Showing 105001 words to 108000 words out of 130495 words
Chapter 36 - Wa Yasan Gobe Compelet Book by Safiya Abdullahi musa huguma
kaba habarta yana cewa "o'o'o,sannu mara kunya,to anqi din har sai ta yarda da kanta" ya kama qafar momin yace "wallahi momi fadeelah ta haqura" ta dake dariyar dake cinta "kaga,mu bata gaya mana ba yallabai sai ka jira har sai ta gaya mana da kanta"ya marairaice "momi kunya fa kinsan take ji,ba zata iya gaya muku ba"momin ta tabe baki "ok,sai kai wato rasa kunga shine kazo kayi rashe rashe a gabana kake gaya min ko,don Allah tashi ka tafi gidanka ni na gaji da ganinka anan"
Kai yake gyadawa kamar qadangare "shikenan momi,shikenan sai da safe"ya miqe ya fice cikin zuciyarsa yana fadin "zan shuka tsiya kawai,komai ta fanjama fanjan,su momi basu yanda nake ji bane"uncle abba dake can tsaye yana kallonsu yqna shan dariyarsa ba tare da sun sani ba ya qaraso "haba maimunatu,ayi haquri haka nan a bashi matarsa,tunda sun sasanta kansu,ni kam na fara tausaya masa,kinsan ciwon da namiji ma na da namiji ne"ya qarashe fada cikin zolaya,dariya uncle abban ya bata sosai"shikenan tunda abun wariyar launin fata ce nima ai ciwon 'ya mace na 'ya mace ne,sai na gyara diyata nima,idan yana so jibi ko gata sai a bashi ba don halinsa ba"
Ya sunkuya yana qoqarin dauke mata iftihal daga kan cinyarta "mudai tunda za'a bamun ai shikenan godiya muke,bari in dauke miki amaryar taki,kije ki huta kema"ta saki murmushi tana cewa "godiya nake abba"ta miqe tabi bayansa tana barwa sumayya da rabi'ah dake kitchen auna wanke kwanukan da aka bata don basa barin wanke wanke ya kwana sallahun idan sun gama su kashe duk qwaya qwayai da kayan electronic na parlour da kitchen din
Tunda ya zaunar da ita a gun ta bingire ta kwanta saboda kasala,juyi kawai take tana tariyar abinda ya farun a wunin gau gana daya tsakaninsu,babuabunda take saki sai murmushi,shi din ma koda ya fito daga wanka kasa hasala komai yayi,sai da ya zauna gefan gado ya dauki wayarsa ya kirata,tana tsaka da juyin nata ne kiran ya shigo mata,ta gyara kwanciyarta hadi da rungume pillow sannan ta amsa,sallama ta masa da muryarta mai sanyi wadda ke saka susuta shi "fadeelah bazan iya bacci ba sai naji muryarki"
"But...."sai kuma tayi shiru
"But what?,pls gaya min abu daya wanda zai sani samun nutsuwa idan nazo baccina"
numfashi ta ja sosai sannan tace"i love you for all that you are,all that you have been,and all you're to be my haidar"kalaman sun tsaru sosai cikin kunne da zuciyarsa,ta kashe masa jiki da zaqin kalamansa,idanunsa na a lumshe yace "are you sure babe?" "Yes am sure,duk abinda na fada I mean it"dogon sumba ta bashi a wayar sanna ta kashe tana murmushi qasa qasa,shi kuwa mutuwar zaune yayi gaba daya tsigar jikinsa ta zuba..........
*Mrs muhammad ce*๏ฟผ๐
๐๐๐๐โ๐ปโ๐ปโ๐ป
[10/16, 2:16 PM] ๐๐ฌ๐Salma๐๐ฌ๐: ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ
*WA YASAN GOBE?....*
๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ
๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ
๐๐ผ *PART 3* ๐๐ผ
2โฃ1โฃ&2โฃ1โฃ
Shi kuwa mutuwar zaune yayi gaba daya tsigar jikinsa ta zuba
โโโโโ
Zaune take a nutse cikin office din,sanye take da shadda dinkin riga da zani rapper marun,sosai shigar ta yi mata kyau matuqa ta kuma dace da fatarta,hakanan take kullum ba dai tayi kwalliya a kushe ba,ta iya dressing sosai,hannunta dan madaidaicin cup ne cike da coffee tana dan kurba kadan kadan don babu abinda ta iya ci tunda gari ya waye,gaba daya hankalinta na gun aliyu tunaninsa take,amma idan ka kalleta a zahiri qata news paper dake gefan hannunta ta zubawa ido tamkar mai nazarin wani abu a cikinta
Yafi minti goma a atsaye bakin qofa,sam baya gajiya da kallonta,baiqi su dawwama a haka ba,tsarin shigar tata yayi masifar tafiya da shi tayi wani das tamkar fure,sai kuma aka taki sa'a shi din ma marun din shaddar ce a jikinsa
Har ya iso bata ankara ba,a hankali yasa hannu ya zare cup din coffeen dake tsakiyar tafukan hannayenta "irin wannan zurfi a tunani bai dace da kyakkyawa ba" ya fadi yana maida cup din gefe,yaja kujerar dake opposite dinta ya zauna yana cewa "nasan dai ji kike tunani ko....to gani na iso ai sai abar hasashe a koma zahiri"murmushi ta saki a kunyace tayi qasa da kanta,ya sake binta da mayun idanun nan nasa,gani yake tamkar kullum wayewar garin Allah kyau ake dada mata,ya jawo tattusan hannunta dake zube saman table din yana matsawa,ji tayi kamar wani sinadari yake zubamata cikin jikinta,ta soma qoqarin zame hannunta tun kafin yayi mata illa cikin kunya "no baby,your hand fits in mine like its made just for me,kada ki cire"
Ta dan zame dag kan kujerar ta gaidashi,noqe kafada yayi "naqi,ni ban irin wannn gaisuwar nake so ba,let me show you irin wadda nake so"kafin tace komai ya zagayoda ita zuwa inda yake zaune yayi mata mazauni kan cinyarsa,qam ya matseta,sai da ya yamutsata son ransa sannan yace "irin wannn gaisuwar nake so ko a ina muke right?"gyada ka tayi cikin jin nauyinsa,ta bishi ne da haka amma itakam rashin kunyar aliyyun tafi qarfinta "a'ah dear,ki daina min rowar sweet voice dinki,ki dinga bude baki kina magana sannan ki dinga bude idanunki sosai kina kallona,zuciyarmu ta riga ta zama daya....dubi"ya fadi yana juna mata dressing din da suka yi "baki san me zansa ba nima bansan me zaki sa ba amma saboda zuciyarmu na manne da juna mukayi shiga iri guda"
Murmushi ta saki tana kwantar da kanta a kafadarsa,"ok,I hope kin shirya,don daga nan sai asibiti,gwara muje kiga doctor sa'adah"ya fadi yana sunkutarta kamar wata bebin roba,wutsil wutsil ta soma yi da qafafunta "please my haidar,zan iya tafiya kada ka fita da ni a haka"dariya taga ya saka,ta dan saci kallonsa don bata taba ganin dariyar tasa haka ba,ya maimaita abinda tace cikin kwaikwayar muryarta sannan ya direta "matsoraciya,dama tsokanarki nake"duk da haka bai qyaleta ba sai da ya kamo hannuwanta,a haka suka isa bakin motar,ya bude mata ta shiga sannan shima ya shiga
Ko a office sai da doctor sa'adah tayi masa wayo koreshi waje da qyar don ya hana fadila sakat ,kunyar doctor din fadilan keji shikam ko a jikinshi,da zarar fadilan ta bude baki zatayi magana sai yayi sauri ya rigata cewa "doctor rabu da ita,awo na kawo miki ita,na jefa qwallo a raga" mamaki da kunya suka kama fadila haka aliyyun yake?,tamkar ba wannan aliyyun nata ba,ita kanta doctor sa'adah din tayi mamakin yadda ya sake yana ta raha har irin haka kamar ba aliyu salim maitama ba,mintina talatin doctor sa'adah ta gama duk wani bincike da gwaje gwajenta,madaukakiyar fara'a da farinciki da ta gani kan fuskar doctor din shi ya bata mamaki "congratulations fadila,naji dadi da ya zamo nice ta farko da zan taya ki murna,Allah ya albarkaceki da samun juna biyu"ta fadi tana sanya tafin hannunta cikin na fadilan
Sak fadilan tayi tanajin kunnuwanta kamar basu ji mata dai dai ba,ciki gareta da gaske?,cikin aliyyu a jikinta?,aliyyu masoyinta?, *alhamdulilahil lazi bini'imatihi tatimus salihaat*,wannan baiwa da ni'ima ta Allah da me tayi kama?,Allah kenan mai kyauta da qari,buwayi gagara misali,mai azurta bawa a duk sanda ya so,mai amsa addu'ar bayinsa,yau ga aliyyun Allah ya bata kuma ya bata dan aliyyun cikin cikinta,ya zabeta cikin matansa yace ita zata haifa,batasan lokacin da hawayen farinciki suka balle mata ba,a hankali bakinta ya soma salati ga fiyayyen halitta,sannan ta dora da godiya ga ubangiji, "na godewa Allah gwanin iyawa,doctor pls bana son ki sanar da aliyu batun cikin nan yanzu,nasan bazai iya shiru ba sai kowa ma ya ji,kuma....."
Dai dai nan aliyyu ya turo qofa ya shigo,da sauri ya qaraso a rude ganin hawaye kan fuskar fadilan,dagota yayi ya rungume yana goge mat fuskan"me ya faru ?,doctor me kika yiwa mata ta?"ya fadi cikin hade rai,dariya sa'adah tayi "farinciki ne yayiwa matarka yawa,don ance lafiyarta qalau shine don shagwaba take kuka"ta miqa masa takardar magunguna "wadan nan zata dinga sha,but gaba buqatar hutu da kulawa sosai,idan an gama lallashin ku rufe min qofar office din sir,zani inyi round na marasa lafiya,ta sanya lab coat ta fice tana musu dariya"
Ko cikin motar kanta na langabe ne jikin sit,gaba daya jikinta yayi sanyi,sai ta ruda aliyyun gaba daya ya kasa driving din dole yayi parking din motar yana tambayarta,murmushi ta saki"am fine my haidar" duk da haka sai da ya sanyata cikin jikinsa sannan ya samu ya iya ci gaba da tuqin,ga zatonta zai maidata ne gurin aiki amma sai taga yayi nassarawa da ita,cikin rashin fahimta take dubansa "nayi zaton zaka maida ni ne office ko tunda ban tashi ba"ya girgiza kai "no fadeelah,yau gidammu zamu koma"
da sauri ta dubeshi "gida haidar?,bada izinin su uncle abba ba?"
"Shshshshsh!" Yace "nafi kowa iko da ke fadeelah,na gaji da rashinki,na qosa kiyi haquri kawai idan naje gidan ni zan sanar musu,zan fahimtar da su ba laifinki bane,bare ma ba zasu ce komai ba I know"
Ta zumburo zata sake magana "tuni ya sanya bakinsa cikin nata ya hanata cewa komai,saura kadan sitiyarin ya kubce masa Allah ya taqaita ya kamo shi
Da kanshi ya bude mata part din nata don babu key din a a lokacin a hannunta,sai zumbure zumbure take ita a dole fushi takeyi da shi,shi kam dariyarsa ma yake lokaci lokaci,bai damu ba tunda burinsa ya cika,fridge ya nufa ya ciro ruwa duk da babu sanyi kasancewar wutar bangaren a kashe take,ya jawo gabanta ya durqusa,ya jawo ledar magungunan ya ballo mata,ya bude gorar ruwan sannan ya kalleta "haa" yace da ita,shiru ta masa sai da ya sake cewa "bude bakinki"nan ma tayi shiru,sai ya dire ruwa da maganin kan center ya miqe yana shirin core rigarsa yana cewa "tunda kin zama kurma inada muqullin bude bakinki" a razane ta dubeshi,bata san lokacin da tace "me zaka yimin?"yadda ta razanar da kuma yanayin yadda tayi maganar shi ya bashi dariya,ya tuntsure da dariyarsa yana maida rigarsa da ya soma cirewa har fara qal din vest dinsa ta soma bayyana,ya koma gabanta ya tsugunna yana cewa "ashe dai matsoraciya ce,baki shirya fadan ba amma kika takaloshi,oya bude bakin"bata ko sake musawa ba ta bude ya sanya mata magun gunan sannan yasa maya ruwan a baki har sai da ta hadiye
Ya miqe ya cire mata mayafin da dankwalinta,ya zare mat sarqa da dan kunneta duk tana kallonsa,ya debe qafafunta ya maida saman kujera ya dora mata pillow sanann ya harde hannayensa a qirjinsa yana duba agogon dake manne a bango "oya,maza kwanta kiyi bacci ko na one hour ne don maganin yafi saurin bin jikinki,after one hour sai ki tashi kiyi sallah ok?" Cikin shagwaba wadd ta ruda aliyun tace"amma dai kasan ban kyauta ba ace daga zuwa gun aiki ace na dawo gida na ko?"sauje hannun nasa yayi ya dawo gaban kujer ya tsugunna har yana jingina gwiwoyinsa jikin kujerar,ya koma serious sosai,yasanya tafin hannunta cikin nasa,sosai ya sa qwayar idonsa atata "fadeelah" kallon cikin idonsa tayi,yadda taga ya zama serious hakan yasa ta bawa maganar tasa muhimmanci "duk duniya babu mai haqqi a kanki daya kaini,bana so ki dinga sawa ranki damuwa kan binda yake mai sauqi ne,su momi sun ajjiyeki ne don ku sasanta kanmu da kanmu ba tare da kowa ya shiga ciki ba,sannan ni na sake gane kuskure na,to yadda suke so din duk ya faru,me kuma ya rage?uumm?,sai mu dawo gidan mu fadeelah mu shimfida sabuwar rayuwar auratayya wadda zata kuma farantawa iyayemmu rai,ina kuma fatan zan samu goyon baya daga gareki?"
Sosai take gyada kai "insha Allah mijina,na yi maka wannan alqawarin" ta dam zamo daga saman kujerar ta durqusa itama a gabansa "ka yimin afuwa ranka ya baci,ya saki qayataccen murmushi "ba komai baby na,bakya taba yin laifi a guna"ya sumbaceta sanna ya maidata ya kwantar saman kujerar,"kiyi bacci sosai,banda cewa zaki tashi kiyi aiki,gidanki babu dattin komai,don kullum sai na share miki shi"tana daga kwancen ta qwalalo ido "shara?kuma da kanka?"murmushi ya kuma saki"kina mamaki ne?,kinfi gaban haka,mene ke baki bani ba a rayuwarki fadeelah?"itama murmushin tayi "haqqina ne ai In maka har fiye da hakan" "jiniina kai yayi cikin zuciyarsa yana godewa Allah,babu shakka yayi gamo da katar da mace ta gari,wanda samuntabke matuqar wuya a wagga zamani "ina sonki my baby fadeelah har bansan adadi ba,ina alfahari dake,ina alfahari da kasancewarki cikin rayuwata"ta rufe fuskarta da tafin hannunta "ina sonka haidar dear,nima kuma ina alfahari da kasancewar ka miji a gareni har abada"wani dadi yaji ya kama shi,ya sake sumbatar bayan hannun nata yave "na gidewa Allah fadeelah,sai na dawo,zansa nasiru ya kawo miki motarki ,sannan zan daukar miki excuse gurin aiki su baki hutu na sati"bata ce komai ba don bata son ta kasance mai yawan musu da shi,bare itama zata so hakan,don tana buqatqr lokaci da zatayi wasu 'yan gyare gyare,sabida haka kai kawai ta gyada masa tana satar kallonsa ta tsakanin yatsunta har ya fice,wani annushuwa da farinciki da kwanciyar hankali mara misali taji yana ratsata
Ta janyo wayarta ta nemo number din farida,bugu daya ta dauka tamkar dama tana jiranta ne,cikin ihu take cewa "yeyyyyyy sister yaushe kuka dawo haka babu labari?"cikin murmushi fadeelah ke cewa "wayyo Allah zaki kashemin dodon kunne mana,cikin satin nan ne,kiraki nayi dama nace miki ki turo min mai gyaran jikin nan don Allah"wani ihu faridan ta sake saki cikin dariya "kai mutuniyata,wallahi da labari,tafiya tayi kyau mune winners ko?" "Kai....faridaaaa....sai yaushe zaki girma ne don Allah?" Tayi qasa da murya "kai sister,rowar story zaki mun kenan don Allah?"dariya ta bawa fadilan don tasan farida akwai son jin tsurku "hab abokin kuka ai ba'a boye masa mutuwa,zaki sha labari har sai kin gaji kin toshe kunnuwanki" "a'ah nasan halinki fa sister,zaki dai bani wanda kika ga dama,yanzu zan mata waya na gaya mata"tayi dariya "yauwa ko da yamma ne sai tazo,sau nake ta fara yimin yau don gaskiya nag ta iya" "kai sister sosai ma,ko sau daya fa ta miki sai kinga kin canza gaba daya,akinta da kyau sai tsada,bayan gyaran jiki har kitso da qunshi ma ta iya sosai"
"to yayi,ina humairata,Allah sarki aishana,nayi missing dinta a lot"
"Yanzu babanta ya fita da ita sitting room yayi baqi"hamma ta kubcewa fadilan har sai da faridan taji "idan sun shigo kice ina gaidasu ita da abban nata,ni zan kwanta"
Dariya farida ta saka "tabdi lallai sister,kai saidai na zo kawai"
Katse wayar fadila tayi taba murmushi don tasan halin farida bata qi su kwana suna abu guda ba.........
*Mrs muhammad ce*๏ฟผ๐
[12/16/2016, 10:12 PM] Ameenah Abdulmajeed๐: ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
*WA YASAN GOBE?...........*
๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
*PART 3*
2โฃ1โฃ
Doctor sa'adah ta kammala rubuce rubucenta,ta dago ta kalli aliyyu "masu qaramin ciki kamar hakan suna buqatar daga qafa adinga sassauta mata gaskiya"
Zaro ido yayi kamar yaro"what?!,su waye Duke da ciki?"cikin mamaki ta sake dubanshi "oh,baka sani ba.....anyway kaji a bakinta,ga magunguna nan ,ba za'a yi birede a gaba na ba,idan kun tafi nurse zata zo ta kulle qofa"tayi haka ne don tasan za'ayi budurin yadda tasan alin da son yara na masifa
A hankali ya duqa gabanta "da gaskene Fadeelah kina da ciki?"cikin jin kunya ta gyada kai,sai ya hade fuska tsam,ciki tsawa tace"don me yasa zaki boyemin kyautar da Allah yayi min?shin ban can can ci in sani bane?"
A Dan tsorace ta kalleshi,sai Kuma taga ya rungumeta "am sorry dear,banji dadi bane da kika boyemin,kunya Daren jita na cutar da ke,da wa ni Abu ya faru daku keda baby na bazan yafewa kaina ba Fadeelah,bazan gaji da roqamiki rahamar Allah ba,bazan gaji da roqarmiki albarkar ubangiji ba,ke din wa ni alkhairi ce a tartare da ni ,bani d halin da zan miki godiya don tayi kadan,bansan da me zan saka miki da shi ba fadeelah,Abu day dai da na sani kin zama mahadin rayuwata Fadeelah,na tabbatar idan babu ke rayuwata bata da amfani"
Ga mamakinta sai taji ya fashe da kuka sosai,tabbas rabo ajali,rabo ne mai zafi ashe tsakaninsa da fadilan,hawayene sosai ke sauka bisa fuskarsa,hakan ya sake nunawa fadila yadda Aliyyu ke tsananin son yara,ita din ke share masa hawaye tana lallashinsa
"Allah shi ya cancanci ka godewa bani ba,ni da kai duka bayinsa ne yadda yaso haka zamu gani"
Baiyi qasa agwiwa ba Kuwa ya kama"alhamdulillah"ba qaqqautawa
"Allah ka yimin dukkan wata ni'ima a rayuwata,Allah ka bani ikon saka maka ta hanyar yi maka da'a da biyayya da bin dukkan wani umarni naka"
Addu'ar d aliyyun y dinga yi kenan gwiwoyinsa kafe a qasa hannayensa a sama,ba fita daga asibitin ba sai da ya yiwa doctor sa'adah albishir din Kujerar umrah,fadilan ma haรฑata tafiya yayi ya kafe sai dai ya dauketa,sai da tasa masa kukan shagwaba sannan ya bari,roqarsa ta dinga yi cikin mota don Allah kada ya fadawa kowa
Girgiza kai yayi"mummunan labari ake boyewa,ban miki alqawari ba ruhina,na dai yarda bazan fada ba amma Duk wanda ya tambayeni zan fada masa"ba yadda ta ita haka ta qyaleshi,motsi kadan yace"sannu,yaya?"
Tun tana amsawa har ya soma bata dariya,
Marairaice masa tayi kan sai ya kaita gida taga umminta,dole ya kaita ganin tanason sa masa kukan nan nata da ba yaso,tayi Sa'a kuwa ta tadda Farida tazo,wayyo dadi gun Fadila ba'a magana,humaira nata rarrafe abunta,yarinyar ta sake kyau kamanninta da fadilan ya sake fitowa,sai ta sake shiga zuciyarta,Fadila na shirin daukarta ummi tace"Allah yasa ta yarda da ke 'yar nema,wai nan qiwa fa take"sai kuwa ta ba su mamaki don luf tayi abunta jikin Fadilan
Can jimawa saiga 'yan biyun Anty hafiza,tunda cikinta ya tsufa ya Ahmad ke tarkatosu gun ummin lokaci bayan lokร ci musamman weekend dob mamansu ta huta, ummi ce ta kalleshi"gayamin kwana nawa za suyi,don bazasu zo tafiya amira rigima ba"yayi murmushi"anjima ma zan dau ke su,idan natashi daga kasuwa,naji tana gobe can gidansu za'a kaisu za suyi taro"
Sai kuwa hussaina tace"abba da hassana kawai zaka tafi ko?ni a gun ummi sanya kwana"ta fadi taba fadawa saman cinyar ummin"kiji mai ka irin wayo wato don kin fita baki ko"inji Muhammad daya dungure mata kai din shi hasana ce mutuniyarsa
Ummice ta bige masa hannu"ina ruwanka ,baban kawai"ya qyalqyale d dariya ya dauke hassanar sukayi ficewarsu yana yiwa hussainar gwalo,bata damu ba don ta saba da hakan ta fada cinyar ummin tayi kwanciyarta
*Mrs Muhammad ce*๐
๐๐๐๐๐๐โ๐ปโ๐ป
[12/16/2016, 10:12 PM] Ameenah Abdulmajeed๐: ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
*WA YASAN GOBE?..........*
๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
*PART 3*