Showing 93001 words to 96000 words out of 130495 words
Chapter 32 - Wa Yasan Gobe Compelet Book by Safiya Abdullahi musa huguma
ta shirya mata yaran da safe
๐
๐
๐
๐
๐
๐
Gudu sosai ya dinga yi shi daya cikin motar,cikin ikon Allah ya sauka lafiya,saidai tun daga yadda su ya gana ke faman tambayar fadilan ya sare da al'amarin ya tabbatar bata garin ma baki daya bare gidan,sallah kawai yayi ya baro garin,bai damu da yawan tafiyar da yasha ba bare ya nemi hutawa har yaci abinci,juyin duniya ya gana tayi ya tsaya yaci abinci amma qeme me yaqi,ya bata haquri bayan ya ajjiye musu kudade masu dama yace yana da abubuwan yi masu yawa a kano,haka ya kamo hanya ya taho,gudu na ban mamaki ya dinga shararawa ba qaqqautawa,sai da yaji tuqin na neman gagararsa sannan ya samu wani shago kam hanya ya siyi yoghurt yasha,bai fasa gudun nasa ba wanda ikon Allah ne kawai ya kawoshi garin kano lafiya
๐
๐
๐
๐
๐
๐
Kwana hudu bai cikin daidanshi,matansa mata ne marasa kulawa,tabbas sunga canji sosai tattare da shi amma babu wadda ta damu da tambayarsa mene damuwarshi,momi kam ganin baice komai ba yasa ta tsuke bakinta ta qyaleshi don ta sani ida dai ya soma zurfin cikin nan nasa bai gayawa kowa komai sai lokacin da yaga dama
*G*idan anty hauwa shine gida na qarshe da hankalinsa ya kai kai,anan ya tattara dukkanin fata da tsammaninsa,duk da wata zuciyar na tantamar mai zaya kaita can bayan ko gidansu bata je ba?,qarfe biyar da shirin na yamma ya gama shirinsa cikin qananun kaya da sukayi matuqar yi masa kyau
Suna kitchen ita da fadilan suna hada abincin dare sunayi suna hirarsu,yara suka jiyo wadanda suka bari a falo suna kallo da yake alhamis ce suna cewa "ina wuni uncle....ina wuni uncle" gaban fadila yayi mummunar faduwa ta saki mirfin hannunta da take shirin rufe miya da shi,"shikenan yau zan amshi takardar rabuwa da shi" abunda zuciyarta ke gaya mata kenan "anty aliyu ne"ta fada tana kallon anty hauwa dake tace shinkafa "aliyu?" Ta fada tana kallon fadilan cikin kasa kunne,"ina zuwa" anty hauwa fada bayan ta ajjiye tukunyar hannunta ta fice da sauri,komawa fadila tayi jikin drawer ta jingina bayan ta hatde hannayenta a qirjinta tana jiyo sweet voice din sa,batasan me yasa take jin qunci a qirjinta dalilin gaya mata da zuciyarta ke yi takardar sakinta aliyun ya biyota da ita
Ruwa aliyun yace ma anty hauwa ta bashi,duk ruwan dake freezer din falonsu ya qare sai lemo,da hanzari anty hauwa ta miqe ta hau sama ta dauko masa a parlour din abban kausar don bata son ya shiga kitchen din,ji yayi bazai iya jiranta ba don haka ya miqe ya shige kitchen din,a hankali fadila ta bude idanunta da a da ke a lumshe,cikin jikinta take jin tahowar tasa,nan da nan tayi wuri wuri da ido tana neman maboya,a asukwane ta shige bayan qofar wadda a kusa da ita freezer din take
Kai tsaye ya qaraso ya dage freezer din ya sunkuya yasa hannunsa ciki,cak ya tsaya da qoqarin ciro ruwan da yake yi,sai yake jin qamshinta cikin hancinsa,irin qamshin da ya ji cikin bargo pillow da undies dinta,sakun murfin yayi ya soma kallen kallen kitchen din yana neman ta inda qamshin ke fitowa,ko ina ya kai idanunsa sai yaga babu kowa,tuni fadila tayi surrender bayan qofa numfashinta kamar zai dauke musamman da taji ua jingina a bayan qofar ya kuma qin barin gurin,yafi minti uku cikim kitchen din yaqi fita din qamshin turarenta na ahlamul arab kawai yake ji,hat sai da anty hauwa ta shigo hankalinta a tashe tana tsammanin ya ga fadilan,sai ta tadda shi a tsaye kawai jingine jikin qofar hannayensa harde a qirjinsa,"ina ka shiga ga euwan can na kaimaka" "ok" kawai yace ya gewayeta ta fice daga kitchen din itama ta rufa masa baya
Ta maida yara dakinsu daga ita sai shi a falon,zuba masa ido tayi sosai tana kallonsa canji qara ta hango tattare da alin,fara'arsa ta sake qaranci sosai,tsiyayar lemon kawai yake yi yana dirkawa cikinsa,yadda bai tanka ba itama bata ce kamzil ba har sai da ya tashi da roba biyu ta ruwa da lemo,ya dago kai ya kalli antin hadi da sakin ajiyar zuciya "ni wai uncle meke damunka?tunda kazo naga kamar a hargitse kake?"wata ajiyar zuciyar ya kuma saki "fadeelah nake nema mummyn kausar" kamar gaske ta nuna alamun rashin fahimta sosai "kamar yaya?fadilan da kuke tare,yaushe dududu sumayya ta ke gayamin kun dawo daga china zaka ce ita kake nema kamar wadda ta bata" "bata tayi....bacemin tayi"ya fadi yana jingina jikinsa da kujera,yayin da fadila dake labe cikin kitchen ta zaro ido jin cewa wai nemanta yake "yayimin me? Me zayayimin ne?"ta tambayi kanta ba tare da tasan amsar tambayar ba
Ya dora cikin wata iriyar murya "tayi tsammanin bana sonta ne bayan nima na dade ina sonta,tayi zatin maqiyinta ne ni alhali duk duniya babu mai sonta kamar ni...ta dauka ina zaune da ita ne bisa dole bayan kan son raina nake zaune da ita.....anty ta yimin gurguwar fahimta,ta gujeni a lokacin da na qara zurfi cikin qaunarta....ta gujeni a lokacin da dukkanmu ni da ita muka fi buqatar kasancewa da juna"ita kanta anty hauwa baki ta saki tana tsammanin ba aliyu bane,aliyyun da tunda take tare da shi zata iya cewa bata taba ji ko ganin yana kwatanta qaunar da yakewa wata diya mace ba aduniya koda uwar 'yarsa,fadila kam dake cikin kitchen duburburcewa tayi,sai jikinta ya fara rawa qafafunta suka gaza daukarta ta lallaba ta ja jikinta ta zauna kan kujerar roba bakinta rufe da tafin hannunta yayin da hawayen da sukayi kwana da kwanaki tana qumshe su yau suka samu qofa.
Lallai ma yaudararta aliyu keson yi?,dama shi din shahararren mayaudari ne,shine a yanzu zai furta cewa yana sonta?wanne irin zama ne basu yi ba baice yana son nata ba sai ayanzu?sai yanzu da ya kwanta da ita?,ya tabbata kenan jikin nata yake so kamar yadda tayi zato tun farko? (Illar zato),sha'awarta yake kenan ba qauna yake mata ta cikin zuciya ba?,kuka ne sosai mara sauti ya kufce mata yayin da shi din ma ke can zaune dirshan gaban anty hauwa yana fayyace mata irin zaman da sukayi da fadilan,kunne sosai ta saka tana jinsa duk da yake tamkar tishi yake mata,duk yadda fadilan ta fada hakanne harda wasu abubuwan da fadilan ta boye ta qi fada
Kafin ya kammala tuni har qwalla ta cika idanunsa duk da bata gai ga zubowa ba amma qiris take jira,soyayyar 'yan uwan taka sai Allah tuni tausayinsa ya kamata don zata iya dafa qur'ani kan aliyyu bai taba shiga makamancin wannan halin ba akan wata mace,ta karanto gaskiyarsa qarara,don dama ko ada bai iya qarya ba tun yana qaraminsa,zai gaya ma gaskiya ne ko za'a tsireshi don haushi,to saidai bata jin kuma zata shiga haqqin fadilan ta karya alqwari da ta daukar mata don aliyyu nata ne,bata jin zata sarayar mata da haqqinta tunda nata din ne,ita ke da iko da abunta,ita kadai tasha haqurinta ita kadai tasan me ta hadiya
Cikin sanyin jiki da qunar rai yace"wai anty roqona take na saketa,tana tsammanin sakin nata abu ne mai sauqi har irin haka a gurina?" Ya kada kai yana cewa"bazan iya ba,bazan iya furta wadan nan kalmomi gareta ba koda duka duniya zata taru a kaina" dole ka sake ni aliyyu dole mu rabu ,bani kake so ba jikina kake sha'awa" ta fadi haka qasa qasa cikin kuka mara sauti,ya miqe "zan tafi tafi tunda kema bata gunki zan ci gaba da nemanta",tuni ya juya ya fice daga gidan,tausayin dan uwan nata ya kamata don tasan wahla kawai qanin nata zaici gaba da sha tunda fadila na tare da ita
Kifa kanta tayi kan cinyarta ta sake sakin wani sabon kukan mai dan qaramin sauti,wani qunci zugi da radadi data rasa na meye take ji cikin ranta,anty hauwa ta kama hannayen fadila tana kallin qwayar idonta "fadila.....fadila,naga abubuwa da dama cikin qwayar idanun aliyu,naga soyayya naga qauna cikin cikin idonsa irin wadda ban taba gani ya yiwa wata 'ya mace ba,kinji komai da kunnuwanki no need na maimaita miki"
Kada kai fadilam keyi,"anty na yarda aliyu na sona a yanzu bazan qaryata ki ba,anty amma ba ni fadilan yake so ba wani abu dake gareni yake so,tun yaushe anty....tun yaushe nake tare da shi nake kyautata masa bai taba cewa yana sona ba sai yanzu?sai yanzu da wani dalili ne ya jawo hakan?...Thank god aliyu na sona yanzu anty,saidai ......is too late anty I already displaced him from my heart,na goge cikin kundin rayuwata zan rayu da shi" kalmar ta fito daga bakinta hade da hawaye
Sai dariya taso kama anty hauwa amma ta gimtse,with confidence fadila ke fadin maganar saidai qwayar idanunta kadai ta ta qaryata ta,bata sani ba ita kanta qaunar aliyyu tayi mata illar wadda take huduwa tun daga zuciyarta har zuwa idanunta da bakinta,bata da abunyi anty hauwa ta sani wani daci ne da fadilan ta dade tana guntsa taje fesarwa idan ta hanata kuma bata yi mata adalci ba,tasan cewa kokwanto ne yasa fadila fadin wadannan maganganun amma ba har cikin zuciyarta bane,ta kuma gama gasgatawa wani irin salon rikicin soyayya ne ya kunno kai kawai tsakaninta da aliyyun,sanoda haka sai kawai tave mata "shikenan fadila kici gaba da addu'o'inki ki yi ta istihara,Allah ya zaba abinda yafi alkhairi"
Har anty hauwan ta kai bakin qofa fadila ta dakatar da ita ta hanyar cewa"am sorry anty idan maganganuna sun bata miki rai" murmushi ta saki "don't mind,banji komai ba araina fadila" murmuahi itama tayi mata tace "na gode" haka Allah yayi fadila bata aon bacin rai ko yashin hakai ko kadan kamar yadda bata son taa ta batawa wani rai ko ta shiga haqqinsa
Kwana biyu yama cikin wannan hali,duk wasu harkokinsa na gida dana waje yaqi maida hankali kan kowanne,daga qarshe dai kasa jurewa yayi gani yake kamar su suka boye masa fadila,yana ganin da wani yashin hankalin gwara wani,da ya rasata gwara a yanke masa duk wani hukunci da za'a yanke masa idan yaso su bashi ita,ya gaza jure kewarta komai nasa ya yi missing dinta,
๐
๐
๐
๐
๐
Tsakiyat uncle abba da momi ya zauna ya warware masu abinda ke faruwa kamar yadda halayyarsa take fadin gaskiya,momin ce ta saki salati mai nauyi yayin da uncle abba yayi shiru gami da yin tsai da ransa,sai a lokacin ne kuma hankalinsa ya soma tashi momi tayi shiru ne tana jiran jin umarni ko me mijin natazaya fada?,yayin da uncle abba ya rasa me ma zaya ce din?,sama da minti biyar kafin ya dago yace "tashi kaje aliyyu" cikin firgici ya dago kai yana kallon uncle abban,ya sake maimaita masa"ka tashi kaje nace mu zamu nemota" alhaji yaje fa kace?" Momi ta fada cikin fushi,a nutse uncle abba ya kalleta "to maimunatu mai zai zauna yayi min?,yaje kawai tunda ya gama nasa aikin ko,mu kuma ba sai muyi namu ba?"
Tasan sarai halin mijin nata saboda haka ta gamsu da abinda yace "gaskiyane"shi kam aliyyu yadda bai tanka ba sabida rudani haka ya kasa tashi kansa na sunkuye jinsa yake kamar wani mutum mutumi,har sai da uncle abban ya gaji da ce masa ya tashi shi da momin suka taahi suka bar masa falon
Da azahar momi ta dauki wayarta ta kira anty hauwa kamar yadda uncle abba ya ce ta ce mata yana son ganinta ko zuwa najima ne,sai kuwa aka taki sa'a suna cikin gaisawa kausar ta soma qwala kiran "anty fadilah!anty fadila!!na kasa daukowa"nama ne tace ta ciro mata cikin fridge sunce suna son dambun nama to naman ya riga yayi qanqara,tuni momin ta tsaya da amsa gaisuwar "maijidda wace fadilance a gidanki?" Cikin son boye boye tace "am ....fadila ce ta zo mu gaisa,dazun aliyun ya sauketa" "mu kuma dazu aliyyun ya bar nan yana cigiyar ta ba"momi ta katseta "aljanu ke miki wasa da hankali ko gida biyu su aliyun suka rabu?" "A'ah momi ai" "kinga dakata shi aliyun ya riga da ya sanar da babaku komai da kansa,dama maganar da na kira ki kenan akai,saboda haka idan anyi magariba ki dauko ta kuzo"
Hawaye bibbiyu fadilan keyi"anty me yasa kika sanar musu anty,munyi alqwari dake anty,me yasa suka sani?" "Fadila aliyyu da kansa yakai kansa gun abba,momi kuma ta san kina gidan nan dazun da kausar ke qwala miki kira" "me yasa aliyyu zai min haka?,don me yasa zaije ga uncle abba?,me yasa baiyi sakin cikin rufin asiri ba?,so yake kowa sai ya ga laifinshi kenan?"sai lokacin tayi dana sani,tayi data sanin da ta fito tun ranar da yazo gida anty hauwan ya bata takardarta ba tare da kowa yaji ko ya gani ba,suna sake doso unguwar bugun zuciyarta na daduwa,tabbas da kafin su yi nisa naty hauwan ta gaya mata inda zasu babu shakka ba zata ba sauka zatayi,gaba daya jikinta rawa yaje ta kasa nutsuwa sai da anty hauwan ta riqeta sannan ta iya shiga falon.........
*mrs muhammad ce*๐
๐๐๐๐๐โ๐ปโ๐ป
[10/16, 2:11 PM] ๐๐ฌ๐Salma๐๐ฌ๐: ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ
*WA YASAN GOBE?....*
๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ
๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ๏ฟผ๐บ
๐๐ผ *PART 3* ๐๐ผ
9โฃ&1โฃ0โฃ
Umminta ta gani da mominta zaune kujera daya,uncle abba da abban nata kuma na kujera daya,sai iftihal dake zaune dare dare kan cinyar abban nata,duk kansu suka amsa sallamar,sosai taji dadi cikin ranta don rabon da tasa iyayen nata a ido har ta manta,sai dai hararar da ummin nata ta watsa mata ita ta sagar mata da gwiwa,anty hauwa ce ta fara gaida su sannan itama ta gaidasun,sama sama ummin ta amsa mata don har gwara abbanta,cikin salubewar jiki ta koma gefan kujera ta rakabe
Aliyyu ne ya shigo cikin sallama yana sanye da shadda dinkin tazarce kansa babu hula,da gudu iftihal tayo gurinsa,hannunta kawai ya iya riqewa bayan da ta gaidashi,gaida su yake saidai abba da umminta ne kawai suka amsa masa,yana shirin samun guri ya zauna uncle abba ya dakatar da shi ta hanyar cewa "kai....dakata ba zama na kiraka kayi ba...ungo nan" ya miqa masa farar takarda da abun rubutu "rubutawa yarinya sakinta tunda Allah yasa mun ganta" da sauri ya daga kai ya soma rarraba ido cikin filin falon yana neman inda fadilan take,can ya hangota a takure a gefan kujera kanta a qas
Gaba daya idanunsa suka rufe,tuni ya manta da cewa akwai wasu wai iyayensa a falon ya durfafeta,idanunsa qir bisa kansa,wani shauqi mai cakude da matsananciyar qaunarta yake fisgarshi,sai da yaje daf da ita uncle abba ya daka masa tsawa wadda ta sashi dawowa cikin hayyacinsa "qaniyarka nace dawo nan" inji uncle abba yana masa nuni da gabansa inda zai zauna din bayan daquwar da ya watsa masa,a salube ya nufi gun yana tafiya yana waiwayen fadilan da kanta ke qasa idonta na digar hawaye,takardar ya sake miqa masa "ungo nan rubuta" sai a lokacin abban fadila yayi magana "haba alhaji bai kamata ba,ya za'ayi yaro da matarsa kuma yana son abarsa a tilasta masa saki,abinda ya faru ai ya riga ya faru,kuskurene kuma babu wanda baya yi,kuma ni idan banda shirmen quruciya irin na fadilan ma banga abun da yayi zafi haka ba,tunda kuma alhamdulillah ya gane sai muyi addu'ar Allah yaci gaba da hada kansu"
"Wa?wannan?"uncle abban ya fada yana nuna aliyu da yatsa, "ai bai isa ba tunda tafiso ya saketa sai ya saketa,ai zaluncin ma alhaji yayi yawa,mun zaba mata miji ba tare da jin ta bakinta ba ko musa mana bata yi ba ta karba harda godiya tayiana biyayya,taje ta zauna da shi zuciya daya amma ya dinga azabtar da ita,babu kuma wanda ya taba sani ko sau daya sama da shekara guda har da kusan rabi,kuma yanzu don bamu da adalci tace bata da buqatar zama sai mu tilasta?don me?,mu zamu yi mata zaman auren?," sai lokacin itama ummi ta tanka "to alhaji tunda ya gane kuskurensa don Allah sai abar maganar,ke fadila wallahi tallahi na kuma jin kin furta mijinki ya sake ki ko mai ya hada ku kuwa sai....." "a'ah hajiya,ya kuke neman daure ma yaro qarqashi ne?" Inji momi" "barsu indai baso suke su nanamin su suka haifi fadila ba"inji uncle abba
Cikin sauri hajiya amina(ummi) tace cikin girgiza kai "Allah ya kiyaye alhaji Allah ya sawwaqe,haba haba da kai da kaya ai duka mallakar wuya ne"ya dauke kansa ya maida kan aliyyu "saketa nace ko?"ya nuna shi da yatsa "kuma don ubanka" (aliyyu bai yaba jin yayi zagi ba ko da wasa sai ranar "a gidan nan zata ci gaba da zama ni ne dai ubanta "qasa yayi da kansa yaqi furta uffan,babban abunda yasa jikinsu yayi sayi ganin hawaye nabin fuskar aly,mutumin da komai tsanani ba zaka ga koda qwalla bane bisa fuskarsa yau shi ke kuka saboda mace?,anty hauwa kamar ta tayi haka take ji don dai kawai zancan manya ne kuma basj bata damar shiga ba,sauqinta daya ma iftihal tayi bacci kan cinyar ummi
"Abba wallahi ko wuqa zaku sa ku dinga yankan naman jiki na bazan iya sakin ta ba,kuyi min afuwa abba" abban fadila ya dubi uncle abban "don Allah salim a naci albarkacin amintaka ina mai baka haquri kan ka sassauta fushinka kan yarona"falon ya dauki shiru na wasu lokuta kamin abban ya saki ajiyar zuciya "naji...naji,abu na farko da zan fara fada shine alhj abbas kai da hajiya amina ku yimin alqawarin babu wanda acikinku zai tursasawa fadila koda ta bayan fage ne kan sai ta koma gidanta ba tare da ita ta yanke hakan ba?" Ba yadda alh salim ya iya don yana tausayama aliyun yace "nayi" ummi ce tayi shiru har sai da hajiya maimuna tace "baki ce komai ba" "nima nayi"itama ta fadi cike da tausayin aliyu
"Abu na biyu,anan gidan fadila zata zauna har sai taji ta amince don radin kanta zata koma,idan yaso naga mara kunyar da zai koreta don ba gidansa bane haka nan ba da qwandalarsa na hada na gina gidana ba"ya fadi yana muzurai,sarai aliyun ya sani da shi abban yake amma sai ya sunkuyar da kansa,saboda shi kam a yanzu kome zasu fadi yaji ya gani kuma ya yarda suyita fadin,ko bulala dukkansu zasu dauka suyita zabgarsa yaji ya amince zai kuma shanye tunda dak an janye batun saki cikin lamarin,uncle abba ya nuna shi da yatsa "saura kuma naga qafarka inda take bare kace zakayi yunqurin takurawa ko tursasa mata sai na saba maka fiye da tsammaninka,tashi ka bawa mutane guri mutumin banza kawai",bashi da zabi illa barin falom kamar yadda abban ya umarcesu