Showing 1 words to 3000 words out of 56271 words

Chapter 1 - KURKUKUN KADDARA 3 Original Document Takun karshe by boss Bature .txt

23 Nov 2024

3605

BOSS LADIES WRITERS*~




KE GABATAR MA KU👇




_🔥💫THE PRISONERS🔥💫_




~TAKUN🔥🔥🔥ƘARSHE~




Daga Alƙalamin Boss Bature




Dedicated To Aunty Kubra😍








_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty❤._






_______________________✍️










Bayan ƴan mintuna Pravin ya fito daga toilet fuskarshi a jiƙe da ruwa kamar wanda ya ɗauro alwala, maimakon taga 6acin rai akan fuskarshi sai taga akasin hakan, wani irin shu'umin murmushi yake sakar mata, hakan ba ƙaramin 6ata mata rai ba, ɗaure mashi fuska tayi haɗi da kau da idonta daga kan shi, taci gaba da cin abincinta.




Gefen ta ya zauna"idan akwai wani punishment din daya fi wanda kika bani a yanzu, A shirye nake dana kar6e shi, Ni dai buri na ki yafe min mu shirya tsakanin mu, My Sarah bazan juri fushin ki ba" daɗin baki Pravin yaci gaba dayi mata, tun da ya fara magana Hajiya Saratu bata dube shi ba.


Abincin ta take ci, hannu takai zata ɗauki apple ciki Jerin kayan marmarin dake shaƙe a plate da sauri Pravin ya ruƙe hannunta yana faɗin"Bai kamata kina share ni ba, tun ɗazu nake yi maki magana kinyi banza kin ƙyaleni inata zuba kamar aku," a marairaice ya ƙare maganar, ranta ya 6aci ta tsani tana cin abinci a takura mata, a harzuƙe ta fuskance shi da niyar ta 6al6aleshi da masifa sai dai kafin tayi hakan yai saurin shammatarta ya haɗe bakinshi da nata, kafin tayi yunƙurin janye bakinta yayi saurin zagaye hannayenshi ya ruƙe qugunta ruƙo bana wasa ba, still bata daina kiciniyar raba kanta dashi ba sai dai yaci ƙarfinta, lokaci ɗaya ta soma jinta a yanayin da bata shirya kar6arshi ba, kissing ɗinta ya fara yi cikin ƙwarewa yake sarrafa ta, har yayi nasarar zuge zip din rigarta slowly ya zame wuyan rigar har zuwa kan flat stomach dinta, abunda ya jima bai samu damar yi da ita ba, numfashinshi har wani hauhawa ya ke yi kamar mayunwacin zakin da yaga nama, zame tonge dinsa yai daga cikin bakinta ya shiga manna mana mayataccen kiss tun daga kan wuyanta har izuwa saman big boobs dinta da suke acike fam, ƙoƙarin 6alle hannun bra din yayi asusuce yakai hannu zai yi grabbing dinsu kamar daga saman Yaji ta bangaje shi da ƙarfin gaske har sai da Ya faɗa kan mattress din, da sauri ta maida bra din ta gyara wuyan rigarta daya kwale mata, idanuwanta sun kaɗa jawur sun ƙanƙance fuskarta babu annuri ko misƙala zarratin sai faman huci take yi alamun 6acin rai.


Lumshe idanuwansa yayi tsabar takaici da ƙululun baƙin cikin da yaji na katse mashi enjoyment dinsa da ta yi ne yasa shi fitar da ruwan hawaye suka soma gangarowa saman kuncinsa, muryarshi ƙasa ƙasa ya furta


"Meyasa za ki yi min haka? Kin hana ni jin daɗin rayuwata sai kace ba mijin ki ba, gaba ɗaya kin juya min baya ta 6angaren bani hakkina, Saratu ba ki yi min adalci sai naci wahala kafin nake samu ki bani haɗin kai, ada ba haka ki ke yi min ba kin canza, Idan laifi nayi maki ki faɗamin mana" zuciyarshi na tafarfasa ya ƙare maganar.


Gaba ɗaya abincin Ya fita aranta, yunƙurin amai ta soma yi da gudu ta nufi toilet ta shiga, ranshi ya 6aci gani yake kamar don saboda kiss din da yayi matane yasa take yin amai saboda tana ƙyamar shi.


Daƙyar Ya iya miƙewa zaune ya jingina bayanshi da headboard idanuwanshi sun kaɗa jawur, Ya rasa gane dalilin da yasa ya gaza haƙura da ita duk irin wulaƙancin da take yi mashi, ga dukkan alamu ya manta da abun da ya kawo shi ɗakin.


Kusan mintuna biyar kafin Hajiya Saratu ta fito daga toilet, hannunta ɗaya dafe da saitin zuciyarta, Cak ta tsaya da tafiya ta ɗaura idonta akanshi, kamar yadda take kallonshi haka shima ya ke kallonta, ba ta yi mamakin ganin hawayen dake akan fuskarshi ba, aranta ta furta"jarababbe kawai" a fili kuma tace"dama ka shigo ɗakin ne donka takura min da jarabarka ne"? Meyasa ita wadda ta taya ka kwana adaren jiya bata biya maka buƙatarka ba? Kai ne fa da kanka ka faɗamin cewa tafi ni Iya tarairayar miji ko ba haka ba"? Ta faɗa tana jifar da shi da harara.




Dafe kanshi yayi da hannu ɗaya, sai yanzu ya gane dalilin dayasa tayi mashi wulaƙancin nan, Kishi ne ke damunta, duk da yasan bata gasgata abun da ya faɗa mata ba.


Cikin sanyin murya yace"kin 6ata min rai jiya shiyasa na faɗa maki hakan saboda kiji abunda naji, amma ba dagaske nake ba, duk da baki ƙaunata ni bazan iya haɗaki da wata ƴa mace ba, saboda ke kaɗaice acikin zuciyata har abada, shiyasa nake haƙuri dake duk wulakancin da zakiyi min bazan iya cin amanarki ba......." Yana magana hawaye na cigaba da wanke fuskarshi.




Duk irin zafin da ta ɗauka sai taji jikinta yayi sanyi, lokaci ɗaya tafara sassauta fushin fuskarta, koda Pravin Ya fahimci raunin da zuciyarta tayi sai yai amfani da wannan damar ya ƙara sanyaya muryar shi haɗi da marairai ce mata fuska Yaci daga da cewa"bansan meyasa ki ke son 6ata min rai ba, burinki ki ƙuntata min, bayan ba haka mu ka yi wa juna alƙawari ba, kada ki manta Saratu, ƙaunar da nake yi maki itace tasa nabar dangina saboda kin nuna baki ra'ayin zama a india ahaka na amince na biyoki Nigeria, kuma na zauna a family house dinku saboda kin buƙaci kinfi son zama tare da ƴan uwanki, babu irin gorin da ba'ayi min ba akan ina zama gidan surukaina amma saboda son da nake yi maki yasa na jure duk wani wulaƙancin da nake fuskanta, naci gaba da zamana, har muka tara zuri'a, ban ta6a buɗe baki na faɗa ma wani cewa bada son raina nake zaune gidan surukaina, ke ce ki ka nuna kina so ni kuma saboda ƙaunar da nake yi maki yasa nake yi maki biyayya" dakatawa ya ɗanyi da yin maganar yana binta da kallo, tsantsar nadama yake gani akan fuskarta.




"Idan naga dama zan Iya sakin ki, In kama gabana saboda ni ban dogara dake ba, da Allah na dogara ki daina tunanin dukiyarki take sanyawa ina atare dake ba haka bane ko ɗaya, Ni ƙaunarki nake yi don Allah ba don wani ba in ba haka ba ai da tuni na koma ƙasarmu".


Ƙafafuwanta ne suka Gaza ɗaukarta, a daddafe ta nufi mirror chair ta zauna akai tana fuskantar shi.


"Saratu ki faɗamin kin daina sona ne"? Yanayin yadda yayi mata maganar, ba ƙaramin karya mata zuciya yayi ba.


Runtse idanunta ta yi, ita kanta ta rasa gane meyasa take yi mashi haka? kuma a yadda ta ke jin shi babu abun da ya canza na daga ƙaunar da take mashi.




Jin motsin shi yasa tayi saurin buɗe idanuwanta, saukowa yayi daga kan gadon ya nufi ƙofar fita daga ɗakin Yana share hawayen shi da hanky.


Har ya ruƙo handle din ƙofar Aranshi yana Allah Allah ta dakatar dashi yaji ta ambaci sunanshi"Pravin" shu'umin murmushine ya bayyana akan fuskarshi, a hankali take tafiya tana tunkararshi, da sauri ya 6oye murmushin fuskarshi Ya juyo yana dubanta tamkar mai fama da ciwon ido, unexpected tayi hugging dinshi ta zagayo da hannayenta saman bayanshi, muryarta ƙasa ƙasa ta furta"I'm really sorry, my hubby. I've realized my mistake, and I won't hurt you any more"


Kwantar da kanshi yai kan kafaɗarta Ya zagayo da hands dinsa ya ruƙo waist dinta, yaushe rabon da yaji ɗumin jikinta haka harya manta sosai yayi tighting ɗinta, Yana shaƙar ƙamshin turaren jikinta, bai ta6a tsammanin zaiyi nasara akanta ba, sai gashi cikin sauƙi ya yaudareta da kalamansa.


"Ki yi min alƙawarin ba zaki ƙara 6ata min rai ba? sannan zaki dinga bani haƙƙina akai akai, duk time dana buƙace ki" ya faɗa batare daya raba jikinshi daga nata ba.


"Bazan iya yi maka alƙawari ba, kasan ɗan adam ajizine, dole wata rana mu samu sa6ani bawai fatan hakan nake yi mana ba, but in sha Allah zanyi ƙoƙarin ganin na kawar da duk wani abu da zai 6ata maka rai"


Ƙara ƙanƙameta yayi, hada manna mata kiss kan kafaɗarta.


Tsawon mintuna kafin ya raba jikin shi daga nata, Ya ruƙo hannunta acikin nashi, fuskokinsu ɗauke da murmushi.


"Ina fata kanka bai yi maka ciwo, naga idanunka sun kaɗa jawur"
"Kada ki damu, dama kece damuwata kuma Alhamdulillah yanzu komai ya wuce tun da kika kar6i laifin ki, fatana shine Allah Ya dawwamar da zaman lafiya a tsakanin mu"


"Ameen my husband" daɗi yake wai yau shi hajiya saratu take kira da hubby da kuma sunan mijinta, Ya manta when last yaji hakan daga gare ta.


Janyo hannunshi tayi"ka dawo mu zauna mu ci abinci a tare, nasan kana jin yunwa"


Girgiza mata kai yayi"no bana jin yunwa my wife" ya faɗi hakanne saboda cikinshi acike yake, Hajjaty ta bata shi lafiyayyan abinci yaci ya ƙoshi babu yunwa atare dashi.


"Namanta ban faɗa maki ba" a hanzarce ta kalle shi tana jiran jin ƙarashen zancen
"Game da abun da ya faru jiya, dangane da shigowar maciji gidan nan........" a tsanake Pravin Ya labarta mata komai, hatta ƙaryar da yayi masu Senate Lateef bai 6oye mata ba, a ƙarshe yace"na faɗi masu hakanne donsu ɗauki abun serious, saboda bana son abunda zai cutar min dake da kuma ahlinki, shiyasa nayi masu ƙaryar cewa kin kwana idonki biyu"


Tun da ya fara maganar, Yanayin fuskarta ya canza zuwa 6acin rai, a ruɗe ta furta"Wai kana nufin yaya Hateem shi ya tura da jet aka dauko sheikh imam from sudan to Nigeria? Sannan shi macijin dama mutun ne!? Kuma a gidan Owais dake acikin estate din nan Yake zaune....." Hankali amatuƙar tashe ta furta maganar.


Jinjina kai pravin Yayi"ƙwarai kuwa duk abunda kika ji na faɗa maki dagaske ne, yakamata mu ɗauki tsastsauran mataki idan ba haka ba owais da prime minister zasu ja mana bala'e garin son taimakonsu, In ba haka ba taya zasu taimaki Yaron dake canza halitta Ya koma Maciji? Ni dai nafi tunanin wasu miyagunne daga cikin abokan hamayyar Jam'iyar su baba Obie suka shirya maƙarƙashiya donsu kashe baba, shiyasa macijin Ya faɗo gidan nan maimakon sauran gine ginen dake akusa da gidan owais din......" a firgice hajiya Saratu take faman zazzare idanunta duk tabi ta ruɗe, maganganun da Pravin Ya faɗa mata sun yi matuƙar yin tasiri Acikin Zuciyarta, Jiki na 6ari ta nufi ƙofa zata fuce don taje ɗakin baba obie, Ko mayafi babu akanta, da sauri pravin ya ruƙo hannunta a haushine ta juyo tana kallonshi.


"Bari in ɗauko maki mayafi," ya faɗa tare da sakin hannunta, Ya juya cikin takun sauri ya nufi closet dinsu, jim kaɗan Ya dawo hannunshi ruƙe da mayafinta Ya lullu6a mata shi akanta, da sauri ta fice daga ɗakin.


Fitarta keda wuya Pravin Ya tuntsire da wata irin mahaukaciyar dariya mai matuƙar razanarwa sautinta tamkar ba daga bakin shi take fitowa ba.


Lokaci ɗaya ya haɗe fuskarshi tamkar bai ta6a yin dariya ba, Ya juya cikin ɗakin Ya nufi gaban mirror Ya tsaya yana kallon fuskarshi, kafin Ya zura hannu ya zaro wayarshi daga aljihun suit dinsa.


Pressing dinta ya soma yi, kafin Ya kara wayar a kunne.


da kakkausar Murya Ya furta"mugun Bawa komai yana tafiya yadda muka tsara!!!


Yana ƙarasa faɗar hakan, Bai Jira amsar da mutumin zai bashi ba yai rejecting call din, akan mirror Ya ɗaura wayar, ya juya da sauri ya fuce daga dakin yabi bayan hajiya Saratu.




*💋UNAISAH❤*




Idan muka koma 6angaren Unaisah tamkar mai gadi haka ta tsare Danish, duk wani motsinshi akan idanunta, a yanzu haka tana daga kwance gefenshi ta ɗaura kanta saman chest dinshi, ta aza hannunta saman flat stomach dinsa ta natsu tana shaƙar ƙamshinsa, sai faman lumshe idanunta take yi wani irin bacci ne ke ƙoƙarin fisgarta, lokaci yana ta tafiya ba tare data ankare ba ko sallah bata yi ba, gaba ɗaya ta shagala ta saki jikinta, ba zato ba tsammani tajiyo muryar babban mutun Yana faɗin"Allah Yasa ya farka" rass taji gabanta ya faɗi, da ƙarfi ta ware manyan idanuwanta tare da yin wuff ta miƙe zaune tana kallon glass door din a hankali ƙofar ta soma zugewa, a hanzarce ta rarrafa ta faɗo daga saman gadon ta shige cikin labulan ɗakin ta la6e kamar wata 6arauniya, jikinta sai kerma yake yi kamar wadda tayi ma sarki ƙarya.




Gaba ɗayan su ne suka shigo ɗakin tun daga kan Prime minister, sheikh Imam, chief owais, Big guy da salsabeel sai Boss Man, a bakin gadon nashi suka dakata da yin tafiyar idanuwansu akan Danish dake a kwance.


Unaisah dake a la6e bayan labule zuciyarta ce ta soma bugawa tunawa da ma6allin rigarshi data bari a buɗe, tasan zasu iya gani kuma zasu gane wani ya shigo ɗakin, sai faman cizon yatsanta take yi, tayi danasanin shigowa ɗakin.


"Har yanzu bai farka ba ko"? Prime minister ne yayi maganar Yana duban fuskar salsabeel.


"Eh Yalla6ai, amma idan kana buƙatar Ya farka sai atada maka shi, Inyaso daga baya sai ya koma baccin"


"A'a banaso na takura mashi, zan jira har zuwa lokacin da zai farka"


da mamaki akan fuskar Boss man yace"ya akai ma6allin rigarshi suka cire"? Sai da ya ambaci hakan su ka yi saurin kai idanuwansu kan Ƙirjinshi dake a buɗe, lamarin Ya ɗaure masu kai.




"Ko Shi ya buɗe da kanshi? Ko wani ne Ya shigo" Prime minister ne yayi tambayar da alamun ruɗu akan fuskarshi.


Sheikh Imam Yace"bana tunanin shi ya buɗe da kanshi, sai dai wani iko na Allah ko kuma wanine Ya shigo ɗakin bayan fitar mu"


"Wanene zai shigo? Yaran gaba ɗaya na tattarasu a ɗakinsu Unaisah, Ummi tana aɗakinta, babu yadda za'ai ma ta Iya ƙetare Iyakarta, Ƴan uwansu maza kuma tare dasu muka tafi masallaci balle ace ko sune suka shigo" big guy ne ya kora jawabin.


Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba Chief owais da baice komai ba, A hankali yake bin ɗakin da kallo kafin Ya sauke idanuwanshi kan bedsheet din gadon dake a yamutse alamar wani ya hau gadon.


"His bedsheet is squeezed. which means someone came into the room after we left," chief ne ya furta maganar, nan take suka kai dubansu ga zanin gadon, Ya yamutse sosai.


"Amma wanene Ya shigo" Acewar Boss,"Karfa ace wani mugun abunne"
Damuwace ƙarara akan fuskar Prime minister, ya dubi Shiekh Imam dake a gefenshi"Ni dama hankalina bai kwanta ba tun da muka tafi masallaci muka barshi shi kaɗai a ɗakin"


Cikin kwantar da murya sheikh Imam Yace"In sha Allah babu abunda ya faru dashi, Ina da tabbacin hakan"


Shiekh Na rufe baki Big guy yace"Sir, please give me a chance to check the CCTV footage, that way we'll be able to find out if someone else entered the room.( Ka bani dama in bincika cctv footage, ta hakan zamu Iya gane wanda ya shigo ɗakin idan har mutunne")


Shiru Chief Owais Ya ɗanyi har Ya buɗe baki zai bashi amsa karaf idanuwanshi suka sauka akan labulan dake lilo Yana mutsi nan take Ya fahimci mutunne Ya la6e aciki




"There's no need to check the CCTV."


Ya faɗa tare da ɗaga Voice dinsa Ya furta"Come Out!"


Rass taji gabanta Ya faɗi, duk da ranta bai bata da ita Yake yin maganar ba.



"I'm commanding you to come out from behind the curtains. Don't make me repeat myself," babu wasa akalamansa.


Jin wannan maganar yasa gaba ɗayansu su ka kalli direction din da chief owais Yake kallo, Tsantsar mamaki ne akan fuskokinsu ganin labule Yana motsi.


"Amma koma wanene wannan jikinshi zai gaya mashi, kayi kuskuran shigowa ɗakin nan" big guy ne ya furta maganar.


Prime minister kuwa Ya ƙura ido Yana jiran ganin wani me ƙarar kwanan ne.


Tsawa Boss man Ya daka da karfi tare da fadin"zaka fito ko sai mun harbe ka da harsashin bindiga"


Ƙiris Ya rage ta saki fitsari a wando, tuni ta haɗa uban gumi, jikinta ya hau yin kerma, ita da ba mai laifi ba amma ta firgita kanta, hakanan ta tsinci kanta da jin faɗuwar gaba, gani take kamar in suka kamata a ɗakin zasu zargi wani abu, kodan saboda ma6allin jallabiyarta data cire masa, zasu iya tsammanin da wata manufar tayi hakan.


"Bawan Allah ka fito salin alin ka bayyana kanka tunkafin mu fusata" acewar big guy, shiru babu alamun na cikin labulan zai motsa.


Moving quickly Chief Owais Ya nufi labulen yayin da yake nannaɗe hannun Rigar shi, har ya miƙa hannu zai damƙi wuyan mutumin ta cikin labulen muryar Boss man ta dakatar da shi.


"Sir, Unaisah ce," cak Ya tsaya tare da juyawa yana kallon Boss, gaba ɗaya mutanan dake a ɗakin shi suke kallon cike da mamakin taya akai yasan wanene.


"Raina ne ya bani itace, kuma ita kaɗaice zata Iya shigowa ɗakin nan don ta duba ɗan uwanta" Ya faɗa tare da ɗaga muryarshi ya furta"Unaisah come out" A hankali kowan nan su Ya ɗaura idanuwanshi kan labulen.


Janye labulen tayi ta fito tana faman zare gray eyes dinta, nauyin haɗa ido dasu taji da sauri ta duƙar da kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.


"Jari mai kasada, da ace kinbari chief ya shaƙi wuyanki sai dai ki ganki a Emmergency room" Big guy ne yai maganar da zolaya, gaba ɗayansu suka saki murmushi, prime minister yace"idan na fahimta wannan itace Yarinyar nan ko" Ya faɗa idanuwanshi akan fuskarta, Boss Man yace"itace My daughter"


Sheikh Imam Yace"Tabarakallahu ahsanul khaliqin, zonan ƴata mu gaisah" yai maganar tare da miƙa mata hannu.


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login