Showing 21001 words to 24000 words out of 47716 words
Chapter 8 - 'YAN GUDUN HIJIRA Complete BY Dr. Zain.txt
hadari da ke ga wannan wurin saukar, musamman da ga alama ba wanda ya taba sauka ta wurin bare, su bi hanyar da ake sauka, su ne zasu buda hanyar.
Ganin sun yi tsaye ba wani motsi, Sajida ta ja hannun Bilkisu, ga Amisha goye a bayanta, ta fara sauka.
Cike da mamaki, mutumin da ke bayan su sai kallonta yake yi yana girgiza kansa, a ransa yana cewa. “tabbas duk duniya ba wanda yakai uwa mace son yaranta, ji wannan masifar, amma a ko da yaushe yaranta take fara kallo, ita ba ta damu ba matsawar dai yaranta za su rayu” ya girgiaza kansa yana mai jinjina mata.
Ganin abinda mahaifiyarsu ke so ta aikata, na jan hannunta domin su sauka tare, Bilkisu ta kwace hannunta, ta ce, “kar ki damu Inna, ki kula da kanki kawai da kuma Amisha insha Allah zan iya sauka, ina daga bayanki, saboda ke ba zan bari na fadi ba. Ba da son ranta ba, dole ta bar ta, ita kuwa ta kara gyara goyon da ta yi wa Amisha, ta ci gaba da sauka. Ganin ta fara nisa, sai Bilkisu ta biyo bayan ta, suna sauka, suna amfai da rike itace da ke jikin dutsen gudun kada su subuce. Mutumin ya umarci dayan matar da ta bi bayan Bilkisu, cikin tsoro ta fara bi ta bayanta, jikinta sai rawa yake yi, da ya ga ta fara nisa sai shima ya biyo ta bayansu, a haka suka dinga saukowa daga kan wannan dutsen. Cen suna cikin sauka, sai matarnan ta subuce, ta fado, haka ta dinga gangarowa ta doki nan ta doki cen har ta fado kasa, amma tun a lokacin gangarowar rayuwarta ta fita daga gareta, gawarta kadai ta isa kasa. Cikin sauri Sajida ta kalli sama, a zatonta Bilkisu ce ta fado, duk da bataji dadin mutuwar wannan matar ba, hankalinta ya dan kwanta ganin ba ‘yarta ba ce ba ta fado. Ta jima tana kallon yadda Bilkisu ke kokarin saukowa kafin ita ma ta ci gaba da saukar.
Haka suka ci gaba da sauka, har suka dauki wani lokaci mai tsawo, kasancewar dutsen yanada tsawo sosai.
Masu biyarsu kuwa, haka suka ci gaba da biyarsu ta amfani da sawu da kuma alamun wucewarsu, ba wanda za ka kalla ya nuna alamun gajiya ko yunwa a tattare da shi sai tafiya suke yi, kamar wadanda aka karawa karfi da kaimi.
Sajida ta fara sauka, kafin Bilkisu ta karaso sai mutumin da ke tare da su. Har yanzu jikin Amisha da zafi, ga shi gaba daya yawun bakinta ya kafe, ba ta iya furta komai, ga yunwa ga ciwo, su kuwa ga yunwa ga gajiya a tattare da su.
Kallon tausayawa take yiwa ‘yarta ganin yadda jikinta ya fashe wurare da dama sai fitar da jini suke, sanadiyyar saukowa daga kan dutsen, amma ko a jikinta, ita ma ta nuna alamun cewa su ci gaba da tafiya, musamman da take ganin duhu ya fara shigowa.
Suka tada kawunansu sama suka kalli ta inda suka sauka, a ranta tana cewa. “lallai ubangiji yana yadda ya so, wannan wurin da mutum zai rantse cewa ya sauka ta nan, ba zan aminta ba, amma yau ni Sajida, ni ce na sauka a nan”
Suka ci gaba da tafiya ba tareda sanin ina za su nufa ba, su dai burinsu kawai su fita daga wannan jejin.
Su kuma suka ci gaba da biyo su har suka kawo ta inda suka sauka, cirko-cirko suka yi, suna kallon ikon Allah, suna kallo da tunanin ya aka yi har suka iya sauka ta wannan wurin. Duk da sun sha training kuma suna kokarin gwada training nasu a aikace, sai da suka karaya da tsorata wurin saukowa daga wannan dutsen. Sai kara tunzura suke yi da sakawa a ransu, matsawar suka kama su, to ba za su yi musu da sauki ba.
Suka fara saukowa daga kan wannan dutsen, wasunsu, dole suka fara saukowa duk da ba da son ransu ba ne. shugabansu shi ne a gaba, sauran na biye da shi, a haka suke amfani da itacen da ke kafe a jikin sutsen gudun kar su fado, suna sauka a hankali, duk da haka sai da mutum uku suka subuce suka fado a mace. Amma sauran ko a jikinsu. Suka ci gaba da saukowa.
Har suka sauko gaba daya, suka ci gaba da biyar sawunsu, wannan karon cikin gaggawa da sauri har da hadawa da gudu, tuni suka kunna fitillunsu masu masifar haske da nan take sukan makantar da wanda duk aka cinnawa haskensu a idanu. Sai sauri suke da zinmar cinma su Sajida.
Su kuwa sai tafiya suke, a gajiye, kawai dai suna yin tafiyar ne saboda ta zame musu dole, amma gaba daya sun yanke tsammani da za su tsira.
Tafiya ta yi tafiya, duk da sanyi na dare ya fara sauka amma gaba daya zufa ke ke fita daga jikinsu, a haka suka ci gaba da tafiya ba hutu, duk inda sua ga wani ice da suke tunani zai iya zama magani, sais u tsaya su diba, ta tattauna shi a harshenta, sai ta sakawa Amisha ruwan a baki, cikin ikon ubangiji kuwa sai ga shi ta fara samun sauki.
Ganin ta fara samun sauki, sai suka sami wuri suka yada zango, suka yi amfani da damar suka yi taimama suka yi sallah, suka dan huta na wasu mintuna kana suka ci gaba da tafiya wacce su karan kansu basusan ina za su dosa ba, kawai dai su fatansu su kubuta daga wadannan azzalumai su kuma fita daga wannan masifaffen jejin.
Su kuwa sai kara sauri suke yi, da nufin cinmusu, domin sunada yakinin cewa ba nesa suke da su ba, musamman da yake sunsan akwai mata da yara tare da su, dole su bukaci hutawa, domin a zatonsu sunada yawa sosai.
Cen dare ya raba tsakiya suka fara hango hasken fitilunsu, dalili da ya sa suka shiga sabon gudu kenan, duk gajiya da suke ji ta kau a lokaci daya, suka fara gudun ceton rayukansu, wurin yunkurawa Sajida ta fadi, dalili da yasa Amisha ta rafka kara kenan, ta fashe da kuka mai karfin sauti har sai da masu biyar su suka jiyo, ai ko suka hasko inda suke, suka tabbatar su ne. suka ce da wa aka hadamu idan ba da ku ba, suka nufato su a guje. Ba tareda jiran su tashi ba Mutumin da suke tare da shi ya ranta a na kare, Bilkisu kuwa ta tada mahaifiyarta suka dauki sabon gudu na ceton rai.
Karshen rayuwarsu kenan?
Duk wahalar da suka yi nan ne karshen rayuwarsu?
Za su tsere musu kuwa?
Me zai faru da su?
Duka amsoshinku suna cikin shafi na gaba.
DR. ZAIN
[2/3, 4:57 PM] Saudat A J: *'YAN GUDUN HIJIRA*
_Labarin Sajida_
-----------------------------------------
_based on true life story_
🐾
1⃣9⃣
Na
*ZAINUDDEEN ZAIN*
_DR. ZAIN_
dedicated to: _Marayun da suka rasa mahaifansu a sanadiyyar boko haram_
® *PEN WRITERS ASSOCIATION*
```QUOTE OF THE DAY```
_Be the first rate version of yourself and not the second version of someone else_ 💃
*Shafin Masoya*
*PEN WRITERS ASSOCIATION*
MAMAN ALEESHA
MAMAN SADIQ
NUSAIBATH
MEENERT FARUK
AMINA GUNABI
KHAUSAR M NASEER
YAR FATHER
AUNTY MUMMY
KAMAL NO LOVE
NORDEEN AMRABAT
NABILA DIKKO
ZAINAB USMAN
DIYUART YUSUF
SHAFA SALFAZ
***CI GABA***
Cikin rashin shiri suke gudu gashi tsakiyar dare ba sa ma gcanin inda suke dora kafafuwansu. Sai kitar jeji suke yi ba shiri, har suka cinma mutumin da ke tare da su suka wuce shi a guje. A duk lokacin da suka yi nisa da gudu sais u waigo su ga har yanzu biyarsu suke yi, su kuwa sais u kara gudu. A haka har suka cinma mutumin da ke bayansu, suka kama shi. Gani haka hankalin Sajida ya tashi matuka. Suna cikin gudu, sai kafafuwan Bilkisu suka shige cikin wasu ciyawu suka sarke, ta fadi, dalili da ya sa dole mahaifiyarta ta tsaya kenan domin ta tada ta, kafin ta sami tada ta, har sun zagaye su, ganin haka ta rungume yaranta tana fadar, “kuyi wa yarana rai, ni ku tafi da ni, amma don Allah kada ku cutar da marayun Allah”
Sai dariyar mugunta suke yi mata suna zagayar su. Cen sai babbansu ya karaso, aka yi masa hanya ya karaso ta kusa da ita, ya ce, “wannan ce ta wahalar da mu haka, tabbas yau karyarki ta kare, nag a yadda gudunki zai kubutar da ke daga hannunmu, tun farko mun baku damar mika wuyanku, da hakan ba ta faru d ku ba”
Ya bayar da umarnin a zo masa da su. Nan take aka daure hannayensu aka iza su kamar bayi, tareda mutumin da suka fara gudu, ana tafiya ana dukansu da bulala ana kuma izar su sai kace wasu bayi. Cikin mamaki taga babban nasu ya fiddo da wata waya, ya dora a kunne ya koma gefe bayan ya danna lambar da yake so ya kira, ya yi waya tad an lokaci kadan, saai ya dawo suka ci gaba da tafiya. Zuwa wayewar gari suka yada zango a wani katafaren fili mai yalwa sosai. Cike da mamaki tag a sun fito da abinci kalar wanda za a dafa kadai ko a siyo a shago, ko shago irin manyan shaguna, suka fara ci, suka basu suma suka ci, cen sai suka fara jiwo karar mashuna da mota. Ashe wayar da ya yi ya kira ne ya yi kwatancen inda suke, shi ne mutanensu suka karaso domin su wuce da su masauki.
Aka tura su cikin hilux ta baya, sauran suka shiga ta gaba, sai wasu suka hau Babura, suka buga ya zuwa masaukinsu, sai wakoki suke yi da kuwwace-kuwwace.
Sansanin wuri ne mai yawan gaske, wanda aka killace da wata gina da aka yi da laka, wacce ita ce aka yi wani gini da ita da zai ba wad an garin kariya daga masu kawo hari, haka duk wanda zai shiga garin dole tan an zai iya shiga, bayan masu fakon kofa sun aminta da ya shiga. Idan ka shigo harabara kallo dole za ka dinga mayarwa, boda yadda aka kawata wurin da gine-gine dole ka kira shi da kauye mai zaman kansa, ga mutane nan saai sha’aninsu suke yi ana kai da kawo, a ce karshen garin ma bowhole ne da ke bayar da ruwa a duk lokacin da aka bukata, wanda ake amfani da generator wurin ta yar da shi. Akwai dabbobi cikin garin kama daga shanu har ya zuwa kaji da zabbi, lamarin da ya kara nutsar da Sajida cikin mamaki ke nan.
Duk sun ga wadannan abubuwan ne, a lokacin da ake wucewa da su ya zuwa wurin shugaban wurin. Haka aka ci gaba da tafiya da su, inda yara da mata da ke cikin dan karamin garin sai kallonsu suke yi cikin tausayi. Sune ba su tsaya ba har sai da suka karaso wani katafaren wuri, wanda ga alama nan ne ake taruwa domin yin jawabi ko wani babban abu idan ya taso.
Ba da jimawa ba da tsayuwarsu, sai gad an aiken shugaba ya zo, ya sanar da wadanda suka zo da su cewar, an umarce su da su kais u inda za su watsa ruwa su wanke jikinsu su saka wasu kaya kafin shugaban ya zo ya gabatar masu da jawabi.
Cikin gaggawa kuwa aka hada su da wadanda za su sada su da inda za su yi wankan. Shi mutumin aka hada shi da wani tsoho, ita kuwa Sajida wata tsohuwa ta zo ta ja hannunta suka tafi.
Da suka kammla wankan suka canja kaya.
Sosai Sajida ta yi kyawu da tufafin da ta saka, kai ka ce dama tufafinta ne, uwa uba Bilkisu, amisha tuni jikinta ya fara sauki, ashe dama yunwa ce ta haddasa mata zazzabi. Da cikinta ya cika sai gashi ta fara surutu da tsohuwa, har da wasa, duk da hankulansu a tashe suke, Sajida ta ji dadin ganin yarinyarta a cikin wannan yanayi na walwala.
Daga cikin wadanda suka kamo su ya gabata, ya fara yi wa Sajida da yaranta bayani tareda mutumin da ke tare da su. “ajuma kadan shugabanmu zai zo ya maku jawabi, inaso ku karkade kunnuwanku sosai ku saurare ni, kada ku sake ku kalle shi ido cikin ido, haka kadda wanda ya yi magana idan ba umarni aka ba shi ba. Idan kunne ya jiya jiki ya tsira”
Ya tashi fu ya wuce, ya bar sun an sai kallon juna suke yi.
Mutumin ne da ke basu labarin Nusaiba, ya juyo ya kalliSajida ya ce, “yawwa ku bari na karasamuku labarin da muka fara a sansaninmu.” Sai da ta saki murmushi kafin ta gyra zama, bayn sun hada idnu da tsohuwa ta yi wa Amisha alama da hannu cewa ta zo ta zauna a jikinta.
Shi kuwa sai ya ci gaba da labarinsa,
DR. ZAIN
[2/3, 4:59 PM] Saudat A J: *'YAN GUDUN HIJIRA*
_Labarin Sajida_
-----------------------------------------
_based on true life story_
🐾
2⃣0⃣
Na
*ZAINUDDEEN ZAIN*
_DR. ZAIN_
dedicated to: _Marayun da suka rasa mahaifansu a sanadiyyar boko haram_
® *PEN WRITERS ASSOCIATION*
```QUOTE OF THE DAY```
_If you can't find the right words for certain situations just give a smile. Words have potential to confuse but a smile convinces... 😇_
*Shafin Masoya*
MANSUR SUFI
USMAN ANGO
***CI GABA***
Dandano daga littafin SAKACI na ZAINUDDEEN ZAIN DR. ZAIN
Fitowarsu sai tace “ka bari mu bi wannan hanyar” sai ta nuna hanyar garin MAKERA wacce take hagun JUNCTION din fitowa daga garin TARASA
“Okay” ya fada “akwai inda zamu je ke nan?”
Ta ce “eh!”
Ya cigaba da taka motar basu sami wurin PARKING ba har sai da suka karaso a garin MAKERA, a dai dai lokacin da aka tayar da ‘yan makaranta, makarantar da ke a garin MAURIDA wanda titi kadai ne ya raba garin da garin MAKERA, shiyasa sau da yawa wasu sukan dauka duk gari daya ne.
MAURIDA shi ke bangaren dama idan ka fito daga BIRNIN KEBBI, MAKERA kuwa ita ce bangaren hagu, galibin mazauna garin MAURIDA ARAWA ne sai FULANI da ZABARMAWA
Nan ya cigaba da tafiya har suka karso JUNCTION da zai iya sadaka da garin TILLI da ZOGIRMA da BUNZA idan ka cigaba da tafiya, haka zai iya sadaka da KANGIWA da su BUI idan ka bi barauniyar hanya, a dama kuma sai BIRNIN LAFIYA da su ARGUNGU.
Sai suka bi hanyar dama sukacigaba da tafiya har suka wuce wani dan kauye wanda tanan ne zaka iya daukar barauniyar hanya zuwa garin BUI da su GIGANE suka sami ‘yar karamar hanya sai suka yi PARKING na mota, ya dawo ta SEAT na baya, sai suka cigaba daga idan suka tsaya, kasancewar kafin su tsaya ya rigaya ya gaya mata cewa ta cire wandonta na makaranta, bayan ‘yan wasanni da yayi da ita sai suka fara, suna cikin yi kwatsam sai ga wata bakauya ta zo ta wuce, tabbas ta hango me sukeyi kasancewar kan hanya suka yi PARKING amma sai ta kawar da kanta kamar sam bata ga me ke wakana ba, asali ma sai kara sauri takeyi, wanda saurin shi ya kara tabbatarwa da SALEEM cewa lallai ta gansu.
Ganin haka sai suka kammala a gurguje duk da cewa ko kusa SALEEM bai gamsu ba, ita NUSAIBA da zarar ka kalle ta zaka fahimci haka, nan sukayi sauri ta dawo ta gaba, suka dauki hanyar dawowa gida, suna gudun kar bakauya ta gayawa ‘yan garinsu a illata su.
Sai gudun fitar hankali yake yi a dai dai lokacin da ya hau babban titi da zai sadaka da MAKERA zuwa BIRNIN KEBBI, kasancewar titin yana a tsakiyar fadama ne, a gefukansa kakan ga masu sayar da kankana da dankali da dai sauran kayan gwari irin su timatir da albasa. Saurin da yake yi shi ya hana ya tsaya duk da NUSAIBA ta bukaci hakan domin tana so wai ta siya kankana.
Sun jima da baiwa MAKERA baya har sun wuce JUNCTION na garin TARASA suka karaso dai dai inda ‘yan sanda ke tsayawa, sai ta ce, a makaranta ance mukawo dari biyar, wai za a buga wasu takardu, ba tareda ya ce komai ba a ransa ya ce, yanzu idan na bata kudinnan ta yuwu karshen haduwarmu kenan, tunda ga shi ta gayamin cewa batada waya.
Sai ya juyo ya ce