Showing 18001 words to 21000 words out of 44401 words

Chapter 7 - MAFIYA Part 1 By MRS SADAUKI .txt

03 Dec 2024

3190

haɗe rai na ce “ tashi ka bani wuri,ka yi abin da na ce su kuma mutanen da zaka samo ka sanar da su zan biya su ne” da saurinsa kuwa ya tashi,ni kuma na kai baki na sumbaci Tony don wannan dubarar daga gare shi ta fito.
Bayan sallar la'asar kuwa sai ga mutane sun cika gidanmu,gefe guda ƴan jaridu biyu ne sai bayan na gama bayanan ƙarya kan cewa ina warkar da dukkan cututtukan duniya sannan mutane suka soma faɗin abubuwan alkhairin da na yi musu,na biya masu gidan rediyo da tv domin yi min talla da kuma lambar wayata da za a kira ni.Su kuma masu shaidun ƙarya Illiya na baiwa kuɗi ya raba musu,kuɗin da ace sun san sune ajalinsu to da tabbas ba za su karɓa ba amma ƴan magana na cewa kwaɗayi mabuɗin wahala......




NB:Ina ƙara yawan free page ne,niyyar kaina.


My book is only 500 via2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank DM +22795045822








Talla! Talla! Talla!!!




DULLAHZ CAKES AND MORE 💕




Ina jamaata mutanen kirki ji'bin arziki? Yan kurna, rijiyan lemo,bacirawa,da duk abunda y jibanci Nan Ina mutanena mutanen Kano kanawan dabo mutanen kirki mutanen da sukasan Kansu,


Ina mata yangayu wadanda basaso gayu y wucesu,biki gareki? Suna? Ko kwarya kwaryan liyafa qawata? Kinji labarinmu ko yenzu batun ke tafe gareki,


Munayin cake me dankaren dadi cake hadadde a musulmin farashi,akway cupcakes,samosa, spring rolls,Muna gashin kaji da kayan kwalam d maqulashe kala kala,09111648884


Yayata Muna girkin biki,suna,ko tarbon baki komi kikeso,inma grkine bakijinyi Dan Allah ki kira dullarz zatamaki shi nantake a gyaremaki cikin warmers me delivery ykaimaki,09111648884


Yar uwata inkinyadda d Allah kibamu yardarki bbu cuta babu cutarwa b ha'inci zaa mki komi fiyeda yenda ke zakiyi 09111648884


Call:09111648884
[01/12 à 09:18] MRS SADAUKI 💫: *MAFIYA*☠️



LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️


*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)


*Lambar waya:* +22795045822


*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
_____________________






13




Washegari,afujajan Illiya ya shigo ofis ɗina ko neman izini bai yi ba.


“Yalaɓai ya haka? Dukkan mutanen da suka bada shaidar ƙarya a kan kai malamin tsibo ne sai ɗauki ɗaiɗaya mutuwa take yi musu”




Da wani mugun kallo na dube shi na ce “ au! So kake na bar su da ransu daga ƙarshe su tona min asiri? ”


“Yalaɓai kisan kai fa ne jinin wajen mutum goma” ya faɗa hawaye na zubo masa akan kumatu waɗanda suka sa na ji zuciyata ta yi mugun sanyi don tsabar daɗi,don a yanzu in ga mutum cikin baƙin ciki shi fi faranta min rai.




Ido na lumshe ina tuna yadda Tony yayi amfani da madubin tsafina ya dinga tsotse jinin duk mutanen da na bai wa kuɗi,sosai hakan ya ƙara mini ƙarfin power ta yadda a wannan karon har na yi nasarar toshe bakin Ammy ta yadda duk abin da zan yi ba za ta ga abunsa ba ko kuma ta yi min magana.




“Yalaɓai ciki fa har da mace mai ciki ” Illiya ya faɗa cikin gwanjin kuka,na buɗe ido jin furucinsa .Na ce “ ya zancen Salima ka kuwa fara wani shiri a kai?”


Ya saka idonsa cikin nawa yana zancen zucin da nake jinsa raɗau kwanyata na karanto min shi,‘ dama duk rashin imanina akwai wanda ya fi ni ? Anya akwai zuciya a ƙirjin yalaɓai? Wato duk wannan iftila'in da ya jefa mutane shi ko a kwalar rigarsa?...’




Tunanin nasa ne na katse ta hanyar cewa “ wani abun jin daɗi ma daga cikin wannan lamari shi ne kuɗin za su ci gaba da yawo a doron duniya,kuma iya masu son zuciya ne kawai za su je hannunsu haka kuma zan ci gaba da amfani da tataccen ƙarfin jikin mutane domin inganta gobena.Illiya ina so ka sa a ranka babu abin da ba zan iya yi ba yanzu,don haka kar ka kai ni bango yin haka ban kwana ne da rayuwarka.Je ka yi aikin da na saka,ka tabbatar Salima ta kasance cikin tsaronka sannan duk wani motsi nata ka sanar da ni”


Ba tare da ya ce komai ba ya juya zai tafi,na tsayar da shi “ mene ne sunan matarka?”
Ya juyo da sauri yana kallona tambayar ‘ me za ka yi da sunanta?’ shimfiɗe akan fuskarsa.Na ƙara haɗe rai ina juya idona zuwa na mage,murya na rawa ya ce “ Mariya ” na sakar masa murmushi,shi kuma ya fice.






Kan kujera na zauna ina tunanin hanyar da zan ɓullowa mijin da Malama Zainab za ta aura,wanda alƙaluman tsafina sun tabbatar min da tabbas auren babu fashi .Na ja tsuki ina jin takaici,kukan Tony na ji ƙarƙashin kujerar da nake zaune.Na duƙa na ɗauko shi na ɗora shi kan table,jikinsa na fara shafawa tare da soma yi masa magana ina neman shawara “ Tony a daren jiya na yi bincike akan Malama Zainab kuma an nuna min sai ta auri mijin nan nata,ban so ya kusance ta ya zan yi?”


“Turen aljani za ka yi wa mijin,tun da ita tana tsare iyakokin Ubangiji sosai babu ta hanyar da jinnu zai shiga jikinta.Amma kamar yadda ka yi bincike haka ni ma a jiya na yi bincike kan shi Sheikh ɗin,duk da yayi karatun addini amma fa bai amfani da shi in taƙaice ma dai fuska biyu ce da shi har da giya yake sha” Tony ya faɗa min da idonsa amma raɗam nake jin sautin murya na fita daki-daki.Tsabar murna ban san lokacin da na ɗauke shi na rungume tare da miƙe wa tsaye na soma yin rawa,“ ashe babban sirri ne da mage baƙa har haka? Hohoho! Wato shi yasa Tony ka kasance na musamman abin da ban saka ka ba yi kake yi domin sauƙaƙe min aiki”


Tony ya ce “ yalaɓai ka manta a daren jiya ka yi min sacrifice? Ai muddin zaka bani jini abin da zan yi ma sai ka yi mamaki” sam ban damu da cewa illata rayuwar wasu babbar cutarwa ce ba na ce “ in dai jini ne Tony kar ka damu”.




Ina nan zaune Illiya yayi min waya kan cewa Salima ta tashi daga makaranta,kuma shine ya kai ta gida da sunan ya rage mata hanya.Duk wayar da nake Tony ya buɗe kunnuwa yana saurare,bai ce komai ba ya fita da gudu.Na saki murmushi don na tabbata kuwa wani aikin ne zai yi min,wayata da key na ɗauka tare da ficewa .


Ina draving ina tunanin surar Mariya matar Illiya ,na lashi leɓena na ƙasa ina mai cewa “ ko fyaɗe ne sai na yi miki muguwa!” a haka na ƙarasa gida.Ina shiga na ga Salima a zaune kan kujera tana taya Ammy saƙar kayan sanyi,na saki wani murmushin jin daɗi ganin Laure ta fito daga kitchen hannunta riƙe da kofin zoɓo ta kai wa Salima.


“Ga wannan ki sha Madam yana ƙara gani musamman gare ku masu kallon zare” Laure ta faɗa amma kafin Salima ta kai ga amsa Ammy ta ce “ Laure miƙo min ganin zoɓon nan har maƙoshina ya bushe,je ki kawo wani”


Da sauri na ƙarasa ina cewa “ haba dai Ammy ya za ki ce haka? Ita fa wannan baƙuwarmu ce ita ya kamata a fara karramawa,kuma kin ga ke kina da mura.Laure je ki kawo wa Ammy marar sanyi,ki dinga kula don Allah ko ta ce ki bata abu mai sanyi kar ki biye ta”


Laure ta miƙa wa Salima kofin,za ta ajiye shi ita ma na tari numfashinta “ Hajiya ƙyanƙyamin mu kike shine ba za ki sha ba?” da sauri ta girgiza kai ta ce “ a'a wallahi bari na sha to” sai ta kai kofin bakinta har sai da ta sha rabi sannan ta ajiye sauran.Laure na fitowa na yi mata nuni da ido kan ta tafi da ragowar wanda Salima ta ajiye,ai kuwa tana miƙawa Ammy nata sai ta ce “ bari na ɗauke sauran kar ya zuba ga capet”




“Laure wane irin abu ne wannan? Ta sha abu ta ajiye shine za ki tafi da shi? In kuma tana son ƙara sha?” Ammy ta faɗa cikin faɗa ,a doli Laure ta ajiye kofin tana kallona ta koma kitchen.


Hira suke tsakanin Ammy da ita Salimar ni kuma ina gefe ina danna waya,hannun Ammy na gani ya ɗauki kofin zoɓon ban san lokacin da na ce “ Tonyyyy!” ban ida rufe baki ba ji kake Ammy na salati haɗi ƴar ƙara tuni Tony ya saka bindinsa ya buge kofin daga hannunta ya faɗi ƙasa ya zuba a ƙafarta.




Laure ta fito tana tambayar lafiya,na soma shafa bayan Tony da tuni ya zo ya ɗare cinyata kafin na ce “ zo ki tsabtace wurin nan please ”


Jikinta na rawa ta zo ta goge wurin da ya ɓace ita kuwa Ammy sai faɗa take,a ƙarshe dai na tashi na bar wurin na koma part ɗina.Ta cikin madubina na ga hanyar da Tony ya bi ya bai wa Laure maganin da ta zuba a zoɓon Salima,ya ajiye mata shi ne a kitchen da kuma ƴar guntuwar takardar da yayi bayani daki-daki.






★MALAMA ZAINAB




Matashiyar budurwa ce ƴar kimanin shekara ashirin da bakwai a duniya,ta mallaki hankalin kanta.Duk wata cikar halitta da ƙima da ake nema wurin cikakkar mace mai ƙima duk ta mallake su.Mace ce ita wacce ta riƙi bautar Ubangiji matsayin abu na farko a rayuwarta,duk sauran abubuwa suna biyo wa baya ne.Tausayi,kyauta,jinƙai su ne suka luluɓe duniyarta suka ƙawata kyakkyawar fuskarta mai cike da hasken ni'imar imani.Tun da take ba ta taɓa soyayya ba,duk da kuwa maza dayawa sun nuna ra'ayin haka amma ita ba ta ji wanda take so ba.Sheikh Ali ya kasance cousin nata,tun da ta tasa ya ga tana da addini ya ɗauki son duniya ya ɗora mata tare kuma da zage dantse wurin nuna mata abin da zai kawo ci gaban karatunta.Wannan yasa ba tare da wani tunani ba ta amince za ta aure shi har aka yi musu baiko,bayan haka ne ya tafi Misira wurin karatu.Tun da ya tafi kuma ba wata gamsashiyar waya suke ba kasancewar shi da ita ɗin duk ba su da wani isasshen lokaci.Kwana biyu da dirar shi a ƙasar Nijar ya nemi a yi walimar aurensu,wacce kuma tuni aka soma shawarwari tsakanin ahalin biyu kafin shi ma angon ya nemi su keɓe domin tattaunawa.




Ko da ta fito daga gidansu HAROON direct gida direba ya ajiye ta,zuciyarta cike da fargabar abin da take gudu take kuma zato kar ace gaskiya ne wato tana son HAROON .




Ɗakinta ta shiga ta yi wanka ta canza kaya,bayan ta yi sallar magrib sai ta shafa mai.Tana nan zaune tana saƙa da warwara Innarta ta shigo tana cewa “ Zainabu ki fito ga Ali nan ya zo”


Sai da gabanta ya faɗi,amma ta daure ta ce ” to Inna gani nan” sai kuma ta miƙe ta zaɓo wani farin hijabi ta saka tare da fesa turare marar ƙamshi.
Sai da ta yi jarumta sosai sannan ta ƙaƙalo murmushi ta yaɓawa fuskarta mai cike da damuwa.Da sallama ta fita falon,yana ganin ta ya kafe ta ido ko ƙyaftawa bai yi.Ta zauna ƙasan capet ta ce “ ina wuni Imam?”


“Alhamdullah malamata fatan kin wuni lafiya?” ya faɗa ba tare da ya janye idon nasa a kanta ba,cike da tsarguwa ta ce “ Imam babu fa kyau kallon mutum haka”
Yayi murmushi mai sauti ya ce “ haka ne ! Amma kar ki manta saura ƙiris ki zama tawa na yaye duk wani hijabin kunya a tsakaninmu”


Ba ta ce komai ta miƙe ta je ta kawo masa ruwa da abin da Innarta ta gyara mata domin tarben baƙon.Tana zuba masa ruwa ya kafe hannunta da ido,nan take jikinta ya soma yin rawa ta ɗaga kai ta banka masa wata muguwar harara.
Ya ja ajiyar zuciya ya ce “ sai da na ji wani yarrr ” ruwan ta ajiye masa ya ɗauka ya sha,sannan ta zuba masa abinci har da su cewa ta zo su ci amma ta ƙi.


Bayan ya gama ne ya ce “ Malama Zainab yau muna wace rana?”
Ta basa amsa kai tsaye da “laraba”
Ya ce “to rana irin ta yau kin shiga lalle da yardar Allah,sai a yi ɗaurin aure juma'a,taron biki kuma asabar”
Shiru ba ta ce komai ba sai ma duniyar tunani da ta lula,ranar farko da suka soma ganin juna da HAROON ,yadda suka yi baya ta faɗa kan ƙirjinsa,yanayin yadda yake kallonta cikin tako da kuma salo,yadda yake mata murmushi...
“ Zainab ?” Sheikh Ali ya katse mata tunanin,a ɗan firgice ta ce “ na'am HAROON !”


“Haroon kuma?” ya tambaya da mamaki,sai ta diririce ta soma kame-kame,ita ɗin ba ma'abociyar yin ƙarya ba ce shi yasa ya gane.
“Kar ki yi min ƙarya Zainab,wane ne HAROON ?”
Ba tare da ta basa amsa ba ta tashi da sauri har da ɗan gudunta ta shige ɗakinta tare da faɗawa kan bed ta fashe da kuka.......




My book is only 500 via 2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank DM +22795045822.
Ki zo ki yi payment domin a yi tafiyar nan da ke, wannan karon salon na daban ne salo ne da ban taɓa yin irinsa ba.




BONUS! BONUS! BONUS!!!


Ina makaranta kuma ma'abotan son littafan soyayya ko kuma na tsafi? To ku zo MRS SADAUKI ta yi muku gwanjon Books ɗinta akan farashi mai sauƙi,duk book ɗin 500 za ta bar muku shi ne a 300 kacal,wanda kuma yake 700 ko sama da haka za ku same shi a 500 kawai .Me kuke jira kawai ku tuntuɓe ta WhatsApp +22795045822. Domin ku kwashi garaɓasar.
[02/12 à 15:50] MRS SADAUKI 💫: *MAFIYA*☠️



LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️


*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)


*Lambar waya:* +22795045822


*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
_____________________




14




Sai da Zainab ta ci kuka ta ƙoshi sannan ta shiga toilet.Tana shiga ƙarƙashin shower tunaninta ya soma nuna mata ga HAROON nan tsaye tare da ita suna wanka tare da wasanni irin na ma'aurata.Murmushi ne yayi nasara bayyana a kyakkyawar fuskarta wacce a ɗazu take shimfiɗe da baƙin ciki.Tamkar wata zautata haka take murmushi na wasar ruwa da niyyar nan HAROON ne take watsa ma su haɗi da yi masa shagwaɓa.Towel ta ɗaura ta fito ,sai ta tarar da Inna zaune bakin gado.Ta ƙara sakin ranta kafin ta ce “ Inna?”


“Ungo wannan ki sha,su kuma waɗannan ki dinga zuba a abinci kina ci yaji ne” cewar Innar tana mai miƙa mata kofi.Karɓa ta yi ta zauna tare da yin Bismillah ta soma shan madarar har ta shanye,sai da Inna ta ƙarara jadadda mata kar ta saki ta yi wasa da su kafin ta fice.Ita kuwa tsaf ta shirya cikin riga da wando na bacci ,ta yi sallar isha'i sannan ta zauna ta soma duba takardun jarabawar da ta yi wa ɗalibanta.Sai dai sam hankalinta ya kasa kwanciya sai aukin tunanin HAROON ,wayarta ta ɗauka ta kira Ammy bayan sun gaisa sai ta yi shiru.Can dai ta ce “ ina HAROON ?”


“Yana ɗakinsa,ko na baki shi?”


“A'a turo min dai lambarsa” sai kuma ta yi saurin kashewa tana dafe saitin zuciya haɗi da waro ido.“ Zainab mi kika yi haka?” ta tambayi kanta,ƙarar shigowar saƙo ta ji da sauri ta duba sai ta ga lambar ce aka turo mata sai da ta yi ta kallon lambar kafin ta yi saving da “ NAWAN” sai ta ɗora love daga ƙarshe.




Data ta kunna tana addu'ar Allah sa yana WhatsApp,tsawon lokaci kafin a nuno mata lambarsa mai ɗauke da hotonsa da Ammy su duka biyun suna murmushi.Da sauri ta ɗauki hoton sai ta yanke daidai nasa kawai ta tsura masa ido can kuma ta rungume wayar tana mai jan numfashi.Duba takardun da ba ta yi ba kenan ta je ta haye bed,MP3 ɗinta ta kunna ƙira'ar Sudais ta soma tashi tana biyar karatun tana kallon hoton HAROON a haka bacci ya ɗauke ta.




Washegari sai da ta tsarkake jikinta kafin ta gabatar da sallah saboda mafarkin da ta yi.Bayan ta gama ta yi shara da gyaran ɗaki sannan ta ɗumama abincin kari,sai kuma ta je ta yi shirin makaranta.Cikin ƴar ƙaramar kula ta zuba abincinta kafin ta yi wa Inna sallama,sai da ta zo bakin titi sannan ta samu abin hawa .Tana isa makaranta ɗalinta suka fara gaishe ta ita kuma ta wuce cikin aji,sai a lokacin ta ci abincinta cike da tunanin mafarkinta na jiya.Sai da ta yi da gaske sannan ta hakice tunanin HAROON daga ranta ta gabatar da darasi wanda shine ya zama na ƙarshe.Tana komawa gida aka shafa mata lalle,don dole ta haƙura tuni kuma aka fara shirye-shiryen biki kamar yadda abin ya zo mata a bazata haka su ma dangin da abokai amma duk da haka sai da aka fitar da anko.Har aka kawo lefe aka yi ɗaurin aure ko sau ɗaya Sheikh Ali bai kira ta ba haka ita ma ta share shi ko saƙo ta kasa tura masa.Yanzu ma da ake ta hidimar biki babu abin da take sai tunanin da ya daɗe da aurenta,na masoyin da igiyar aure ta yi mata iyaka da shi .Da zarar ta tuna cewa yau ɗin nan wani zai karɓe budurcinta sai hawaye su yi ta mata zuba,mutane kuwa tunaninsu kukan rabuwa da Inna ne kasancewar ita ɗaya ce tal ta rage musu a duniya duk ƴan uwanta sun rasu tun suna jarirai.




Har aka yi kiran sallah magrib Malama Zainab na kuka,da aka ce ta je ta yi wanka domin shirin kaita ɗakinta ji ta yi kamar ta fasa ihu ta yadda kowa zai fahimci tsananin damuwar da ta luluɓe sirrin zuciyarta.






Da ta yi wankan sai da ta yi sallar isha'i sannan mai kwalliya ta soma yi mata simple make-up ba irin tarkacen nan ba.Doguwar rigar less fari sol ta saka sannan ta ɗora alkyaba sama a haka ma sai da aka ƙara ɗora mata darar amare.Sai da aka yi hotuna da bidiyo da abokan arziki kafin a ƙara yi mata wata nasihar,daga nan aka ja ta zuwa can waje inda motocin da ango ya turo suke jira.Banda kuka babu abin da Malama Zainab take yi amma hakan bai hana aka kai ta ɗakinta ba,har aka gama addu'a kuma ba ta buɗe fuskarta ba.Nan mutane duk suka watse yayi sauran ƙawarta guda tal Hafsat wacce sai yanzu ta samu damar yi wa Zainab ɗin nasiha “ kukan nan ya isa haka don Allah! Abin da muke ta jiran ranar nan amma ta zo sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login