Showing 51001 words to 54000 words out of 56271 words
Chapter 18 - KURKUKUN KADDARA 3 Original Document Takun karshe by boss Bature .txt
da ruƙe hannun batool, suka juya atare suka nufi ƙarshen falon inda babu mai jin su
Shafa gefen fuskarta tayi da hannu tana fadin"meya faru? Chief ɗin Ya dawo"?
Batare da batool ta furta kalma ba ta miƙa mata Paper din hannunta
da sauri Unaisah ta sanya hannu ta kar6a, A fili ta karanta.
"How did you get into my room? And why are you crying at me like I'm a monster? nayi maki wani abu ne"?
Murmushin gefen fuska unaisah tayi"meyasa ki kuka? Faɗamin?
Tana faman jan numfashi tace"tsoro ya bani, ya damƙi gashin kaina da hannun shi kuma babu kaya a jikinshi, short towel ya ɗaure a qugunsa.... " tun kafin ta ƙare maganar Unaisah ta tuntsire da dariya
Batool dake kallonta ganin tana yi mata dariyane yasa ta ji jikinta yayi sanyi laƙwas, in cool voice tace"Nayi ƙauyanci"? tambayar da tasaba yi mata kenan a duk lokacin da take tunanin ta aikata ba dai dai
Dafa kafaɗarta Unaisah tayi fuskarta da murmushi tace"My own sis ba ki yi ƙauyanci ba,
"To meyasa kike min dariya"?
"Saboda kin bani dariya, meye nayi mashi kuka? Ba bugu ba zagi kin fashe da kuka kamar wata ƙaramar yarinya ni danake so ki zama big girl, matar manya.
"Ni dai bazan ƙara komawa ɗakinsa ba, Tsoronsa nake ji sai dai ke ki je" ta faɗa tana nuna ta da hannu.
Maƙe kafaɗa Unaisah tayi"Batool ki fahimta ni bazan iya shiga dakin sa ba, bayason ana sharing aiki a part dinsa, idan mutun ɗaya ya fara shi zai cigaba da yi har sai in shi yace ya gaji baya so, nima big guy ne ya gaya min hakan.
Fuskarta ayamutse ta ƙare maganar tana dubanta, itama batool din kallon ta take yi, taƙi gane cewa wayau Unaisah take yi mata.
"Ya zanyi? Ni wallahi tsoron shi nake ji, baki ga launin idanuwanshi ba kalar na danish ɗinmu, kuma ma suna kama sosai don dai shi launin fatarshi chocolate ne"
ta fahimci Batool ta tsorata da chief, idan tana magana yatsun hannunta har kerma su ke Yi.
"A hankali zaki saba da shi, dan Allah ki daure Sister, za ki ji dadin yi mashi aiki" da wayau da dabara Unaisah ta shawo kanta, har ta amince zata cigaba da zuwa.
"Yanzu idan kika koma ki fada mashi cewa, Big guy ne ya baki aikin kula da part dinsa, ke zaki cigaba da daukar ɗawainiyarsa kina gyara mashi daki da kuma kai mashi abinci, haka zaki faɗa mashi,"
Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"amma ba yanzu zan koma ba ko"?
"Idan baki koma ba kayan abincin da kika bar mashi a ɗaki wazai kwashe su? Na fada maki bayason kazanta, sannan bai saba da wahala ba komai yi mashi akeyi"
tana ƙarasa fadan hakan Taja hannun Batool suka nufi Hanyar zuwa Part dinsa, A bakin ƙofar shiga unaisah ta saki hannunta.
Jiki na rawa Batool ta sanya hannu ta kwankwasa ƙofar,
A hankali Ta zuge, saida ta fara dadaita natsuwarta tukunna ta yi mashi sallama, shiru bai amsa mata ba, a tsananin tsoro ce ta zura kafarta, a lokacin Harya kammala Yin breakfast dinsa, yana daga kwance saman lallausar mattress dinsa, Ya ɗaura kanshi bisa pillow, Yayin da idanunsa ke akan Laptop dinsa da yake operating
Yawu ta haɗiya Muryarta na rawa ta furta"am.. dama Big guy ne yace in dinga zuwa inayi maka aiki a part dinka, kuka kuma da nayi kaine ka bani tsoro daka kama min gashin kaina"
Dakyar ta ƙare maganar, batare da ta motsa daga bakin ƙofar ɗakin ba, tamkar baisan tanayi ba, yayi shiru yana sauraronta, babu alamun zai kalleta
Jin shiru bai tanka mata ba, yasa ta yanke shawarar shiga dakin donta kawar mashi da kayan abincin da ya gama amfani da su.
Cikin sanɗa take yin tafiya kamar 6arauniya, duk a tunaninta bacci yake yi saboda idanunsa dake a lumshe batasan cewa idonshi biyu ba kuma yana kallonta, yayi mata hakanne saboda baison Ya ƙara firgitar da ita, tunda ya fahimci ruɗaɗɗiyace ita.
Tana ƙarasawa gaban table din tayi saurin kwashe kayan abincin, sam bata yi tunanin ɗaukar mayafinta data gani akan pillow ba saboda saurin da take Yi, bayan ta fita abakin bene ta tarass da unaisah tana jiranta.
Murmushi ta saki tare da nufarta tana fadin"Sister, nayi mashi bayani amma kamar bacci ma yake yi, ga tray din abincin na dauko Ina zamu kai shi"?
"Nikaina bansan ina ne kitchen dinsu ba," unaisah ta fada tare da kar6ar tray din"bari naje na nemo kitchen din, Ki tafi falo," amsa mata tayi da toh, da sauri Batool ta sauka daga kan benan ta nufi falo.
Unaisah tana cikin tafiya, Tajiyo motsin buɗe kofar Falon, su biyu suka shigo Boss man tare da Big guy, wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta, Allah Ya taimaketa, Ta kar6i tray din daga hannun Batul da kuwa Big guy saiya gane ba ita taje yima chief aiki ba.
Tunkararsu tayi fuskarta dauke da fara'a tace"Yalla6ai nagama yi mashi aikin, A ina zan ajiye tray din"
Big guy yaji dadin Jin hakan daga gareta, alamar jinjina yayi mata da yatsan hannun shi kafin Yace"ai tunda naga kina yin fara'a raina ya bani cewar Kin samu kar6uwa awurin chief, bani labari daya ganki meya ce maki"? boss man dake sauraronsu murmushi ne dauke akan fuskarshi dake asanye da facemask.
"Bayan na gaishe dashi Ya amsa min, sai nace mashi me yakeson ci in zuba mashi, to daya fada min saina zuba mashi na tsaya har ya cinye na ƙara mashi wani, kusan fa plate uku ya cinye ya kuma sha Tea" da mamaki Big guy ya maimaita kalmar plate uku!
"Kina nufin chief shi yaci abinci har plate uku"?
Ɗaga mashi kai tayi alamar Eh, saboda karfin hali irin nata ko tsoron yace zai buɗe warmer din batayi ba
Boss man yace"wow, My daughter kin ciri tuta, ai ni tunda nake da chief bai ta6a yarda wata mace tayi mashi aiki a part dinsa ba saboda bayaso"
Sai faman washe masu baki take Yi,
"Ga tray din abincin, Yanzu saura aikin kai mashi lunch ko"? Ta tambaya tana kallon big guy
Boss man yace"a'a, Sai kuma dinner, idan yakai Rana bai ci breakfast dinsa da wuriba to baya cin lunch na safen daya ci ya ishe shi sai kuma Dinner dinsa.
Wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta"Allah Yakaimu daren Lafiya" suka amsa mata da ameen, daga bisani big guy Ya kar6i tray din hannunta Yace tabiyo bayanshi zai nuna mata kitchen dinsu.
Atare suka tafi shi kuma boss Ya wuce dakin chief, Bayan Ya bashi iznin shiga, Yana zura kafarshi karaf idanunsa suka sauka aka Mayafin dake yashe kan pillow, farat ɗaya ranshi ya bashi cewar Na unaisah ne da ta shigo kawo mashi abincin, zuciyarshi ta musa da cewar ba mayafinta bane, saboda ita yaganta da mayafi tayi rolling,! Kenan na wanene wannan"!
A hankali Yakai hannu Ya ruƙo mayafin Yana dubanshi Kafin Ya kalli chief dake a kwance Ya lumshe idanunsa
"Yalla6ai barka da hutawa"
In a calm voice Ya amsa mashi yawwa
"Naga missed call dinka awayata ina fata lafiya"?
"Alright. I'm just reminding you about the plan we have for Hateem's farewell dinner tomorrow.
Murmushi Boss man Ya saki"Ina sane da komai Yalla6ai, Kuma in sha Allah babu wanda zaisan da zancen zuwanmu tare da Yaran, ba zata zamuyi masu, Sai dai yalla6ai naso ace hada Danish zamuje, ko dan saboda Prime minister Hateem, Ina so su gana da junansu, har magana nayi ma sheikh imam akan ko zamu iya kaishi asibiti aduba lafiyarshi sai yace min babu abunda likitoci zasu Iya yi mashi a halin da yake aciki" cikin sanyin murya ya kare maganar
A hankali chief Yaɗan ware idanunsa tare da cewa"nima nayi fatan hakan sai dai har yanzu babu wani cigaba a lafiyarshi, Allah Ya bashi lafiya"
Boss ya amsa mashi da amen, kafin Ya fuce daga dakin hannun shi ruƙe da mayafin daya tsinta.
..shigar shi falo keda wuya, Idanunsa suka sauka akan Batool, dake sanye da Pakistan launin Mayafin hannun shi, girgiza kai yayi don ya riga da ya gane itace taje dakin Chief Yi mashi aiki ba Unaisah ba, baiyi mamakin hakan ba saboda Ya riga daya san halin kayansa, idan bata son yin abu babu wanda Ya isa ya tursasa mata akan tayi shi, shiyasa da big guy ya bata aikin kula da part din chief sai ta tura Batool don tayi a matsayin itane taje, dole ya ɗauki matakin akan hakan don bayason ya samu tangarɗa akan alƙawarin daya daukarwa kanshi.
Batare da Batool Ta luraba, Ya daura mata mayafinta saman kanta, Kafin Ya nufi su sajeed dake ta faman daukar hotuna Daya bayan ɗaya ya rungume su sai dadi suke Ji yazo, Nan fa suka fara daukar hoto tare da shi.
*🌹ANEELARH❤*
A kwance take saman gado tana sharar baccinta, tun da ta sallami baby junaid ya tafi school ta koma kan gado ta kwanta bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita,
Can cikin baccinta ta soma jin ana ƙwanƙwasa ƙofar dakinta, da wata irin kasala ta farka tana yin miƙa, doguwar rigar jikinta duk ta yamutse, saukowa tayi daga saman gadon ta nufi ƙofar tana tanbayar wanene
Daga waje muryar Ana ta amsa mata da cewa"Aunty ni ce"
Buɗe ƙofar tayi tare da bata iznin shigowa daga ciki.
A hankali ta zuro kafarta Jikinta sam babu kuzari ta rame tayi duhu, v-neck shirt da pencil skirt ne ajikinta black and white, ta daure guntun gashin kanta da ribbom.
"Aunty barka da safiya, Ina fata ban takura maki ba, Na katse maki baccin ki" ta fada tana faman duƙar da kanta ƙasa
"Babu komai, Ina fata dai lafiya kike ko"? Cikin kulawa tayi maganar
"Lafiylou, dama nazo ne in ƙara yi maki godiya...." kafin ta ƙare maganar Aneelerh ta ɗaure mata fuska tare da cewa"Ana bana son abunda kikeyi min, na fada maki bana son godiyar da kike yi min amma kinƙi ki daina, "
Cikin sanyin Murya tace"kiyi hakuri Aunty idan na 6ata maki rai," dakyar ta ƙare maganar saboda kukan daya ciyota nan take ta fashe mata da kuka.....
Lamarin ya ɗaurema Aneelerh kai Daga maganar batason godiya sai kuka? Anya kuwa ba wani abunne na daban ke damun Ana ba?
Dafa kafaɗarta tayi da hannu daya"ya Isa haka, bana son kukan nan, Idan wani abu ke damunki dan Allah ki fadamin kada ki ji komai, In sha Allah zan yi ƙoƙarin ganin na taimaka maki mun magance koma menene".
Yayin da Ana ke kallonta idanunta sun kaɗa jawur, fuskarta ta jiƙe sharkaf da hawaye,
Muryarta na rawa ta furta"Aunty Aneelerh bakomai"
Girgiza kai Aneelerh tayi"wallahi ban yarda dake ba Ana! Nifa ba haihuwar yau bace, Duk wanda Ya kalleki sai ya gane baki da koshin lafiya, kuma da akwai wani abu dake damunki, Don haka ki fada min kawai! Rashin. fadamin shi zaija maki yin danasani"!
Su6ul da baka tayi wurin furta"kona faɗima babu wanda zai yarda dani, zai yi wuya afahimce ni"!! Rass Aneelerh taji gabanta ya fadi, muryarta da alamun ruɗu ta furta"Meke nan"?
A firgice ta zare ido tare da yin saurin cewa"babu komai, babu komai! Na tafi sai anjima" juyawa tayi da sauri ta nufi ƙofar dakin zata fuce, sai dai kafin ta haura kafarta Aneeleeh tayi saurin ruko hannunta ta juyo da ita suna fuskantar juna
Wani irin kallon kallo suke jefa ma juna batare da sanin ma'anar hakan ba
"Ana! Ki faɗamin meke damunki? Menene kike son fadamin wanda kike tunanin babu wanda zai yarda dake?dan Allah kada ki 6oye min, idan ma sirri ne nayi maki alƙawarin bazan fada ma kowa ba"
Numfashi Ana taja, gaba dayanta a tsoroce take babu kwanciyar hankali atare da ita
"Babu komai!Nabar Girkin dana daura a kitchen zanje na duba" tana karasa fadan hakan ta zame hannunta daga ruƙon da Aneelerh tayi mata, da sauri ta fuce daga ɗakin.
Bayan fitarta, Hankalin Aneelerh Yaƙi kwanciya, Ta jefata a ruɗani, ga wani bugun zuciya da take ji a kirjinta.
kalmar Da ana ta fadi ta tsaya mata aranta, da tace kota fadi babu wanda zai yarda da ita meke nan"?!
Tayi zurfi acikin tunaninta Wayarta dake ajiye kan side drawer ta soma ruri, a hanzarce ta juya ta nufi drawer ta dauki wayar, sunan zahra ne ya bayyana akan screen din wayar,
Bayan ta ɗaga kiran ta kara a kunne
kafin tayi sallama Muryar Zahra ta katse mata hanzarinta
"Auntyna ya ki ke ya gida"?
"Lafiyalou Sister, Bakya a gidan ne"?
"Na tafi wurin aiki, har dakin ki na shigo don inyi maki sallama sai na tarar kina bacci, bana so na takura maki shiyasa ban tada ki ba"
Shiru Aneelerh tayi tana sauraronta har ta ƙare maganar babu alamun zata tanka mata, Jin shiru yasa zahra cewa"auntyna kodai baccin bai ishe ki bane? Naji kinyi shiru?
Numfasawa tayi tare da samun wuri gefen gado ta zauna tukunna ta samun natsuwar yi mata magana
"Ban jima da farkawa ba, Har yanzu kasalar baccin bata sake ni ba, shiyasa zaki ji ni wani iri"
"Kiyi wanka zaki ji dadin jikin ki" acewar zahra
"Zanyi in sha Allah, yanzu dai fada min meya faru ne kika kirani awaya? Naji muryarki kamar akwai farin ciki atattare dake"? Ta fada tana murmushi tamkar suna atare da juna
"Kamar kin sani auntyna, shiyasa nake ƙara ƙaunarki saboda kina fahimtata fiye da kowa, abunda Ya faru Ina awurin aiki, Hajiya sarah ta kirani awaya.... " a ƙagare Aneelerh tace"me tace maki"?
"Ta faɗamin suna buƙatar za'ayi masu decoration gobe friday, Za suyi Farewall dinner, Na bankwana da prime minister Hateem, Jibi zai bar ƙasar tare da Iyalansa zasu koma Canada"
Wani irin farin cikine Ya bayyana akan fuskar Aneelerh"Zahra na tayaki murna, Alkhairi ne ke bibiyarki, hajiya sarah bata manta dake ba, Ashe kina aranta"
Sautin murya zahra da annushuwa tace"bana tunanin zan iya runtsawa a daren yau, saboda farin cikin zan halarci family dinner dinsu, wallahi aunty naso ace tare dake zamu je amma nasan bamai yiwu bane tunda nima tace daƙyar tayi mana hanyar da zamu samu halartar taron, saboda tsaron da za'a sanyama Estate din a goben"
"Kada ki damu zahra, Nima inason zuwa amma koda nasamu damar da zan biki bazan je ba, idan ma kikaje kamar naje ne, bani da damuwa nasan zaki bani labarin komai daya faru a shagalin, Harma Ki dauko min hotuna da videos don inga Ƴan family din Obinna"
Zahra tace"in sha Allah auntyna, yanzu zan koma bakin aikina, Sai na dawo gidan ki kula min da kanki,"
"Nima ki kula min da kanki sai anjima" baya sunyi sallama Aneelerh ta ajiye wayar saman pillow, ta miƙe da sauri ta nufi toilet ta shiga ciki, after some minutes ta fito daga wanka, shaf shaf ta canza suturar jikinta, ta sanya
Primcess vest tare da wrap skirt, ta ɗaure kanta da mayafi, da sauri ta fito daga dakin ta nufi bedroom din mami.
Tunkafin ta shiga ta soma jiyo muryarta tanayin karatun kur'ani, da sallama ta shiga ciki, a zaune ta taras da mamie saman darduma sanye da hijab, idanunta akan kur'anin da take karantawa, gefen gadonta ta zauna tana jiran ta kai Aya.
"Aneelerh kin tashi daga baccin lalacin"? Mami ce ta faɗa tana dubanta
Murmushi tayi mata"mami bansan baccin ya ɗauke ni ba,"
"Na gaji da ganinki zaune a gida, zan tuna ma Abie dinki maganar aikin da Uncle ɗan Iya yace zai sama maki a asibitin Obinna, Indai dagaske yake zai yi maki hanya"
"Mami nikaina nagaji da zama babu aikin, Dan Allah ki tuna mashi idan Ya dawo su yi magana asama min aikin in fara zuwa"
"In sha Allah zanyi mashi magana, ai nafi son ganin cigaban ki"
Murmushi suka sakar ma juna
" shiru sukayi kowa da abunda yake saƙawa acikin zuciyarshi.
"Dama zuwa kikayi don kiyi ta kallona"? Mami ce tayi maganar fuskarta da murmushi.
"Dangane da Ana ne, mami Yarinyar nan akwai abunda ke damunta, taƙi ta sanar dani, ina ɗaki ta shigo daga yi min godiya akan kudin da muka bata ni da zahra, sai nace mata bana so tana min godiya kawai sai ta fashe mini da kuka.... " gaba ɗaya Aneelerh ta sanar da ita abunda Ya faru.
Mami ta jinjina kai tana dubanta tace"tuntuni fa na lura da canzawarta, tayi baƙi ta rame kamar bata da koshin lafiyar, har tambayarta nayi meke damunta sai ce min tayi babu komai lafiyarta ƙalau Ni bansan ya zamuyi da ita ba" Mami ce ta fada tana mai nuna damuwarta.
"Mami yakamata ki ja ta a jiki kiyi mata magana wata'ƙil ke ta faɗa miki tunda kin haifeta zata ji tamkar mahaifiyarta ce keyi mata magana"
Shiru mami tayi na wani lokaci kafin tace"Toh, zan jaraba yi mata magana mu ji meke damunta"
"Tana a ina ne yanzu"?
"Ta fadamin zata je kitchen duba girkin da ta daura"
Mikewa mamie tayi"muje wurinta Inji" da sauri aneelerh ta miƙe ta dauki kur'anin mami da cazbaharta ta ajiye su a ma'ajiyarsu, Kafin Tabi bayan ta suka fito daga dakin,
Adai dai Lokacin Ummi ta fito daga daki sanye da dogon Hijab taci karo da su atare
Fuskarta da fara'a tace"Uwa da ɗiya ina zuwane haka"
"Wurin Ana zamuje, Yarinya duk ta rame tayi baƙi, Taƙi fada ma mutane abundake damunta ko ke baki Lura bane"?
Jim ummi tayi kafin tace"kamar kun shiga zuciyata, fitowar nan da nayi dakin ki nake shirin zuwa don inyi maki magana game da ita, na jima da lura da hakan, duk ta canza ba kamar yadda nasanta ba farkon zuwanku gidan nan, Yanzu tayi baki ta rame babu ƙugun nan