Showing 60001 words to 63000 words out of 170683 words
wai tun ɗazun data fita ta dawo ta shige office ta rufe kanta har yanzu bata fito ba. Ta mata knocking kuma yafi sau ashirin batako ji motsinta ba sai yanzu babu jimawa taji maganarta kamar cikin surutai”.
Ƙirjinsa ne yaji ya ƙara bugawa, ya kai yatsunsa biyu saman goshi ya ɗan murza. Basai ya nema ƙarin bayani ba yasan wani abu tasha. Sai dai bai taɓa tunanin har a wajen aikinta ma tana shan abubuwan nan ba. Ɗagowa yay idanunsa har sun kaɗa da ɓacin rai. “Kozan iya shiga office ɗin nata?”. Ya tambayi security ɗin.
“Ah eh mana mizai hana. Ai gara a je a duba mike faruwa ko?”.
Miƙewa kawai yay, security ɗin yay masa jagora har office ɗin. Sun samu sakatariyarta tsaye jikin ƙofar tana knocking da faman kiran “Aunty! Aunty Please ki buɗe ko kiyi magana dan ALLAH.”
“Kinga ƙyaleta idan da key bani”. Ya faɗa cikin dakewa. Cikar kamala da kwarjininsa yasa Zainab jin bazata iya musa masa ba. Duk da kuwa yau ne karo na farko data taɓa ganinsa anan ɗin. Sai kuma ganin harda security ya ƙara mata ƙarfin gwiwa. Muryarta a sanyaye ta ce, “Sai dai na duba ko zanga extra keys dan ta shiga da key ɗin ciki”. Kansa kawai ya jinjina mata, ta koma wajen table ɗinta domin bincikawa. Shi kuma ya jingina da bango tare da harɗe hannayensa a ƙirji ya lumshe idanunsa. Kusan mintina huɗu tana ta binci-bincike har dai ta samo keys ɗin da ƙyar. Gabansa tazo ta miƙa masa cikin girmamawa.
“Thanks” yace a hankali yana amsa. Koda ya buɗe ƙofar bai yarda ita da security ɗin sun biyosa ba sai da ya leƙa. Saurin rumtse idanunsa yay tare da yo baya, cikin ɗan furzar da huci ya gyara yanayin fuskarsa yanda zasu fahimcesa. “Inaga bata da lafiya ne, kun san halin ogar taku kuma maybe bata buƙatar kowa ya sani shiyyasa taya rufe kanta a ciki, ku barni da ita kar ku samu rabon faɗa kuma”. A yanda yay maganar dole ne ka gamsu, dan haka security ɗin yay murmushi dan kuwa masifar Mawaddat kowa ya santa, idan sukai sanya wajen buɗe mata gate kota saka wani aikin kai mata wasa sai ta tsefeka tas. Balle ma Zainab da tafi kowa sanin wacece uwargijiyar tata. Sallama security yay ya fita, Zainab kuma ta koma mazauninta ta zauna duk da ya kamata ace ta tashi, amma dai tafi yarda taga sai Mawaddat ta fito lafiya sannan. Ƙofar ya sake turawa ya shiga ya maida ya rufe tare da jingina jikinta kansa a ƙasa bai yarda ya sake kalloba. Kamata yay ya kira Zainab, sai dai baya son ta ganta a yanayin. Har yanzu tana kwance a tsakkiyar sofas ɗin da aka shirya dan zama bayan ta zamanta da wanda ke a gaban table ɗin nata. Ta ture Centre table ɗin tsakkiyar kujerun tana kan carpet ɗin gashinta yaɗan barbaje. Har yanzu idanunta na kallon p.o.p ɗin office ɗin, hira take da mamanta da idanunta ke gani ko nace ƙwaya take siffanta mata. Hawaye share-share a fuskarta ga murmushi. Tsaiwarsa gurin shiru na wasu sakanni ya sashi ɗan jin soki burutsunta. A karo na farko ya ɗaga kansa ya dubi p.o.p ɗin shima jin tana faɗin, “Mammah karki sake tafiya ki barni kinji. Kiyi zamanki muyi hirarmu, inma bazaki min magana ba ni zan na miki murmushinki ya wadatar dani. Kar kiyi kuka a kaina bana son ganin hawayenki ki bari Please ki bari...” ta faɗa cikin wani irin sanyin murya sai kuma ta fashe da kuka. Da farko bai ɗauki surutun nata komai ba sai shirme irin na masu shaye-shaye, sai dai Mammah da take ambata ya tsaya masa a zuciya. Ganin yana ɓata lokaci ya sashi furzar da ƙaramin iska tare da cigaba da takawa cikin office ɗin, ƴan dube-dube yake yi duk da baiyi tsammanin zai iya dacewa da abinda yake neman ba. Dama baiyi tsammanin ganin ba ai. Fita yay inda sakatariyarta ta take, tana zaune dai har yanzu sai dai yanzu da waya a hannunta, dan tunda ta turama Uncle Yousuf text take tsammanin shigowar kiransa amma shiru kake ji.
“Ko zamu samu Hijjab?”.
Firgigit ta dawo a hayyacinta dan jin saukar deep voice ɗin sa a bazata cikin kunnen ta. Sake maimaita mata yay ganin kamar bata jisa ba. Kanta ta gyaɗa masa da sauri tana nufar inda ta jiye hijjab ɗin sallarta ta ɗakko masa. Amsa yay kawai ya koma ciki. Yana ɗan sauke ajiyar zuciya, yanzun ma bai yarda ya kalletan ba ya warware hijjab ɗin tare da kaiwa duƙe gabanta. Karan farko na rayuwarsa ya ambaci “Mawaddat!” cikin ɗacin murya da tausasawa, sai dai acan ƙasan makoshinsa zaka iya fahimtar jin zafinta. Ƙarfin muryarsa da yanda yay kiran nata ya saka shigar sautin cikin kunnenta a bazata. Kamar wadda aka farkar a cikin barci ta juyo idanunta da suka sake girma da ɗan juyewa kansa. “What!” ta faɗa a zabure tana tashi zaune sosai. Sai kuma ta kalla sama da ɗaga hanunta. “Mammah ki jirani dan ALLAH”.
Kallonta yay jin abinda ta sake faɗa, hakan sai yay dai-dai da yanda ta zuba masa juyayyun idanunta fuska a yatsine tana wani ƙwaɓeta ta ce, “Who are you? Miya kawo ka nan?”.
Tsaki ya saki tare da ɗauke idanunsa ya yafa mata hijjab ɗin a jiki. Hannun da takai cikin yar kokawar ture hijjab ɗin ya buge. Da sauri ta janye tare da faɗin “ouch!” saboda zafin da taji. Baibi takanta ba ya ƙarasa saka mata hijjab ɗin batare da ya yarda ya taɓa mata jiki ba. Wata muguwar harara ta watsa masa ta ƙara kai hannu zata cire hijjab ɗin ya daka mata tsawa.
“Idan kika cireshi na rantse sai na canja ma fuskarki kammani da mari!!”
Sosai tsawar tasa ta ratsata. Gaba ɗaya sai ya sake juye mata a cikin idanu kamar wani bahagon zaki. Kuka ta saki da duban p.o.p ɗin ta ce, “Mammah kinga yana min ihu ko. Bana son shi yanada girman kai”.
Bakinsa kawai ya taɓe da cigaba da tattare kayayyakinta data barbaza a office ɗin waje guda, a zuciyarsa yana faɗin (aike naki kan ƙarami ne). A dai-dai nan aka turo ƙofar aka shigo. Juyowa yay da ɗan sauri dan a tunaninsa sakatariyarta ce, amma sai ya ga Uncle Yousuf ne. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke dan gaskiya yaji daɗin zuwan nasa. Dama sai faman ƙullawa da kwancewar ta yanda zai fita da ita a office ɗin yake. “Barka da yamma Alhaji”.
Murmushin ƙarfin hali Uncle Yousuf ya saki yana jinjina kasa, sai kuma ya maida dubansa ga Lulu da har yanzu ke sambatunta irin na rashin kasancewa a hayyaci. Idanu ya ƙura mata da kamar wanda ya zurfafa kansa a tunani, maganar Smart ta sakashi yin firgigit. Cikin ƙoƙarin shanye abu mai ƙona zuciya ya sake dubansa da murmushi. “Aliyu ya jikin naka? Kai da nace yau karkazo aiki shine kuma ka fito?”.
“Naji sauƙi ai Alhaji. Kasan zaman gidan isar mutum yake yi shiyyasa na fito. Nafito ɗin kuma na rasa ina zan nufa shine kawai nace Bara na duba ko bata tashi aiki ba sai na maidata..”
Uncle Yousuf da ke jin zuciyarsa babu daɗi ya kai zaune yana mai tallafo haɓarsa. Kusa da shi ya nunama Smart da ke kallonsa. Babu musu ya zauna sai dai a kujerar gefensa. Ya fahimci irin damuwar da Uncle Yousuf ɗin ya shiga, dan haka sai shi ya ɗan sassauta tasa cikin furzar da ƙaramin huci. “Alhaji damuwa bata zama maganin matsala ba, sai dai ta zama sanadin ƙirƙirar sabuwar matsala wa rayuwa.....”
“Hakane Aliyu. Amma ka duba fa kenan har a wajen aikinta ma tana sha? Hakan kuma na nufin duniya ta jima da sanin halin da Mawaddat ke a ciki amma mu bamu sani ba”.
“Banajin hakan gaskiya Alhaji”.
Idanu kawai Uncle Yousuf ya tsira masa, dan haka office ɗin yay shiru sai surutan Lulu kawai ke tashi cikin sambatun maye. Kiran da ya shigo a wayar Uncle Yousuf ɗin ce ta katse shirun nasu. Kamar zai share sai kuma dai ya cirota a aljihu. Daddy ne, yasan jiransa ya keyi dan sun zauna zasuyi magana ne Zainab ta tura masa saƙo shine ya taho hankali tashe. Wayar ya ɗaga tare da kaiwa kunnensa. Muryarsa a sanyaye ya ce, “Yaya!”.
Daddy da tun fitowar ƙanin nasa ya kasa zaune ya kasa tsaye ya ce, “Yousef miya faru da ita?”.
“Babu komai yaya ka kwantar da hankalinka dan ALLAH. Dan nama tadda Aliyu har yazo ma shi....”
“Waye Aliyu? Ko drivern ta?”.
“Eh yaya.”
“Ka faɗa min gaskiya Yousuf abubuwan tasha ko?”.
“Yaya dan ALLAH k...”
“Yousef please”.
Daddy ya faɗa cikin tare numfashin Uncle Yousuf ɗin. Cikin sakin ajiyar zuciya ya ce, “Hakane. Amma dan ALLAH ka kwantar da hankalinka, gamu nan tahowa gidan ma”. Daga haka ya yanke wayar. Shi ya ɗauki Lulu kamar ranar, Smart kuma ya fita da kayayyakinta a hannu. Zainab da gaba ɗaya hankalinta ya tashi da ganin yanda aka fiddo auntyn tata ya kalla. “Ki rufe office ɗin ki sameni waje a maidaki gida”. Daga haka yay ficewarsa.
Kamar yanda ya bata umarni hakan tayi, lokacin data fito har Uncle Yousuf da ya saka Mawaddat a motarsa yana ƙoƙarin ficewa a gidan. Yayinda smart ke tsaye yana jiranta. Batare da yi mata magana ba ya shiga motar, itama sai ta buɗe ta shiga kusa da shi. Har gida ya kaita abisa kwatancen da tai masa, godiya taita masa cikin girmamawa, karan farko yay mata guntun murmushi cikin jinjina kai ya ja motar ya wuce........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣4️⃣
.......Idanu kawai Daddy ya zubama Mawaddat hawaye na kwaranya saman dattijuwar fuskarsa. Itako sai surutai take musu. Sai ta kalla Daddy tayi ta kalla Uncle Yousuf shima tayi. “Yaya kukan nan fa bashi da wata ma'ana, addu'a itace kawai. Sannan bazan gaji da faɗa makaba ka bada kaso mafi yawa akan shiga wannan yanayin nata. Sai dai kawai muyi ƙoƙarin gyara kuskuren a yanzu. Ga kuma wannan matsalar data kutso kai, duk da dai ni da za'a bi ta tawa da kawai a aura ma Tajuddeen ɗin tunda mun san dai yaron nan bashi da wani aibu a rayuwarsa.....”
“Yousuf matsalar ba daga Tajuddeen take ba da ga mahaifinsa ne. Nasan abinda baka sani ba akan sulaiman sani na haƙiƙa. Kamar yanda na faɗa maka tun a wancan karon Tajuddeen an kwaɗaita masa son Mawaddat ne kawai da manufa, sai dai shi yaron ya afka batare da sanin manufar mahaifin nasa ba, ko kuma dama yana son nata shiyyasa Sulaiman yay amfani da wannan damar wajen sake jan zuciyarsa da tunanin hakan zai bashi nasara akaina.”
“To amma yaya ai shine zai zauna da ita ba Mahaifinsa ba. Indai har mun tabbatar da yana son nata kamar haka banga aibun aura masa ita ba. Na sani ka sani Mawaddat bata kula kowa, ta ina shi mijin daka ambata gaban Baba zamu samar da shi? Dan kasan dai in har babu wannan mijin to dolene Mawaddat ta auri Tajuddeen tunda baba da dangin mahaifiyarta duka sun ɗauki abin da muhimmanci bakuma zasu taɓa bijirema umarnin mahaifinsu ba kamar yanda suka saba”.
“Duk nasan da wannan Yousuf. Kuma nima damuwata a yanzu shine ta yanda zamu samar da mijin koda ace na wucin gadi ne kafin ƙura ta lafa.”
“Wucin gadi kuma?”.
“Yes wucin gadi, dan ba zan taɓa yima yaranmu ko ɗaya auren dole ba. Auren ma da jini irin na Sulaiman mai shirye da manufofi masu yawa da sai anyi auren ne sun fara bayyana zaka fara dana sani kai kanka”.
Shiru kawai Uncle Yousuf yay yana kallonsa, shi kam gaba ɗaya ma a wannan gaɓar ya shiga ruɗani zai ce. Ya kasa fahimtar ainahin abinda ke tsakanin yayan nasa da yayan matarsa da a shekarun baya suka kasance shaƙiƙan abokai da ko ƙuda baya iya jin sirrinsu. Anya kuwa yayansa baya ɓoye masa wani babban al'amari da ya kamata ace ya sani.....
“Assalamu alaikum”. Sallamar Smart a ƙofar falon ta katse tunaninsa. Daddy ne ya amsa tare da bada izinin shigowa dan ya shaida muryar yaron. Akan Lulu da ke kwance a ƙasa barci na neman rinjayar idanunta tana kokawar hanashi ya fara sauke idanunsa. Kaudasu yay duk da sanye take da hijjab ɗin da ya saka mata har yanzun. A nutsensa ya gaishe da Daddy, tare da ajiye key ɗin motar hannunsa. “Sannu da ƙoƙari fa, ALLAH ya saka maka da alkairi kaji”. Daddy ya faɗa a karo na farko. Ɗan murmushi Smart yay cikin jinjina kai. “Babu damuwa ai Alhaji. Nima na gode. Bara na wuce gida”.
Godiya Daddyn ya sake masa, tare da zaro kuɗaɗe masu yawa da ga aljihunsa ya miƙa masa. Kallon kuɗin Smart yay da sake sakin murmushi mai ma'anoni da yawa sai kuma ya girgiza kansa. “A'a Alhaji nagode sosai. Amma bazan amsa ba, albashin da ake biyana ya wadatar dani ALLAH ya ƙara buɗi”. Mamaki matuƙa Daddy ya shiga, dan haka ya kalla Uncle Yousuf da tun shigowar Smart ɗin baice komai ba. Kafaɗa ya ɗage masa alamar haka yake. Ai Daddy kasa ƙara cewa komai ma yayi har Smart ya sake musu sallama ya fice abinsa.....
★★ *_8:25pm_* ★★
Ƙarfe takwas da kusan rabi na dare tawagar Hon. Babale Nakowa da su Alhaji Baita suka isa gidan Alhaji Sufi Ado Garko kamar yanda suka tsara. Ziyara ce ta bazata, dan haka Alh. Sufi yay mamakin zuwan nasu duk da kuwa su dukansu sun kasance yaransa ne ta fannoni daban-daban kafin yau. Sai dai duk da kasancewar wannan zuwa nasu ya kasance na bazatan hakan bai hana su sami tarba ta mutuntawa ba. Bayan sun gaisa da Alh. Sufi cikin girmamawa a matsayinsa na _God Father_ nasu sai kuma hira ta ɓalle mafi ƙarfi akan kasuwanci da siyasa. Sun ɗan taɓa hira kafin Hon. Misau ya fara bayani akan abinda ya kawosu.
“Ranka ya daɗe mufa zuwan nan namu kamar gaisuwa ce da roƙon iri. Munzo mu maka Barka da dawowa da kuma yaya jiki sai kuma babbar magana mai alaƙa da son ƙulla sabon zumincin da muka san kaima zakayi farin ciki da shi”.
Cikin mamaki da dattijantaka Baba yay murmushinsu na manya idonsa akan Alhaji Misau. “Jeka maganarka kai tsaye Ɗan kande! kasan ni a koda yaushe nafi buƙatar abu abuɗe fiye da rufa-rufa”.
“Hakane Baba”.
Cewar Hon.. Misau cikin murmushi da sake gyara zama. Sai da ya ƙara juya zancen a ransa ta yanda zai fito da armashi sannan ya cigaba da faɗin, “Akwai wata yarinya a cikin zuri'arka da Alhaji Haruna ya gani ya kuma ji ta kwanta masa matuƙa a rai saboda nutsuwarta da hankalinta. Da farko mun shirya tunkarar mahaifinta sai kuma mukai tunanin ai baba ma da babansa. Shiyyasa muka dakata har sai yau daka dawo mukazo da ɗumi-ɗumi dan a tabbatar bada wasa muke ba”.
Murmushin mai cike da jin daɗi Alhaji Sufi Garko ya saki tare da faɗin, “Kai kai Masha ALLAH. Masha ALLAH, naji daɗin hakan kuma zanayi matuƙar farin ciki saboda sani da naima Haruna a rayuwa da nagartarsa. Amma wace yarinya ce wanna haka?”.
Yanzu kama Hon. Baita ne ya nisa shima da murmushin shinshino nasara akan fuskarsa ya ce, “Baba sunanta Mawaddat. Ƴar wajen Alhaji Isma'il Jiƙamshi. Kaga a gareku ku jikace.”
“To to! Ko kaine dama yake faɗa mijin data fidda ɗin? Dan ɗazun dama muke magana akan ɗan wajen Sulaiman da aka taɓa son haɗa su sai abin bai yiwu ba da yake a lokacin ba matarsa bace.”
Kallon juna sukai kowanne zuciyarsa kamar zata ɓallo ƙirji ta fito, sai kuma suka haɗa baki wajen faɗin, “Aiko bazai wuce hakan ba kam”.
Duk da maganar ta ɗan yima Alhaji Sufi Garko gingirin a zuciya sai kuma hakan bai hanashi jin daɗi ba da nuna farin cikin sa. Dan haka babu wani kwalo-kwalo ko jan magana ya tabbatar musu suje gida insha ALLAHU zuwa gobe su dawo garesa da shirinsu bayan sallar azhar zasu samu amsa mai gamsarwa. Dan ya tabbatar musu duk da shi kaka ne ta ɓangaren mahaifiya yana da nasa ƙarfin ta wani fanin ma ubane shi ga mahaifin nata shima ai. Farin ciki iya farin ciki sun shiga, dan haka suka tafi da ƙwarin gwiwar samun nasara batare