Showing 51001 words to 54000 words out of 60852 words
Chapter 18 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
jinin sarauta mai bak'in jini kamar Khalid ba. Kowa gudunsa yakeyi yan uwan duk sun juyamishi baya saboda ganin shi kadai ne ba uwa ba uba.(Ta manta itace ta janyomishi tsanar,don akwai randa yayansa waziri yana son ganinsa yace bai zuwa. Kusan sati shiru har da kanshi wazirin yazo gidan,ganin babban mutum yasa maigadin budemishi dakin bak'i,yayita zaman jira amma raliya ta rike abba ta hanashi fitowa a karshe waziri ya fusata yabar gidan da alkawarin bazai kara shiga harkar Khalid na tunda bashi da bukatarsu hakanan ya gargadi dukkam zuri'arsu kada wanda ya k'ara lek'awa gidansa. Wannan labarin nima baba Maigadi ke bani,hankalina ya tashi don har gidan waziri naje na bashi hakuri ya sakarmin fuska sosai ya nunamin ai mu d'in nasu ne. Yace kuma zai sanya ayi addu'a sosai gareshi don bai amince da yanayinsa ba. Shima ya d'agawa mahaifinmu kafa ne har zuwa wani lokacin.
Abba ya cigaba da labartamin,yace tun sadda yaji wannan zancen yaji kamar bashi ba,komai na rayuwarsa ya daidaita,kirjinsa yabar nauyi. A ranar kuwa ya yiwa raliya abunda bai tab'a yinsa ba sakamakon tsanarta da yaji,duka yayi mata sosai sannan ya saketa. Tace wallahi bazata bar gidan ba,saida ya hado da jami'an tsaro har jikokinta yace duk ta tattara ta tafi dasu shi kam baisan menene ya kwasheshi ya auro wannan kaddarar ba. Hakanan ya kori nura wanda har ya nemi ya zageshi. Hindatu kam tasha kuka,ta hau rokonsa ya barta a wajensa itama ta tsani uwarta. Haka dai ya hakura yabar yaransa. Washegarin faruwar al'amarin ne yayi kirana yake sanar dani. Nayi godiya ga Allah da baisa zan mutu kafin wannan rana ba. Nan Abba ya tambayeni game da mamma,na bashi labarin komai har zuwa gidana da kikayi da sauransu. Anan ne nadama tsantsa ya kamashi. Tun dai daga lokacin ya kamu da rashin lafiya,karshe yasa na kaishi wajen waziri. Muna shiga waziri yana zaune a fada,yana ganin Abba cikin yanayin zubar hawaye yana nufoshi,tsam ya mike har na tsoraci ko marinsa zaiyi kawai sai ya rungumeshi wanda hakan ya bawa abba kuka sosai a jikinsa. Ya jashi inda fadawan suka mike suna zuba kirari,sukayi ciki. Kinji yanda aka sasanta,Abba ya tsanantawa su Hamid ya hanasu fita ko'ina ya santa ido sosai a kansu,ganin batanci da rashin maida hankalin Hamid a karatu zaiyi yawa yasa shi turashi makarantar horo. Hamida kuwa kasancewar tana tsoron abba alokacin ganin irin korar da yayiwa mamanta sannan taje taga muhallin da raliya take babu wani kayan morewa rayuwa dolenta ta nutsu,Abba yace ya bata sari ta fiddo miji ko kuma ya aurar da ita ga wanda yaso. Har nan kazaure na rakoshi ya roki gafararsu kafin ya koma kuma rashin lafiya ta hau shi. Yayimin fadan dalilina na boyewa iyayen mamma inda kike karshe abba ya hau yawaita addua da tsayuwar dare da kuma zubar hawaye duk saboda rashinki da alhakin daya dauka namu. Raliya kuwa gobara sukayi a gidan babu wanda ya tsira daidai da nura,sakamakon jonin wuta direct da Nura yayo musu acewarsa bazai iya rayuwa ba wutar lantarki ba ya gama zage mahaifiyarsu tas akan bakin cikin data janyomusu suna cikin daula. Karshensu kenan. Yanzu haka hamida tayi aure ga wani alhaji mai mata biyu har ta haihu,duk da wulakancin da take sha hakanan take zaman hakuri. Hindatu kuwa tana nan tare dani a Abuja ta soma karatunta a jami'a, hakanan Abba da nake jinyarsa saidai yanzun jikinsa da sauki sosai. Waziri ma ya matsamin na maidoshi gabansa inajin hakan zaiyi tunda shima Abban yace ya gaji da zama gidana saboda kunyar hasina. Duk da dai yanzu gidane na kashin kaina."
Tasleem tayi shiru,tabbas rayuwa abar tsoro ce. A sanyaye ta kara tambayarsa
"Ina labarin Ridwan kuma?"
Murmushi Abdullah yayi
"Allah Sarki,abbansa fa ya jima yana fushi dashi har korarsa yaso yi na hana. Amma yanzu yayi aure yana zaune acan London wajen uncle dinsa da matarsa Jidda. Yaransu biyu ma,daya taci sunanki dayar kuwa sunan mamansa."
Tayi murmushi kawai.
*****
Washegari yaya abdullah yana tafiya,itama ta shirya koda ta yiwa mamma sallamar komawa wajensu inna bata ko kalleta ba. Haka nan ta wuce a sanyaye.
Da la'asar Liman ya tura ayi kiranta.....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar
(55)
Bata kawo komai ba ta mike ta yafa mayafinta ta nufi dakin Liman jikinta akwai yanayin sanyi wanda tun dawowarta daga gidan mamma take cikinsa. Koda inna ta tambayeta ta amsa da babu komai.
Yana zaune yana duba wani littafi na hadisai yaji sallamarta wanda hakan yasa shi ajiye littafin a gefe yana mai amsawa fuska a sake. Ta shigo tana yamutsa fuska kadan kafin ta soma kokarin zama tana fad'in
"Nidai wannan tsohon kana neman matsamin fa,yanzu kuma menayi aka d'agoni bama a tarbeni da 'yar shila ba."
Yayi dariya
"Shak'iyiya,wanda kika ci bai isheki bane a k'aro maki gobe? Nutsu don magana zamuyi."
Ya soma da yi mata doguwar nasiha akan muhimmancin aure wanda tun daga haka tasha jinin jikinta,kirjinta kuma bai bar bugu da sauri da sauri ba. Saida ya kammala sannan ya bijiro mata da bukatarsa na neman amincewarta kan batun aurenta da Haris.
Cikin tsananin mamaki da fargaba ta dubeshi
"Shi Haris dinne yace yana sona baffa?"
Jin dadi game da amsar da zai bata yasa Liman yin wata 'yar dariya
"Shakka babu,harisu ne yazo da batun kamar yasan fatanmu kenan ni da aminina. Kuma munyi na'am da batunsa nasan bazaki watsa mana k'asa a ido ba kasancewarki yarinya mai biyayya."
Tayi k'asa da kanta,nan da nan abokan hirarta suka ziyarci fuskarta(hawaye). Ina ita ina Haris wai? Haris yasan abunda yake kuwa? Me zaiyi da sauran maza? Sam bazata bari ta cuci mai niyyar taimakonta ba,kai ta kasa gaskata da gasken shine yayi tayin auren nata.
"Kuyi hakuri bafamfa,bazan iya aurensa ba!"
Nan take annurin dake saman fuskarsa ya dauke,tamkar bai taba dariya ba ya koma Abdulmaleek Hussein dinsa sak!
"Nufinki zaki bani kunya ne Tasleem? Toh bari na fadamaki wallahi tunda nake da Aminina tun zamanin kuruciyarmu dayanmu bai taba zuwar wa dayanmu da bukata ba munyi watsi da ita. Baki isa ba Tasleem! Ko uwarki k'arya takeyi na nemi bukata awajenta tak'iyi,na takaice maki ma aminina shine ya wuce gaba wajen aurenta da Ubanki tun a farko domin a baya banso tayi nesa har haka ba. Ki tashi ki barmin d'akina,aure kuwa keda Harisu saidai idan anyishi ki mutu."
Daga haka ya maida fuskarsa gefe babu wata walwala a samanta.
A sanyaye tasleem ta mike tana k'ara mannewa da abokin hirarta harda sheshshek'a.
Kallo daya tayi mata kafin tabar murza robb a hancinta
"Lafiya kuwa?"
Cikin kukan dai ta labarta mata yanda sukayi da Liman,inna taja tsaki gami da fadin
"Allah Ya kyauta,ina goyon bayan Liman,wannan hukuncin yayi. Domin kuwa samun yaron mutunci irin Harisu a zamanin nan akwai wuya. Nikam dari bisa dari na amince kuma banga aibu da aurenku ba. Budurwa sharab dake,ai wallahi sai yanda kikayi dashi ta hanyar biyayya da kissar d'iya mace."
Ji tayi tamkar magana take yab'a mata,da sauri ta mike ra shuri takalmanta batayi wata wata ba ta fada gidan gwaggo Hajara bazata kwana a gidan ba. Meyasa Haris zaiyiwa rayuwarsa haka? Duk a zatonta jihadi yake niyyar yi don tausayinta batasan kudurin da Haris ke shirin yi ba. Gwaggo Hajara ma yabo da hamdala ta shiga yi,ai ita kam tun farkon ganinta da Haris takeso aure ya kullu tsakaninsu sai gashi Allah Ya amsa. Nan tayita lallashin tasleem gami dayi mata nuni akan illar bijirewa umarnin babba.
******
"Nayi zaton ai da Zahra za'a hadashi?"
Murmushi Malam yayi kafin ya bata amsa
"Ya kike wata magana kubra? Da Zahra da Tasleem basu da wani bambanci a wajena. Tunda yaro ya nuna yanason Tasleem sai a bisu da addu'a inajin hakan zaifi."
Ba haka taso ba sanin da tayi Zahra ita kadai take iya gayawa sirrinta,kuma ta tabbatar mata cewar tana son Haris. Bata hakura na dai ta k'ara muskutawa
"Malam fadamaka ne banyi ba amma hakikanin gaskiya Zahra banda alkunya ya hanata magana tana son Haris kwarai dagaske,mezai hana a had'a mishi su biyu duka a aura mishi na tabbata Harisu bazai watsa mana k'asa a ido ba."
Malam ya dubi hajja kubra a mamakince
"Harisun ya gayamaki yana da ra'ayin mata biyu da wurwuri haka ne?"
Ta girgiza kai,zatayi magana ya dakatar da ita
"Bazan hanaki abunda kikaga zaifi ba,saidai ni da kaina bazan tunkari Harisu da zancen ba. Ki tuntub'eshi da kanki idan yaga zai iya toh nawa bai wuce daura aure ba."
Ranta ya d'anyi sanyi jin hakan. Tana matukar kaunar Zahra,bata tab'a tsayawa kula samari ba sai gashi rana tsaka ta kamu da son Haris wanda har ta kasa b'oye mata ita kuwa mezaisa ta kasa yin wannan kokarin gareta?
"Shikenan Malam,Allah Ya zab'a abunda yafi alheri. Zan gwada hakan."
"Ameen." Kawai yace mata kafin ya nemi ta kawomishi furarsa.
******
Momi tayi wani murmushi kafin ta rausaya idanuwa
"Ka kwantar da hankalinka Kb,na tabbatar maka baby zata dawo. Bata komai saida shawarata. Koda ya tabbata auren zatayi na tabbatar maka da cewar zata nemeni bada jimawa ba. Nima ban sameta a waya ba,saidai nasan wacece baby tunda har ta furta maka tabar wannan harkar tabbas da gaske takeyi. Mu kuwa a sharuddan kungiyar,lallai idan mace zata bar harka sai ta tattaro mana dukkan kadarar data mallaka cikin harka idan kuwa ba haka ba zamu hanata auren gaba daya muyi sanadiyyar gurb'acewar dukkanin rayuwarta wanda nake da yak'inin Baby bazata iya ba. Yanzu kawai mu jirayi dawowarta."
Kabir ya jefa hannu aljihu ya zaro bandiran kudi 'yan dari bibbiyu har uku ya dire a kusa da Momy yana murmushi
"Ga wannan asha ruwa,burina ta dawo na ganta."
Tana taunar cingam gami da wani irin murmushi na duniyanci ta dauki kudin a wulakance tana juyawa kafin ta watsa mishi kallo tana fari da ido
"Bukatarka zata biya da zarar Baby ta dawo. Zanbi kowacce hanya don ganin ta amince da aurenka."
Ya shafi suma yana dariya kafin ya jinjinawa Momy
"Dakyau momynmu,anjima zanbi jirgi zuwa Abuja,sai naji wayarki."
Daga haka yasa kai ya fice yayinda Momy ta bishi da murmushi na musamman.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(56)
Kwance yake akan restingchair a farfajiyar gidansa daga can poolside. Idanunsa a lumshe fuskarsa ma'abociyar kyau da kwarjini sai shek'i takeyi. Yammacin juma'a ne,garin yayi luf luf sai wani ni'imantaccen iska ke busowa da kamshin k'asa kasancewar da safiyar yau din anyi ruwa sosai. Sanye yake da jar t-shirt,da wando wanda da kad'an ya rufe gwuiwoyinsa.
Sallamar isah mai gadinsa ne ya sanyashi bude idanunsa yana mai amsawa bayan yayi kokarin danne damuwar dake shimfide kasan ransa.
"Yallabai kayi bak'o yace a sanar dakai cewa Deen Bukar ne."
Jin sunan wanda ya jima baiji daga gareshi ba ya dago yana murmushi
"Kayi mishi iznin shigowa isah."
Matsakaicin saurayi ne,mai d'an kiba. Yana sanye da kananun kaya shima,kallo d'aya zakayiwa bak'ar fatarsa ka fahimci yana hutawa sakamakon lukui lukui da tayi. Ganinsa yasa Haris mikewa tsaye yana bayyana hakoransa a waje cike da farin cikin ganin oldclassmate dinsa na Malaysia. Deen Bukar. Rungume juna sukayi suna masu dariya kafin su cafke.
"Shegen sama,deen kana hutawarka,irin wannan k'iba kamar ba soja ba?"
Deen yayi dariya yana nunoshi da yatsa
"Zaka fara ko Gent? Toh ai kaine za'ace baka aikin komai. Ka ganka kuwa?"
Sukayi dariya kafin Haris ya dauki wayoyinsa da tab
"Bismillah."
Suna tafe suna hira har suka shiga falon Haris wanda ya k'ayatu iya k'ayatuwa. Haris yayi kiran kuku dinsa,Henry. Ya sanyashi ya kawowa bak'onshi abun motsa baki. Bayan tafiyar henry ya dubi deen
"Sai fa hakuri kasan abunka da gwauro."
Deen yayi dariya
"Kai ka sowa kanka,ya dace ka nemo mana mata musha biki. Gashi dai twins dinka(yaran deen) suna k'ara girma. Kb fa,ya labarinsa?"
Haris yayi dariyar yak'e
"Yana nan da bebinsa d'aya,Nasreen."
Deen ya jinjina kai lokacin Henry ya iso ya soma zuba mishi juice a kofi.
"Banji dadin rashin aurenka Gent,ko still now tsoron matan kakeyi?"
Haris yayi murmushi
"Aure lokaci ne Deen, sannan idan nace ma ina tsoron matan na yanzu ai ba laifi bane."
"Magana ta fito,kacemin kawai tsoronsu kakeyi."
Murmushin dai Haris ya k'ara yi kawai,shi kadai yasan matsalarsa. Duk sadda ya tunano da tafiyarsu kazaure a gobe damuwa kadai ke dabaibaye zuciyarsa.
"Last two months ai,inajin 5th of may ne,na hadu da wani kamar KB naka a Ni'ima hotel da wata baby. Naso nayi mishi magana duk da dai ina kokwanton ko shi d'inne tunda kaga bazan kawo har yanzu KB yana yayin wasu bebs din ba tunda he's married. Kafin ma nakai wajensu sunyi gaba,na rako oganmu ne wajen wani abokinsa. Saidai yanzu kace yana ina ma?"
Haris ya kara zuciya da lamuran KB, yana kara jin kwarin gwuiwar auren Baby don ya fahimci ita kadai ce yake tarayya da ita yanzu. A zahiri ya murmusa
"Hum, bana zaton shi ka gani dai,mutumin dake zaune a Abuja ba."
Deen ya tabe baki yana mai daga kafada kadan
"Zai iya yiwuwa."
Daga nan suka share zancen,zuwan Deen shi ya mantar da Haris damuwarsa sukayita hira yana bashi labarin yanda wasu rundunarsu ke fama da matsalar boko haram,bai bar gidan ba saida sukaci girkin henry. Bayan magriba ya wuce.
*****
Abdullah kuwa,koda ya koma Abuja bai rufewa Abbansa komai dangane da halin da Tasleem ta shiga ba. Abba yayi kuka kamar me a karshe yayi nadamar watsi da rayuwar yaransa da yayi wanda sanadin hakan gashi har karuwanci diyarsa wacce ta samu kyakkyawar tarbiyya tayi. Abdullah kuma ya sanarmishi da zancen aurenta da za'ayi da Haris din kamar dai yanda Baffa ya sanarmishi kafin barinsa Kazaure. Abba yaji dadi matuka musamman jin cewar Haris din da kansa ya amince zai rufawa diyarsa asiri yana sonta ba tare da kowa ya tilasta mishi ba. Sannan kuma ya d'okantu da ganin tasleem ko don ya nemi gafararta,amma Abdullah yace mishi ya saurara dai tunda can gidan basu san komai ba. Ya hadashi a waya da baffa ya nuna amincewarsa dari bisa dari ya kuma nunawa Baffa ai tasleem ikonsa ce. Baffa yaji dadi matuka,bayan hakan ne ma ya nemi tasleem yayi maganar gareta.
Wannan kenan!!
*****
RANAR ASABAR!!!!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(57)
Kabir yana zaune a falonshi bayan ya kirayi wayar
Momy har zuwa lokacin babu kwakkwarar
magana ta inda Baby take. Ya damu kwarai,har
abun yana neman shafar walwalarsa. Daidai
lokacin Yasmewn ta zauna tana amsa waya cikin
dariya ta karashe maganar data soma tun kafin
shigowarta da cewa
"Aa yayana,mudai kam kada a tsawaita mana
lokaci munason shan biki da wuri."
Ta danyi shiru a nishadance tana sauraron amsar
da Haris ke bata,yayinda KB ya mike zaune yana
zuba mata ido cike da dumbin mamaki.
"Toh Allah Ya tsare hanya,agaishemana dasu
Malam."
Daganan ta katse wayar ta ajiye.
"Sorry prince,abinci saura kad'an."
"Wane yayan naki ne zaiyi aure?"
Tayi mamakin tambayarsa,bata dauka koda wasa
baisan da zancen ba kuma ganin agabansa aka
danyi maganar tafiya kazauren a kano duk da dai
ba'a fadada zancen yanda zai fahimta
"Baka da labarin sanya ranar auren Yayana
za'aje yi Kazaure?"
Ransa ya baci jin tambayt daya kalleta matsayin
rainin hankali
"Da ina da labarin zan tambayeki ne?"
Ganin ransa ya baci yasa ta sanyaya murya
domin yanzu batason batamishi ko kusa
"Kayi hakuri,ganin yanda kuke dashi shiyasa nayi
zaton bazaka rasa sanin komai ba. Ni kaina
bansan cikakken zancen ba. Amma Daddy ne ya
turashi Kazaure zab'ar matar aure cikin yan
uwanmu. Kuma yanzu ya zab'a shiyasa Malam
ya nemi ganinsu gaba daya harma dasu Daddy
din."
Kb jikinsa yayi sanyi, me ya yiwa Haris da zafi
har haka? Duk irin shakuwarsa amma ya kasa
sanar dashi labarin aurensa? Ya jinjina kai kawai
baice uffan ba.
"Hadomin Coffee."
Ta mike ta fita itama din dai ta lura yayan nata
saboda abunda KB yayi gareta ne ya kullaceshi
wanda ba halinsa bane(wato kullata).
Shi kuwa KB wayarsa ya dauka ya kira Haris
dake shirin tayarda mota zuwa gidansu Daddy
don tafiya. Kamar bazai dauka ba sai kuma ya
dauka da sallama.
Kb ya amsa yana yar fara'a kafin yace
"Wani tsastsauran laifi nayi da har dan uwana
kuma aminina ya kasa sanarmin da