Showing 165001 words to 168000 words out of 170683 words
kame ƴaƴan nata ram a hannu sai yanda tace musu, Alh. Sulaiman ɗin nema dai kan botsare mata a wasu lokutan dan shima dai halayyar tata ce ya ɗebo tsaf. Shiyyasa takanji shakkarsa duk da kasancewar itace ta haifesa, san nan tana sonshi sosai wannan a bayyane yake a wajen kowa ma, dan sam idan rashin mutuncinsa ya tashi ba raga mata yake ba tun ma yana ƙaraminsa, balle yanzu da yake jin ya gawurta da tumbatsa a gidan ta fanin dukiya da yin suna a cikin ƴaƴan nasu. Amma a kullum Dada bata ganin laifinsa sai ma bashi goyon baya da takeyi....
__________★
Matuƙar tashin hankali Smart ya shiga a lokacin da ya fahimci halin da Lulu ke ciki. Ta sanƙame masa babu alamar rai tattare da gangar jikinta, da ƙyar tunanin zuba mata ruwa yazo masa a rai, sai dai koda ya shafa mata ruwan ma shiru kake ji. Gaba ɗaya ruwan ya zazzage mata zuciyarsa na wani irin dokawa tamkar zata faso ƙirjinsa ta fito waje. Wata irin zaburowa tai jikinta na jijjiga. A tsahon rayuwarsa baya jin ya taɓa fuskantar makamancin farin ciki da tashin hankali masu gogayya da juna irin haka. Duk yanda yake tunanin iya shawo kan matsalar hakan ya gagara, dan yanayin nata ya wuce dukkan tunani. Yasan idan yace zai ɗauketa zuwa asibiti a wannan halin bazai ma iya driving ba, to yama manta motar su Amrah sun tafi da ita gida, dan haka ya shiga neman wayarsa. Da ƙyar ya iya samota a ƙasa harta fashe. Bai damu ba ya shiga neman Ahmad dan shine kawai yazo masa a rai.
Shigowar kiran ta saka Ahmad kwashewa da dariya, amma daya ɗaga sai ya dake dan shi duk tunaninsa Smart ya gano ne. Sai dai kuma jin muryarsa ta saka gabansa faɗuwa. Da sauri ya ce, “Mawashi Are you okay?”.
“I am not Ahmad. Ina cikin tashin hankali ka taimakeni kazo mukai Mawaddat asibiti, Ahmad akwai matsala wlhy na saka yarinyar mutane a masifa....”
Sosai zuciyar Ahmad ta jijjiga, amma sai yay saurin tarar numfashin Smart da faɗin, “Kaga Aliyu dan ALLAH ka kwantar da hankalinka, ka faɗamin mike faruwa ne. Ka sakani a tashin hankali nima....”
Cikin ƙaraji Smart ya katsesa da “Mi kake son sani ne Ahmad!! Ina faɗa maka kazo muje asibiti kana gaya min na kwantar da hankalina na sanar maka mike faruwa?. Ahmad ka taimakeni karna rasata, bazan iya yafema kaina ba idan hakan ta kasance”. Ya ƙare maganar cikin sanyin murya hawaye masu zafi na gangaro masa a karo na farko...
Kaɗan ya rage Ahmad yin aman zuciyarsa. Muryarsa na rawa da daburcewa ya ce, “Ka.. ka yi haƙuri gani nan zuwa.” baima jira amsar Smart ɗin ba ya miƙe tare da figar jallabiya ya saka. Karo suka kusan ci da Coach da ke ƙoƙarin shigowa ɗakin nasa, da mamaki ya ce, “Ahmad kana lafiya kuwa? Ina zaka haka?”.
“Yaya babu lafiya, na aikata babban kuskure wlhy.”
“Kai miye haka wai, nutsu mana”.
Coach ya sake faɗa yana riƙo Ahmad da ke ƙoƙarin turesa ya fita.
“Yaya dan ALLAH kayi haƙuri idan na dawo zan maka bayani. Aliyu ne ya kirani...”
“Kai bana son shashancin ka nutsu kamun bayani mana”.
Rasa mi Ahmad zaice yayi, sai kawai cikin matuƙar gundura ya ce, “Asibiti yaya. Asibiti zan kaisu, na tabbata koma minene yanada alaƙa da abinda na aikata wlhy. Dan girman ALLAH ka barni naje”.
Hankalin Coach ya fara tashi shima, dan Ahmad yana magana ne kamar zai yi kuka.
“Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Ahmad Please ka faɗa min mike faruwa? Miya samu Aliyun ne? Mika aikata masa kuma?”.
“Yaya nayi kuskure, abu na saka musu a fura, bana raba ɗayan biyu koma miya tada hankalin Mawashi nada alaƙa da abinda na aikata ɗin. Yaya kamarfa kuka yakeyi da tabbatar min zai rasata. Yaya ka barni naje dan ALLAH”.
Kai Coach ya dafe domin ya samu amsar abinda ya kawoshi sashen ƙanin nasa dama. Dan dama matarsa ce ta bashi maganin da Ahmad ɗin ya yarda ɗazun batare da ya sani ba kuma an ɓalla maganin, kasancewarta likita yasa hankalinta tashi fahimtar maganin datai kona minene. Taso danne zuciyarta ta binciki Ahmad ɗin ita kaɗai amma saita kasa haƙuri ta tunkari mijin nata da batun shine dalilin fitiwarsa zuwa inda Ahmad yake. Yanzu kuwa jin zantukan Ahmad ɗin ya tabbatar masa su Aliyu ya bama maganin ke nan. Ba lokaci bane na dogon tunani, dan haka ya ciro wayarsa da ga aljihu yana faɗin, “Kaga bari Khadijah tazo kuje tare, yanzu dare yayi duk asibitin da zakuje zaku iya fuskantar matsalar ganin doctor.”
Tuni Lulu ta sake fita a hayyacinta wa Smart, zuwa yanzu kam koda ya zuba mata ruwan ma batako motsa ba. Sai kawai ya dafe kansa dake wata irin masifar sara masa. Ya auna kiran Ammah sau shuri masaƙi zuciyarsa na gargaɗinsa. Hakama Abba. A wannan halin ya tsinkayi horn ɗin da yake ƙyautata zaton na Ahmad ne. Zumbur ya miƙe ya fito, dan yasan dole sai ya buɗe masa gate ya shigo. Doguwar riga ya samo ya saka mata, dama shi tuni ya suturta nasa jikin. Yana buɗe gate ɗin bai jira ƙarasa shigowar Ahmad ɗin ba ya juya cikin gidan da sassarfa. Fitowa aunty Khadijah tai tabi bayansa, yana ƙoƙarin shigewa bedroom ta kirayi sunansa. Da sauri ya juyo dan shi idonsa ma yay rufewar da bai kula da ita ba, sannan ya manta ma ita likita ce har sai da tai masa bayani. A tare suka shiga ɗakin, ta ajiye ɗan akwatin dake hannunta ta haura gadon ta ɗagota Lulu zuwa jikinta....
Smart da gaba ɗaya dauriyarsa ta gama ƙarewa cikin sarƙewar murya ya ce, “Aunty mun rasata ko?”.
“A'a Aliyu da ranta. Dan zuciyarta na harbawa suma tai kawai. Amma miya firgitata haka? Dan irin wannan sumar mai nauyi mummunar firgici ko tsorata mai tsanani akan abinda mutum baya so ke kawota”.
Kasa bata amsa yay dan tana cikin mutanen da a rayuwa yake matuƙar ganin girma da jin kunya. Itama fahimtar hakan ya sata cewa, “Shike nan ɗan bani waje mugani”. Babu musu ya fita, inda ya samu Ahmad a falo na faman kai kawo. Da sauri ya taresa da tambayar “Ya ake ciki?”. Zaune Smart ya kai cikin kujera dan ji yake jiri na ɗibarsa kamar zai zube a ƙasa shima. Ya dafe kansa da duka hannayensa kamar bazai cema Ahmad ɗin komai ba. Sai zuwa can ya furzar da zazzafan numfashi ya ɗan kallesa ya girgiza kansa, dai-dai nan Aunty Khadijah ta leƙo ta sake kiransa. Ta shi yay cikin ƙarfin hali ya nufi ɗakin. Batare da aunty Khadijah ta kallesa ba tace, “Kaimin ita Bathroom ka sakata a ruwan dana haɗa, ka riketa da ƙyau dan zata iya zabura”.
Duk yanda tace masan hakan yayi, sai ko gashi Lulu tai wata gigitacciyar zabura lokacin da yake sakata a ruwan. Da ƙyar ya iya rirriƙeta ajiyar zuciya mai nauyi na suɓuce masa yayinda wanin sashe na zuciyarsa ke matuƙar jin tausayinta da jin haushin kansa mai tsananin gaske. Sai da ta shafe kusan minti biyu tana fisge-fisgen kafin ta saki wani irin kuka mai tsuma zuciya tana mai ambaton sunansa da kausasashiyar muryar ta data gama ɗashewa cikin roƙo da magiyar ya barta, karya aikata. Kalamaine data dinga roƙonsa da su a lokacin da ya gaza amsa mata dan yakai fagen da bazai iya fahimtarta ba a lokacin. Goshinsa ya haɗe da nata yana ambaton, “Kiyi haƙuri Mawaddat kiyi haƙu......”
Bai kai ƙarshen kalma ta ƙarshen biyar ɗin ba ta ƙwalla wani masifaffen ƙara da zabura........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣8️⃣
.........Aunty Khadijah bata ma san sanda ta afko bayin ba. Da ƙyar suka iya riƙe Lulu su biyun, alamar ya fita aunty Khadijah tai masa, badan yaso ba ya fitan ita kuma ta shiga cikin ruwan ta riƙe Lulun da jikinta ke karkarwa sosai. Ta gama fahimtar minene matsalar Lulun, ko muryar Smart ɗin bata son ji sam dan firgitata take sake yi, dan haka ta fara mata magana cikin lallashi da kulawa, sannu a hanakali yanayin nata ya shiga canjawa, ta koma laƙwas sai kuma ta saki kuka da riƙe aunty Khadijah. Cigaba da lallashinta Aunty Khadijah tai da canja mata ruwa har sai da ta tabbatar ruwan zafin yay mata ratsawar da zai iya bata nutsuwar da take buƙata sannan ta fito ta ɗaukar mata kaya. Smart na zaune ya dafe kansa bayan ya gama ƙarfin halin yaye bedsheet ɗin saman gadon ya canja da wani. Shiya ɗakko kayan ya bama aunty Khadijah ta koma bayin, babu jimawa sosai sai gata ta fito riƙe da Lulu da ke takawa da ƙyar tana hawaye. Ya nufosu da niyyar taimaka musu aunty Khadijah ta girgiza masa kai, dole yaja ya tsaya badan yaso hakan ba. Sai matsanancin tausayinta da ke ratsa shi ganin yanda take tafiyar a wahalce duk da dama rabin jikinta a jikin aunty Khadijah yake. Saman gadon ta kwantar da ita sannan ta ɗaura mata ruwan data riga ta haɗama alluran barci a ciki masu ƙarfi. Cikin sa'a ruwan baifi mintuna bakwai da fara shiga jikinta ba barci mai nauyi ya ɗauke ta, ajiyar zuciyar da take saukewa a jajjare kawai kake iya ji.
Aunty Khadijah ta sauke numfashi da ajiyar zuciya tana kallonsa, yanda ta kafesa da idanun ya sashi kasa jurewa yay ƙasa da nasa. Zama tai a bakin gadon da masa nunin ya zauna shima. Zaman yay kamar yanda ta buƙata.
“Aliyu ka kwantar da hankalinka abinda ya faru bashi bane dalilin shigarta a wannan halin.”
Da sauri ya ɗago ya kalleta, cikin nuna mamaki ya ce, “Amma aunty kafin yau ban taɓa ganinta a irin wannan yanayin ba”.
“Bazaka gantaba dama, saboda ba'ai mata abinda zai kaita ga shiga irin yanayin bane. Dan akwai ɓoyayyen al'amari a rayuwarta. Yanayin da ta tsinta kanta a ciki yayi kama da na mutanen da aka taɓa ma fyaɗe....”
“Fyaɗe!..”
Ya maimaita kalmar da wani irin yanayi mai kama da almara. Ko ruɗani.
“Tabbas fyaɗe Aliyu, shiyyasa a wannan gaɓar abinda ya faru a baya ya shiga tariyo mata kansa, dalilin da yasa ta firgita kenan har tana neman rasa tunaninta”.
Kai ya shiga girgizawa da sauri. Duk da yau ne karansa na farko da fara mu'amulantar mace bazai yarda da hakan ba. Shi mai ilimi ne, sannan mai zurfafa bincike akan abubuwan da yake buƙatar sani tun bai kai haka ba. Ya nema sani matuƙa akan mace da suffofinta. Taya ma zai yarda waninsa ya aikata abinda shi shaida ne akan zama na farko a yau ɗin nan bayan wasu awanni kaɗan. Sake girgiza kan nasa yay da janye idanunsa da ya zuba akan Mawaddat ya maida su ga Aunty Khadijah. “Aunty mudai yi wani tunanin ba wannan ba, Mawaddat she is virgin hundred percent”.
Cikin mamaki ta ce, “Aliyu kasan mi kake faɗa kuwa?”.
“Tabbas wannan shine gaskiya. Na baki kowace irin dama kuma ta tabbatarwa ta hanyar aikin ki”.
Sosai hakan ya nema saka Aunty Khadijah a ruɗani, amma kuma tabbas ta san Aliyu akan gaskiya da furtata, sannan ita kanta a yanayin data ga Mawaddat ya tabbatar mata yau ta fara sanin ɗa namiji a rayuwarta, dama tana son sake tabbatarwa ne. Miƙewa tai tsaye ta fara kaikawo kusan na minti guda, sannan ta juyo tana kallon Smart da ya sake zubama Mawaddat dake barci da sauke ajiyar zuciya har yanzu idanu. “Aliyu indai hakane kuwa akwai ɓoyayyen al'amari ƙunshe da rayuwar Mawaddat. Tunda har ka tabbatar min na yarda da kai, amma tabbas an taɓa harar rayuwarta da wannan siffar kuma lamarin bai kasance ƙarami a gareta ba, dan ta ajiyesa a zuciyarta da har takai yake iya firgitata irin haka. Ba kowa ne ake kai masa harin fyaɗe ya ke tsintar kansa a irin matsanancin firgicin nan ba har sai ya tabbata an aikata masan. Shiyyasa kaji nace maka an aikata matan da farko”.
Kansa yake jinjinawa cike da nazarin kalamanta. Tare da haɗasu waje guda da wasu ɗabi'un Lulu da mabanbanta kalamanta a wasu lokuta. Idan ya ɗauki kalamanta na safiyar yau da ta tabbatar masa zata iya halakashi kamar yanda ta kashe wancan, hakan na nufin abinda Aunty Khadijah ta faɗa tabbas dole ne ya zama gaskiya, sai dai ba'a cimmata ba. Idan aka ɗauki yanda take kallon maza, da yanda ta tsani duk wani da ya aikata fyaɗe da tsaiwar da take akan case irin hakan cikin zafi da zafafawa. Waɗan nan duk hujjojine abin kallo da dubawa. Maganar Ammah a randa ya kaita gidansu da take ce masa ya kusanta kansa da ita ya fahimci damuwarta, dan akwai ɓoyayyen al'amarin data fahimta game da ita a cikin hirarsu. Anya kuwa ma shaye-shayen yarinyar nan baida alaƙa da wannan al'amarin? “Oh my God!” ya faɗa a zahiri yana furzar da iska mai zafi.
Aunty Khadijah ta ce, “Ka kwantar da hankalinka Aliyu. Wannan damar gareka take na bincika ainahin gaskiya a yamzu. Dan inhar ta iya faɗar duk abinda ke a ranta tamkar mun yaƙi kaso sittin ne cikin ɗari na halin da take a ciki, in ba hakaba zakuyita fuskantar matsala ne kai da ita matsayin ma'aurata dan kaima zata dinga kallonka ne da wannan siffar a duk sanda ka raɓeta. Dan al'amarin ya matuƙar taɓa brain ɗinta da rayuwarta.”
“Insha ALLAH Aunty zanyi iya bakin ƙoƙarina akan hakan. Sannan ni kaina ina son sanin kowanne tsinanne ne wannan domin ɗanɗana masa fiye da azabar daya dasama ruhinta na tsawon lokaci. Sai dai ina roƙon alfarmar kar wanda yasan wannan zancen dan ALLAH”.
“Karka damu Aliyu aikina ne hakan. Akwai amana tsakanin likita da majiyaci, balle ma abinda ya shafeka muma ya shafemu. Kallon ɗaya daga cikin ahalinmu nake maka tamkar Ahmad. Haka itama Mawaddat tana da alaƙa damu mai ƙarfi. Dan haka in sha ALLAH a duk sanda kake buƙatar wani taimako ka nemeni”.
“Insha ALLAH aunty Nagode sosai, ALLAH ya saka da alkairi”.
“Amin. Sai kuma kayi haƙuri dan yanzu koda ta farka gaskiya akwai daru, dole sai ka kauda kai dan itama ba daga gareta bane tun farko an dasa mata tsoron hakanne a zuciya. Dan ma kayi matuƙar yin farar dabarar kiran Ahmad ɗin kuje asibiti, da ace kace sai har zuwa safiya brain ɗinta zai iya birkita fiye da hakan. ALLAH dai ya rufa mana asiri yay mana maganin azzaluman mutane”.
Ya amsa mata da amin zuciyarsa na masa ƙuna. Da ga haka ta ajiye masa magunguna suka fito falon inda Ahmad ke zaune cikin damuwar daɗewar tasu. Dan a ƙalla sun samu cikakkiyar awa guda a ciki. Suna fitowa ya miƙe zumbur idanunsa akan Smart. Aunty Khadijah batace masa komai ba ta nufi hanyar fita tana kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunta. Smart zaiyi magana Ahmad ɗin ya taresa da faɗin, “Please Mawashi ka gafarce ni!”.
“Akan me? Ahmad kaida ka taimakeni ka kawo min aunty Khadijah akan lokaci, ni ya kamata na nema afuwar taso ku da nai a daren nan”.
Kai Ahmad ya girgiza masa da cewa “Aliyu laifina ne, na aikata kuskure”.
Sosai ƙirjin Smart yay masifar bugawa, dan abinda Ahmad ke nufi daban shi abinda zuciyarsa ta kawo masa daban. Sai kuma yay saurin ture hakan a ransa ya zubama Ahmad ɗin idanu. “Mi kake son faɗa Ahmad, ka bani abuɗe kasan bana son kwana-kwana”.
Hannu Ahmad ya kai saman kansa ya shafa, sai kuma ya furzar da huci mai ƙarfi. “Na zuba abu a cikin FURAR nan ɗaya. Saboda ma an tabbatar min maganin nada ƙarfi yasa na saka ɗaya kawai, sai dai zuciyata taita angizani akan na ƙara ta yadda zaka kasa control ɗin kanka har sai ka tabbatar da abinda muke fata.”
Shiru kawai Smart yay yana kallon ƙasa hannayensa duka a cikin aljihun