Showing 15001 words to 18000 words out of 44401 words

Chapter 6 - MAFIYA Part 1 By MRS SADAUKI .txt

03 Dec 2024

3199

hankali. A wani lokaci, tunanina ya lummm a gabana ya kasance da dabara irin ya ɗan jinkirta abin da na yi .


Na fara firgita sosai, amma na gaya wa kaina tabbas tunanina ne. A daren nan na yi bacci a kan kujerar falo, kuma madubin yana can hangen nesa na. Da tsakar dare na tashi ba zato ba tsammani, sai na ji wani yana kallona lokacin da na buɗe idona, sai na ga inuwa a bayana a cikin madubi, kamar a mafarki amma gaske ne.






Na juyo ba zato ba tsammani sai dai ba komai babu kowa a cikin ɗakin .Zuciyata ta fara bugawa ba zato ba tsammani na sake duba madubin, kuma wannan lokacin ya fi muni,inuwar ba ta da kyau, yana can a cikin tunanina can tsakiyar madubi amma ba a cikin ɗakin ba. Ita wannan inuwar irin siffata ce da ita amma jikinta duk ko ta ina jini ne ke fita,yadda na ƙure ta da ido ita ma haka take kallona babu motsi. A yadda ake son na fahimta wannan na cikin madubi ni ne da kaina kamar yadda kowanne mutum in ya tsaya a gaban madubi zai ga kansa,amma ni nawa ya sha banban da na sauran.In na yi motsi shi na cikin madubin bai motsa wa yana nan a daskare kamar saƙaƙo,in kuma ni na tsaya ɗam ba tare da na yi wata alamar motsi ba sai na ga shi ya motsa. A firgice na bar ɗakin a wannan ranar ban dawo ba sai da safe.


Washegari, na yanke shawara mai tsauri. Na rufe madubin da farar ƙatuwar zanen gado. Tun daga wannan lokacin, ya kasance a can a ɓoye. Amma kuwa duk da na rufe shi har yanzu ina jin kasancewarsa. Wani lokaci ina tsammanin ina jin ƙararrakin hayaniya suna fitowa daga wajensa kamar surutu da sautin faɗuwar wani abu kamar tasa ko kuma an cilla dutse a rijiya.


Kamar wanda aka yi wa dole haka kuma na ƙi fitar da madubin,na ci gaba da rayuwa da shi har wata baƙar rana ta zo wacce ba zan manta ba.Ina kwance ina baccin bayan la'asar aka kira ni a waya Ammyna ta zame jiki ta faɗi babu hannu babu ƙafa ga kuma zuciyarta ta kumbura.Ko wanke fuska ban yi ba na ɗauki makullin mota,a ƙa'ida sai jibi zan yi jigilar dabbobi kamar yadda tsarin yake in na zo asabar sai kuma ranar Laraba zan koma can gida Agadas.Kwana ɗaya da wuni na yi a hanya kafin na isa,direct kuma asibitin da aka sanar da ni take na nufa,a yadda na tarar an banzatar da Ammyna sai na ji takaici ya rufe ni don babu wata kulawa ta musamman tsabar wulaƙanci ma kan tabarma take ba a gado ba.
Ba ta iya yin magana ,bakinta ya juye yawu na yi mata dalala,motsin kirki ma ta iyawa sai idonta da ta kafe ni da su masu cike da rauni da neman agaji a gare ni.


A wancan lokacin da na tambayi nurse dalilin ƙin bai wa mahaifiyata taimako yadda ya kamata sai ce min ta yi “ sai kun biya kuɗi na gwaje-gwaje,na gado,da kuma alluran da za a dinga yi mata tausar ƙafarta da ta sandare ” ƴan kuɗaɗen da na samu waɗanda sun kasance na uban gidana ne da su na yi amfani na bayar aka ba Ammy gado ,sannan da taimakon da ba a rasa ba.Dandanan goshinta ya fara fitar da zufa sai bacci,ganin haka sai yasa na wuce can gidanmu domin yin wanka.Mahaifina na tarar wanda shine silar duk halin da Ammy ke ciki,kayan jikinsa na tarar yana haɗawa da alamu garin zai bari.


Ina kawo daidai nan na kashe shower saboda a duk lokacin da nake tuna rayuwata babu gaɓar da na tsana irin ta Abbana.Cike da takaici na kimtsa na fito na zauna kan kujera,ina jin tabbas ya zama dole na mallaki matar Illia direbana.






ILLIA POV




Babu wani tashin hankali da ya taɓa shiga wanda ya wuce wannan,babban takaici ne yau ace ya miƙar matarsa ta aure ga wani namijin da yayi imanin cewa imani bai wanzu a ƙirjinsa ba ballantana ya sa ran ba zai keta haddinta ba.
Kamar wani marayan uwa da uba haka ya takure jikin katanga ya rungume Abdul gam a ƙirjinsa wanda tuni ya gaji da kuka yayi bacci,ido kawai Illiya ya ƙura wa ofis ɗin HAROON tunani iri-iri na ta zuwar masa .Ya san halin Mariya da tsoro tun a tashin farko za ta sallama kanta ko da kuwa bai yi amfani da tsafinsa ba.Yana nan jibge kamar kayan wanki ya ga ta buɗo ƙofa ta fito,da sauri ya nufe ta yana cewa “ me yayi miki?” ba ta basa amsa ba ta karɓe ɗanta ta yi gaba.Ya take mata baya yana kiranta,duk mutane na kallonsu amma ta ƙi tsayawa haka suka dinga yin tafiyar ƙasa su biyu har suka isa gidansu duk da kuwa uban nisan da ke da kwai.






“ Mariya mene ne haka? Ina tambayar ki amma kin yi shiru” Illiya ya faɗa bayan sun shiga ɗaki.
Ta dube shi da idonta da suka yi jajur tsabar kuka ta ce “ abin da ka kai ni dominsa shi yayi! Wato Illiya ban taɓa sanin cewa baka ƙauna ta ba sai yau amma ka sani wallahi na gama aurenka!” sai kuma ta wuce can uwar ɗaka ta soma haɗa kayanta.




Shi kuwa zaman ƴan bori yayi jin HAROON wai kusance ta,kukan baƙin ciki ya soma yi kamar ransa zai fita yana da kishi sosai amma yau yana ji yana gani an ɗauki abunsa mafi daraja an tozarta shi .Wata irin tsanar HAROON ce ya ji ta ɗarsu a ransa,ya ƙudiri aniyar zai yi masa aiki amma kuma tabbas shine ajalinsa......




My book is only 500 via 2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank DM +22795045822








Talla! Talla! Talla!!!




DULLAHZ CAKES AND MORE 💕




Ina jamaata mutanen kirki ji'bin arziki? Yan kurna, rijiyan lemo,bacirawa,da duk abunda y jibanci Nan Ina mutanena mutanen Kano kanawan dabo mutanen kirki mutanen da sukasan Kansu,


Ina mata yangayu wadanda basaso gayu y wucesu,biki gareki? Suna? Ko kwarya kwaryan liyafa qawata? Kinji labarinmu ko yenzu batun ke tafe gareki,


Munayin cake me dankaren dadi cake hadadde a musulmin farashi,akway cupcakes,samosa, spring rolls,Muna gashin kaji da kayan kwalam d maqulashe kala kala,09111648884


Yayata Muna girkin biki,suna,ko tarbon baki komi kikeso,inma grkine bakijinyi Dan Allah ki kira dullarz zatamaki shi nantake a gyaremaki cikin warmers me delivery ykaimaki,09111648884


Yar uwata inkinyadda d Allah kibamu yardarki bbu cuta babu cutarwa b ha'inci zaa mki komi fiyeda yenda ke zakiyi 09111648884


Call:09111648884
[30/11 à 07:46] MRS SADAUKI 💫: *MAFIYA*☠️



LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️


*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)


*Lambar waya:* +22795045822


*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
_____________________




12




Cike da takaicin Illiya da matarsa na dawo gida,ina shigowa da sanyi idaniyata na fara cin karo wato Malama Zainab.Cak na tsaya a bakin ƙofa jin zazzaƙar muryarta na fitar da sautin karatun Alqur'ani wanda ya zama barazana ga ruhina,ji nake tamkar an watsa mini ruwan zafi.
Tamkar Ammy ta san halin da nake ciki ta dakatar da ita da karatun ,“ Malama gobe in sha Allah mu ci gaba ga HAROON nan ya dawo,ƙaraso ku gaisa ” Ammy ta faɗa tana murmushi,sai da na je na ɗauki gorar ruwa mai sanyi na sha sannan na ƙarasa wurin su.


Ammy na fara gaishe wa kafin na zuba wa malamar ido,ta ɗago a hankali ta ce “ ya ƙarfin jikin?”


“Ai na ji sauƙi” na bata amsa ina mai ci gaba da kallonta,da dukkan alamu kuma ta tsargu da hakan don sai wani takure jikinta take.


“Ka zauna bari na kawo ma wani abu” Ammy ta faɗa tare da nufar kitchen,nesa da Malama na zauna ina son tantance ta amma sam babu wata ƙofar tauraronta da ke buɗe wacce za ta bani damar ganin sirrin ruhinta.




Na ja ajiyar zuciya na ce “ ya aka yi yau kuka fara karatu da wuri haka?”


Kamar mai tsoron magana ta ce “ ina da wani aiki mai muhimmancin ne bayan sallar magrib ɗin”


“Mene ne shi?”


Sai da ta ɗan ƙara sunne kai kafin ta ce “ dama... Dama wanda aka yi mana baiko ne ya d...” sauran maganar ƙarar fashewar gilas ta maƙale ta.


Ammy ce ta yi ɓarin lemun zoɓo,hankali tashe kuma ta bi ta cikin kwalbar tana mai cewa “ an miki baiko?”




“Eh tun shekaru uku da suka wuce ni da Sheikh Ali,ba ki dai ji ciwo ba ko Ammy?” ta ƙarashe da tambayar Ammy wacce ta zuba min ido,ƙila mamakin ganin ban wani razana sosai ba ko na tayar da hankali.




“Allah sa alkhairi,je ki direba ya mayar da ke” Ammy ta faɗa tare da zubewa kan kujera yayin da ita kuma Malama Zainab ta fice.A hankali na tashi na tsuguna a gaban Ammy na kamo ƙafarta da ke zubar da jini.Kwalbar na cire sannan na ɗauko ɗan akwatin da ke da kayan magani na shafa mata tare da naɗe ƙafar da bandeji.




“ Ka kuwa ji abin da Malama Zainab ta faɗa ?”


“Eh Ammy na ji”


“Shine kuma baka ce komai ba?”


“Ammy a kullum fa ke ce da kanki kike min nasihar cewa duk wanda ya yarda da Allah to komai nasa zai zo da sauƙi,kin ga kar ki damu Malama ba ta da wani miji da ya wuce HAROON zan je har gidan nasu na fallasa mata sirrin zuciyata ”




Ammy ta shafi sumar kaina tana wani ɗan murmushi kafin ta ce “ haka take yarona” na miƙe tare da sakar mata murmushi sai kuma na nufi step,a cikin kwanyata na soma jin ana yi min magana “ HAROON lokaci yayi da za ka fara amfani da powerka domin sato taurarin mutanen kirki,ta wannan hanyar ce zaka samu Malama Zainab ”


Kamar wani zararre na tambayi kwanyar tawa “ ta ya kenan zan soma?”


“Je ka fara yin wanka tukunna,sai ka je madubinka zai sanar da kai”


Haka kuwa aka yi,bayan na yi wanka na je na shiga cikin madubina.Direct ajin nan da ake koyar da karatu na shiga,yau ma Mr Zulu ne ke darasi akan allo yayi zanen baƙar mage mai jajayen ido yana kuma yin bayani.


“Baƙar mage , waɗanda galibi ana lulluɓe su cikin sirri da camfi, koyaushe halittu ne masu ban sha'awa, musamman a duniyar mayu da ayyukan sihiri.


Baƙar mage a zahiri suna ɗaukar kuzari mai zurfi, kariya da sihiri. A cikin wasu al'adun arna da sihiri, ana ganin baƙar fatar mage a matsayin mai kula tsakanin talikai, mai tsaro na ruhaniya. Ya ƙunshi ma'auni tsakanin haske da inuwa, bayyane da ganuwa.


Wataƙila wannan duality ne ya sa bokaye da matsafa suka zaɓi baƙar mage tamkar abokan hulɗa masu mahimmanci a cikin aikin sihiri. Suna kawo hikimar dare da ikon kewaya wuraren ruhi na ɓoye.


A cikin gogewar kaina, baƙaƙen ƙuliyoyi sun kasance sau da yawa jagororina da masu kare ni a lokutan canji ko haɓakar ruhaniya. Suna tunatar da ni cewa inuwa ba abin tsoro ba ne, amma illa fahimta. Suna ɗauke da sihiri mai hankali amma mai ƙarfi a cikin su, ƙarfin canzawa wanda ke ingiza mu mu wuce fiye da kamanni don rungumar ɗaukacin halittarmu.


Baƙar ƙuliya kuma alamun sa'a ne a wasu al'adu, suna kawo albarka da kariya ga waɗanda ke maraba da su cikin gidajensu. Kasancewarsu na iya zama abin tunatarwa akai-akai game da sihirin da ke kewaye da mu, yana ƙarfafa mu mu kasance a buɗe kuma mu yi maraba da mutane wanɗada ba mu sani ba da gaba gaɗi.


Shin kun taɓa haɗuwa da su a cikin ayyukanku ko rayuwar ku ta yau da kullun? Menene ma'anar waɗannan sahabbai masu ban mamaki a gare ku? ”


Hannu na ɗaga hakan yasa ya ce “ ina jin ka HAROON ”


Na ce “ ta ya za a yi mutum ya mallaki ita baƙar magen? Sannan mutum ɗaya zai iya ɗaukar ƙuliyoyi biyu a lokaci guda don yin aiki da su ko kuwa sai ƙwaya ɗaya kawai aka yarje masa?”




Mr Zulu ya bani amsa da “ a'a in kana so duk launinkan ƙuliyoyin da muka lissafa zaka iya aiki da su muddin dai zaka iya ciyar da su.Bari na faɗa muku wani sirrin iya ƙuliyoyinka iya ƙarfin tasirin alƙalumanka,mai son baƙar mage ina da su da yawa na sayarwa ga su nan na kawo” ya faɗa tare da buɗe wani tsohon akwatin ƙarfe .Cike yake da jariran baƙaƙen ƙuliyoyi duk idonsu kuma jajur suke ,nan fa duk kowa ya soma cewa yana so ganin kamar za su ƙare yasa da sauri ni ma na isa gaban akwatin don zaɓar tawa.Akwai ƙwaya ɗaya wacce ta banbanta da sauran ta fi su girma haka yanayin fuskarta ma kicin-kicin yake babu fara'a.




“Wannan nake so” na furta tare da kai hannu na ciro ta,Mr Zulu yayi min kallo kafin ya ce “ HAROON ka tabbata ?”
Ba tare da tambayar dalilin da yasa sai ni kaɗai ya yi wa tambayar ba na ce “ eh yalaɓai ita nake so ” ya saki ɗan murmushi kafin ya ce “ shi yasa Oganku ya ce kai ɗin na musamman ne taurarinka masu matuƙar ƙarfi ne” ni ma murmushin kawai na sakar masa,magen hannuna ta yi wani zillo ta ruga da sauri na take mata baya kawai sai na tsinci kanmu a wajen madubi a tsakiyar ɗakina.




Da ido nake kallon magen wacce ta haye bed ɗina ta yi min ƙuri da ido,da sauri na nufe ta na ɗauko ta na rungume.Sai yanzu na lura ashe namiji ne muzuru,kansa na soma shafawa na ce “ daga yau sunanka Tony” daga bakin ƙofa aka soma buga wa tare da kiran sunana “ na'am Ammy gani nan zuwa” na furta tare da tashi na buɗe mata,da faɗa ta soma “ HAROON me yasa kake son zama da towel,to in ka shirya ka fito ina son ganin ka” har za ta tafi sai kuma ta yi saurin juyowa tana kallon gadona,sai na kai dubana na ce “ Tony ne fa”


“Yaushe ka fara son ƙuliya ban sani ba?”


“Na sosa ƴar ƙeya kafin na ce zan yi miki bayani daga baya”


Ta fice,ni kuma na rufe ɗakin.A tsanake na shirya na ɗauki Tony muka sauka ƙasa sai wani kuka yake “minyau!”


Ammy ta ce “ Laure zuba ma magen nan abinci ƙila yunwa take ji,kawai haka nan ka kama ka rufe ta a ɗaki”
Tony ya wani zille ya bi Laure mai aiki can kitchen,wani tsohon plate ta samu ta zuba masa abinci tana masifa ƙasa-ƙasa “kawai don mugun hali ka rasa magen da za ka kawo cikin gida sai baƙa mtsww!” ta ja tsuki,ƙafa ta sa ta bugi Tony ya tsaya yana kallonta “ ni bari kallona shegiya da wasu ido nata kamar mayya” sai kuma ta fito.






Na dube ta na ce “ kin zuba masa abincin?” yau ne karon farko da na taɓa yi mata magana saboda ni da ƴan aikin gidanmu gaisuwa ce ke haɗa mu ita ma sai na ga dama na amsa.


“Eh ga ta can tana ci” ta bani amsa.
Na ce “ namiji ne ba mace ba,sunansa Tony ”


“Sai kace dai wani mutum yalaɓai ai duk ƙuliya da sunan mace ake kiranta” Laure ta faɗa cike da jin haushi tana mai ɗaukar kwanon abincinta ta kama hanyar fita tana gunguni ƙasa-ƙasa sarai kuma kwanyata ta sanar da ni abin da ta ce.








“Tun da baƙin hali gare mu don muna da kuɗi da kuma jiji da kai ki je an sallame ki daga aikin” na faɗa cikin ɗaga murya,da wani mugun sauri ta juyo tana kallona kafin ta zo da gudu ta zube a gabana tana bani haƙuri,tsakiyar idonta kawai na kalla na fahimci Laure irin mutanen nan ne waɗanda akan kuɗi babu abin da ba za su iya yi ba,sannan tuni hassada da baƙin ciki sun gama gurɓata ruhinta.Jin daɗina guda da Ammy ta gusa ba ta falon,na saki makirin murmushi na ce “ zan maido ki aiki zan kuma ƙara miki da wani wanda ya fi wannan albashi na san za ki iya ”


Ai kuwa ta washe baki tana cewa “ sosai yalaɓai in dai zaka bani kuɗi”
Na ce “ yawwa yarinyar nan Salima ƴar gidan Yakubu soja kin san ta ne?”
Ta ƙara washe baki ta ce “ Salima mai mage ko? Ai har gidansu Hajiya ke aikina”
“Yawwa a kanta nake son baki aiki”


“Koma mene ne zan yi Alhaji in dai zaka bani kuɗi”


“Ok za ki iya tafiya,gobe zan faɗa miki bayanin aikin naki ” ta miƙe ta tafi da ƙarfin gwiwarta,sai lokacin kuma Tony ya fito daga kitchen yayi tsalle ya ɗare kan cinyata na soma shafa bayansa ina jin wani irin daɗi na mamaye ni.




Ina nan zaune sai ga Illiya ya shigo fuskarsa kawai na kalla na fahimci damuwarsa,ya zo ya gaishe ni tare da zama kan capet idonsa suka fara tsiyaya.
“Ai zata dawo ba za ta iya barin ka ba,sai dai ka sani ban janye ƙudirina ba ya zama dole na ɗanɗani zumarta” na furta ina cije leɓena na ƙasa.


Da sauri Illiya ya ɗago yana cewa “ yalaɓai dama baka kusance ta ba?”
Na kawar da kai gefe ina kallon cikin idon Tony da nake tsintar wasu abubuwa a ciki.


“Yalaɓai wannan muzurun fa?” Illiya ya jefo min tambayar da tasa na maido dubana gare shi na ce “ faɗa min Illiya ta ya aka yi a kallo ɗaya har ka san muzuru ne? Kana da wankin ido ne ko yaya?”


Ya ɗan washe baki ya ce “ yalaɓai lokacin baya fa na ɗan taɓa aikin tsibo sai kuma na bari saboda kusan haukata ni jinnu suka yi”


“Ita ma matar taka da tsafi ka aure ta kenan?”


“A'a wallahi auren soyayya ne ko rubutu ban taɓa bata ba”


“Ya ake samun costumer Illiya ? Ina nufin malaman tsibo ta wace hanya ce za su bi domin ganin sun samu mutane da yawa?”


“Ta hanyar shiga gidan rediyo da tv,ka yi musu alƙawarin aiki kyauta ne sai buƙata ta biya sannan mutum sai bayar da abin sadaka”


Na saki murmushi na ce “ to ka shirya min zama da manyan ƴan jaridu da kuma wasu mutanen da za su bayar da shaidun ƙarya akan na yi musu aiki ya ci sun zo godiya”


Ya saki baki yana kallona kafin ya ce “ yalaɓai kuma bayar da magani zaka koma?”
Na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login