Showing 21001 words to 24000 words out of 56271 words
Chapter 8 - KURKUKUN KADDARA 3 Original Document Takun karshe by boss Bature .txt
maganar, ganin wani mugun kallo da chief owais Ya watsa mashi, nan take Ya haɗiye yawu ya soma ƴan kame kame
Rai amatuƙar 6ace yace"malam, fuce kabar ɗakin nan, meye alaƙarka damu da har zaka katse Prime minister Yana magana, wannan abune daya shafi dangin mu bana ka ba" Tsabar mamakin kalaman Owais Yasa kowan nan su Ya dube shi, musamman Hajiya saratu ta muzanta da jin cin mutuncin da Owais Yayima mijinta.
Babu kunya Pravin Yace"Owais kai har yanzu yarone, duk abunda zaka fada min ba zan ji haushi ba, Ina yi maka uziri, kuma magana da kaga Inayi don in kare dangin ku ne saboda halaccin da kuka Yi min....." Azafafe Owais Ya yunƙura Ya miƙe tsaye, Yana naɗe hannun rigarshi tamkar Mayun wacin zaki haka Ya tunkari Pravin, An rasa wa zai dakatar dashi, kafin Owais ya ƙaraso Pravin yayi saurin nufar ƙofa ya buɗe ya fuce yana huci Ya maida ƙofa Ya datse.
Juyawa owais yayi ya koma inda ya tashi ya zauna.
Da buɗar bakin Prime minister sai cewa yayi"My son ka yi abunda Ya dace" wannan maganar Ta hateem ta ta6a zuciyar Hajiya saratu
Ranta a6ace tace"yaya hateem, kana goya mashi baya saboda Yaci mutuncin mijina"?
Prime minister bai tanka mata ba, bai kuma ɗago da ido Ya kalle ta ba. Hakan Ya ƙara 6ata mata rai, harara tadinga jefawa Owais Ko kallo bata ishe shi ba, baima san tana yi ba.
Shi dai baba Obie, Ya zubawa sarautar Allah ido, don wannan fadan Yafi ƙarfin shi.
His excellency abdul Razak ne Yace"Owais, Kai muke sauraro muna son jin ƙarin bayani dangane da Yaron daya rikiɗa da kuma Yarinyar dake atare da shi"
Kusan mintuna da Yin maganar abdul Razak Kafin Ya furta"Marayune su goma sha ɗaya nake ruƙo a hannuna, dukansu agidana suke da zama, a ƙarƙashin kulawata," Iya abunda Ya furta mashi kenan
"A ina ka tsince su"? Shiru yayi bai bashi amsa ba Har saida His excellency abdul Razak Ya maimaita mashi maganar a tunaninshi kobai ji mai yace bane
"Sojojin america ne suka tsince su A daji, shine suka damƙa case dinsu a hukumarmu, saboda Yaran sun faɗi cewa Su Ƴan Nigeria ne, ɗaya daga cikin Yaran ma akwai mahaifinta mun same shi, muna zargin masuyin garkuwa ne suka sace su daga Ahlin su, shi kuma yaron aljanune suka shige shi a dajin sune suke canza mashi halitta, wannan shine Iya abunda nasani dangane da su" atakaice Ya ƙare bayanin.
Gyaran murya senate Lafeef Yayi kafin Ya soma magana
"Mun riga da mun Yanke hukunci, Bamu buƙatar Yaran su ci gaba da zama a estate dinmu! Saboda Lafiyar mahaifinmu, sannan mun yanke alaƙarka da su, shi kuma prime minister zai koma canada adai dai date din da aka bashi umarnin komawa, don ba zamu lamunci gangancinku na son taimako Ya jefa rayuwar Ahlinmu cikin matsala ba, don ni har Yanzu ban yarda da Yaran ba, tunkafin ma in gansu Hankalina bai kwanta da su ba, tayaya za'a tsinci Yara adaji sannan akawo su estate dinmu? Meyasa su sojojin american basu ruƙe su ba a hannunsu ba? Saboda sunsan ba alkhairi bane shiyasa suka manna maku su" fuskar shi babu annuri yayi maganar.
Hankalin prime Minister Ba ƙaramin tashi yayi ba Jin abunda suka ce, kasancewar shi mutunne mai biyayya ga yayyan sa ko kara suka ajiye mashi bai iya ƙetare wa, mutun ɗaya ne zai Iya dakatar dasu wato mahaifinsu sai dai ga dukkan alamu shima Yana goyan bayan hukuncin da suka Yanke,
Muryarshi asanyaye ya furta"kada kuyi min haka, saboda ku nazo ƙasar nan a ƙalla nakusa shekara ban samu damar zuwa gida ba, Yanzu Idan na koma bansan ranar dawowa ba, Baba ka sanya baki a maganar nan"
His excellency Deen dake zaune Yace"Idan saboda mu kazo ƙasar nan, kada ka damu, ka tafi kawai mu zamu zo inda kake, idan ma takama duk sati zamu Iya shigowa Canada kasan bamu da matsalar abun hawa" ya faɗa yana ƙara jaddada mashi"zamu Iya barin aikinmu mu ɗauki hutu saboda kai, munyi maka alƙawarin hakan, zamanka a ƙasartamu ne bamu yarda da shi ba, don ba zamu yi gangancin da zaka cutu ba har wani abun Ya same ka, Idan ka manta wanene kai bari in tuna maka, prime minister na ƙasar canada" duƙar da kanshi ƙasa yai hawaye tuni sun cika idanuwanshi, bakomai yake jimawa ba face Yaron daya ƙwallafa ran shi, yasan idan harya haura ƙafa yabar ƙasar nan da wuya su sake haɗuwa, watakil ma daya daga cikinsu yabar duniyar batare da sun yi tozali da juna ba.
Jikin Chief owais yayi sanyi laƙwas, hankalinshi na akan prime minister, shi kadai Yasan damuwarshi
His excellency abdul Razak ya numfasa kafin ya ɗaura da cewa"kai kuma Owais, ba zamu hana Ka Yin aikin ka ba, sai dai babu zancen Yara su cigaba da zama agidan nan, ka kaisu gidan marayu ka haɗa su da wadanda zasu cigaba da rainonsu"
Takaici Ya hana Chief Owais furta masu komai, gaba ɗayansu hankalinsu ba akwance Yake ba.
A hankali Baba Obie Yake kallon fuskar Prime minister data Chief owais, ga dukkan alamu Ya fahince su sai dai Yana jin tsoron wani abu Ya same su ta silar taimakon da suke Yi, shiyasa bai dakatar dasu senate lateef ba.
"Baba, dan Allah kace wani abu, nasan zaka fahimce ni, wallahi Ina ƙaunar Yaron, baka ganshi ba Yana kama dani da Nazli, komai namu iri ɗaya kamar ni na haife shi" muryarshi tamkar zai fashe da kuka yayi maganar, basu ta6a ganin raunin prime minister ba sai Yau da Allah Ya jarabce shi da ƙaunar wani bare
"Hateem! Wannan bai shafe mu ba, kowani ɗan adam yana da masu kama dashi a duniyarnan, shi kuma mugun mutun ba'a gane shi a suffar shi yakan shiga cikin mutanan da yake hari yayi rayuwa dasu na tsawon lokaci Yana kyautata masu rana ɗaya yake tarwatsa su da makircin shi, na fadi wannan maganar ne don ni har yanzu ban yarda da yaron ba, dashi da sauran ƴan uwanshi, mutanan da aka tsinta a daji, wama yasani ko ƴa'ƴan aljanu ne kuka dauko mana" senate Lateef ne ya faɗa Yana watsa hannayen shi.
A hankali prime minister Ya zura hannu cikin aljihu ya ɗauko wayarshi, wadda tun safe rabon shi da ita, a gida yabarta gudun kada atakura mashi da kiraye kirayen waya, sai ɗazu da suka shiga gidan Ya kar6eta daga hannun gimbiya mujeedat.
Layin Sharufudeen Ya dannawa Kira, bugu uku Yai picking,
"Ina agida, dan Allah kazo, idan ba haka ba komai zai Iya faruwa"
On the other hand muryar sharafuddeen Ta amsa mashi da toh, gani nan zuwa, ka kula min da kanka" amsa mashi yai da toh kafin yai rejecting kiran
"Meye amfanin Kiran Sharafudden da kayi? Dakai dashi duka a ƙarƙashin ikon mu kuke, mune agaba daku" cikin nuna isa senate lateef Ya furta maganar
Cikin sanyin murya Hateem Yace"nasan da hakan Yaya, amma shi zai Iya fahimtar zuciyata fiye da kowa, kuma zai kwantar min da hankalina"
"Kana nufin mu bamu Iya kwantar maka da hankalinka? Kodan saboda shine shaƙiƙinka"? A harzuƙe senate Lateef Ya furta maganar
Da sauri Baba Obie Yai masu gyaran murya gudun kada su fara Yi mashi ƴan ubanci abun da Ya tsana arayuwarshi.
Gaba ɗaya Hankalinsu ya dawo kanshi"Ya Isa Haka! ya Isa, bana son nasake Jin wani Ya furta magana acikin ku" Shiru sukayi batare da wani ya kuma cewa Uffan ba
"Baba abincin fa Yana hucewa, Yakamata Kaci" hajiya saratu ce tayi maganar cikin nuna damuwarta
Kallon Owais yayi nan take Ya fahimci me Yake nufi
Hannu owais Ya sanya cikin plate din da hajiya saratu ta zuba mashi abinci
Ya soma ɗebowa Yana bashi abaki Yana ci,
Hakan Ya ƙara 6ata mata rai, wato ita ta bashi abinci da hannunta Yaƙi Ci sai Owais daya fi ƙauna, shi ya za6a ya bashi abinci
Bazata juri kallon su ba, miƙewa tayi tana fadin"Baba Allah Ya ƙara Lafiya, Ni zan wuce ɗaki" bata jira amsar da zai bata ba tayi saurin fucewa daga ɗakin.
Senate latef ma ranshi ya sosu, duk irin rashin ɗa'ar da Owais Yayi ma Pravin baba obie bai dakatar da shi ba, after that Ya sanya shi bashi abinci abaki, bayan Hajiya saratu itace tafara Yunƙurin bashi amma Yaƙi kar6a, ba tun yau ba ya saba nuna banbanci akan Sauran Jikokinshi da Owais, Hatta Ya'yan Hateem Yafi Ji da su akan nasu me hakan ke nufi"? Aranshi ya saƙa maganar
(Nidai nace na shiga uku, Kada afara Ƴan uba A family Obinna, Rikicin zai haɗe mana)
Yayin da chief Owais Yake ba baba Obie abinci abaki, Ya tsare shi da ido Yana bin shi da kallon so da ƙauna kamar zai haɗiye shi, Lemu mai sanyi ya zuba mashi a cup Ya miƙa mashi, Ya sanya hannu Ya kar6a Yana sha, har cikin ranshi Yaji dadin hakan aduk lokacin da ranshi ya 6aci indai Owais Yana atare dashi wani irin sanyi ne yake ratsa zuciyarshi tuni yake neman damuwar Ya rasata.
In a respectful voice Chief Ya soma yi mashi magana, ta yadda babu mai iya jin su.
"Kai kadai ne zaka Iya fahimtata, saboda kai ka raine ni tun ina ƙaramina, aduk lokacin da na sanya buri akan abunda nakeson cimmawa kaine kake ƙarfafa min gwiwa don ganin nakai ga matakin nasara, babana kada ka bari wannan karan in faɗi ƙasa, yakamata ka sanya baki awannan maganar, kasan bazan ta6a kawo wani abu da zai cutar dakai ba, Haƙƙina ne in kareka daga dukkan wani abun farmaki, yaran nan mutanene kamar kowa, basu da niyar cutar da kowa, saida na zurfafa bincike akansu na tabbatar da hakan tukunna na kawosu cikin gidana, bazan Iya yin nesa da su ba, Kuma bazan Iya dakatar da hukuncin da iyayena suka zartarba, amma kai zaka Iya dakatar da su,' cikin tausasa harshe Ya ƙare maganar tare da ruƙo hannayen baba obie acikin nashi, Ya ruƙe su sosai.
"Baba, Yaran nan basu da kowa, suna buƙatar wadanda zasu tallafi rayuwar su, nasani ba dole saini zan taimake su ba amma na riga dana daukarwa kaina alƙawarin bazan ta6a rabuwa dasu ba, A yau ina so ka nuna min ƙaunar da kake Yi min, da goyan bayan da kake bani, baba kada ka bari arabani da yaran nan ko a tursasamin akan in fitar da su daga gidana......." yanayin yadda owais yake yi mashi maganar yayi matuƙar karya mashi zuciya, tuni jikinshi yayi sanyi laƙwas, launin idanuwanshi har sun ɗan canza kala.
Shi kadai Yake jin me owais Yake Fadi mashi, sauran saidai su bi da ido, prime minister dai tunda ya dukar da kanshi kasa bai ƙara dagowa ba, shi kadai Yasan abunda ke damun shi, zuciyarshi tafarfasa take yi tamkar ana rurata da garwashin wuta, Aranshi ya ayyana koda zai bar ƙasar bazai daina bin diddigin rayuwar yaron ba, bazai ta6a bari Ya wulakanta ba.
Lumshe ido Obie Yai a hankali ya ware su kan fuskar Owais
"Zanyi tunani akai" atakaice Ya furta mashi maganar, ajiyar zuciya chief owais ya sauke, ya riga dayasan ƙaunar da yake mashi bazai Iya jurar 6acin ranshi ba
"Allah ya ƙara maka lafiya kakana, da anjima kafin ka kwanta bacci zanyi maka tausarnan dana saba yi maka duk idan nazo nigeria, nasan zaka ji daɗi"
Dariya baba Obie Yai har hakoransa suka bayyana fafare ƙyal da su
"Owais ka iya fadanci, kasan duk wata hanya da zaka faranta min, Allah yabarmin kai jikana" amsa mashi yai da Ameen.
daga haka basu ƙara Yin magana ba, sai dai kallon juna da sukeyi jefi jefi, su sanate lateef sun zama Ƴan kallo, kamar hotuna haka suka zauna zugudun suna kallon su.
Bayan wani lokaci Jiniyar Motoci ta karaɗe Estate din, nan take ransu Ya basu cewar Mai girma sharafudeen ne Ya ƙaraso gidan, tun abakin entry hall din shiga falo, Security details dinshi suka dakata da take mashi baya kamar yadda ya basu umarni, shi kadai Ya shiga Gidan Cikin shiga ta alfarma tsadaddiyar shaddace a jikinshi launin kore, duk Inda Ya gifta masu aikin gidan a gaggauce suke russinawa su gaishe dashi kamar zasuyi mashi sujjada, A main falo din gidan Yaci karo da sheikh Imam tare da Taj zaune saman Royal sofa, Hankalinsu kwance suke tattauna fira atsakaninsu, sunyi jiran ganin mutanan gidan shiru basu fito ba har sun fara tunanin kodai babu lafiyane? Musamman lokacin da pravin ya fito daga dakin baba obie ko kallo basu ishe shi ba, har kallonsu yayi amma yaƙi tanka masu, hakan ya sosa zucuyarsu, haka itama hajiya saratu tazo ta wuce ta falon bata bi takansu ba, har ƙwara su twins sun gaishe da sheikh Imam, suka kuma gaida Taj kafin suka wuce.
Zuwan sharafudeen Obinna, Ya faranta masu rai, tunkafin Ya ƙaraso garesu Yake Fadin"wa nake gani kamar babana Imam malik," miƙewa Imam yayi ya nufe shi suka rungume juna kafin suka raba jikinsu
"Ashe rai kanga Rai? Baba Imam sai yau zansa ka a idona? Gaskiya nayi fushi" Ya faɗa Yana haɗe fuskarshi
Dafe kafaɗarshi sheikh Imam Yayi"Masha Allah, Sharafuddeen Bana ƙasar, shiyasa baka ganina akai kai, amma yanzu tunda nazo in sha Allah zan dinga shigowa Villa muna gaisawa'
Sharafudeen na murmushi Yace"Idan ma bakazo ba, Ni zanzo har inda kake, wallahi nayi farin cikin ganinka, tun yaushe kazo ƙasar"
Shiekh Imam Yace"Yau da sassafe Nayi sammakon shigowa ƙasar, saboda kiran da ɗan uwanka yayi min"
"Masha Allah, Ina fata komai lafiya"
Sheikh Imam Yace"lafiyalou, Ga abokin Aikin Owais Ku gaisa da shi" Ya faɗa Yana nuna mashi tajudeen dake azaune, kamar ya sanshi haka Ya nufe shi da fara'a, da sauri Taj Ya miƙe suka rungume juna, haƙiƙa yasha ruwan mamaki, bai ta6a ganin mutane masu ruƙe da babban muƙami da suke da sauƙin kai irin Hateem da ɗan uwansa sharafuddeen, yajima yana mamaki da al'ajabinsu, kowa nasu ne basu ɗauki duniya da zafi ba.
Raba jikinsu yayi daga na juna"yalla6ai sannu da zuwa, Ina wuni, Ya hidima da jama'a, ubangiji Allah ya taimaka"
"ameen mutumina, Ina fata na same ka Lafiya"da mamaki Taj yake kallonshi jin ya kira shi da sunan mutumina kamar yadda yaji ɗazu Hateem Ya kira shi da sunan
Ganin alamun ruɗu akan fuskarshi yasa mai girman sharafudeen cewa"Owais Ya fada min komai dangane dakai, ganinka ne kawai ban ta6a yi ba, nasan zakayi mamaki dana gane ka ba tare dana tambaya ba" ya faɗa yana sakar mashi murmushi, shima taj din murmushin yayi har cikin ranshi ya ƙara ƙaunar Chief owais.
"Babu isasshen lokaci, In sha Allah zan samu time din da zamu tattauna dakai" ya fada Yana bubbuga kafaɗar taj da hannunshi.
"Toh Yalla6ai, nagode sosai" kallon shiekh Imam yai"baba mu shiga daga Ciki" yai maganar tare da ruƙo hannunshi suka nufi part din baba obie,
Zama taj yayi akan sofa, fuskarshi ɗauke da murmushi, Ji yake tamkar ya zuba ruwa a kasa yasha, acikin ranshi ya furta"Allah nagode maka da haɗani da mutanan kirki acikin rayuwata"
Wayarshi Ya zaro daga aljihu ya soma tunanin Kiran Big guy don Yaji awani hali su Unaisah suke aciki sun ci abinci ko kuwa.
Kiran na shiga big guy yayi picking
"Ya mutumina kana Ina ne? Na dawo gidan na taras baku nan"
"Mun shigo gidan baba Obie ne mu dukanmu muna anan"
"Okey, Ina fata komai na tafiya yadda yakamata"
"Taya zan sani, nifa ka ganni nan a falo, Ina zaman jiran fitowarsu, Allah yasa dai mu ji alkhairi, don kuwa naga wannan ba'indiyan da kake bani labari sai mazurai yake yi, ko gaishe mu bai yi ba"
Sautin dariyar big guy ne Ya karaɗe kunnuwanshi
"Itama wannan matar, mai kama da su chief owais ta fito tagan mu bata gaishe damu ba"
"Dama ya za'ae ta gaishe dakai, taga baƙuwar fuska, matar da bata sakar ma bare fuska, sai dai shi sheikh Imam din ne dai bata kyautaba tun da aminin baban su ne, wata'ƙilma bata ganku bane shiyasa bata gaishe da shi ba"
Boss yace"nima nayi tunanin hakan"
"Shi kuma wannan gabjejen ƙaton dangin su kirishna, kabarshi kawai, mutumin banza, baida mutunci, shi da yazo cin arziƙi yayi kane kane a dangi" da zolaya big guy yayi maganar, taj yayi dariya cike da nishaɗi yake sauraron shi.
"Very soon zamu yi mashi korar kare daga family din, tun da ba gidan ubansa bane" acewar big guy gaba ɗayansu suka tuntsire da dariya
Bayan sun tsagaita Boss man Yace"dama na kirane don inji lafiyar ƴa'ƴana"
"Kai dai fadi gaskiya, Ko dai ka Kira Kaji Lafiyar Jarin ka, Ifrituwar Yarinya wlh ɗazu data la6e a bayan labule, naso ace ka bari chief Ya shaƙi wuyanta, Yasin sai tayi jinya a gadon asibiti, Yarinya sai ƙiriniya kamar ansanya mata battery" fashewa taj yayi da dariya
"Cin mutuncin Ya isa haka, Na lura baƙin ciki kake Yi da ita shiyasa ka sanya mata ido, Ni dai yanzu fada min suna ina.
Sai da Ya Mula Yasha Iska tukunna Yace"Sun ci sun ƙoshi, kowannansu Ya koma dakinsa, harma sunyi wanka sun canza sutura, Na rakasu dakin Danish sun ganshi, Yanzu haka kowan nan su Ya koma dakin shi,"
Ajiyar zuciya Boss man ya sauke"Alhamdulillah, Naji dadin jin hakan, inataso in tambaye ka ka tuntu6i 6angarensu Salsabeel"?
"Bakasan meya faru ba" nan fa big guy ya kwashe duk abunda Ya faru Ya sanar dashi, hankalinshi Ya dan tashi
"Bawan Allah jazz, abu baiyi dadi ba, Allah ya bashi Lafiya, In sha Allah zamu fidda lokaci muje duba shi, Har Yanzu suna a asibitin ne"?
" Na kira Major Waya Ya fada min cewa An sallame su, Jikinshi yayi kyau da sauki, naso