Showing 15001 words to 18000 words out of 56271 words

Chapter 6 - KURKUKUN KADDARA 3 Original Document Takun karshe by boss Bature .txt

23 Nov 2024

3619

gudun in jefa rayuwarmu cikin hatsari, ke kanki kinsani samun mace tagari wahala ne dashi a duniyar nan, ina jin tsoron in auro wadda zata yi silar tarwatsewar farin cikin mu, ko in auro maki Yarinya da zata raina ki, Ina fata kin fahimce ni"?
Ajiyar zuciya ta ɗan sauke fuskarta ɗauke da murmushi tace"na fahimce ka, mu shiga daga ciki" ta fada tare da buɗe murfin motar ta fito ta buɗe mazaunin baya ta ɗauko baby junaid ta rungume shi a kirjinta, ta rufe kofar, atare da uncle abdallah suka nufi entry hall na shiga gidan Uncle abdallah


Tunkafin su ƙarasa Aneelerh da zahra suka fito fuskokinsu dauke da fara'a sun dauki wankan Atamfa riga da skirt, ɗaurin ɗan kwalinsu kala ɗaya, Aneelerh ta yafa Mayafi akanta, yayin da zahra ta daura nata mayafin kan kafaɗarta,
"sannunku da zuwa, Ina wuninku," zahra ce tayi maganar, Uncle abdallah Ya amsa mata da Lafiyalou, Fatan mun same ku lafiya" ya faɗa yana kallonta tace"Lafiyalou,"
Kafin ta kar6i baby junaid daga hannun Hajiya adama, rungume juna sukayi ita da Aneelerh
"Mommy sannu da zuwa, nayi murnar ganinku," Aneelerh ta fada tana murmushi ta dago da kanta, Itama hajiya adaman murmushin ta sakar mata
"Surukar arzuƙi, kullum ƙara kyau kike yi," cikin jin kunyarta ta dan dukar da kanta tana fadin"daddy Ina wuni Ya gida Ya aiki"
Uncle Abdallah Yace"lafiyalou daughter, fushi nake yi dake, kinƙi zuwa kiga gidan mu"
"Naso zuwa mommy adama ce tace nabari zata zo kawo shi, badan haka ba ai dani zan zo dauko shi daga nan ma har inga gidan, amma ay min afwa in sha Allah zan fidda lokaci ni da zahra mu shigo gidan" yaji daɗin maganarta
Zahra tace"mu shiga daga ciki," ta fada tare da basu hanya suka nufi ciki,
A lokacin Mami tana cikin jera masu abinci a dining, Ummi kuma ta fito daga daki jikin ta sanye da hijabi, tana ganinsu ta nufesu fuskarta dauke da annurin farin ciki, Itama mami ta ajiye jeran abincin da take yi ta nufesu da fara'a suka gaisa da junansu, kafin suka zazzauna saman sofa, fira suka fara ta6awa a tsakaninsu, Zahra da Aneelerh suka basu wuri, Ɗaki suka shiga a saman gado Zahra ta kwantar da baby junaid tana fadin"Baby boy dinmu Yaji hutu, sati biyu kacal har ƙiba ya ƙara, fatarshi tayi kyau"
Aneelerh tace"ni kaina na lura da canzawar da yayi, gaskiya mommy adama ta iya raino, kalli kumatunsa sunyi 6ul6ul da su" gaba daya suka sanya dariya
"nasan baby junaid ba ƙaramin ta'asa yayi masu ba, Allah kadai yasan adadin madarar da ya shanye masu" cike da shakiyanci zahra tayi maganar tana jan kumatunsa da hannunta
Aneelerh tace"kamar wanda yasha ƙwaya sai bacci yake yi yaƙi farkawa duk surutun da muke yi, Allah na gani nayi kewar babyna" daga gefen gadon suka zauna suna kallonshi kamar zasu hadiyeshi, farin cikin ganin shi ne Ya cika su
"Auntyna bari naje kitchen in dauko mashi Cake dinsa nasan zai yi farin ciki idan Ya ganshi" Miƙewa zahra tayi jiki na rawa ta fuce daga dakin.


Fitarta ɗakin keda wuya Baby junaid Ya fara mutsi mutsin farkawa daga bacci, tunkan Ya buɗe idanuwanshi Ya fara yin sambatu yana fadin Ni wurin mommyn baby zanje, ni ku kaini gidan mamana"
Dariya Aneeerh tasaki batare da tace komai ba, ƙarasa buɗe idanuwanshi yayi Biji biji Ya fara ganinta kafin ya ƙara ware idanuwan akan fuskarta, zazzaresu yayi tamkar yau ya fara ganinta, muryarsa da shagwa6a ya furta"Mommyna, bacci nake yi ko mafarki" tuntsirewa tayi da dariya tare da sanya hannayenta biyu ta daukoshi ta daura shi kan laps dinta haɗi da rungume kanshi saman kirjinta
"Baby mommy ni ce, ba mafarki kake Yi ba, mommy adama ta dawo mun dakai kana bacci"
Fashe mata yayi da kuka Ya ƙanƙameta da hannayensa biyu, Hankalinta atashe ta ke fadin"My baby boy meyasa keke yin kuka? Maimakon kayi farin cikin ganina, ko ba ka so dawowo gida bane"?
Cikin shessheƙar kuka yace"mom..my wallahi bazan ƙara zuwa gidansu kwana ba, Ni bazan ƙara tafiya in barki ba, duk inda zamuje sai dai mu tafi atare......" bata bari ya ƙare maganarba tai saurin toshe masa bakinsa da tafin hannunta, gudun kada su Hajiya adama su jiyo sautin kukanshi da maganarshi
"sorry my baby boy, Nima bazan ƙara bari kayi nesa dani ba, kayi hakuri idan hakan ya 6ata maka rai" dakyar ta lallasheshi Yadaina yin kukan
Shafa sumar kanshi tayi da hannunta"yanzu fada min me ya faru bayan zuwanka gidan" tamkar baison furta maganar yace"Bakomai" dariya ta yi donta fahimce ranshi a6ace yake
"Tunda bazaka fadamin ba, Ni zan fada maka meya faru bayan tafiyarka" ƙura mata manyan idanuwanshi yayi fuskarshi babu annuri
"Idan dare yayi bana Iya bacci saboda rashin ka atare dani, nayi maraicinka my baby boy, bani da aikinyi sai tunaninka, dakai nake kwana dakai nake tashi, har mafarkinka nake yi, idan abun ya dame ni sosai, sai in dauki pillow Ina kuka ina Kiran sunanka, wayyo Allah baby junaid dina ka tafi kabarni....." da wasa takeyin maganar tana kwatanta mashi yadda ta ke yin kukan, Murmushi taga ya fara sakar mata hakan ba ƙaramin dadi yai mata ba
"Mommy kema kinyi kuka da bana nan"
Ɗaga mashi gira tayi alamar eh, dariya yasaki har fararen haƙoranshi suka bayyana tar dasu
"Wallahi naji dadi, ke ma kinji abunda naji," wannan maganar da yayi mata ta bata dariya.


Shigowa ɗakin zahra tayi hannunta ɗauke da plate daga saman shi chocolate cake ne, an ajiye cake knife daga gefe ɗaya.


Akan table zahra ta daura mashi cake dinshi, kafin ta zauna daga gefen Aneelerh
"Ashe Ya farka, rigimamme naga sai haɗe min fuska yakeyi, ko ba ka ji dadin ganina bane"?
Washe mata baki Yayi idanuwanshi akan cake din data kawo mashi yace"na wanene wannan"?
Aneelerh na murmushi tace"naka ne, aunty zahra ce ta haɗa maka"
Wani irin farin cikine ya bayyana akan fuskarshi, da sauri ya sauka daga kan laps din Aneelerh Ya rungume Zahra yana fadin"I miss U sis zahra," dariya suka saki, Zahra tace"yau naci albarkacin cake, Har ana fadin Anyi missing dina, toh nagode Nima nayi kewarka our baby boy," ta fada tana shafa sumar kanshi
"Ni zan yanka cake din" Ya fada Tare da raba jikinshi daga nata, da zumuɗi yakai hannu zai dauki wukar aneelerh tayi saurin rigashi daukarta"Ni zan Yanka maka" ba musu ya amsa mata da toh
Zahra dake kallonsu gwanin ban sha'awa tace"Aunty Aneelerh ki cigaba da tayani addu'a Allah Ya bani miji nagari inyi aure kafin in mutu, wallahi inason ƴa'ƴa idan ina kallonki ke da baby junaid sai inji dama ni"
Fuskar Aneelerh dauke da murmushi tace"in sha Allah zahra, zan cigaba da tayaki addu'a, very soon kema zakiyi aure har ma ki haifa mana babies"


"Ameen Ya Allah Auntyna, Bari in dauko wayata Inyi maku hoto" acewar zahra, Ta miƙe da sauri ta fuce daga dakin, har zata gifta ta falo tajiyo sallamar Abie da Uncle dan Iya, da sauri takai idonta kansu, atare suka shigo fuskarsu dauke da fara'a suka nufi su uncle abdallah,
Kau da idonta tayi da sauri ta nufi bedroom dinta ta shiga, akan gado ta dauko wayarta, ta ɗan dakata tana daddana wayar, wi-fi ta kunna ta shiga whatsapp dinta, messages ne suka fara shigowa ta ko'ina, wasu sakonnin daga abokan aikinta wasu kuma daga mutanan da suke mutunci dasu,
Shagala tayi da karanta sakonnin mutane, har tazo kan sakon da Hajiya saratu ta tura mata tun jiya da marace bata gani ba sai yanzu, Gajiyar aikin da su ka yi ne ya hanata hawa whatsapp din jiya.


Tsabar zumuɗi yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin buɗe chat dinsu
Unexpected Tayi tozali da hotunan da hajiya saratu ta tura mata, Na twins dinta, Sunyi matuƙar yin kyau hotunan a ƙalla sunkai guda biyar, Hoto na farko a london suka yi shi, Hoto na biyu sunyi shi a ƙasar dubai, sauran hotunan an dauke shi a dakin taron da aka gabatar da shagalin birthday din baba obie, Jiya kenan"
Abun kallo ya samu, Komawa zahra tayi gefen gadon ta ta zauna tana mai mamakin turo mata hotunansu da hajiya saratu tayi? Takasa gane me take nufi da hakan.
Message ta gani daga ƙasan hoto na ƙarshw da sauri ta soma karanta shi kamar haka






*Daga Alƙalamin Boss Bature🫶*




*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*


3196407426


First bank


Bature Hafsat Muhammad,


*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida*


~TAKUN ƘARSHE~










_______________________Boss Bature✍️












Rubutun dake a ƙasan hoto na ƙarshe ta karanta kamar haka

_"If you had the chance to choose between them, which one would you like?"_


A ruɗe zahra take kallon screen din wayar, a ƙalla ta maimaita karanta sakon yafi sau a ƙirga, duk tabi ta ruɗe ga wani farin ciki daya lullu6eta duk da bata gane me hajiya saratu take nufi ba.


Miƙewa tayi jiki na rawa ta fito ta nufi dakin Aneelerh.


Tana shiga ta taras da su suna Cin cake, Ita da baby junaid.


Jin motsin shigowarta yasa duk suka ɗago suna kallonta.


"Zahra, meye faru naga kina murmushi"?


"Aunty na, duba ki gani abun da hajiya saratu ta rubuta min" miƙa ma Aneelerh wayar tayi, bayan ta kar6a ta soma duba hotunan, Baby junaid dake cin cake Ya ce"Aunty Zahra, Kin iya cake, Yayi daɗi, Idan Angel dina ta dawo gida, zaki hada mata kalarshi"


ɗaga mashi kai zahra tayi"me zai hana my baby boy, ai dole baby Angel taci cake" Murmushi yasaki"thank u sis zahra"


Ɗagowa Aneelerh tayi ta ɗaura idonta kan zahra dake atsaye tana kallonta.


"Na taya ki murna, wata'kil burinki ne zai cika, a fahimtana, Hajiya saratu tana son haɗa ki da ɗaya daga cikin ƴa'ƴan ta shiyasa ta baki za6i"


Cike da kokwanton maganarta Zahra tace "Anya aunty Aneelerh? Gaskiya bana tunanin hakan, tayaya ma zata hada ni da ɗanta? Ni da ba yar kowa ba, nifa nasan masu kudin nan basa auran bare sai dai yasu yasu jinin arziƙi" cikin sanyin murya ta furta maganar"kuma ni waɗannan sunfi karfina wallahi, ko lokacin da muke zuwa gidan yi masu hidima basu yi ma mutane magana suna da girman kai, idan muka gaishe dasu da hannu suke amsawa, ko kallo ba mu ishe su ba"


Dariya Aneeleeh tayi"kin bani mamaki zahra, sai kace bake bace kike da burin auran Chief owais, sai gashi yanzu kina maganar ƙannansa sun fi ƙarfin ki"


Dariya zahra tayi"ki gane mana, Chief Yafi ƙarfina nesa ba kusa ba, Haukana kawai nake Yi, daga baya kuma na zauna nayi ma kaina karatun tanatsu, Na lallashi zuciyata na haƙura na barma Allah za6i"


Aneelerh na murmushi tace"Yanzu dai zoki zauna daga gefe na, In taya ki za6an wanda Ya dace dake, duk da naga kamannin su ɗaya ban iya banbanta su"


Zama zahra tayi daga gefenta, hankalin baby junaid baya akansu, Ya samu cake sai ci yake yi duk ya 6ata bakin shi.


Ƙura ma hotunan ido su ka yi"zahra idan hasashena ya zama gaskiya wani irin farin ciki za ki yi?


"Mara misaltuwa" amsar da zahra ta bata kenan.


"Za ki zama ɗaya daga cikin surukan Baba Obie, Uwa Uba ɗan gidan Hajiya saratu minister of health, gashi itace autarsu, gaskiya zaki more wlh gata ta ko'ina zaki samu idan familyn suka kar6e ki hannu biyu" da fara'a akan fuskarta ta yi magana.


Zahra bata ce komai ba, Ita dai gani ta ke kamar hakan ba mai yiwuwa bane


"A cikin su wanene ne yafi kwanta maki a rai"?


Aneelerh ta jefa mata tambayar


"Aunty aneelerh nabar maki za6i dan Allah, Ni kaina bana iya banbanta su, amma kamar wannan shine Zayn idan kika kalli fuskarshi da kyau zaki fahimci yana da masifa" ta faɗa tana ɗaura yatsanta kan face din Zayn.


Shi kuma wannan shine zaid a hasashena, Yafi zayn saukin kai.


Aneelerh tace ƙwara mai saukin kan, akan mai masifar, amma fa kamar yafi kyawun sura.


Zahra tace"Eh, hakane, zayn yafi zaid.


"Nidai nafi yi maki sha'awar zaid, indai yana da kyakkyawar zuciya"


Shiru zahra ta ɗan yi kafin tace"An ta6a faɗamin basa jin magana, kamar suna kula mata, Har page dinsu na insta na ta6a shiga, suna yawan ɗaura hotunansu da matan banza masu bayyana tsiraicin su"


Yanayin fuskar Aneelerh ne Ya canza zuwa damuwa.


"Zahra kin tabbatar basu jin magana"?
Ɗaga mata kai zahra tayi alamar eh
Kwa6e fuska Aneelerh tayi"akwai matsala, but mommynsu tasan da hakan"?


"Bana tunanin ta sani, saboda mutane suna jin shakkar yi mata magana kinga kuwa babu wanda zai Iya tunkararta da wannan maganar mara dadin ji"


"Banji dadi ba zahra, Har na fara yi maki murna amma yanzu sai naji abun ya fara fita raina, bazan hana ki za6ar wanda kikeso ba acikinsu, Idan Allah yasa sanadin shiriyarshi ce sai kiga ya shiryu ta silarki, babbar matsalar shine ace baya sonki, da ace idan ta haɗa kun zaku son juna har ma son shi ya rinja yi naki tabbas zai Iya canza kanshi, amma idan ke ki ke son shi baya sonki baki Isa ki iya tanƙwarashi ba sai dai wani iko Na Allah"


Jinjina kai zahra tayi ta gamsu da bayanin Aneelerh sai dai bata Jin zata Iya haƙura da damar da take da ita, Allah na gani ta jima tana son Hajiya saratu da ya'yanta duk wani abu da zai hadasu son shi ta ke yi.


Cikin sanyin murya tace"Auntyna, addu'arki nake buƙata nima zan dage da addu'a, Idan Har dagaske zata hadani da daya daga cikinsu toh Allah yasa ya zama alkhairi agare ni da kuma shi kanshi wanda zata haɗani dashi din, Idan yana da kyan hali zanyi farin ciki, imma akasin hakan zan dauki hakan amatsayin ƙaddarar rayuwata, Allah na gani Ni bazan Iya janye tayin da tayi min ba"


Dafa kafaɗarta Aneelerh tayi"Zahra, bana so ki jefa rayuwarki inda zaki ƙuntata, babban kuskure ne ki auri miji mai neman mata, Ni nafison kiyi aure inda bazaki ta6a yin danasani ba, ko dan saboda Ƴa'ƴan da zaki haifa yakamata kiyi nazari kafin ki yanke hukunci"


Damuwace ƙarara akan fuskar zahra, Ga samu ga rashi.


"Nagode da shawararki auntyna, but ni yanzu bansan wani amsa zan bata ba, gashi na riga da na bude sakon zata ga alamar nagani"


Shiru Aneeleerh tayi naɗan wani lokaci kafin Ta furta"Ki bata amsa da sunan wanda ya birgeki, zamu jira muga martanin da zata mayar mana"


Amsa mata tayi da toh, ta kar6i wayar daga hannun Aneelerh, sunan zaid ta rubuta ba tare data ankare ba keyboard Ya canza mata sunan ya koma zayn, ahaka ta tura message din.


Bayan ta kammala ta soma daukarsu hotuna tare da baby junaid, sun dauki lokaci a dakin kafin suka fito falo don ay fira dasu, Hajiya adama da uncle abdallah sun ji dadin tarbar da akayi masu, An mutuntasu an kuma karramasu kamar kada su tafi, ga lafiyayyan abincin da su zahra suka girka masu, sunci sun ƙoshi sun kuma sha fira, wuraren marece suka bar gidan.


*Shin Meke Faruwa A Obie Estate 🔥🔥🔥*


Bayan fitowar Chief owais da Prime minister Tare da Boss man, jami'ai suka yi gaggawar bude masu motar da za su shiga.


Ta ƙofar baya suka bi wadda zata 6ular dasu zuwa cikin Obie estate, kasancewar Gidan Owais shine ƙarshen ginin dake acan bayan estate din, Gate dinsa Biyu, akwai gate na gaba wanda zai fitar dakai titi, Gate din baya kuma zai shigar dakai Cikin estate.


Prime minister Ne Ya buƙaci Yana son su fara zuwa gidanshi don su taho da sheikh imam kafin su wuce gidan baba Obie.


Da matsakaicin gudu motocin suka ƙaraso babban katafaren entry na gidan prime minister dake a tsare da jibga jibgan canadian polices da sojoji.


A harabar Ajiye motoci su ka Yi parking, A hanzarce Sojoji suka nufo motar, Tare da buɗe masu ƙofa.


Kusan atare suka fito, ba tare da bata lokaci ba, su ka ɗunguma zuwa babban falon gidan.


A lokacin Nazli tana zaune saman Sofa ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, Hankalinta na akan laptop dinta, Yayin da Yazrin Take zaune a gefenta hannunta ruƙe da tsadaddiyar Wayarta.


Ba zato ba tsammani, sallamar su prime minister ta ratsa kunnuwansu.


Yazrin ce tayi saurin ɗagowa da idonta yayin da ita Nazli tayi tamkar bata ji sallamar su ba, dama halintane idan tana aiki a laptop ba ƙaramin abu ke Iya dakatar da ita ba.


Tsantsar farin ciki ne akan fuskar Yazrin, da mamaki ta furta"Big Bro"! da sauri Ta miƙe ta nufe shi, tunkafin ta ƙaraso Chief ya buɗe mata hannu alamar tazo gare shi, hartana tuntu6e garin sauri duk zumuɗin ganin shi ne, prime minister Yace"bi a hankali daughter ba guduwa zaiyi ba" sai faman washe mashi baki take Yi, hugging dinsa tayi, ya ɗaura hannayenshi biyu asaman Bayanta Yana ɗan bubbugashi ahankali Ya furta"Long time no see, I missed You so much"


Ɗagowa tayi da kanta tana fadin"I miss you too, rabin raina You forgot about us, and you stopped coming to Canada, ko kiran wayarka akayi baka picking" voice dinta tamkar zata fashe mashi da kuka Ta ƙare maganar.


Ɗaura hannunsa yayi kan mayafinta"Am sorry, Kuna araina, aiki ne Ya 6oye ni, amma hakan ba yana nufin aikina yafi ku mahimmanci ba, Ina fata kin fahimce ni" jinjina mashi kai tayi alamar eh.


Boss man Dake atsaye Yana kallonsu yayi mamakin yadda owais Yake Yi mata magana, bai ta6a ganin yana sakar ma mace fuska haka ba sai Yau da Allah Ya kawo su gidan Prime minister, Hakiƙa Ya yaba da Haɗuwar daular, sai yaji tamkar Yabar Nigeria ne, ga wani ni'imtaccen sanyin A.c mai ratsa hudojin fatar mutun, ya yaba da kyawun Yazrin, Jefi jefi yakan dan saci kallon falon, badan Ya fito daga gidan chief Owais ba, da Allah kadai Yasan ƙauyancin da taj zaiyi agidan prime minister.


"Mu shiga daga Ciki mutumina" Muryar prime minister ce ta fargar dashi daga tunanin da yake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login