Showing 6001 words to 9000 words out of 60852 words
Chapter 3 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
a rayuwarta. Ta tsaya kyam tana dubansa bata ko iya bud'e bakinta ba. Jin tayi shiru ne yasa shi juyowa a fusace ya karasa hawa matattakalar baiyi wata wata ba ya d'aga hannu da niyyar marinta,sai lokacin ta iya karfin halin rike hannunshi. Kallon juna sukeyi ido cikin ido,wani kwarjini yakeyi mata wanda ya hanata yin magana cikin tsiwa. Ta saki hannunshi ta kauda idanuwanta fuskarta a daure
"Ganganci ne tab'a lafiyata,gaba ka kiyaye."
Ta ja baya ta janye kafafuwanta daga matattakalar zuwa sama. Ya zamana matattakala uku ce tsakaninsu,ta tsuke baki kafin ta kad'a idanuwa ta k'ara dubanshi,har lokacin kallonta yakeyi saidai cike yake da mamakin karfin halinta,ganin yanda ta iya rike hannunsa da nufin dakatar dashi.
"Game da tambayar da kayi,ka tambayi kb. Inaga shine yafi cancanta ya baka wannan amsar ko?"
Ta k'arashe tana mai murmusawa,daga haka ta juya ta tafi. Haris na tsaye har saida ta b'acewa ganinsa,ransa idan yayi dubu toh ya b'aci. Ashe har yanzu Kabir bai bar neman mata ba? Ya rasa irin wannan akuyanci na Kb,menene amfanin auren nasa toh? Tsananin tausayin Yasmeen ya turnukeshi. Saidai ya rantse bazai tafi ya bar tsinanniyar karuwar nan a gidanta na sunnah ba,dole ta fice yanzu kuwa!
Gama tunaninsa keda wuya ya nufi hanyar data bi a fusace,saidai kuma tunanin da yayi na watakila a wannan lokacin tana shiryawa ne,ya sanyashi tsayawa a falon gami da samun waje ya zauna. Layin wayar Kb ya shiga nema......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(10)
"Assalamu alaikum warahmatullahu wabarakatuhu."
Cikikkayiyar sallamar da a yau ta fito daga bakin Kb kenan,wanda ya k'ara nuna tsantsar rashin gaskiyarsa. Tunda dai a sanin da Haris ya yiwa aminin nashi,baya taba cika sallama haka tun suna k'ananu sai idan yana cikin firgici.
Dariya taso kubcewa Amadu maigadi,yayi saurin tosheta. Harara kb ya watsa mishi da sauri ya sauke jakar ya fice.
Haris ya amsa ciki ciki,har kb ya iso ya zauna kallonshi kawai yakeyi cike da tsabar bakin ciki. Tun kafin Kb yakai ga cewa komai ya tareshi
"Ka bani mamaki Kb,abune da koda ace za'a tareni acemin baka bar aikatawa ba zance karya akeyi. Karuwa fa!! A gidan da kake raya sunnar ma'aiki?!!! Da sunan kana da aure? Ka gayamin wane jin dadi ne a bibiyar kazaman matan nan da har yau ka kasa russuna?! Ya kake tsammanin su Daddy zasu dauki wannan zancen?"
Haris ya dakata,kallo d'aya zakayi mishi ka gane yana cikin tsananin bacin rai,wannan farin fatar tashi ta fuska ta chanja launi zuwa ja,hakanan kwayar idanunsa. Ya numfasa
"A ture maganar iyayenmu,me zaka cewa Mahaliccinka akan wannan d'anyen aikin da kakeyi na aikata zina? Baka tsoron mutuwa ta riskeka a wannan yanayin Kabir? Inace Ubangiji Ya halatta mana auren mata hud'u idan har zamuyu adalci? Why not ka nemi wata ka aura tunda mace daya bazata iya kashe maka kishirwarka ba. Amma wannan(yayi nuni da matattakala) ba alheri bace gareka face halakarka.!!"
Kb wanda tsananin kunyar Haris ta mamayeshi,yana ganin tamkar Yasmeen ce a gabanshi. Ya runtse ido kafin ya bude cikin sassanyar murya na rashin gaskiya
"Hakane,nasan ban kyauta ba. In sha Allah daga yau bazaka k'ara kamani da laifi makamancin wannan ba. Na amsa laifina,babu shakka bakayi karya ba duk abunda ka fad'a na aikatashi. Kayi hakuri,don Allah ka rufamin asiri a matsayinka na dan uwana kuma amini...."
"Its ok,baka da matsala dani Kabir,fatana ka gyara tsakaninka da Ubangijinka. Abu na gaba,yarinyar nan tazo ta fice yanzu yanzun please."
Kai da kaga yanayin fuskar Haris kasan yana tsananin kyamarta. Kyakkyawar matashiyar budurwa saidai fa kyawun dan maciji ne.
Shi kuwa Kb,mikewa yayi ya nufi saman gami da jin dadin cewa Baby batayi fushi tabar gidansa ba.
Tana zaune taga mutum tsaye a kanta,ganin kb ya sanyata mikewa tana murmushin jin dadin ganinshi,bai ankara ba har takai ga rungumeshi. Kamshin jikinta da taushin fatarta,ya mantar da kb dukkan wasu nasihu na Haris. Sai yaji sam bazai iya rabuwa da Baby ba,tun haduwarsa da Baby,baya iya hada shimfida da kowace Yar Bariki sai ita. Yasmeen ma,gudun kada takai korafi ga iyayensu ya sanya yake mu'amala da ita. Ta dago ta sumbaci lebbansa har lokacin da murmushi dauke a fatar bakinta. Baisan lokacin da shima ya sakar mata murmushin ba. Ta fidda earpiece daga kunnenta,ta zuba mishi shanyayyun idanuwanta kafin daddad'an sautin muryarta ya ratsa cikin kunnuwansa
"Welcome back my dear."
Ya riko hannuwanta cikin nashi salon kallon,ji yakeyi nan duniya bashi da farin ciki sama da Baby. A shirye yake ya aureta idan har hakan zaisa ya dauwama tare da ita bata haramtacciyar hanyar da za'a gani a rabasu ba.
"Thank you my baby,hankalina a tashe yake."
Ta janye jikinta tana murmushi kafin ta nufi hanyar sauka k'asa
"Daukomin handbag dina, kada ka damu na fahimci matsalar."
Yayi mamakin yanda akayi ta fahimceshi sosai har haka. Cikin jin dadi ya shige dakin,ya dauki harda mukullin motarta.
Haris dake zaune yana jiran fitowarsu,suka dubi juna,ta sakarmishi murmushinta mai burgewa saidai ko kad'an bata burge Haris ba. Ta zagaya ta bayan kujerar da yake,daidai saitin kunnenshi ta furta
"Sai had'uwa ta biyu."
Daga haka tayi gaba cikin takunta na jin ta isa. Mamaki ya sanya Haris binta da kallo. Amma ta tabbata Baby tsohuwar 'YAR BARIKI ce, ya kauda kansa yana takaicin yanda mace kyakkyawa har haka ta b'ata wayonta. Son duniya ya sanya tana siyarda jikinta ga wanda ya isa da wanda baima isan ba. Tunaninsa ya tsaya sa'ilin da abokin nashi ya taho da sauri rike da jaka da mukullin mota. Ya zuba mishi ido yana duban ikon Allah,Kb ya tsuke fuska
"Mantuwa tayi,banason komai nata ya rage a gidana domin daga yau na barta kenan."
Shi dai Haris baice komai ba,fuska a daure. Kb ya fita a fusace wanda zaka rantse zancensa har zuci ne.
Yayi ta hangen inda Baby ta shiga, hon yaji. Ya juya ga daya daga cikin motocinsa,hantar cikinsa ta kad'a. Wannan ma fa wata matsalar ce, ta yaya zata shiga motarsa? Ya dubi hanyar gidansa,Haris bai fito ba,da gudu gudu ya isa bakin motar. Fuskarta a daure kai ka rantse bata tab'a dariya ba.....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(09)
Ringing uku ana hud'u,Kb ya d'aga.
"Yadai mutumin? Kana ina ne kazo ka daukeni a airport. Allah Yayi zuwana bisa neman da Abbana(Alhaji Aliyu) ke yimin akan harkokinmu."
Haris ya runtse ido cikin jin haushin Kb,dakyar ya iya dannewa yace
"Banajin zan iya zuwa,ina gidan naka yanzu haka tare da matarka wacce bamu da masaniyar sadda kuka kullawa junanku aure. Kana iya shigowa taxi kazo ka samemu."
Daga haka ya kashe wayar,a bangaren Kb kuwa,hankalinsa idan yakai dubu toh fa ya gama tashi. Kada dai baby ce? Ya salam! Yanzu menene abunyi?"
Ya lalubi lambar Baby ya danna kira.
Ta kammala shiryawa cikin riga da wando gajera marasa nauyi,ta kunna karan sigari ta soma zuk'a hankali kwance kafin ta sanya earpiece a kunnenta tana shirin danno wak'a ne kiran Kb ya shigo wayarta. Murmushi ta saki kafin ta d'aga alokacin data nufi falo.
Kafin takai ga cewa wani abu,Kb ya soma magana
"Babyna kina ina?"
Daidai lokacin ta fito falon,lokaci d'aya suka dubi juna dashi,ta dauke kanta ta nufi kicin.
"Ina gidanka,wani abu?"
Ya zaro ido,hantar cikinsa ta kad'a
"Baki ga wani bak'o ba da yazo?"
Daidai lokacin ta fito dauke da glasscup tayi hanyar firij,
"Gashinan zaune,da alama baisan wacece ni gareka ba ko?"
Kb ya dafa goshi,ya rasa ta inda zai b'ullo. Ashe a gaban Haris take magana dashi?
"Look,he's my bestfriend. Please kada ki sanar mishi komai dangane da relationship dinmu dake kin fahimta? Gani a airport,na iso Kano. Yanzu zan zo gidan."
Ta tab'e baki,daidai lokacin ya kashe wayar. Ita kuwa freshmilk ta tsiyaya ta koma ta zauna a kujerar dake kallon Haris. Kurb'a takeyi tana duban fuskarsa yanda duk yabi yayi kicin kicin tamkar ya tashi ya rufeta da duka. Saida tayi kurba uku kafin ta ajiye ta cire earpiece dake kunnenta.
"Nice meeting you."
Ta fad'i a tausashe. Bakin ciki ya sanyashi watsa mata kallon da taga ya k'ara fiddo kyawunsa zallah. Murmushi ta sakar mishi kafin ta d'ora tafin k'afa d'aya akan kujerar da take zaune
"Fuskarka ya nuna baka son ganina."
Ta tabe baki inda ta k'ara zuk'ar sigari ta fesar da hayak'in.
"Abun mamaki,bamu tab'a had'uwa ba sai yau. Ban fiye kaunar naga mutum yana kuntata rayuwarsa ba musamman akan abunda ba matsalarsa...."
Tashin da yayi ya hanata k'arasa zancenta. Dubanta yayi cike da tsana,ya soma tafiya saidai ya tsaya cak ya juyo
"Da gaskiyarki,ban sanki ba,asalima yau na tab'a ganinki a inda bai cancanci ace kina nan ba. A matsayinki kuma na kilaki. So,as you said,bake zaki bani amsar kowacce tambayata ba. Ke kuma kiyi hankali da kazantacciyar rayuwar da kike ciki,na lura baki da damuwa ko kuma d'igon bakin cikin wannan rayuwa taki. Saidai fa..."
Ya dubeta,sai lokacin ya sakar mata murmushi wanda daga gani kasan na yak'e ne
"Akwai ranar k'in dillanci."
Daga haka ya sauka zuwa falon k'asa domin jiran aminin nashi.
Ta maido dubanta ga falon,ta lumshe ido tana murmushi
"He's very handsome,saidai ba wayewa."
Ta furta cikin zazzak'ar muryarta,bata ko damu da kalamansa ba ta maida earpiece dinta ta kunna wak'a abinta tana kurb'ar lemo,a gefe kuma zuk'ar taba.
*******
Taxi yana tsayawa,kb ya biyashi ya fito. Da azama Maigadinsa ya iso a guje yana kokarin karb'ar akwatin hannunsa. Kyakkyawan mari yayi mishi a kunci,kafin ya soma magana a fusace
"Don ubanka wace doka na sanya maka?!!! Bance maka idan bana gari ba,banda baby kada kabar kowa ya shigomin gida ba?!!"
Matashin maigadi wanda yaci suna Amadu,yana rike da fuskarsa ya russuna cike da girmamawa
"Kayi hakuri yallabai,wallahi ina fama da ciwon ciki shine na lek'a kemis bansan da zuwan Madam ba."
"Mts!"
Kb yaja tsaki yayi gaba,da azama Amadu ya ciccib'i akwatinsa jiki yana rawa yabi bayanshi bayan ya watsawa Ado maigadin makwaftansu kallon baka kyautamin ba.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(11)
"Babyna wannan motar kuma?"
Ta dubeshi
"Nufinka na sauka na baka abarka?"
Yayi azamar dakatar da ita
"No,bance ba. Saidai kinga Haris zai iya d'ago..."
Ta soma kiciniyar bud'e mota, yayi saurin dakatar da ita.
"Haba babyna,please ni bance ki sauka ba. Ga handbag dinki,daga baya zanzo gidan please. Kada kiyi fushi dani."
Sai lokacin ta sakar mishi murmushi na gefen kumatu
"Ko kaifa."
Daga haka ya matsa tayi ribas,tuni Amadu ya bud'e mata k'ofa ta fice.
Kb ya dawo da hankalinsa akan motar Baby,dabara ta fad'o mishi,ya sami k'usa ya sace taya d'aya kafin ya mike. Ido hudu sukayi da Haris wanda fitowarsa kenan,ya dubi motar kafin ya nufi tasa a fusace ya hau kokarin budewa. Kb ya isa da sauri ya riko hannunsa
"Don Allah kada kayimin gurguwar fahimta mana,tayar motarta d'aya ne ya sace shine dalilin daukar tawa da tayi. Amma idan an gyara zan aika mata sai a karb'omin tawa. Kada.."
"Ya isa Kabir,gyara kuma ya rage tsakaninka da Mahaliccinka. Shi yafi cancanta ka tsorata ba kowa ba. Kayi tunani da ka haihu,baka gudun ace yau diyarka ce cikin wannan..."
"Haris please! Banason wannan irin zantukan! Ya wuce,na fadamaka kaddara ce yasa nake kula wannan d'inma amma nayi maka alk'awarin daga yau ta k'are. Don Allah ka rufamin asiri."
Ya tabe baki gami da daga kafad'a
"Ka tsaya mana muyi sallah,nasan ko magrib bakayi ba. Gashi kafin ka kai gida nasan anyi isha'i."
Sanin da yayi haka dinne,ya sanyashi dakatawa. Sukayi sallah,sannan ya wuce.
******
Tun komawarsa gidansa,tunani da matsanancin tausayin kanwarsa Yasmeen sun hanashi sakat. Har lokacin surar yarinyar ya kasa b'aceqa daga idanuwansa,ba don komai ba saboda tsanarta da yakeji tare da mamakin karfin hali irin na karuwan mata masu maida gidan wani nasu. Kodayake dai babban laifin yana ga Kb wanda har ya iya bata wannan fuskar. Zina fa!! Wai ma menene abun dadi da tunkaho a cikinta?!! Me Kb yakeji idan ya tafka irin wannan sab'on? A gefe d'aya ga Yasmeen,a yanda yasan kanwarsa,yarinya ce mai hakuri da halayen mijinta. Tabbas bata boyemishi dukkan sirrukanta tun tana budurwa ma. Dukkan abunda hankali zai dauka na neman shawara,daidai da wanda ya dace ya sani takan sanarmishi ta waya. Ko kuma idan yaje su kwashi fin awa suna hira. Duk da ba gida d'aya suka taso da Yasmeen ba,sun shaku sosai dashi.
Idanunsa suka kad'a sukayi jazur,hakikanin gaskiya,ko kusa kanwarsa batayi sa'ar miji ba. Manemin mata wanda har yake zargin yana shaye shaye. Duk da har zuwa yanzu bai taba kamashi dumu dumu cikin mayen ba saidai ganin yanda neman matan nasa yayi yawa yasa ya soma gaskata komai akace kb yayi zai aminta da haka.
K'arar wayarsa ce ta katse mishi tunani,dakyar ya lalubota ya duba mai kiran. Yasmeen dince. Murmushi ya saki wanda yafi kuka ciwo,kafin ya daga. Tun kan yace wani abu,ta soma magana cikin farin ciki
"Yayana kasan wani abun mamaki kuwa? Au,Assalamu alaikum,yayana barka da dare."
Nan da nan ransa ya danyi sanyi jin cewar kanwarsa tana cikin farin ciki. Cikin tattausar muryarsa ya amsa sallamar ya d'ora da fad'in
"Fadamin da sauri little,bazan iya jira na wani lokaci ba."
Tayi dariya mai nuni da tana cikin farin ciki
"Wallahi yayana wannan zuwan naga chanji sosai a wajen Prince..."
"Me yayi maki?!! Gayamin ko menene?!!!"
Ta danyi shiru kad'an jin ya fusato,a sanyaye tace
"Cool down yayana,bafa wani abu yayimin na bacin rai ba. Kawai dai umm...mun dawo tamkar new couples."
Ta karashe tana dariya kasa kasa,ya lumshe ido yana mai sauke ajiyar zuciya.
"Alhamdulillah little, burina na ganki cikin kwanciyar hankali. Ina diyata?"
"Allah Sarki yayana,nima farin cikinka shine nawa. Ai bansan ya zanyi ba idan aurenka yazo don murna."
Murmushi yayi wanda bai shirya mishi ba,ita kam Yasmeen bata gajiya da tunasar dashi batun aure sai kace wani karamin yaro. Ya shafi sumar fuskarsa
"Zanyi,lokaci ne baiyi ba little. Ki tayani addu'a. Baki amsamin tambayata ba."
"Oh,nasreen tayi bacci. Ai yanzu muka gama waya da babanta yace min ma Monday zai juyo da safe."
"Kabir kenan."
Ya fad'a a zuci,don ya fahimci ba karamin razana yayi ba yau.
A fili kuwa ya amsa da ok.
"Bari na kyaleka kaji da gajiyar ofis. Bye."
Sukayi sallama ya ajiye wayar. Tausayin kanwarsa ya k'aru a zuciyarsa,tabbas har yanzu batasan waye Kb ba,kuma baya fatan tasan wannan boyayyen al'amarin,daidai da iyayensu baiso zancen yaje wurinsu. Shi kam,sai inda karfinsa ya k'are akan ganin rayuwar amininsa kuma dan uwansa ya daidaita.....!
*****
Misalin (1:00am) na dare......
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(12)
Kwance suke a dakinta kan makeken gadonta,tayi
matashi da cinyarsa.
"Babyna."
Ba tare data amsa ba ta dago idanuwanta
lumsassu ta dubeshi,ya sanya hannu yana wasa
da girarta kafin yace
"Inason muyi wata magana ne."
Batace komai ba,sai kallo da take binsa
dashi,wannan ya bawa Kb damar cigaba da
zancensa.
"Kinga dai a yanzu babu damar haduwa a gidan
ko? Sannan yanzu idanun Haris a kaina yake na
tabbatar bai gamsu cewar na rabu dake da gaske
ba."
Ya danyi shiru kamar mai nazari,kafin ya riko
hannunta yana cigaba da duban kwayar idanunta
masu k'ara dulmiyar dashi kogin kaunarta.
"Abu ne da bazan taba iya aikatawa ba,saidai
zuwa yanzu ina tsoron kada Haris yakai k'arata
wajen iyayenmu....."
"Menene dangantakarku da guy dinnan ne? Na
lura ka bashi matsayi da yawa a rayuwarka KB."
Baby ta katseshi ta hanyar jefo mishi wannan
tambayar. Murmushi yayi ya shafi gashin dokin
dake kanta wanda sai yace shi dai tunda yasan
baby bai taba ganin