Showing 39001 words to 42000 words out of 60852 words
Chapter 14 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
"Oya,ga wannan sauka ki wanke fuskar nan taki, ki d'anyi kwalliyar nan taki bebinsu."
Harararsa tayi a wasance,kafin ta narkar da fuska
"Au ba taka bace?"
Ya dubeta kafin ya basar da zancen ta hanyar fitowa ya bud'e b'angarenta ya amshi robar ruwan,yana kokarin budewa yace
"Juyo ki wanke fuskarki."
Ba musu ta gyara ta mika hannunta na hagu,yana zuba mata tana wankewa har fuskarnan tayi fayau,Baby ta gasken ta bayyana sannan ya zagayo ya bude boot ya dauko mata handbag dinta ya shigo motar kafin ya dire mata a cinya yana murmushi
"Ayi make up please."
Murmushin tayi kafin yayi addu'a ya daga gilasan ya kunna Ac,ya sanyamusu karatun al-kur'ani don kara nutsar da zuciyar Tasleem daga bisani yaja motar suka dauki hanyar Kazaure. Ita kuwa ta hau fente kyakkyawar fuskarta da kwalliya saidai bamai yawa ba. Bayan ta kammala ta dubeshi
"Baka sanar dani abunda zai kaika garinmu ba?"
Dam! Gaban Haris ya buga. Shaf ya mance da ainahin silar zuwansa Kazaure sai yanzu da Tasleem tayi tambayar. Ashe fa wai matar aure zaije zab'a.
"Kayu shiru??"
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(42)
Ya dan dubeta,ya rigaya ya gama tabbatarwa kansa cewar baby kyakkyawa ce ta gani a fada,tabbas baiga laifi ga KB dake makale mata ba domin kuwa idan zaka biyewa kyawun halitta da surarta,bakasan sadda zaka fada tarkonta ba. Yayi murmushi kafin yace "Garin iyayena ne."
Ta fiddo ido kadan fuskarta ta washe "Haba? Ashe kaima dan garinmu ne? No wonder na ganka da kyau kamar aljani."
Kallonta kawai yayi ya sakar mata murmushin da saida ta jishi har tsakar kanta. Tasan tun haduwarsu ta farko,tana jin wani al'amari bak'o game da Haris,saidai ita kanta tasan Haris yafi karfinta. Me zaiyi da 'YAR BARIKI? Ta maida kanta ta kwantar tana sauraron karatun Al-Kur'ani mai girma. Shi din ma kogin tunanin ya fad'a. Anya bai fada tarkon son 'YAR BARIKI ba? "A'a ban fada ba,just ina girmamata ne a matsayinta na wacce ke bukatar taimako. Ina kuma tausayawa rayuwarta."
Ya fadi a ransa.
*******
Hankalinsa a tashe,nutsuwa tak'i samun mazauni a kwakwalwarsa da jikinsa. Yana zaune sai afkin kiraye kirayen waya yake. Daga ya kira Manal,sai ya koma Dalal kafin a karshe yaji ta bakin Hibba. Momy ma ya kirata sau d'aya saidai ita kanta bata da labarin duniyar da Baby ta shiga. Zuciyarsa tayi bak'i har hasko Baby yakeyi kwance a kirjin wani da namijin. Kishi matsananci wanda har ya janyo sauyawar kalar kwayar idonsa.
Tun tsawon daren jiya take lura da mijin nata, hakanan ko lokacin daya fidda kunya ko shayi yake waya a gabanta duk tana sauraronsa,hankalinta ya tashi jin cewar mace ce ta rikita Kabir har haka. Ta soma sharar kwallah saidai gogan baisan tana yi ba,kwata kwata ma baisan da wanzuwarta ba sai sambatu yakeyi a fili
"Ina kikaje? Wane dan iskan kika samu har kika kashe wayoyinki Babyna?"
Ire iren abunda yake fadi kenan. Maganarta ta katseshi
"Wacece haka prince?"
Ya dubeta,gaba daya baisan da ita ba a falon. Tsaki yaja ya mike ya dauki wayoyinsa zai shiga d'aki
"Yanzu akan wata 'yar iska kake..."
Fisgota da yayi ne a fusace ya sanya sauran maganar makalewa a fatar bakinta. Ya hau jijjigata cikin tsawa yace
"Koda wasa kika kuskura kika k'ara kiran Babyna yar iska wallahi Yasmeen saikin raina kanki."
Ta fisge jikinta tana hawaye itama a fusace tace
"An fad'a d'in! Yar iska! Yar bariki..."
Tass! Ya kwasheta da mari,kafin ya hankadata ta bugi bango ya nunota da yatsa
"Wannan kadan kika gani! Wallahi akan Baby zan iya rabuwa dake Yasmeen! Sannan ki ajiye a ranki! Baby saita shigo gidan nan matsayin matata!"
Ya kwashi wayoyinsa da suka tarwatse a k'asa yayi daki ya buga kofar a fusace. Yasmeen ta tsorata ainun,mikewa tayi ta nufi dakinta. Mayafinta da fos na kudadenta ta dauka,ta sab'i diyarta Nasreen dake bacci tayi waje. Ta rantse yau bazata kwana Abuja ba kuma ma a gidan mutum irin Kb. Maigadi yana tambayarta ko lafiya ta dakamishi tsawa "Budemin kawai!" Yayi mamaki don baisan Hajiyar tasu da haka ba,akwai ta da girmama na gaba da ita komin kankantar matsayinsa. Mace mai hankali da tunani,ga fara'a da hakuri. Ba musu ya bude a hanzarce ta sanya kai ta fita tana zubar hawaye. Yau kam sai KANO......!
****
Karfe uku da mintuna na rana sai gasu a Kazaure. Gaba daya garin ya chanjawa Baby harma ta kasa sanin ta yanda zata soma kwatantawa Haris gidansu. Ga mamakinta taga yana ta shiga wurare bai tsaya ko'ina ba sai kofar gidan Liman. Tabbas gidan kakan nata ma yaso ya sauya mata sakamakon fenti da shukoki da aka k'ara mishi. Ta tsaya cak tana kallon tsohon dake zaune akan tabarma tare da makwaftansa suna hira,saidai suma hankalinsu ya dawo kan motar. Fitowar wata yarinya karama ce ta basu mamaki,tamkar an tsaga kara an karya ita da Baby saboda tsananin kamar da sukayi,tana wani yanga irin ta kananun yara masu iyayi ta isa ga tsoffinan ta zauna saman cinyar tsohon nan. Haris da Baby suka dubi juna,ganin hawaye a fuskar Baby da kuma murmushi yasa ya girgiza mata kai. Ta kwashesu da hannunta
"Haris kayimin abunda har abada bazan mance dakai ba. Ka samu babban gurbi cikin zuciyata. Ina jinka sosai a jinin jikina kana yawo akowane sassa na jikina. Wallahi banajin zan taba mancewa da abunda kayimin. Nagode sosai."
Yaji maganganunta har cikin k'ok'on ransa,ya kasa dauke idanunsa daga kanta. Ya rasa me yakeji game da ita,ji yakeyi tamkar kada su rabu. Inama zasu shekara a haka bayajin zai damu. Murmushin nan nata wanda yake tayar mishi da tsikar jiki ta k'ara yi mishi.
"Fito muje,gaskiya ka bari ka huta saika karasa gida."
Ya girgiza mata kai ya saki lallausan murmushi idanunsa a kanta
"No,ki bari zan shigo anjima kinsan gobe fa zan tafi. Zanzo mu gaisa sai na kaiki ku gaisa da Kakannina."
Ta marairaice fuska,kwalla ta ciko idonta
"Gobe zaka tafi ka barni Haris?"
Maganar ta shigeshi,yana kara jin zuciyarsa na shiga wani yanayi. Kwankwansa gilashin da akayi ne ya maido hankulansu ga wajen,Haris ya sauke gilas kasancewar gilasan daga wajenm akwai duhu. Dan saurayi ne,yana murmushi yace
"Malam tambaya kukeyi ne?"
Haris ya girgiza kai,baby ta sanya dariya
"Baharu." Ta fada kafin ta fito,da gudu gudu ta isa ga Kakanta wanda da alama shi kam ya ganeta. Domin gaba daya ya mike yana farin cikin ganinta sosai,ta rungumeshi kafin kuma su zauna ta saki kukan farin ciki. Zuciyar Haris tayi babu dadi,ba abunda ya tsana sama da kukan nan. Dolensa ya bude motar ya fito suka gaisa da wanda ta kira da Baharu.....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(44)
"Tasleem,kukan na menene kuma? Me ya samu hannun naki?"
Ta share fuskarta ganin yanayin Haris shima kamar baiji dadin ganin hawayen nata ba,ta dubi hannun kafin tace
"Buguwa ce nayi Malam,amma yanzu da sauki sosai ma."
Tsohon ya kurawa Haris ido da murmushi wanda haka halittarsa take,da wuya kaga gushewarsa akan fuskarsa.
"Yaro kana yimin yanayi da aminina Hussein."
Furucin Malam yasa Baby zubawa Haris ido kasancewar tasan Baffa Hussein sosai jefi jefi takan lek'a gidansu a baya idan tazo domin har baffa Hussein ya santa yana nuna kauna agareta har takanyi mamakin irin soyayya da shakuwar dake tsakanin wadannan bayin Allah biyu. Haris cikin murmushi yace
"Lallai ma tsohon nan,tabbas idan na koma zan fadawa Baffa ka mance da autan jikansa,Haris."
Mamaki karara ya sauka akan fuskar Baby hade da dariyar nan nata mai burgewa,haris ya daga mata gira yana murmushi. Malam kuwa hakora ya washe ya rungumo kafadar Haris yana dariya sauran tsoffi uku suna tayashi.
"Allahu,daman kaine Harisu? Haka ka girma? Lallai Harisu baku da zumunci,da ace kun yo halin iyayenku da ba haka ba. Ina d'an wajen dan auta?(Alhaji idris)"
"Yana can Abuja da zama. Kayi hakuri dan tsoho ba rashin zumunci bane,ayyuka suke rikemu acan."
Malam ya jinjina kai,baby kam murmushi takeyi,yayinda ta kasa dauke fararen idanunta akan kyakkyawar fuskar Haris wanda samun namijin daya hada komai irinsa a fannin kyau na sura da halayya abune mai matukar wuya a zamanin nan. Ya kallota,tayi azamar mikewa tsaye tana basarwa da cewa
"Bari naga kishiyoyina,don Allah dan tsoho kada ku bari yayana ya gudu tun yanzu,kunga fa ko abinci bamu ci ba."
Haris ya hararota yana murmushi,tayi mishi gwalo kadan. Malam yayi dariya
"Ai babu inda zai tafi yanzu,Baharu shigar da yayan naka dakinku yayi alwala yazo muyi sallah sai yaci abinci ko?"
Suka mike,tuni Baby tayi gaba tana fadin zata turo yaro ya shigar mata da akwatin kayanta.
*****
Tun a hanyarta take ta kiran wayoyin yayan nata amma yana ringing bai dauka ba. Taci kuka har ta koshi,ganin baya kusa yasa tayimishi dogon text inda ta gutsura mishi halin da suke ciki da KB da kuma tahowarta Kano da tayi. Daga karshe ta kashe wayarta gaba daya.
Yasmeen kenan!!
*****
Murna da hira ta karade bayan tsakanin mutanen gidan bayan da Baby tayi wanka da sallah. Tana sanye da doguwar rigar kanti. Alokacin tana zaune tana cin abinci anata hira. Makwafta sai shigowa sukeyi,Gwaggo Hajara ma nan tazo da kwanonta. Kowa yaga bandejin hannun Baby sai ya tanka,tana rufesu da fadin buguwa ce tayi. Wayoyinta kuwa har lokacin a kashe suke ta jonasu a chaji. Sallamar da akayi ta maido hankulansu,Haris ne a gaba sai Yaya musty a baya. Ganin Yaya musty yasa Baby sakin ihu ta mike ta rukunkumeshi suna dariyar farin cikin ganin juna. Gaban Haris ya shiga dukan uku uku,haka kawai ya tsinci kansa da jin haushin wannan rungumar da Baby ta yiwa wani.
"Yaya mustyna,ashe da rabon rai ya k'ara ganin rai tsakaninmu?"
Sai kuma ta soma hawayen farin ciki.
"Yaya mustyna??" Ya maimaita a zuciyarsa,ashe har yanzu Yasmeen bata mance dashi ba?
Har lokacin hannuwansu harde cikin juna,Haris ya kauda kansa ya wucesu zuwa ga mutanen gidan suna gaisawa. Kasancewar gwaggo Hajara ta samu labarin kowanene a wajen Baharu wanda yakai mata tsegumin zuwan Tasleem yasa ta ganar dasu. Nan fa murna ta k'aru,suka shiga tambayarsa mutanen Kano yana amsawa. A karshe yayi musu sallama bayan ya dire musu rafar kudi 'yan dari dari guda biyu ya mike suna fadin ya barshi amma da azama ya nufi waje. Ganin haka tasleem tabar hirar bayan rabuwa da Musty tabi bayansa a da sauri. Ganin yana shirin wuce zaurensu ne yasa tayi azamar riko hannunsa wannan yasa shi juyowa ya watsa mata kallon da yayi kama dana farkon ganinta dashi. Ta saki hannun dayake kanta a waye yake ta nuna kamar bata gane yanayin fuskarsa ba ta hanyar marairaicewa da langabar da kanta
"Yanzu tafiya zakayi shine babu ko sallama?"
Ya dan tabe baki yana mai zura hannunsa cikin aljihun wandon jeans dinsa,ya daga kafada
"Gani nayi kina hira da yan uwanki banson katseki ne."
Murmushi tayi kawai,ta soma fahimtar wani abu kadan akan fuskar Haris, mai yiwuwa yana dauke da ciwon da itama take dauke dashi. Ya katse tunaninta
"Zan wuce."
Ga mamakinsa yaga ta durkusa har k'asa tana dubanshi
"Har na rasa manyan kalmomin da zanyi amfani dasu kuma wajen yin godiya agareka yayana,kayi jihadi babba wajen ceto rayuwata daga halaka. Daga yau na baka matsayi babba gareni. Zuwa yanzu bani da wanda yafimin.."
Ya katseta shima ta hanyar yin durkuson a gabanta,yana kafeta da wannan idanuwan nasa masu kara fama mata ciwon dake ranta. Saidai ita kanta tana raina kanta a gaban Haris,duk wani haduwarta ganinta takeyi tsumma a gabansa. Ita kanta ta riga tasan Babban Goro sai magogin karfe,me namiji irinsa zaiyi da 'YAR BARIKI? Ta kauda kanta daga dubansa ganin bashi da niyyar kauda nasa akanta. Wai daman akwai abunda take ko kuma zata tabajin kunya acikin mutane? Bata taba kawowa ba kuwa ko a kanta,ya katseta a karo na biyu ta hanyar mikewa
"Tashi Tasleem."
Ta mike tsaye,bai kara dubanta ba yace "Kina iya rubutamin lambar wayarki,watakil na leko gobe kafin na wuce."
Har ya soma tafiya sai kuma ya juyo dauke da murmushi saman fuskarsa wanda bata taba ganin irinsa ba a tattarr dashi. "Sannan ki sani,matsayin kanwata kike Tasleem. Bana bukatar ki yawaita godiya gareni. Ki cigaba da godewa Ubangijinki. Hakanan ya dace kiyi istibra'i. Sai Allah Ya kaddara saduwarmu Tasleem."
Ya soma tafiya da baya da baya, hawaye taji sun taho mata yayinda ya juya ya fita da sauri saurinsa. Ta tsaya cak tana binshi da kallo zuwa lokacin hawaye sun sauka saman fuskarta. A gaban idanunta yaja motarsa bai k'ara ko kallon kofar gidan nasu ba.
"Small."
Taji muryar Yaya Musty ya fadi ta bayanta,wannan ya fargar da ita a inda take tsaye.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(45)
Ta dubeshi tana murmushi,yayinda damuwa ta sauka saman fuskarsa shi kuma.
"Kin tsaya anan? Ko bakiso ya tafi bane?"
Abunka da wacce bata iya boye damuwarta ba tace
"Banso ba,ya tafi ya barni da damuwa marar misaltuwa saidai yace watakil kafin ya wuce ya biyomin muyi sallama."
Musty ya k'ura mata ido yana kallon kwayar idanunta. Akwai wani kwantaccen sirri game da Haris a cikinsu.
"Kanwata are you in love?"
Tayi tsai domin batayi mamakin jin wannan tambayar ba,inda takeson Yaya mustin nata kenan,nan da nan ya dago damuwarta ko wace iri ce. Ta basar ta hanyar dariya ta soma tafiya tana fadin
"Yaya mustyna kenan,ina Haris ina mace irina?"
Ya riko hannunta wanda yayi silar tsayuwarta,ya jawota baya kadan yana dubanta da idanunsa da suka bayyana bacin rai da damuwa karara a cikinsu,mamaki ya hana baby magana sai ya rigata da cewa
"Ya kike irin wannan maganar sisna,wa zaik'i mace kamarki? Ko kina da wani aibu ne?"
Ya karashe bayan ya saketa yana murmushi a sanyaye,bata yardarwa kanta hakan yayi niyyar fada ba sakamakon zafin da ya nuna a farko. Batace komai ba banda murmushi da "Uhm" daga haka tayi ciki.
Ya bita da kallo rai a bace,wai daman Tasleem ba sonshi takeyi ba kamar yanda ya jima yana yaudarar kansa? Yaya mustyna! Yaya mustyna! Me hakan ke nufi?!! Tsaki yaja bazai kuma iya komawa cikin gidan ba kawai sai yayi gaba zuwa gidansa rai babu dadi domin ya gama lura Haris ya samu gurbi a zuciyarta.
*****
Mutanen gidan sunyi farin cikin ganinsa sosai. Nan aka shiga hidima dashi,sai abinci ake ajiyewa agabansa. Hankalin Haris ko kusa baya kan yan matan da suka had'e cikin kwalliya sunata shawagi a falon wajen kawo mishi abinci,ya tabbata an riga an basu labarin abunda ya kawoshi. Sai hirarsu sukeyi da kakarsa,Hajja. Koda ya kammala mikewa yayi ya nufi sashen kishiyoyinta suka gaisa kafin ya nufi bangaren kakansa,Malam Hussein.
Nan ma suna hira yake sanar dashi tare sukazo da Tasleem diyar gwaggo maryama 'yar amininsa Liman. Ai sai Malam Hussein ya tashi zaune fuskarsa a sake sosai. "Jikar Abdulmalik ce? Ikon Allah,daman kunsan juna ne acan Kano?"
Haris ya rasa amsar da zai bashi a karshe yace "Eh munsan juna,tare mukayi makaranta saidai banma san 'yar gwaggo maryama bace saida muka hadu itama zata zo nan take bani labari." Kakan nasa yayi dariya,cike da mamaki yace
"Wai kuwa d'an tsoho wane irin aminta ke tsakaninka da Liman? Na lura kuna kaunar junanku fiye da tsammani."
Jin tambayar ya k'ara sanya Malam dariyar farin ciki
"Bazaka gane ba Harisu,kaunar da muke yiwa junanmu ta samo asali tun daga iyayenmu da suka rasu,saboda karfin zumuncin ne,yasa mahaifina sanyamin sunan mahaifin liman din,wato Hussein yayinda shima yaci sunan nawa mahaifin Abdulmalik. Bayan haka,Allah Ya riga ya sanya mana kaunar junanmu fin tsammani Harisu. Wanda muke burin wataran mu kulla zumuncin da zai d'orar. Saidai kasan a zamanin nan ba'a yiwa yara dole,amma har gobe bamu bar burin wasu cikin jikokinmu ba su share mana wannan hawayen."
Haris yayi murmushi,baffa ya katse tunaninsa
"Ina fatan