Showing 57001 words to 60000 words out of 60852 words
Chapter 20 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
"Da asuba nayi wanka."
"Kina iya tafiya."
Shiru na mintuna,ganin bata da niyyar motsawa yasa shi saurin fita ya rabu da ita a motar. Tana kallonsa ya koma ciki,hawayenta suka kara kwaranyowa karo na ba adadi,toh zaman me takeyi kuma? Kawai saita bude ta fito itama.
*****
"Ayyiriri yiriri! Kai Alhamdulillah. Harda na Zahra?"
Batasan lokacin da cikinta ya murd'a ba,me kunnuwanta ke shirin ji mata ne? Innalillahi wa inna ilaihiraaji'un!
Da azama ta nufi bandaki domin rage cikinta......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar
(61)
Washegari wajejan uku na rana,mutan gidan basunan sunje gaisuwa acan k'asa gidan wani almajirin Liman wanda ya rasu sakamakon hatsari. Tasleem ce zaune a tsakar gidan cike da tunanin kawayenta. Tunani takeyi ko Manal tayi aure? Toh Dalal da Hibba fa ya suke? Tunanin neman layin Hibba ya fadomata. Bata mantawa saboda saukin lambar wayar Hibba ta haddaceta a kwanyarta har akwai ranar data taba karantowa sukayita mamaki har hibbar domin ko ita bata da haddar lambarta aka. Da azama ta mike tayi daki,wayar dai data tsana ita ta dauko ta dawo ta zauna. Ta duba akwai kud'i har dubu daya a ciki. Baki ta tab'e wannan kam a wurinta karamin kudi ne bazai burgeta ba. Batason wulakanci a rayuwa. A nutse ta jera lambar ta kira. Akayi sa'a ta hau ringing.
Hibba alokacin tana zaune a gefan ruwan Tiga Dam ita fa sabon saurayinya,HAYAT. Tunda ta soma bariki bata taba tsintar kanta dumu dumu cikin soyayyar wani d'a namiji ba illah Hayat. Matashi mai ji da naira da hutu. Ganin unknown number yasa ta jan tsaki ta ajiye wayar. Hayat ya dafa cinyarta yana kasheta da kallon kauna
"Lafiya dai my beb."
"Wata number ce da bansan da zamanta ba."
Acan kuwa baby tsaki taja sai lokacin ta tuna ko ita akayi kira da unknown no.a wayarta bata fiye dauka ba. Ta yanke shawarar tura sak'o.
"Hibba,it's me Baby. Pick d call."
Tana shirin turawa yayi sallama ya sanyo kai. Ta amsa bayan tayi saurin ajiye wayar a gefe. Hankalinsa yayi kan wayar cike da zargi kafin ya basar ta hanyar fad'in
"Ina mutan gidan?"
Itama fuskarta ba yabo ba fallasa saidai kirjinta sai bugu yakeyi.
"Basunan sunje gidan gaisuwa."
Bata ankara ba taga yasa hannu ya dauki wayar yayi tsai yana karanta sak'on....
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(62)
Fuskarta a tamke baisan sadda ya daga wayar ya bugata da bango ba kafin ya fisgo Tasleem wacce ta mike tsaye ganin yanda ya yiwa wayar. Murde hannunta tayi ya komar dashi ta bayanta,har suna shakar numfashin juna ita kam na tsoro ne. Tayi ta murza hannun saidai fa iyaka yatsunta ne don kuwa ba rikon wasa ta samu daga wajen maza ba.
Cikin kakkausar muryar da batasan Haris da ita ba yace
"Menene gaminki da ita a karo na biyu?! Me kike shirin yimin? Daga yau ki sani cewa banason mu'amalarki da kowace abokiyar shaidancinki ta baya! Wannan shine gargadina a gareki na karshe."
Daga haka ya saki hannunta,tayi saurin ja baya tana zubar hawaye. Ta dubeshi ido cikin ido kallon nan na alamar tambaya(Kaine kuwa?..lol). Ya kauda fuskarsa,har ya juya zai fita kuma ya dawo baya ya dauki wayar wacce tuni screenface dinta ya tsage,sim d'in ya fidda kafin ya cilla wayar jikinta daga haka yayi gaba cikin takunsa kamar wani basarake.
Ta dubi hannunta wanda har yatsun Haris sun bayyana jikinsa,kafin ta lumshe ido ta zauna d'abas akan sumintin tsakar gidan tana kuka. Karshe dai mikewa tayi ta dauki wayar tayi daki. Jimawa kadan taji sallamar Baharu,bata ko fito ba har ya shigo ya miko mata simcard sabo.
"Gashi inji angonki,yanzun nan suka wuce. Yace ki sanya a wayarki zai kiraki."
Bata ko kalleshi ba ballantana yasa ran zata karb'a,ganin shiru ya ajiye ya fita yana mai jin haushin yanda antin nan tasa ta kasa gano kaunar da Haris keyi mata.
*****
Tsaye yake a farfajiyar hotel din na Nicon dake birnin tarayyar Abuja yayinda yake cike da farin ciki da walwala na ganin wacce bai taba tsammatar ganinta ba a wannan lokacin. Ta karaso bayan ta cewa wacce suke tare tayi jiranta minti biyu. Ta wulka ido irin na kwararrun 'YAR BARIKI kafin ta sakar mishi murmushi wanda ya kara fiddo zahirin kyawunta na asalinta na buzuwa.
"KB manya daman ana ganinku?"
Kb yayi yar dariya
"Gaisheki DALAL,kun b'ata b'at a garin ta dabo. Ashe kina nan kina holewarki."
Dalal tayi dariya
"Kai haba,mu a suwa? Kaine dai gakanan sai fresh kakeyi,nikam tunda mun hadu yau bazan bari ka gudu ba saika kaini na gaisa da k'awarmu. Wallahi just one week kenan da bamu ganta ba amma kewarta ta cikamu."
Cikin rashin fahimta yace
"Wai Dalal kuna zaton Baby tana tare dani ne?"
Tayi k'as k'as da cingam tana kallonsa shek'ek'e
"Bangane manufarka ba KB? Wai bakwa tare da Baby? Toh ina take?"
Yayi wani d'an malalacin murmushi kafin ya zura hannu aljihun wandon jeans nasa. 'Yan dubu dubu ne da baisan ko nawa bane ya zaro da d'an kaurinsu ya mik'a mata
"Idan basu isheki ba kiyi magana na k'ara maki Dalal,fatana da burina bai wuce ki taimaka wajen lalubomin inda kawarku take ba. Ko kuma idan kinsan wani labari game da rayuwarta please ki sanarmin sauran binciken zanyi da kaina."
Ta shinshina kud'in,ita kam ai kud'i koyaushe basu tsufa awajenta sabbi ne. Ta tura a jakarta bayan ta tuno da Manal data tab'a tabbatar mata cewar ita kadai tasan wacece baby da kuma garinsu saidai bisa amana ta gayamata ita kam bazata fadawa kowa ba.
"Aikinka zai cika muddin zaka saki kud'i Hajy KB."
Shima kallo yakeyi mata na kwararren 'Dan Bariki,kafin ya shafi sumarsa yana dariya
"Ba abune mai wuya ba,kina iya bani acc.no dinki hade da phone.no."
Ya amsa kafin suyi sallama ya shige don gabatar da abunda ya kawoshi cike da matsanancin farin ciki....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(63)
A gajiye ta k'arasa kujerar tangameman falon wanda yaji kayan alatu ta zauna tana fadin wash! Manal ta zube gefanta suna dariya
"Shegiya Dalal,kina cin karenki babu babbaka nikam ina nan kamar kullin kayan wanki. Ke a yanda na lura anya kuwa Alhaji Ubalen nan idan munyi aure zai barni na fita wani wajen? Mahaukacin kishi gareshi,ji fa dai daga maganar aure har ya killaceni gidansa,babu wata harka wai yana bukatar nayi istibra'i,mts."
Dalal ta mike zaune tana dubanta bayan ta kyalkyale da dariya
"Kefa baki fahimci wannan d'an fulanin naki ba,toh wallahi dagaske yakeyi sonki yakeyi da gasken gaske."
Ta tabe baki
"Barshi dai yayita haukansa,wani sa'in ni kaina ina jin kauna da tausayinsa wallahi ya iya lallab'a mace ne. Ke nasa fa an bincikamin asalin aurensa da matarsa,ashe dole yabi umarnin mahaifinsa ya aureta har yanzu da suke da yara biyar bai taba sonta ba. Kinsan fa ba wani shekaru ne dashi ba,arba'in da wani abu yake."
"Yara biyar? Kuma ace ba soyayya? A ruwa tasha?"
Manal ta harareta da alama maganar ta bata ranta,Dalal kam murmushi tayi gami da jin tsoron auren wata uku ya koma na har abada....
"Wai kuwa kina samun Baby a waya? Nasha nemanta naji switched off."
Jin an ambaci Baby ya tunasar da Dalal abunda ya kawota. Ta zabura ta matso kusa da Manal har tana firgitata.
"Ke nima bansan inda ta lulluk'a ba,anya ba garinsu ta koma ba?"
Manal tayi shiru tana tunani,daman tun sadda baby ta fito da shigar hausawa jikinta ya bata cewar Kazaure zataje.
"Gayamin sunan garinsu mana,kinga sai na gano mana ko lafiya?"
Cewar Dalal,Manal ta numfasa
"Banason karya alk'awarin dana daukarwa baby na cewar bazan sanarwa kowa ba game da garinta ko asalinta,wannan shine..."
"Haba Manal, bamusan halin da take ciki ba,idan ance ma tana bukatar taimako babu k'arya a ciki. Idan kin fadamin wa zan gayawa,just give me full address ni kuma zan binciko mana lafiyarta koda a b'oye ne. Kinga idan bata garin sai mu sanya cigiyarta ko kuma mu bi abokan harkarta gaba daya tunda ba wani yawa garesu ba muji ko suna tare."
Manal tace "KB fa?"
"Basu tare da KB,domin kuwa Momy tace min yazo nemanta wajenta amma bai sameta ba."
Dalal tayita siyasance Manal har saida ta samu ta shawo kanta tayi na'am da hakan batare data bata ko sisin naira biyar ba. Duk da dai Manal bata da tabbacin baby can tayi amma bata zaton zata je gidan yayanta da mahaifinta domin a yanda ta nunawa Manal ba karamin tsana tayi musu ba,mammanta ce ma take son sanyata ido wataran.
Ta gayamata ta rubuta.
"Idan kinje Kazaure ki nemi gidan babban limamin garin, nan ne gidan da nasan watakila ki samu labarin Baby."
Bayan ta gama rubutawa,Dalal ta tuntsire da dariya
"Amma Baby anyi shegiyar yarinya. Don ubanta ita daman d'iyar Liman ce take bura uba haka?"
Manal ma dariyar tayi,saidai tsoron kada Baby ta kamata da cin amanarta yasa bata gayawa Dalal cewar gidan kakannin baby ne ba ta wajen mahaifiyarta. Da zataji waye uban baby,zata fahimci cewar lallai Baby ta ketaresu kota ina tunda ba kudi ne ya fiddota bariki ba.
******
Kishingide yake a kujera mai zaman mutum uku,Yasmeen tana gefe tana mammatsa mishi kafafuwa yayinda ya maida hankalinsa ga kallon Ball. Wayarsa tayi k'arar shigowar sak'o
"Mikomin wayata."
Ya fada ba tare daya dauke idanunsa daga kallon ba. Ta dauki wayar ta mik'a masa. Ganin sak'on daga Dalal ne,ya sanyashi mikewa zaune.
"Kazaure gidan babban Liman,duk wanda ka tambaya za'a kaika. Idan kaje babu nasara zan k'ara bincika mana."
"Wuuu!"
Shine ihun murnar da KB ya saki. Yasmeen ta iso gareshi
"Lafiya prince?"
Ya mike ya dagata sama yana juyi da ita suna dariya. Babu kamar Yasmeen wacce take jin mamakinsa da kuma farin ciki. Yaushr rabon daya kula da lamarinta haka? Kai a ranar dai ya faranta mata fiye da tsammaninta. Shi kuwa Allah Allah yakeyi weekend yayi yaje ga Baby shi koda bai ganta bama ya samu shiga wajen liman. Domin kuwa yasan kwarai wanene Liman saidai bai taba kawowa shine uban tasleem ba. Har ya soma mamakin abunda zaisa Tasleem wacce ta fito gidan manya haka ta b'ata rayuwarta da barikanci. Meyayi zafi haka toh?
******
Karshen sati nayi,ya yiwa matarsa sallama da sunan zaije Kazaure gaida kakanninsu. Taso ya tafi da ita saidai koda ta matsa da magiya ya bata rai a dolenta ta hakura tana ji tana gani yayi mata sallama ya wuce airport domin hawa jirgin zuwa Kano.
Tunawa da tayi cewar tun angoncewar yayanta bai nemeta a waya ba yasa tayi kiransa. Yana dauka ta soma shagwaba murya
"Haba yayana ashe daman akwai sadda zaka share lamurana? Nikam har na soma fushi da yayyuna nasan waya dasu ya janyo ka shareni."
Haris dake kwance akan gado kawai yana hutawa domin ya jima da tashi daga bacci,darem jiya sun sha waya da Zahra wacce babu laifi ta samu gurbi sosai a zuciyarsa duk da dai karfin hirar itace shi kam yakan rasa abun cewa saidai ta jefo mishi tambaya.
"Kiyi hakuri small,ban manta dake ba. Ai babu matar da zata mantar dani ke. Ya kuke? Ya dotana?"
Yasmeen tayi dariya
"Gatanan tana tsalle tsallenta,babanta ma yanzu ya tafi Airport zai wuce Kazaure idan ya sauka anan Kano. Wallahi naso ya taho dani naga amare amma yak'i."
Tunda Haris yaji wai KB ya taho Kano zaije Kazaure yaji bacin rai matuka ya dirar masa. Bazai fa amince da wannan sakarcin ba,ya dace tun yanzu ya sanyawa lamarin burki.
"Hello." Cewar Yasmeen jin yayi shiru.
"Small,bani mintuna." Ya katse kiran ya mike zaune yana mai zuro kafafunsa k'asa. Dabara ce ta fadomishi na kiran Mamma. Matar da tunda ta ganshi ta nuna mishi kauna hakanan sun jima a falonta su biyu suna tattaunawa game da Tasleem sannan ya nuna mata komai dangane da lamarinta ya sani. Har kwallah tayi don farin cikin jin cewar yaji ya gani yana son diyarta zai iya aura. Bayan sun gaisa yace yanason Nura yaje ya dauko Tasleem a mota harda kayanta ta zauna a wajenta. Mamma ta tambaya ko lafiya. Bai sanar mata ba saidai yace akwai 'yar matsala ne. Tace bakomai zatayi hakan.
Tasleem tayi mamakin ganin Nura yazo wai Mamma da kanta ta nemi komawarta gidanta. Har inna tana fada wai Mamma babu ko kara,bata tambayi ko da iznin Haris ba ko Aa saboda taji Nura yace shine yayi kira. Hakanan ta hau mota,Nura yaja suka nufi gidan Mamma sai tambaya takeyi Mamma da fara'a tayi maganar zuwanta ko a'a shidai Nura tun yana amsawa har tambayoyin sukayita bashi dariya ma.
******
KB yana dira a Kano,direbansa ya kaishi gida. A gaggauce yaci abinci yayi wanka sannan ya saka kananun kaya. Jakar kayansa ya dauka ya saka a mota. Jeep dinsa ya dauki yayi hon Maigadi ya bude.. Sai Kazaure......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(64)
Hankalin Haris bai kwanta ba har saidai ya lalubi layin baby saidai baiyi mamakin jinsa a kashe ba yasan tayi fushi tak'i sanyawa ne. Wannan yasa ya k'ara nemanta ta hanyar layin Mamma. Ya sanarwa Mamma yanason magana da baby. Ta mik'awa Tasleem lokacin tana zaune anan gefen Mamma suna 'yar hira don babu laifi ta sakarmata.
"Sai ki tashi ki shiga daga ciki mijinki ne."
Ta mike ba don taso ba wayar na hannunta. Saida ta zauna gefen gado sannan tayi mishi sallama. Ya amsa ciki ciki
"Kina jina ko? Kb yana hanyarsa ta Kazaure."
Tabe baki tayi,ai daman tasan ko ba dade ko ba jima sai KB ya samu labarin inda take tunda har yasha alwashin nemanta ruwa a jallo.
"Ya akayi yasan da zamanki a Kazaure?"
(Ya fadi hakan da niyyar bugar cikinta duk da bashi da tabbacin saboda ita Kb zaije Kzu.)
Cikin rashin fahimta tace
"Kana zargina ne da gayawa KB inda nake Haris? Ko ka mance garinsu ne?"
Ya lumshe ido ya kara gyara zaman towel din dake daure a kugunsa,fitowarsa kenan daga wanka. Zak'in muryarta daban ce,hakika zai iya rantsewa bai taba sauraron muryar mace a fili ko waya ba, da yayi mishi dadi irin na Tasleem.
"Nidai ina mai gargadinki,stay away from him. Kada koda wasa na samu labarin kun hadu har maganar fatar baki ta shiga tsakaninku. OK?"
Ta rausayar da ido tana tsuke baki cikin jin haushin Haris. Banda abunsa ma,kare ne ya cijeta da zata k'ara waiwayar BARIKI. Don KB barikin ne ma gaba daya a rayuwarta.
"Kin rasa baki ne?"
"Naji zan kiyaye."
"Good,had'ani da Mammana."
"Ko a ina ta zama taka?" Ta fadi a zuci,a fili kuwa da toh ta amsa kafin ta mike ta fita zuwa falon.
Mamma ta karbi wayar,sunyi magana wacce Tasleem batasan abunda yace mata ba saidai ta lura da hararar da Mamma ta dafko mata kafin ta amsawa Haris da cewa
"Kada ka damu d'ana,baza'a samu wata matsala ba."
Daga haka ta kashe wayar ta mike tayi dakinta a fusace. Wannan ya sanyayarwa da Taslewm da jiki ta mike ta rufa mata baya. Kuka sosai ta tarar Mamma nayi. Ganin ta shigo ta zauna Mamma ta ja majina
"Kin cuceni Tasleem. Idan na tuno kinyi karuwanci raina baci yakeyi naji ke kanki ina jin haushinki. Wallahi koda wasa naji kin sab'awa mijinki babu ni babu ke. Ba don Liman ne da kansa yazomin da batun aurenki da yaron mutuncin nan ba wallahi ban yarda a cuci rayuwarsa a aura mishi ke."
Jin haka itama Baby ta fashe da kuka sosai ta durkusa gaban Mamma
"Wannan ya nuna har wannan lokacin baki yafemin ba Mamma. Ya kikeso nayi,Mamma idan bada sanya albarkarki gareni ba komai na rayuwata bazata tafi a daidai ba. Please Mamma kada kiyimin bakin da zan kasa zaman aure."
Jin wannan furucin ne ya tashi hankalin Mamma,ta rungumo diyarta tana fadin
"Na yafemaki Tasleem,bazaki fi haka lalacewa ba. Har abada