zakayi musu ita da Haris ka tabbatar da cewar jini d'aya suke saboda matukar d'ibar kamar da sukeyi da juna. Bata da mazauna sosai hakanan kirjinta baida cika sosai.
Tabbas ta tuno Zahra, itace dai wacce tayi mata rakiya gidansu KB. Murmushi kawai tasleem tayi tunawa da sanyin halinta. Babu ruwanta watakila shine dalilin da yasa Haris ke sonta. Kaico da rayuwarta,ita kam ba abun ta samu su Baffa ba tace bata kaunar auren nan.
"Taso kije Harisu ya aiko kiranki."
Ta bude idanuwanta sosai jin muryar inna. A sanyaye ta mike,ita fa batasan dalilin da yasa take shakkar Haris ba,kai bata taba kawowa bama zataji tsoron wani d'a namiji ba sai Haris.
"Don Allah ki mutuntashi babu kyau wulakanta mutum."
Murmushi tayi mai ciwo,ta mike ta dauki mayafinta ta fita bayan ta zura silifas. Ta nufi zauren saidai bayanan,ta karasa waje gabanta na dukan tara tara. Hon da taji ya tabbatar mata cikin motarsa yake, hakan yasa ta karasa kafin ta bude ta shiga. Bazata mance motar nan ba a tarihin rayuwarta,motar data fayyacewa Haris komai na sirrin rayuwarta?
"Baki iya gaisuwa bane ko kuwa dai rashin tarbiyya zaki gwadamin?"
Ta kalleshi
"Haris wai menayi maka hakane? Haris ka chanja ba haka...."
Kallon daya watsa mata shi ya sanyata yin shiru.
"Ba wannan na tambayeki malama."
"Barka da yamma."
Ya tabe baki kadan
"Rike abinki tunda rok'a nayi. Abunda nakeson sani shine,kinga period naki?"
Ta kauda kanta ga barin kallonsa