Showing 45001 words to 48000 words out of 60852 words
Chapter 16 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
ta lura duk
takalma uku data zo dasu haka suke da tsinin dunduniya. Ta kasa
dai hakuri ta tofa
"Wai Tasleem baki tsoron wadannan takalman su karya maki
k'afa?"(Kamar dai yanda kawata Ummu Abdool ta sanya ta fad'i
cikin taron mutane koda yake farkon zuwanta birni ne👌)
Baby tayi murmushi
"Inna ai na rigaya na saba,inajin dadinsu sosai."
Inna ta tabe baki
"Oh,duk wannan tsawon naki neman k'ari kikeyi. Toh Allah Ya
tsare,sai kun dawo."
Ta amsa kafin ta fita rike da hannun Humaira wacce ta rigaya ta
mamaye zuciyarta.
Tayi mamakin samun Malam Hussein din tare da Liman a falonsa.
Ashe ma yana gidan? Suna ganinta fara'arsu ta k'aru inda Liman
yace "Ga jikar taka ai."
Cike da ladabi ta gaishesu suka amsa,Malam Hussein ya sanya
mata albarka kafin ta mike tayi musu sallama ta fita.
Duk da hakan saida ta nufi gidan ko Allah zaisa ta hadu da wanda
zai bata lambar Haris.
******
Alhaji Aliyu Hussein(mahaifin Haris, su shida iyayensu suka haifa.
Shine d'a na farko namiji,sai mace mai bi masa ta rasu, sannan
Kawu Usman,Kawu Bilal da autarsu Hajiya Barira dake aure a garin
Maradi,jamhuriyar Nijar da kuma Hajiya Mariya(mami,mahaifiyar
Kb)
Gaba dayansu mazan idan an cire Abba dake kano,suna zaune ne
anan gidan kowanne da bangarensa.
Fa'iza,Habiba 'ya'ya mata ne ga Kawu Usman,manyan mazan su
uku ne. Yasir,Abdulmalik(Babban yaya) da Faisal
Rahina,Badiyya da Atika 'ya'ya matane ga Kawu Bilal,rahina tayi
aure sauran Badiyya da atika wadanda sukayi candy. Bashi da d'a
namiji.
Sai kuma babbar diyar Hajiya barira ta fari kafin tayi aure na biyu ta
koma Nijar da zama,Zahra. Wacce ke a hannun kakarsu uwargida
kuma amaryar Malam husseini,Hajja Kubra.
Kyawawan yan mata saidai na wata tafi na wata,hakan bai hanasu
sakin baki wajen kallon wacce suka tabbatar ta ketaresu a komai
ba,wacce kamshinta mai sanyi ya soma ziyartar hancinsu kafin
kyakkyawar surarta ta bayyana a gabansu gami da zazzak'ar
muryarta wacce tayi musu sallama da ita.
Gaba daya kuwa yan matan sun had'u suna masu jimamin tafiyar
Haris wanda bai zab'i d'ayansu ba. Kada ma Zahra taji
labari,yarinya mai tsananin kunya da kawaici saidai a k'asan ranta
ba k'aramin so take yiwa Haris ba. Abunda batasani ba,daman Haris
a farko kafin yazo ya kudurtawa ransa matukar anyimishi dole ya
fito da mata cikinsu toh hakika yafi ganin dacewar zab'ar Zahra. Ya
lura akwai nutsuwa da tarbiyya tattare da ita duk da dai sauran ma
akwai saidai basu da kawaici kamarta. Ko jiya da suke shawagin
nan bai ganta ba saida yasa aka kirata suka gaisa. Wannan ba
karamin dadi ya yiwa Hajja Kubra ba ganin matukar dacen data
hanga tsakanin Haris da Zahra. Hakan yasa ta kudurta yiwa Malam
zancen.
Bayan gaisuwa ta sanar dasu itace tasleem. Zahra ta tareta da
murmushi
"Wow,kece d'iyar gwaggo maryama ta Kano ko? Duk sadda naje
gidanta bamu da hira sai taki. Tabbas kinyi kama sosai da
Humeme."
Kasancewar haka take kiranta,sukayi dariya gaba daya. Bayan
gama gaisuwarsu ta nemi gaisawa da Hajja Kubra,har cikin dakinta
Zahra ta jagorance ta,itama ta nuna murnar ganin Tasleem a karshe
sukayi sallama. Ta sanya Zahra yi mata rakiya sauran sashen kafin
ta dubeta har lokacin tana murmushi haka kawai taji Zahra ta
burgeta.
"Nagode 'yar uwata,bari na karasa gidan Mamma."
"Lah bazaki shiga gidan Malam Ibrahim ba?"
Cikin rashin sani tace "Waye hakan?"
Zahra tayi dariya "Mahaifin amininin Kawu Abba ne dake garin
Kano. Kawu Abba kuma mahaifin Yaya Haris ne."
Jin wannan bayanin,Tasleem ta jinjina kanta,ta hakikance gidan
kakannin KB kenan. Gidan yana kallon juna dana kakannin Haris
suka shiga.
*****
Matansa biyu,Hajja Badi'atu da Hajja Atine. Yaransa tara cif. Hajja
badi'atu tana da biyar yayinda Hajja Atine keda hudu.
Alhaji Idris(Babangida),mahaifin Kb shine babba. Sai Safinatu,
Aisha(mahaifiyar Haris),Bello,Abdulmalik(Baba karami). Ya'yan
Hajja Badi'atu kenan. Matan duka suna gidan mazajensu. Mazan
kuwa idan an cire Daddy suna nan agidan da matansu da yaransu.
Hajja Atine kuwa,Garba,Fatima,Hafsa da Zakari. Suma duk sunyi
aure sun hayayyafa.
******
Babu inda Zahra bata shigar da tasleem ba,a inda Tasleem ta rasa
ma da wanda Kb ke kama tsakanin iyayensa. Idan ta hangi
kamanninsa da Hajja badi'atu saita hango da Malam ibrahim.
Karshe Tasleem ta yiwa Zahra godiya suka kama hanya da
kanwarta wacce tayi wayon sanin gidan mahaifiyarta."
Sai lokacin ta kunna wayarta,da kamar mintuna biyar kiran Kb ya
shigo. Wannan yasa dole ta dakata a gefen wata bishiya domin
amsa kiran nasa....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(50)
Hankalinsa idan yayi dubu ya tashi,Allah Allah yakeyi jirginsu ya tashi yaje ya nemi inda baby take ya dauketa koda ta halin k'ak'a ne. Shaf ya manta da dalilin zuwansa Kano akan matarsa ce,ana kiran masu tafiya Kano yayi zumbur ya mike yayi gaba.
Baby tana neman rainamishi hankali,shi kam bayajin zai iya rabuwa da ita a yanzu. Ko me za'ayi saidai iyayensa su amince su aura masa ita koda na watanni ukun ne yanda kungiyarsu tace idan yaso daga baya zai san yanda zai fiddata cikin shaid'anin kungiyar nan.
******
Da gudu ta isa ga Mamma wacce ke tsaye tana sauraron maganar Nura da humaira duk bata gama yarda dasu ba. Jin tasleem a jikinta tana kuka yasa ta tsaya cak,itama hawayen ne suka cika idanunta. Sallamar dattijon ta katsesu,duk suka waiga suna amsawa. Yayi tsai ganin bakuwar fuska,kafin ya jefo tambaya,nura ya amsata
"Adda tasleem ce fa Dad,'yar anti ta birni."
Fara'arsa ta k'aru,fari fari ne da silkin bak'i,dogo ne yana da jiki. Ganin Mamma ta nufeshi gami da amsar ledar hannunsa a ladabce ya fahimtar da baby lallai shine mijin Mammanta. Murmushinta ya fad'ad'u itama had'e da hawayen farin cikin ganin irin sauyin da Allah ya yiwa mammanta. Tun kafin yakai ga k'araso kusa da ita ta zube gwuiwoyinta k'asa ta gaisheshi
"Ina kwana Kawu."
Ya mikar da ita ta hanyar riko hannunta yana 'yar dariya
"Ashe bazaki bani matsayin uba ba tasleem? Toh ni kuma na daukeki matsayin d'iyata tun kafin na sakaki a kwayar idona. Kiyi kirana da Dad kema amma banjin dadin uncle dinnan."
Mamaki ya kamata tana dariyar farin ciki,kawai saita fashe da kuka,ashe wataran zata samu wannan soyayya irinta uba? Alhamdulillah.
Dad ya katseta ta hanyar duban Mamma fuskarsa ta cika da farin ciki
"Yau duk abunda za'ayi a gidan nan na fannin girke girke da shaye shaye ya zamana yazo daidai da ra'ayin d'iyata kada ayi abunda bataso."
Daga haka ya dubeni
"Menene abun kuka my daughter? Sai kisa naji kamar bakyayin uban dani."
Tayi azamar share hawayenta ta dubi mamma wacce murmushi kawai takeyi tana kallonta kafin ta maida dubanta ga Dad
"Ba haka bane Dad,kukan murna nakeyi."
Ya dafe kanta cikin murmushin yace
"Ya isa hakanan kada yayi yawa kuma. Bari na shiga ciki."
Ya mike ya nufi sama. Baby ta zauna saman kujera tana dariya tace
"Mamma nayi maki murna."
Ta harareta kadan,nura yaja hannun humaira yana fad'in
"Yar kanwata zo mu amso alawa wajen Dad."
Suka haye saman tare,Mamma da Baby suma saman suka nufa d'akin Mamma.
Ta dubi hannun diyarta
"Ya naga kamar hannun naki a kumbure?"
Ta d'an dubi hannun,ashe fa dazu da zatayi wanka ta fidda bandage din,ta dan tabe baki kadan
"Buguwa nayi kuma har yanzu yanamin zafi kadan kadan. Amma da sauki,mamma ya sunan dad din nawa? Ke daya ce a wajensa ne? Waye wannan nuran shima d'anki ne?"
Mamma tayi dariya
"Tambaya uku lokaci d'aya?"
Baby tayi dariya itama
"Allah kuwa mamma ke d'ince duk kin chanja kin k'ara kyau kamar baki da kishiya."
Ta fada don a zatonta wannan katon gidan bazai yiwu ace mata daya ciki ba. Kuma daman a baya gwaggo Hajara ta fadamata yana da iyali.
"Kema kinyi chanjawar data bani mamaki tasleem,kamar ba 'yar makaranta ba anya kina karatun ma?"
Mamma ta fada tana binta da kallon zargi. Tasleem ta diririce sai kuma ta basar da sakin 'yar dariya,mamma tayi tagumi ganin d'iyartata harda b'ulin hanci haka kawai jikinta yayi sanyi duk da tasan kwalliya ce.
"Kai mamma,muda muke karatu. Kuma fa shekara nawa rabonmu da juna kinga dole fa na chanja maki. Don Allah gayamin mamma."
Mamma ta sauke ajiyar zuciya
"Alhaji Kamal Hassan sunansa,kafin ya aureni yana da mace guda daya,Hajiya Aisha. Tana da yaranta manyan maza biyu,suna karatu a turai,sai budurwa d'aya,tana aure a Minna. Sai kuma nura wanda a wajen haihuwarsa Allah Ya dauki ranta. Tun bayan rasuwarta Alhaji yak'i aure har Allah Ya kawo mutuwar aurena ya amince zai aureni bayan da yazo gaida Liman ya ganni yace yana so. Humaira sunan matarsa taci muke kiranta hakan. Kinji tambayarki. Inaso kema ki amsamin tawa tambayar. Menene ainahin abunda ke faruwa? Jikina yana bani akwai abunda keda Abdullah kuke b'oyemin,hakanan nayi mamaki don ko d'azu munyi waya dashi bai bani labarin zuwanki Kazaure ba. Ya cemin mahaifinki na kwance tsawon watanni biyu baijin dadi shine ke d'awainiya dashi,duk sadda na tambayeshi ko kinzo dubashi daga makaranta sai ya hau yimin kame kame. Tasleem ko bakwa jituwa da yayan naki ne?"
Zufa ta karyowa Tasleem,gabanta ya hau dukan uku uku. Shigowar Nura da sallama itace ta ceceta
"Anti kizo inji dad."
Mamma tayi azamar mikewa
"Ina zuwa."
Tayi gaba wanda hakan yasa tasleem sauke ajiyar zuciya. Amma rashin gaskiya ma baiyi ba.
Hawayenta suka kwaranyo,wannan wane irin bala'i ne haka? Ita kam ko za'a kasheta bazata fadi komai ba ko don gargadin yayan nata ala barshi shi da bakinsa ya fad'a d'in. Waya ce ta soma k'ara,ta duba taga mai kiran. "Abdullah1"
Bata d'aga ma ta ajiye. Har yayi ya katse. Haka ya jera kira har uku shiru sannan ya hakura. Tana nan zaune tana tunane tunane har Mamma ta k'ara shigowa tare da Humaira. Ganin wayarta na blinking ya fahimtar da ita anyi kiranta ne. Ta dauka ta duba,murmushi tayi mai ma'anoni tana duban Tasleem wacce ganinta yasa ta d'agowa daga kwanciyar da tayi idanunta bai bar fidda ruwan hawayen ba.
"Ko yanzu kadai maganata ta fito."
Ta zauna tana mai daure fuskarta tamau ta zauna kan gadon
"Humaira tafi wajen gwaggo kuyi hira."
Ba musu yarinyar ta fice a guje,tasleem kallo daya ta yiwa mahaifiyarta tasan babu wasa a tattare da ita
"Baki da wacce ta fini duk duniyar nan,baki da wacce zaki kaiwa kukanta a duniya ta baki shawara wacce ni bazan iya baki ba. Tun rabuwata daku bana bacci mai dadi tasleem. Ga yawan mafarkai da nakeyi da lamuranki,haka kawai hankalina bai kwanta ba akan irin rufeni da Abdullah ke yawan yi idan na tambayeki. Ki fito ki gayamin hakikanin halin da rayuwarki ke ciki,naso na dauko ki alokacin da RALIYA ta rasu saidai kuma hakan bai samu ba sakamakon Abdullah daya cemin karatu kikeyi nima kuma alokacin Allah baiyi zanje gaisuwar ba. Wai menene ainahin abunda ke tafiya dangane dake?"
"Raliya ta rasu?!! Ta maimaita a fili cike da tsananin mamaki. Tuni hawaye sun wanke fuskar Mamma
"Baki kyautamin ba keda yayanki Tasleem,tambayarki ta kara fad'armin da gabana. Mutuwar Raliya baki da masaniya akai,rashin lafiyar abbanki baki sani ba,haihuwar yayanki da takwarar daya samar maki nan ba baki da labarinsa. Wannan wane irin al'amari ne mai d'aure kai? Tasleem ko guduwa kikayi daga gidan mahaifinki kika kasa hakuri har komai ya wuce??"
Kawai sai baby ta fashe da kuka,toh ya ta iya? Mahaifiyarta ce fa.
"Bazakiji komai daga bakina ba wallahi sai kinyi kiran yaya abdullah garin nan. Sai mun hadu mu uku sannan zanyi maganar dake bakina."
Mamma tayi shiru tana kallonta har na tsawon mintuna kafin tayi azamar daukar wayarta tayi kiran Abdullah. Ya dauka ya soma gaisheta gami da tambayar ko lafiya ya kira ba'a d'aga ba?
"Bana dakin,kanwarka ce a ciki."
Bai taba kawo tasleem take nufi ba,a zatonsa ma Humaira ce. Mamma ta katseshi
"Duk abunda kakeyi inaso ka ajiyeshi abdullah,gobe kazo kazaure inason ganinka."
Yayi tsai kamar mai tunani sai kuma a sanyaye yace
"Lafiya dai mamma?"
"Lafiya lau,kazo dai nace."
"Shikenan,in sha Allah ina nan tafe goben."
Sukayi sallama. Mamma ta mike bata kara cewa komai ba ta fita. Ranar basuyi wata hirar arziki da diyarta ba kamar a farko ba itace ke d'okin ganinta ba......
*****
Gaba daya sun hadu a babban falon Daddy ciki kuwa harda Kb.....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(51)
Abba ne ya soma magana cikin nutsuwa
"Kabir."
Cikin sussunne kai ya amsa
"Na'am Abba."
"Jiya yarinyar nan muka ganta kwatsam ta dawo a motar kasuwa,koda muka tambayeta tace kaine kace ta dawo ba tare da ita kanta tasan dalilinka ba,gashi mun taru munason jin hakikanin matsalar data had'aku. Me tayi maka da zafi har haka?"
Kabir ya saci kallon Yasmeen wacce akaci sa'a ita d'inma kallonsa takeyi. Kauda kai tayi gefe,jikinsa ya k'ara sanyi, ga kunya data dabaibayeshi. Toh me zaice? Lallai Yasmeen ta barshi a tsaka.
"Wai bakaji ne ana magana sakaran banza da wofi!"
Cewar Daddy cikin fusata. Yasmeen cikin kuka ta tare
"Wallahi Daddy laifina ne,fad'a yayimin ni kuma nayi fushi nayi tahowa wata. Don Allah kayi hakuri Yaya kabir,ka gafarceni bazan k'ara ba don Allah."
Haris ya runtse ido kansa a k'asa idanunsa sunyi jazur kirjinsa har d'agawa yakeyi saboda bacin rai. Ya saci kallon Kabir,duk alamun rashin gaskiya ya bayyana a fuskarsa.
"Daman nasan kece marar gaskiya Yasmeen. Ni nasan d'ana bazai wulakantaki ba.." Cewar Abba.
"Kada kayi saurin shaidar mutum mana Aliyu,idan anbi ta b'arawo abi ta mabi sahu. Alamun wannan shashashan sun nuna bashi da gaskiya. Idan ba haka ba kayi magana mana."
Kabir ya daure kansa a k'asa yace
"Gaskiyane Daddy,laifi tayimin nayi mata fad'a saidai banyi tsammanin zai mata ciwo har haka ba ta taho Kano bada sanina ba. Na yafemaki kema kuma ina fatan komai daya faru ya wuce,kuskure ne."
Haris ya wurga mishi kallon raini,saidai baice komai ba.
Abba yace komai ya wuce,nan ya k'ara yi musu fad'a akan hakuri da juna daga karshe yace su bari zuwa gobe su juya Abuja.
"Na dawo kanka kai kuma,ya zancenka ya kwana?" Cewar Daddy.
Haris ya k'ara russunar da kansa
"Kamar yanda na fad'awa Daddy ne,Malam yace muje daku karshem sati yanason ganinmu ne."
Daddy da Abba suka dubi juna,kafin Abba ya jinjina kai
"Shikenan,Allah Ya kaimu asabar d'in."
Aka amsa da amin kafin su sallamesu.
Da sassarfa ya nufi wajen motarsa
"Haris!!"
Muryar KB ta dakatar dashi. Kamar bazai tsaya ba sai kuma ya tsaya ba tare da ya juyo ba. Ya karaso ya jingina da motar yana fuskantar Haris.
"Nasan koda yasmeen ta boyewa kowa abunda ya had'amu,toh bazata boyemaka ba. Nayi laifi,please ka tayani bata hakuri."
Haris yayi mai wani irin duba yana d'aga girarsa kadan
"Ka kwantar da hankalinka dan uwana,yanda kaima ka shaidi Yasmeen da nuna maka soyayya tsantsa wacce ba algus hakika bazaka samu wata mishkila ba daga gareta..."
Jin taku a d'an nesa dasu ya sanya Haris juyawa kafin ya dubi Kabir yana murmushi wanda tuni KB ya fahimci can k'asan nurmushin nan bacin rai da haushinsa ne tsantsa.
"As i said,bazatayi fushi dakai ba koda kuwa zata kamaku turmi da tab'arya,ita d'in mai rufa asirinka ce. Sai kayi hattara KB,ba'a cutar irin wadannan matan a zauna lafiya."
Daga haka ya kama handle na motarsa zai bud'e,KB fuska daure ya matsa,daidai lokacin Yasmeen ta k'araso.
"Yayana tafiyarce?"
Haris wanda ke kokarin sanya key ya dubeta yana murmushi cike yake da tausayinta
"Tafiyarce kanwata,kada ki damu zan b'ullo kafin ku wuce. Hope bada wuri zaku tafi ba?"
Ya maida akalar tambayar zuwa ga KB,KB ya d'an tab'e baki
"Banajin da wuri zamu tafi, watakil ma sai zuwa jibi.."
"Meyasa? Kaga fa ban taho da wasu kaya ba sosai,kuma Abba yace lallai gobe mu wuce."
Ya watsa mata kallo kamar yayi magana sai kuma ya fasa, shi fa so yake ya nemi inda baby take. Ganin kallon da yayi mata yasa ta tsoraci fad'ansa tayi azamar cewa
"Yayana saida safen."
Tayi gaba da sauri saurinta,Haris ya dubeta kafin ya watsawa Kb kallo a wulakance,tuni idanunsa sun sauya
"Baby ce ke neman shiga rayuwar aurenka kb,right?"
Kb ya dubeshi a sanyaye,ya numfasa
"Hakane Haris, saidai wallahi bansan meyasa na tsinci kaina da mugun kaunar yarinyar nan ba ni kaina bazance maka ga...."
Figar motar da Haris yayi ne ya sanya Kb ja baya da sauri hakanan hon ya shigayi da karfinsa har Maigadi ya kammala bud'ewa ya fita. Yayi daidai da zuwan Abba da daddy. Abba ne zai shiga gidansa.
Ganin yanda Haris ya fita,Abba yace
"Kai Kabiru,menene ya faru?"
Kb wanda tunani da mamakin yanda