Showing 9001 words to 12000 words out of 60852 words
Chapter 4 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
iyakar jelar gashinta
ba,baisani ba tana da yawan gashin ko babu.
"Haris Aliyu kenan,iyayenmu aminan juna
ne,wannan yasa mukayi sabo dashi sosai fiye da
tunanin mai tunani. Ya kasance dan uwana
wanda bama boyewa juna sirri. Nan da kike
ganinsa ustaz ne,ya fiye takura kansa baison ya
more rayuwarsa."
Kb ya dan tabe baki kafin ya cigaba
"Abunda zai baki mamaki ma,har yau bai taba
sanin diya mace ba sannan har zuwa yanzu yak'i
aure a cewarsa gareni,baiga wacce tayi mishi
bane."
Baby ta lumshe ido kafin ta muskuta ta juyawa
Kb baya
"Karancin wayewa ke damunsa,saidai kasan wani
abu? Da ace nice kai babu wanda ya isa hanani
yin abunda nake ra'ayinsa. Kaban mamaki KB,
akan wannan guy din saika rabu dani."
"No baby,ni wanene da zan bar mace irinki?
Wannan karya ne. Shiyasa na samo mana
mafita,kawai ki nutsu ki saurareni please."
Har lokacin idanuwanta a rufe suke,haka kawai
take tsintar kanta da tunano kyakkyawar halittar
fuskar HARIS,
"Ina sauraronka."
"Zaki aureni Tasleem?"
Cikin matukar razana ta bude idanuwanta,kafin ta
mike zaune tana duban kwayar idanuwan
Kabir,kwarai babu alamun wasa a abunda yace.
Gabanta ya shiga faduwa haka kawai,yayi azamar
matsowa ya riko hab'anta
"Wallahi Tasleem zan iya aurenki,babu kyankyami
ko wani abu. Sonki nakeyi,bazaki gane yanda na
shaku da soyayyarki..."
Ta cire hannunshi ta juya mishi baya gami da
sauke kafarta akan gadon,har lokacin bugun
zuciyarta bai daidaita ba
"Na gayamaka tun a farkon mu'amalarmu kafin
muyi nisa haka. Kamar yanda ka taba zuwarmin
da batu irin wannan a yanzun ma amsar d'aya
ce,bazan iya aurenka ba."
Kb hankalinshi ya tashi,kaunarta na kara karfi a
zuciyarsa. Zuwa yanzu ya amincewa kansa lallai
ba sha'awa kawai yake yiwa Baby tasleem
ba,harda soyayya. Hannunta cikin nasa,yayinda
kalar kwayar idanunsa suka sauya launi saboda
tsabar tashin hankali na jin maganar dake dake
fitowa a bakin baby.
"Me kikeso a rayuwa wanda har yanzu baki samu
ba? Wallahi ki fad'amin ko menene shi zan
mallaka maki Tasleem dan har zaki yarda na
killaceki a gidana ya zamana ni kadai nake da
hakki akanki. Ya zamana kinbar mu'amala da
kowa. Wallahi tasleem zan iya mallaka maki
dukkanin dukiyata matukar hakan zaisa ki amince
dani matsayin mijinki. Please ki....."
Ta mike a fusace
"Ya isheni Kb!!!!"
Ta dakatar dashi kafin ta watsa mishi duban da
tunda suke tare bata taba yi mishi ba. Duba ne na
raini da wulakanci,
"Bazaka taba samun biyan bukatar nan ba. Na
tsani aure! Bazan taba yinshi ba!! Babu komai a
rayuwar aure sai tozarci da wulakanci! Wannan
ikrarin da kakeyi na kana sona,zai tafi da zarar na
kasance matarka."
Kb ya nufeta da niyyar rikowa tayi azamar
dakatar dashi ta hanyar daga mishi hannu. Daga
haka ta fice da gudu tabar dakin. Bata shige
ko'ina ba sai d'akin Dalal ta sanya mukulli jikin
kofar ta rufe. Kuka takeyi sosai wanda ya tada
hankalin kb dake tsaye daga waje yana jiyo
sautin kukan nata.
"Please baby i'm sorry,indai maganar aure ne
bazan k'ara yi maki ba."
Ita kuwa baby,ita kadai tasan me me kalmar aure
yake tunano mata.
Daren babu wanda yayi kwanan farin ciki a
cikinsu.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(13)
Kukan da Baby tasha a wannan daren ne ya sanya ta tashi da matsanancin ciwon kai. Bata fito daga d'akin nan ba saida tayo sallar asubahi ta kara kwanciya bacci,a takaice dai saida rana ta fito. Ta bud'e kofa ta fito,falon babu kowa kamar yanda tayi zato,Kb ya tafi. Ko a kanta bata damu ba,ita kam idan har zancen aure ne bazai tab'a samun goyon bayanta ba. Tabbas saidai alak'arsu ta yanke anan.
Kai tsaye dakinta ta nufa,tsayawa tayi cak,ganin Kb kwance yana bacci bayan ya rungume hotonta dake ajiye gefen gadon. A hankali ta karasa ta durkusa saitin fuskarsa tana duba,murmushi dauke akan fuskarta. Lallai ba karamin so Kb yake yi mata ba,duk da cewar nata zuciyar ba wani sonshi takeyi ba sosai. Tafi daukarshi a matsayin mai biya bukatarta. A hankali ta mike ba tare da tayi yunkurin tashinsa ba. Wanka kawai ta fad'a. Bayan ta fito ta iske har lokacin kb bai farka ba,mamaki ya kamata. Kodai baiyi bacci bane daren jiya. A sannu isa gefen gadon ta zauna kafin ta jijjiga gashinta,ruwa ya fallatsar mishi a fuska. Sannu sannu ya bude ido,kafin yakai ga cewa wani abu ta mike da sauri ta koma gaban madubi
"Ya kamata ka tafi gida kafin ustaz din naka ya nemeka."
Ta karashe tana murmushi,kb ya taso ya janyota ta mike tsaye suna fuskantar juna. A karshe ya zaunar da ita gefen gado shima ya zauna. Yanda ya karanceta ko kusa bata da fushi sosai,tana da saurin hucewa,(hum).
"Na bata ranki Babyna,amma daga yau nabar zancen nan tunda har bakiso,kinji?"
Tayi murmushi kafin ta sauya salon zancen nasu. KB bai bar gidan ba sai wajen goman safe,ya k'ara tabbatarwa kansa bazai iya rabuwa da Baby ba. Ta musamman ce. Cike da nishadi ya koma gidansa.
*****
Dattijai ne guda biyu masu kimanin shekaru Sittin da d'oriya,suna zaune a kayataccen falon gidan. Kowannensu ya sha babbar riga suna hira cikin nishad'i. Lokaci guda kuma fuskar Alhaji Idris ta sauya zuwa yanayin damuwa. Wannan yasa Alhaji Aliyu tsagaita dariya ya dubeshi
"Lafiya kuwa?"
Alhaji Idris ya sauke ajiyar zuciya
"Wallahi lamarin Harisu ya soma tsoratani Alhaji. Ace yaro yak'i zancen aure,har rana mai kama da yau ya kasa kawo mana zancen da zai sanyamu farin ciki? Babu ranar da bana rokon Allah,daidai da liman saida na sanarwa domin a taimaka mana da addu'a. Kaga fa har rukiyya anyi mishi a zatonmu aljanu ne saidai ko gezau babu. Anya tafiya zata yiwu haka?"
Alhaji Aliyu yayi murmushi
"Ka gafarceni Alhaji idris,zuwa yanzu na daina ganin laifin yaron nan nafi ganin laifinku na iyayensa."
Daddy ya dubi Abba da alamun rashin fahimtar maganarsa. Abba ya jinjina mishi kai
"Kwarai ma kuwa Alhaji Idris,wannan laifin bana d'anku bane,naku ne. Kada ka manta fa,yaron nan ba shine ya haifeku ba! Akan wane dalili ne zaku zuba mishi ido sai yanda yakeso za'ayi? Ga yan uwansa nan mata a Kazaure,wadanda sukayi karatun na addini dana zamanin don me bazaku samar mishi wata a can ba? Haba jama'a,yaron nan fa ba fin karfinmu yayi ba. Yau ga dan uwansa nan har ya soma tara zuri'a shi ya zauna jiran autar mata? A'a fa,gaskiya laifi yana wajenka Alhaji."
Daddy yayi murmushi
"Gadanga kenan,zamanin nan da kake gani ba'a yiwa yara auren dole,ba irin zamanin mu bane wanda ko fuskar matanmu bamu gani ba sai bayan an mik'o mana su gidajenmu. Wannan zamanin za'a kuntata rayuwar yaro ne kawai."
"Nima bance kuyi mishi dolen ba idi(ya fada cikin zolaya kasancewar sunan da yake kiranshi kenan a baya da kuma wasu lokutan na yanzu),ku turashi kuce yaje ya zab'a idan yaso sai ya sanar maku wacce ta kwanya mishi ko kuwa?"
Daddy yayi dariya
"Gaskiyane,sai ayi hakan toh. Fatanmu Allah Yasa mu dace."
Abba ya amsa da amin. Daga haka hira ta mik'a.......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar
(14)
Misalin karfe sha biyu da rabi na dare,baby tafe akan hanyarta na zuwa birthdayparty na Hibba da saurayinta ya had'a mata. Taci kwalliya har ta gaji da had'uwa. Kid'a ke tashi kawai a motar,saidai cak motar ta soma kokarin tsayawa. Karshe ta tsaya cak akan titin daya kasance shiru tamkar babu mutane sai tsilli tsillin motoci suke wucewa. Ta buga sitiyari da k'arfi ganin mai ne ya k'are mata. Shaf ta mance cewar Dalal ta ari motar taje kasuwa da ita dazu,gashi babu alamun masu siyarda mai a kusa. Wayarta ta dauko,ta kira lambar Hibba,yana ta ringing bata dauka ba. Hakanan Manal da Dalal. Ta tabbatar dukkansu hankulansu yana wajen party. Taja karamin tsaki kafin ta soma duban hanya taga ko zata samu mai taimakonta.
Tafe yake a hanyarsa ta komawa gida daga meeting da yayi (attending) na aikinsu. A gajiye yake saboda ya mance rabon da yakai war haka baiyi bacci ba. Hannu ya gani an sanya mishi ana tsayar dashi. Ya duba dakyau,mace ce,kuma da alama motarta ce ta sami matsala. Ba tare daya lura da ko wacece ba,ya samu waje ya faka domin shi ya dauka ma kabila ce duba da yanayin suturar dake jikinta na gown marar hannu ga kuma gashi a waje.
"Sannu,please ko..."
Sauran maganar ya makale a fatar bakinta ganin Haris. Shi kanshi baisan ita bace saida ya fito daga cikin motarsa suka nufo juna.
Zallar kyawun fuskarsa ta k'ara fitowa a lokacin daya tamketa,ya juya da niyyar komawa motarsa ya tafi. Tayi azamar tarar gabanshi,cikin marairaicewa tace
"Domin Allah ka tausayamin mana bestfriend,wallahi ka tafi ka barni anan za'a saceni ne. Man motata ya k'are ne."
Sai lokacin ya lura ashe harda hudin hanci gareta,ta maka barima fara akan hancin. Ganin yanda ta marairaice ne ya sanyashi kauda kansa,baice komai ba ya gifta ya shige motarsa. Har ta fidda ran cewa zai taimaketa taji yana mata hon. Cikin sauri ta dauki wayoyinta da fos dinta. Ta rufe gilasan motar ta kulleta ruf sannan ta nufi motar tasa. Sai lokacin hankalinta yakai ga lambar motar,nan da nan ta tunano inda ta santa. Ashe shine ya taba binta a guje sadda ta tuk'o motar Kb. Murmushi ta danyi kafin ta zagaya ta bud'e gaban motar ta shiga. Nan da nan kamshinsu ya mamaye motar, har suka rasa fahimtar na wanda yafi tashi.
"Nagode bestfriend."
"Haris sunana."
Ya fada cikin fusata. Ta dubeshi ganin yanda yayi kicin kicin,ta kad'a idanuwanta
"Ok,Haris."
"Ina zan kaiki?"
"Tahir."
Baisan sadda ya dubeta ba,itama har lokacin idanuwanta na kansa. Saidai baice komai ba ya fisgi motar a fusace,gudu yakeyi kamar zai tashi sama,baby kuwa ko a jikinta. To yau ya soma sanin gudu a mota ne? Kallonsa kawai takeyi cike da mamakin irin kyawu na Haris. Bayan haka ma,tafi mamakin yanda duk haduwarta ko kallo bata isheshi ba. Toh ita kuwa iyakar zamanta a rayuwa bata taba ganin namijin daya ganta bai kara kallo ba saboda zubin da halittar da Allah Yayi gareta.
Taka burki da yayi,ya maidota hayyacinta. Wannan ya sanyata kauda kanta daga barin kallonsa. Ta duba,kwarai sun iso kofar hotel din.
"Rayuwar da kika zab'awa kanki ina mai tabbatar maki akwai ranar k'in dillanci. Sam,wannan bai dace da musulma ba. Kin maida kanki kasuwar da kowa yake da damar shiga. Kin zubda k'imarki ta d'iya mace akan son duniya wanda bazai kwatoki daga azabar Allah da kwanciyar kabari ba. Kiyi tunani,matan aure nawa kika dauki hakkinsu wajen nasarar dauke hankulan mazajensu a kansu? Allah bazai kyaleki ba,da rai da lafiyarki muddin baki tuba ba sai kinga sakayya. Idan zina abun yi ce kije kiyi tayi,ke da karya baku da bambanci."
Yayi shiru yana mai duban titi,murya a kausashe ya kara magana
"Get out."
Kamar wacce aka daskarar,gaba daya ta gaza motsi. Bata ce mishi uffan ba. Jin tayi shiru ya sanyashi juyowa da niyyar fad'a,abun mamaki hawaye ya gani suna zuba daga kwayar idanun Baby. Tayi azamar sharesu,murmushi ta k'ak'alo ta jefeshi dashi
"Nagode da taimakon da kayi gareni,Allah Ya kaika gida lafiya."
Daga haka tayi saurin ficewa tayi ciki,saidai kana dubanta zaka fahimci a sanyaye take ko daga yanayin tafiyarta. Ko kadan bata bashi tausayi ba,saidai har ya tafi yana mamakin yanda akayi kalamansa suka sanyata hawaye. Karshe dai ya watsar a cewarsa,munafunci ne. Wanda yayi nisa bazai tab'a jin kira ba....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(15)
"Kiyi tunani,matan aure nawa kika dauki hakkinsu wajen nasarar dauke hankulan mazajensu a kansu? Allah bazai kyaleki ba,da rai da lafiyarki muddin baki tuba ba sai kinga sakayya."
Har zuwa yanzu da take kwance a gadon d'akin na hotel d'in,ita kad'ai. Wadannan kalaman ke yawo a kwakwalwarta. Damuwar da ta yawaita a zuciyarta ya hanata zuwa bangaren da ake fatin hibba,hakan yasa ta kama d'aki da zummar ta kwana da safe tayi gida. Batayi iya runtsawa ba kalaman Haris sun shigeta matuka. Ta tuno yanayin fuskarsa wanda ke nuni da tsantsar takaicinsa na halin da rayuwarta ke ciki. Bata taba cin karo da wanda ya nuna kyama a harkar rayuwarta ba kamar shi.
"Nan da kike ganinsa ustaz ne,ya fiye takura kansa baison ya more rayuwarsa."
Kalaman Kb akan Haris suka fad'o mata. Tabbas ta yarda da hakan,Haris kamilin mutum ne wanda bai sha'awar rayuwar da suke ganin itace ta arziki a garesu.
*****
Da zarar ya runtse ido,ita yake gani. Bai manta sa'adda ta dubeshi fuska dauke da ruwan hawaye wanda yasan na munafunci ne. Amma meyasa ta kasa b'acewa tunaninsa,bai manta sadda ta fice a motar ba jiki a sanyaye. Toh hakan yana nufin taji nasiharsa ne ko kuwa? Amma ai inda ace ta dauki zancensa,babu abunda zaisa ta shiga hotel d'in. Ya dafa goshinsa yana mai runtse ido,bayason ya dunga tunanin wacce bazata amfaneshi da komai ba. Hakan yasa ya mike tsam yayo alwala ya soma nafila duk domin kaucewa tunanin wacce ko sunanta bai sani ba.
******
"Gobe zan koma Abuja,inaso muyi wata magana ne."
Ya tsayar da rubuce rubucensa sannan ya dago fararen idanunsa ya saukesu akan Kb,fuska ba walwala.
"Na'am,ina sauraronka."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(16)
Kb ya numfasa yana mai sassauta muryarsa,ba tare daya yarda ya dubi kwayar idanun Haris ba ya soma magana
"Look Haris, nasan na aikata ba daidai ba. Nasan zuwa yanzu ka dauki zafi dani baka kaunar sanyani a idanuwanka ma,amma don Allah kayimin uzuri wallahi kaji na rantse maka babu macen da nake mu'amala da ita a waje idan ba Baby Tasleem ba."
"Baby Tasleem."
Haris ya nanata sunan a ransa,sai yau ma yasan sunanta. Kb ya cigaba da magana
"Nasan ban kyautawa Yasmeen ba kamar yanda ban kyautawa kaina ba. Gaskiyar magana rabuwa da Tasleem abune mai matukar wuya agareni,shiyasa na yanke shawarar zan aureta a matsayin matata ta sunna."
Wani mugun kallo da Haris ya watsa mishi ya sanyashi kauda kansa cikin jin nauyi,ya numfasa kafin ya cigaba
"Yes Haris, kabar yimin irin wannan duban,raya sunnah nakeson yi ba wai zina ba. Duk da dai zuwa yanzu Baby tak'i bani had'in kai,ta nunamin babu abunda ta tsana kamar aure,wannan shine hakikanin damuwata. A matsayinka na amini kuma d'an uwana don Allah ka taimakamin da shawara."
Ba tare da ya jira cewar Haris ba ya mike tsam ya nufi hanyar fita cikin jin nauyin amininsa. Saida yakai k'ofa sannan ya dakata ba tare da ya juyo ba
"Ba hakan dana fada yana nufin na rabu da soyayyar matata ba,a'a. Inason Yasmeen matuka saidai inason raya sunna. Idan har ka amince da bukatana,ka taimakeni kayi jihadi wajen shawomin kan Tasleem domin cetomu daga wannan rayuwa please Haris. Goodbye."
Ya fice cikin sauri ba tare da ya juyo ba ballantana ya lura da irin firgicin dake akan fuskar amininsa.
Rike kai yayi yana mai runtse ido,gabansa na duka da sauri da sauri. Aure?!! Tsakanin Kb da baby tasleem?!!
Ya nanata a zuciyarsa,kafin ya kwantar da kansa akan kujerar ya runtse ido. Toh menene matsalarsa? Me zaisa zancen nan ya dameshi? Amma kuma dole zai dameshi ai,ko babu komai,kanwarsa ce fa Kb ke shirin yiwa kishiya da karuwa! Dole yaji tsanar auren,dole ne ya taya 'yar uwarsa kishi. Kishi mai tsanani.
Ya bud'e ido,kafin ya hasko halittar Baby da wayewarta sannan ya dawo ga kanwarsa wacce baby bazata nunawa kyau ba saidai ta fita a halittar jiki da kuma barikanci. Ita d'in ta kasance saliha,domin ko a gida bata fiye magana mai tsawo ba,sam, bata da hayaniya tamkar Haris d'in take. Wannan yasa duk cikin kannensa yafi tausayinta yafi sonta tasu tafi zuwa d'aya. Anya kanwarsa zata iya kishi da gogaggiyar mace irin Tasleem?
"Idan har ka amince da bukatana,ka taimakeni kayi jihadi wajen shawomin kan Tasleem domin cetomu daga wannan rayuwa please Haris."
Ya tuno zancen Kb,wannan ya nuna kenan yayi kokarin shawo kan Tasleem domin ta amince da bukatarsa na suyi aure amma sam,tak'i aminta.
Haris ya girgiza kai cikin takaici da bacin rai
"Tabbas Kabir bashi da kunya."
Ya fad'a a fili. K'arar wayarsa ta katseshi,ya duba yaga sunan Daddy. Da sauri ya d'auka. Bayan sallama da gaisuwa ne Daddy ya sanar dashi ya shigo yazo ofishinsa yana nemansa. Ya amsa kafin ya tashi a hanzarce ya nufi ofishin director kuma uba a gareshi,Alhaji Idris.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(17)
Ya shiga da sallama. Daddy zaune akan kujerarsa sanye yake da riga 'yar ciki da wando ya rataye babbar rigar jikin (hanger). Idanunsa boye cikin farin gilashi. Ya bar danna laptop dinsa ya dago yana