Showing 9001 words to 12000 words out of 44401 words
hannunsa tare da roƙonsa “ please Oga kar ka hukunta ni ta hanyar kai ni ɓoyayyar duniya” sai dai da alamu roƙon nawa a banza ne wai an tsikari kakkausa.Tuni ƙasa ta soma darewa ginin cikin ƙasa ya bayyana,idona na zubar da hawaye na tashi cikin iska kafin na yi nitso cikin dogon ramen a haka ƙasa ta rufe da ni ruf sai gani tsaye a gaban baƙar ƙofar nan a karo na biyu.
Yau ɗin ma Dōr̃anī ne suka buɗe min ƙofar tare da yi mini iso a ciki,sai dai fa wata jahar suka kai ni ba nan fara isa ba.
“Wannan karon kuma wane laifin ka yi mai yawa har Oga ya ce a kai ka sashen bauta ?” ya tambaye ni.
Ƙin basa amsa na yi sai ma tunanin yadda zan yi na fita na soma,“ fatan dai ba wani sirrin ƙungiyar ka fitar ba?”
“Ban fa iya surutun nan yau ka bar ni da abin da ya sha min kai” na faɗa cikin masifa,daidai nan muka iso wata duniyar mai cike da abubuwan ban mamaki mutum da jikin maciji,ko kifi,ko doki,mage mai ƙafa ta fi ɗari,ko kuma mage da kan mutum.Maciji mai magana,kare da shan sigari.
“Ina ne kuma nan? Me zan yi a nan?” na tambaya a firgice,banza suka yi da ni sai tafiya suke ina take musu baya har muka isa gun wasu tsofi.
“Ina ka samo mana ɗan saurayi kuma?” ɗayar tsohuwar ta faɗa tana wani kashe mini ido,yayin da wasu biyun suka taso suka soma shafa ta da sauri na soma ture su ina son guduwa.
Dōr̃anī ya ce “ ladabtar da shi za ku yi,shi ɗin yana da muhimmanci ga uwa MAFIYA don haka kar ku taɓa lafiyarsa”
Yana gama faɗar haka duk suka ɓata rai waɗanda ma suka yi min ƙawanya sun gusa daga jikina,su ma Dōr̃ānī tafiyarsu suka yi.
Wacce ta fi su tsufa duka ita ce ta miƙe tsaye ta ce “ ɗan samari biyo bayana ”
Dole dangin naƙi haka na take mata baya zuwa wani sashe mai cike da yana don ta cikinta ma muke bi muna wucewa,mun ɗan yi tafiya sosai kafin ta ja ta tsaya.
“Ruhinka nada ƙarfi sosai ta yadda har yanzu Octoba ya kasa karɓe shi duka duk da kuwa ka sayar da shi,uhum! Amma me yasa kake fusata shi haka? Ka san mene ne za a yi maka a nan ɗin?” tsohuwar ta tambaye ni.
“Mene ne zan yi a nan ɗin?” na tambaye ta tare da share duk sauran zancen da ta yi.
“Matso kusa ka gani” ta faɗa ,na ɗaga ƙafata na isa gare ta abun mamaki sai na hango duniyarmu ta Bil'adama.Wasu abubuwa ta dinga furta wa nan gidaje da ababen hawa suka dinga wuce wa kamar mai yin tariya har ta isa ga asibitin da aka shimfiɗe ni.
Wani irina na gani zaune kan gado Ammy na ɓare ayaba tana basa yana sha,gefe guda kuma direbana ne ya ƙura masa ido yana kallo.
“Ko ka san me yasa waccan mutumin yake kallon mai kama da kai?” tsohuwar ta tambaye ni.
“Eh saboda ba haka nake zama ba,sannan in zan ci abu da hannun dama nake riƙe shi ba hagu ba.Ban cika son mutum ya ƙure ni da ido yana kallo ba” ina gama faɗa sai na ga mai kama da ni ɗin ya mayar da ayabar a hannun dama yana cewa “ Ammy har yanzu hannun ga nawa ciwo yake,kai kuma lafiya ka tsare ni kana kallo? Fita ka ban wuri”
Direbana ya miƙe da sauri da ya kai bakin ƙofa sai da ya sake waiwaya wa,nan ɗin ma sai da ta tambaye ni “ me yasa ya waiwaya?”
“Saboda yi wa mutum tsawa da hantara ba tabi'ata ba ce” na bata amsa kai tsaye.
“To da zarar ka koma duniyarku ya zama dole ka kashe direban can”
Sai da na dafe ƙirji na ce “ saboda me?”
“Amsar na wurinsa” tana gama faɗa ta wani kamo hannuna muka yi suka tare da sauka can doron duniya mun iso bakin kwalta na ja na tsaya,ta wani ja hannuna tana mai cewa “ kai gara iya ruhinka ne kawai a nan gangar jikinka na can sama”
Haka motoci ke ratsawa ta cikinmu ba tare da mun kauce musu ba,wani gidan cin abinci muka je.Da murna take cewa “ tsawon lokaci kenan da ban shigo duniya ba ,ina son abincin nan ya kamata in nemi gangar jiki na shiga ta yadda zan ji daɗin abinci”
“Ta ya kenan?” ba ta bani amsa ba ta je jikin wata budurwa wacce ke tsaye jikin mota ita da saurayinta,a gaban idona tsohuwar ta shige jikin yarinyar.Ta ja hannun saurayin suka zauna ta yi odar kaji da lemun kwalba,“ yau sai na baka mamaki zan cinye dukkan kaji biyun nan” budurwa ta furta wanda a baɗini esprit ɗin tsohuwar nan ne.Aka kawo kaji biyu ta cinye su tasss ta sha lemun kwalba,tana gamawa ta fice daga jikin nata ta zo daidai inda nake tsaye tana dariya “ na tsani soyayya,yau na yi silar raba su” sai kuma ta ja ni muka tashi cikin iska muka koma can inda muka fito,gangar jikina na gani a tsaye tana zaman jirana sai dai ban san ya zan yi na koma ciki ba........
My book is only 500 via 2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank,DM +22795045822 .Saura page biyu na gama free page kafin nan zan yi discount ga mai so ya biya 400 sai ya tura min shaidar biya ta WhatsApp.
Talla! Talla! Talla!!!
DULLAHZ CAKES AND MORE 💕
Ina jamaata mutanen kirki ji'bin arziki? Yan kurna, rijiyan lemo,bacirawa,da duk abunda y jibanci Nan Ina mutanena mutanen Kano kanawan dabo mutanen kirki mutanen da sukasan Kansu,
Ina mata yangayu wadanda basaso gayu y wucesu,biki gareki? Suna? Ko kwarya kwaryan liyafa qawata? Kinji labarinmu ko yenzu batun ke tafe gareki,
Munayin cake me dankaren dadi cake hadadde a musulmin farashi,akway cupcakes,samosa, spring rolls,Muna gashin kaji da kayan kwalam d maqulashe kala kala,09111648884
Yayata Muna girkin biki,suna,ko tarbon baki komi kikeso,inma grkine bakijinyi Dan Allah ki kira dullarz zatamaki shi nantake a gyaremaki cikin warmers me delivery ykaimaki,09111648884
Yar uwata inkinyadda d Allah kibamu yardarki bbu cuta babu cutarwa b ha'inci zaa mki komi fiyeda yenda ke zakiyi 09111648884
Call:09111648884
[25/11 à 13:14] MRS SADAUKI 💫: *MAFIYA*☠️
LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
_____________________
09
Wannan tsohuwar ce ta nuna min yadda matsafa ke yi wurin fitar da ruhinsu daga cikin gangar jiki da kuma yadda ake yi a koma.
Cike da jin daɗi na isa inda gangar jikina take a tsaye kamar saƙaƙo,yadda ta koyar da ni ɗin da shi na yi amfani na koma ciki.Daga nan sabbin abubuwa ta soma koya min,irin yadda zaka juya tunanin mutum,kashe mutum ba tare da kaca masa wuƙa ko bindiga ba,yadda za ka cutar da wani normal mutum ba tare da shi kansa ya san an cuce shi ba.
Daga wannan kuma sai ta soma yi min wani bayani da ya tafi da ruhina.
“ HAROON ita duniyar MAFIYA da kake ganinta kowanne members yana samun power ne daga aikin da yake yi,wato iya yawan sacrifice iya adadin yadda ƙarfin ikonka zai ƙaru.Samun power ƙwaya ɗaya ya fi a baka miliyan ɗari,saboda su kuɗin za su ƙare ita kuwa power zaka iya sarrafa ta sosai ta yadda za ka samu dubban abubuwa marar ƙirguwa.Ka ga ko ita wannan wacce kake so ko? To tabbas kana iya yin galaba a kanta muddin dai ka samu power dayawa.Bari na nuna maka wani sirri na musamman da ba kowa ya san da shi ba” sai kuma ta miƙe ta ɗauko wani tandun kwalli ta miƙo min.Na karɓa ina dubanta,ta ce “ shafa shi da idonka sai ka sanar da ni me ka gani”
Ban musa ba sai kawai na bi umarninta na shafa kwallin ga dukkan idanuwana,sanyi ne ya ratsa su kamar na ƙanƙara wannan ya sa na ɗan lumshe su.Ina buɗe su kuma na yi tozali da tsohuwar matar nan ta zama tamkar lagwami duk jikinta tattakaken ƙwarangwal ne babu kyawun gani.
Ta ce “ wannan kwallin yana taimakawa wurin gane taƙamaimai asalin mutum da kuma niyyarsa a kanka,sannan zai ƙara ma ƙwarjina ta yadda babu wanda ya isa ya kalle ka cikin ido ciki kuwa har da Ammynka”sai ta yi shiru na wani lokaci kafin ta ɗora da “abubuwan da suka fi kawo maki a Mafiya sune mata da ƙananan yara,sai kuma mahaukata.Kowanna daga cikinsu da tasa rawar da yake takawa,in kana son a kowace irin jarabawa ko sabga taka ka yi nasara to da buƙatar ka yi sacrifice na ƙaramin yaro da bai balaga ba...” da sauri na katse ta da tambayar “ amma saboda me?”
“Saboda ƙwaƙwalwa yaro a wanke take babu komai cikinta na tunanin wata matsala,sannan zuciyarsa ma haka fara ce fesss babu baƙin cikin kowa .Bakinsa kuwa gaskiya ce tsagwaron ta,irin haka ne zaka samu wasu mutanen da daɗin baki in sun yi magana sai ka ji tasu ta fi ta kowa”
“Su kuma mata me yasa ake son sadaukar da su?” na tambaya.
Ta yi wani murmushi kafin ta ce “ akwai wanda ya fi mace wuyar sha'ani a duniya? Ita fa kamar sawun keke take baka gane gabanta ballantana bayanta ,wannan ya saka Mafiya ke da buƙatar mata.A sassan jikin mace akwai waɗanda in aka yi tsafi da su aikin ya fi kyau ,daga ciki akwai al'aurarta da kuma mamanta,abu na ƙarshe kuma shine ana yi mata wankan ƙaddamawar sai namiji yayi amfani da ita irin haka ne ke janyo farin jini da dukiya mai tarin yawa”
Na jinjina kai na ce “ su kuma mahaukata fa wane dalili ne?”
Kai tsaye ta bani amsa da “ a gaskiya sabbin members na MAFIYA waɗanda suke son yin kuɗi sun fi amfani da mahaukata,dalili kuwa shine shi hauka launin cuta ce da ke zuwa daga ƙwaƙwalwa wasu ta jinnu ce wasu kuma haka aka haife su da ita,to ita kanta wannan launin cutar tana da matuƙar muhimmanci a mafiya tana sa member ya ji gamsuwa fiye da in da mutum mai hankali ne ka kusanta”
Shiru na yi ina nazari,abin da na ƙara fahimta game da Mafiya wani rikitacen al'amari ne marar kyau.Duk abu na ƙwarai a wurin su ba mai kyau na ne sai gurɓatace,“ to amma yin mu'amala da mace yayin jinin al'ada fa me yake ƙarawa?” na jefo mata tambayar.
“Yin haka tamkar rufe ƙofofin taurarin ita macen ne,sannan duk wasu lamurranta za su iya kwaɓe mata yayin da shi kuma namijin rayuwarsa ta ɓoyayyar duniyar za ta yalwanta ”
Kasaƙe na yi ina zancen zuci ‘ kenan so ake duk na disashe taurarin Malama Zainab?’
“Bari ka ji HAROON ,babu abin da sheɗanu suka fi ƙauna irin warin jini musamman na al'ada yana da matuƙar muhimmanci a duniyarmu”
“Wane irin sheɗanu kuma?” na tambaya kamar wani gara.
Sai da ta sheƙe da dariya kafin ta jefo min tambayar ta saka zuciyata tsananta bugi,“ kai a tunaninka kai mutum ne? Bani amsa kai mutum ne?” shiru na yi na kasa cewa komai.
Ta ci gaba da cewa “ ka sani tun ranar da ka kwashe kayanka a gaban Manzo ka fita daga sawun mutane,kai sheɗani ne HAROON !” ta faɗa cikin wani sauti wanda ya saka yanar da ke yaɓe ta ko ina ta soma kaɗawa kamar ana iska.
“ Tashi ka bani wuri” ta faɗa cikin fushi,da sauri na ce “ na fita na je ina? Ki yi haƙuri amma ni ban ga abin ɓacin rai ba” ina gama rufe baki ta ja hannuna ta matso ni kusa a nan take madubina da ke can gida ya bayyana a nan.
“Wannan ita ce siffar mutum? ?” ta tambaye ni tana nuna ƙwarangwal ɗin da ke cikin madubi ,na girgiza kai na ce “ a'a ba mutum ba ne fatalwa ce”
Madubin ne ya ɓace ita kuwa sai ce min ta yi “ ai HAROON gwara fatalwa da kai,saboda kai sheɗani ne na musamman.Wai ma mene ne dalilin Oga na zaɓar ka alhalin ga dukkan alamu baka san muƙamin da ke jiran ka ba?”
“Muƙami?” na maimaita.
Dōr̃ānī ne ya shigo yana mai cewa “ lokacin komawar ka yayi” haka na bi bayansa muka fita.
Sai da ya kai ni wani sashe aka yi min wanka da wasu korayen ruwa sannan na ci na sha kafin yayi min rakiya zuwa bakin ƙofa.Yau ɗin ma kamar kullum haka ƙasa ta dare na fito sai dai fa wani uban canji na ji,jin kaina nake yana hayaƙi yayin da kuma zuciyata nake jin tamkar an yi min musanyar ta,sauran tausayin da ya rage min ya kau a yadda nake ji ko wuyan jinjiri zan iya murɗe wa ya mutu.Ban gama mamakin kaina ba sai da na ga sauran members sun miƙe suna gaishe ni cike da girmamawa,yayin da shi kuma Oga yayi kicin-kicin da fuska haɗi da nuna min wata kujera da aka ƙawata ta da ado.A yau sai na yi wa Oga dubin uba mahaifi wanda kuma ban san dalilin yin haka ba,zuwa na yi na zauna nan ɗin ma wani sabon canji na ji amma dai na yi shiru ina ta nazarin komai daki-daki.
“Daga rana irin ta yau na wakilta HAROON matsayin mataimakina wato shugabanku,in ba ni ga wuri shi zai ɗaukar matsayina sannan duk wani hukuncin ƙungiya da za a zarta ko ya shige muku duhu shine zai bada umarnin ƙarshe” Oga na gama faɗa suka shiga taɓa min kafin ya sallame su wurin ya zamana sai mu biyu kawai.
“Wannan ɗin duk na mene ne Oga?” na samu dakyar na tambaya.
Ya bani amsa da “ tun da aka kafa ƙungiyar nan kai ne na farko da ke iya maida min martani, wannan yasa na baka wannan muƙamin kana iya tafiya” ban sake ce masa komai ba na soma yin tsafin da zai kai ni inda mai kama da ni yake,aka yi katari kuwa yana cikin mota direba na tuƙa shi.
Bayyana ta cikin motar yayi daidai da lokacin da direbana ke ƙara saita madubin gaba na mota,yayi ƙara tare da sakin sitiyarin motar sai a lokacin ɗayan ya ɓace saura ni.Na tashi da sauri na tsayar da motar tare da zama gefensa,direba ya dafe zuciya yana kallona kafin da sauri ya maido dubansa gare ni sai na fahimci tabbas ya ganmu mu biyun duka.
Na saki murmushi na ce “ shi yasa bin didigi da ganin ƙwaf bai da kyau,duk yawan sa idon bai yi maka ba sai da ka nemo yadda za ka yi ka tantance shin mu biyu ne ko a'a .To ka tuƙa motar nan izuwa wani wurin cin abinci na ga alamun har da yunwa kake ji daga nan sai na aika ka barzahu”
“Yalaɓai don Allah ka yi haƙuri!” ya furta tare da ƙoƙarin fita sai dai tuni na ƙargame dukkan ƙofofin yayin da kuma na saka motar ta soma tuƙa kanta da kanta .......
My is only 500 via2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank DM +22795045822 saura page ɗaya na gama free page in sha Allah.
Talla! Talla! Talla!!!
DULLAHZ CAKES AND MORE 💕
Ina jamaata mutanen kirki ji'bin arziki? Yan kurna, rijiyan lemo,bacirawa,da duk abunda y jibanci Nan Ina mutanena mutanen Kano kanawan dabo mutanen kirki mutanen da sukasan Kansu,
Ina mata yangayu wadanda basaso gayu y wucesu,biki gareki? Suna? Ko kwarya kwaryan liyafa qawata? Kinji labarinmu ko yenzu batun ke tafe gareki,
Munayin cake me dankaren dadi cake hadadde a musulmin farashi,akway cupcakes,samosa, spring rolls,Muna gashin kaji da kayan kwalam d maqulashe kala kala,09111648884
Yayata Muna girkin biki,suna,ko tarbon baki komi kikeso,inma grkine bakijinyi Dan Allah ki kira dullarz zatamaki shi nantake a gyaremaki cikin warmers me delivery ykaimaki,09111648884
Yar uwata inkinyadda d Allah kibamu yardarki bbu cuta babu cutarwa b ha'inci zaa mki komi fiyeda yenda ke zakiyi 09111648884
Call:09111648884
[27/11 à 09:31] MRS SADAUKI 💫: *MAFIYA*☠️
LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
_____________________
Last free page
10
Ni kaina ban san taƙamaimai ina ne motar za ta je ba,gudu take tamkar aljani ne ke tuƙa ta.Cikin abin da bai wuce minti biyu ba har mun fita daga cikin garin Yamai mun shiga ƙasurgin daji sai a lokacin kuma motar ta tsaya cak tare da buɗe kanta.Na fito zuciyata na sake azalzala banda wani buri baya da na kashe direbana wanda har izuwa yanzu bakinsa bai gushe da bani haƙuri ba.Finciko shi na yi da sauri ya zube kan gwiwansa tare da kama ƙafafuna ya ce “yalaɓai ka yi mini rai ,na yi maka alƙwari zan kasance bafaɗenka mai yi maka hidima.Zan zama tamkar Kare da mai ikonsa,ka yarda da ni zan yi maka duk abin da kake so amma kar ka kashe ni ina da buruka masu tarin yawa da nake son cikawa kafin na bar duniyar nan!”
Cikin ƙaraji na ce “ Illiya ka tabbata duk abin da nake so za ka yi shi?”
“Eh yalaɓai koma mene ne zan yi” ya amsa mini cikin haƙiƙanin gaskiyarsa.
“Za ka zama mataimakina kamar yadda ka ce akwai ayyuka masu tarin yawa da za ka yi min,in ka kuskure kuwa ka sani daidai yake da fitar numfashinka ”
“Na gode sosai yalaɓai” ya furta tare da tashi har yanzu jikinsa bai bar rawa ba,haka muka shiga mota na lumshe idona ina jin wani matsayi ya hau kaina saboda na fara samo wa ƙungiyarmu member sannan duk wani wanda ya shigo ta sanadiyar ka to a ƙarƙashin kulawarka yake kamar yadda doka ta tsara.
Ko da nake buɗe ido sai na tsinci kanmu a tsakiyar babban titin Yamai,na ɗan saki murmushi na ce “ Illiya na tambaye ka mana”
“Eh yalaɓai ina ji tambaye ni” ya faɗa murya na rawa.
“Matanka nawa?”
“Matata guda yalaɓai da kuma yaronmu ɗaya” ya bani amsa a tsorace.
“Zuwa gobe ka kawo min ita a babban ofishina ina son ganinta” na faɗa cike da gadara.
“Yalaɓai ai ba ta yi makaranta ba”
“Yaushe na ce ma zan ɗauke ta aiki ?” na yi masa tambayar a tsawace.
Ya ce “ka yi haƙuri yalaɓai”
Na juyar da kai ina kallon titi har muka isa gida,ina fita sai da na tsaya ina ƙarewa Illiya kallo gajere ne shi baƙi yana da ƴar ƙiba amma ba sosai ba,idonsa irin na munafukan mutanen nan ne