Showing 18001 words to 21000 words out of 102653 words

Chapter 7 - YAR TALLAH Book Complete Document by Jamila .txt

18 Dec 2024

5943

cikin saba, saboda tsabar qazanta da kurar duniya da ya sha. Saude ta dame zuciyarta ta amsa masa don k0 kadan ba tajin za ta iya yi masa wulaqanci saboda girman shekarunsa dan ya yi jika da ita.
Garba ya Kara watso haqoran nan wadanda su kai kore fatau kamar gansa-kuka yana fadar, “Haba Saude na ga alamar kamar ba ki san magana dani, ki yi hakuri ni masoyinki ne ba makiyinki ba kuma ni aurenki zanyi bawai wasa zaikawoni wurinkiba yanzu haka idankika amince min mahaifinki kawai zan nema a yi magana.”
Saude ta watsa masa wani kallo mai kama da harara ta zumburo baki kafin ta ce, “Ni fa ba anre zan yi ba yanzu
Ya yaqe baki yana fadar, “Haba Saude ke yanzu idan bakiyi aureba saime zakiyi?idan ki ka amince: ki‘ka aure ni, killa ceki zan yi a‘gidana, kin gama zuwa talla idan ma kina tunanin matana hudu ne to a shirye nake dana saki daya daga cikinsu Ya kikacene Saude?” ’ Haushi ya kamata ta mike afusace tadauki bokitin tallarta ta yi gaba ta bar shi nan zaune
Garba Gurgu ya yi dariya yana girgiza kai yana fadar‘ “Yaro yaro ne.” Ya mike yana cangala qafa shi ma ya yi gaba abin sa.
Bayan Saude ta gama tallarta da yamma likis ta koma gida a gajiye ta samu ta ci abinci ta yi sallar Magariba, sannan ta dauki tallar dare ta fita kofar gida ta zauna da ‘yar fitilar aci-balbal.
Kamar daga sama ta hango shi tsangal-tsangal haushi ya cunkusheta ta bade fuska a zuciyarta ta kudiri aniyar idan ya sake ya zo inda take sai ta cire kunyarsa daga idanuwanta ta yi masa rashin kuunya tunda ta lura bai san girmansa ta gani ba ta daga masa kafa ba
Da mamakinta sai ta ga ya yi wa kofar gidansu tsinke, ta saki baki da idanuwa tana kallon shi, ta ga ya kira wani yaro ya tura shi cikin gidansu. Yaron bai jima ba ya fito tana kallon su can sai ta ga mahaifinta ya flto sun tsaya suna gaisawa, gabanta ya yi ’mata mummunar faduwa hankalinta ya yi masifar tashi ba dai Garba wurin mahaifinta ya zoba.
Wayyo Allah na shiga uku! Abin da ta iya fada kenan wasu zafafan hawaye suka shiga zarya a kuncinta tana kallon yanda mahaifinta ke ta faman
washe bakivyasa hannu ya karBi kudin da Garba Gurgu ya ba shi, sannan suka sake yin musabaha, sannan ya shiga gida shi kuma ya wuce abinsa ba
tare da ya kalli inda take ba. Saude ta ta kwashi kayan tallarta ta nufi cikin gida. A tsakar gida ta samu mahaifin nata na fadawa
“Laure kin ga wani abun murna k0 wai mutumin nan Garba Gurgu ke son Saude
Laure ta rangada kuda ta ce, “Kai amma abun ya yi min dadi wallahi, ka ga sai a hada su su duka da ‘Yar Baba. don ita ma ta ce yaron nan mai zuwa wurinta da jar motar nan ya ce zai turo ai maganar aure
Malam Bala ya ce, “Ai ko haka za ai dama ni na amsa masa, yanzu haka ya ce jibi za a kawo kayan nagani-inaso yanzu haka har kudi ya ba ni kin gansu dubu biyu. Kai gaskiya mutumin nan yana da mutunci.”
Laure ta ce“To, ai sai ka tsakuro mini nawa tunda ba kai kadai keda diyar ba
Malam ya ce, “Kefa tsiyarki ke nan duk abin ki ai kya bari' na mutu sannan ki rufe ni ai k0?”
Ya ja tsaki ya cimimiya kwarar dubu guda ya cilla mata ya juya zai tafi ya ga Saude tsaye rungume da kayan tallarta hawaye sun gama bata mata fuska.
Malam ya ce, “Ke kuma fa lafiya?”
Cikin muryar kuka Saude ta ce “Ka yi haquri Baba don Allah wallahi bana san shi ba zan iya aurensa ba, sabo...
Malam ya katse ta ta hanyar fadar, “Ke dalla Saurara mini kin jiki Ba kya son shi sai wa ki ke so?”
Saude ta yi shiru tana faman shashshekar kuka Malam ya sake fadar “Na ce idan ba kya son shi, sai ubanwa kike so?Munafukar Allah,nankikaso ki jibge mana kita zama kitsufa a tasha kina talla, tunda kebaki da tunani ko Allah yataimaka kemaya kawo miki dauki, tunda ki ka tashi akwai bakon takalmin da ya taBa zuwa wurin ki da sunan so, iye?
Amma shi ne har kina da bakin magana. Shekarar ki nawa yanzu a duniya? Kin zauna kin jibge babu mai taya ki kek0 kishin kanki ba kya yi, kina kallon ‘yar uwarki kullum wannan ya shiga wannan ya fita, harda masu motoci, amma saboda rashin kishin kai ba ki taba damuwa ba.” mts! Ya wuce yana fadar.
“Idankinada wandakikeso to saikituro shi ai lokaci bai qure miki ba daga nan har ranar daurin aurenki
Wani irin kuka ya Kara kwacewa Saude, ta aje kayan tallar ta yi dakinta da gudunta tana. wani irin kuka mai tsuma zuciya.
Laure ta ja tsaki tatattara kayanta tana fadar, “Ke
dai kya kai su idan kaya ne dan bakin ciki sai dai ya kashe ki don na gaba ya riga ya yi gaba har abada ba zaki iya kamo taba.”
Saude ta sha kukanta har ta godewa Allah bata . da mai lallashinta haka ta kwanta har bacci barawo ya sure ta. Haka ta farka yau idanuwanta duk sun ‘ kumbura sun yi jawur saboda kukan da ta sha jiya. Haka ta je tallanta ta dawo jikinta ba kuzari kana ganinta ka san tana cikin matsananciyar damuwa. Ta yi zaman daBaro kan sumuntin tsakar dakin, don
kuwa dakin bai da arzikin k0 qaramar tabarma
Saude ta jingina da bangon dakin ta rafka wani ; uban tagumi ko tunanin me take? Oho ‘Yar Baba ta dago labulen tana mata wani shakakken kallo kafin
ta ce
“Idan kin gama tagumin sai ki fito ga kayana na ki hado ki wanke mini. ‘
Saude ta dago da jajayen idanuwanta tana « kallonta, haushi da baKin ciki suka turnuqe mata zuciya, tuni dama batun yau ba take jin takaicin abin da ‘Yar Baba ke mata ba sai ka ce ita ce babbar, ita ma kuma ita ce karamar.
‘Yar Baba ta ce, “Ki ka tsaya kina kallona da wasu kananan idanuwanki can masu kama da na kwarkwata kixo ki min wanki na ce
Takaici ya kuma turnuke Saude cikin fusata ta ce, “Wai ‘Yar Baba me ki ka dauke ni ne jakar ki ko
kuma me? Karfa ki manta a girme na girme ki,amma ki rinka! yi min abu kamar wata yar da ki ka haifa. Ai ba ‘yar wanki ki ka aje ba, da ki ka
dama can da ina miki Inna ce ke sani, amma ke baki isakisani inmiki wanki ba” “
‘Yar Baba ta ce ‘Eh, lallai wuyanki ya isa yanka, har ni ki ke gayawa magana yau k0 Saude dan kin ga Laure ba ta nan lallai za ki san kin yi da diya ba shegiya ba, za ki gani.” Ta juya ta yi gaba.
Saude ta ja tsaki ta IaIIaBa ta kwanta ta ci gaba da nazarin abindayadameta. Bata ankaraba saidaita ji saukar kayan wanki a jikinta ta zbaura ta mike tana kallon mai wannan aikin.
0000000000
“Wato kenan har‘ yar iska ce har kin yi girman da ‘Yar Baba za ta sanya ki ki mata abu ki zage ta ki ce ba zakiyi ba.
‘ To yau sai na ga uban da ya ,tsaya miki ki dauke su maza ki je ki wanke mata, ki shanya ki zauna su *bushe ki linke ki kai mata daki, tantiriya marar kunya, ai na godewa Allah morewa ta dama na ga rayuwarki ta wulakanta, kuma na yi nasara, in dai ina numfashi kin auri Garba Gurgu kin gama, bankadaddiya yanda na ga bayan uwarki da wannan
takadarin ke ma sai na ga naki. ’
" Ta ja tsaki ta wuce tana fadar. “Munafukar banza!” .
Wasu irin hawaye masu dumi suka zubo daga idanuwan Saude tasa bayan hannunta ta goge sannan ta' shiga tattara kayan wankin ta wuce tsakar gidan,
Ta. wanke su gaba daya abun bakin cikinta har da bireziya da dan paint, saboda kawai tsabar raini da wulakanci. Rayuwa kenan.
Kamar yanda mahaifinta ya ce za a. kawo kayan nagani-inaso, haka kuwa aka yi Garba Gurku ya aiko mata da kaya cikin Gari ya yi zafi, dinkakkiyar atamfa ce ta roba riga da zani sai dakakkiyar abaya kwaya daya, sai takalmin roba shi ma guda daya da sinqin sabulu guda da Katuwar ’kwalbar mai dangwali-yaBa, sai naira dubu a sama.
Laure ta dauki naira duban sannan. ta mikawa Saude kayan don ba abin da ya yi mata a cikin kayan. Wasu irin hawaye masu zafi suka ziraro daga idanuwanta tasa hannu ta karBi kayan ta wuce daki ‘ da su.
Tana shiga ta wurgar da su tsakar dakin ta durkushe tana raira wani sabon kukan mai cin zuciya. Tabbas tana cikin halin da ya kamata a tausaya mata,Yayanta ya ringa yi mata gizo cikin idanuwanta ko wane hali yake yanzu? Saude ta sha kukanta ta gaji ta lallashi kanta ta yi shiru
Abu wasa-wasa lokaci ya ci gaba da tafiya, Garba Gurgu ya ci gaba da yi wa Saude hidima, idan abun kirki ne sai Laure ta rike, idan kuma ta gajam tagajan ne sannan za ta ba ta, ita k0 ba ta taba kallon kayan ba don yanda ta tsani mai kayan haka su ma kayan ta tsane su.
‘ Ranar: wata Laraba Saude ta dawo daga tallar safe, misalin qarfe daya na rana, Laure tace yau ba tallar rana ta je ta shirya za ta je ta dubo ‘yar Garba Gurgu da ta haihu ta dawo gida wanka jiya ya zo ya gayawa Malarn. .
Wani bakin ciki ya tokarewa Saude wuya, ta rasa ma abin da za ta ce saboda takaici, ta wuce dakinta ta yi kwanciyarta, har aka soma kiran sallar La’asar, Laure ta ji shiru ta leko dakin nata ta ganta a kwance idonta biyu k0 motsin kirki ba ta yi.
Laure ta dauki sallallami tana fadar, “Yanzu zuwa ki ka ki ka kwanta dan kin raina mutane, ya yi miki dadi sosai wallahi. To sai ki fito ki shirya in ga ubandaya isa ya hanaki kije dubiyannan ki ciro cikin kayan da yake kawo miki ki sanya kin ji na gaya miki” Tana gama fada ta juya ta wuce abinta.
Wasu irin hawayen bakin ciki suka zirarowa Saude ta yunkura ta mike jikinta ba kwari, ta fito ta janyo ruwa cikin rijiya ta dauko sabulu guda cikin kayan nasa da ya kawo mata ta nufi bandaki ta yo wankanta wanda rabon da ta yi irinsa ba za ta iya tuna shekarar ba.
Tana gamawa ta fito ta nufi dakinta ta janyo mai ta shafawa fatar jikinta, ta zazzaga farar hoda a hannunta tamurzawa fuskarta, ta bude ledar da kayan ke ciki kala uku .ne daga wata atamfa ‘yar
roba sai wani yadi mai santsi an yi masa dinkin riga da wanda, sai wani leshi marun an masa dinkin jaka tsaye.
Saude ta dauko shi ta saka ta Ciro takalmin robar
ta sanya ta kawo milk din hijabin da ke cikin kayan
ta sanya, sannan ta fltO zuciyarta na faman suya. A lokacin Laure da ‘Yar Baba na zaune gaban murhu
ana ta faman soyen kaji da sanrayin ta ya kawo
Saude ta dubi Laure da idanuwanta wadanda suke san zubar da hawaye ta ce, ‘Na fito.”
Laure ta dago tana kallonta, alamun mamaki bayyane a fuskarta qarara, wanda har ta gaza danne shi a zuciyarta sai da ta furta.
“Saude ke ce haka? Dube ta ‘Yar Baba ki ga abun mamaki.”
‘ Kallo daya ‘Yar Baba ta yi mata ta dauke kanta tare da jan tsaki, Laure ta kada kai kafin ta ce, “To sai ki tafi k0 wa ki ke jira?”
Haka Saude ta kama hanya jikinta a sanyaye ta yi. gaba. ‘
‘ Gidan Garba Gnrgu yana can qasan unguwarsu ta baya, haka Saude ta taka~ da qafa. Gidan qaton gida ne ginin qasa,~rabin katangar duk ta zube a Kasa
wanda aka sa buhu aka zagaye. Saude tasa qafarta cikin dogon zauren wanda aka fito da Katuwar kwata ta tsakiyarsa har tsakar gidan,
gaban ta ne ya shiga faduwa lokacin da ta sa qafa cikin soron gidan, ba ta san irin tarbar da za a yi mata ba, ta san mugunta ce kawai ta sa Laure ta ce ta
zo gidan ba wani abu ba. Saude ta yi sallama a tsakar gidan wanda yake a hargitse sai ka rantse da Allah bai’taBa ganin Shara
ba ga wasu manyan tukwane da murahu a tsakiyar tsakar gidan ko’ina komatsai ne a tsakar gidan ba masaka tsinke, ga yara nan suna ta faman tsalletsallensu a tsakargidan sai ka ce ba su taba ganin ruwa ba a rayuwarsu saboda tsabar Kazanta.
Saude ta Kara daga murya tana sallama sannan matan da ke ta faman zirga-zirga suka ankara da ita aka amsa mata tare da . yi mata maraba, jikinta a sanyaye ta qarasa cikin, gidan tana danne fargabar zuciyarta.
Daya daga cikin matan ta janyo kujera ‘yar tsugunne ta miqa mata ta zauna suka shiga gaisawa, wasu su biyu babu riga a jikinsu sun saki nonuwa a waje sai ka ce silifas suna ta harkokin su babu abin da ya dame su, sai Karamar su ce keda daurin qirji. Kai da gani ka san an yi masu kisan Kuli, an kashesu ko kadan baza akirasu da mata ba.
Saude ta qakaro wani murmushi wanda iyakarsa saman laBBanta kafin ta ce, “Na zo ganin jariri ne.’
Babbar cikin su ta ce, “Au! Ni dai na ce ba mu. ,
waye ki ba, suna daka ki shiga ki gan su.”
mu kishi da jikannu wallahi, ba ta yiwuwa da sake an bawa mai kaza qafa”
A daidai nan Saude ta fito tana qokarin sa takalmanta ta ji matar na fadar, “Munafuka ashe Ieken asiri ki ka zo in dai gidan Malam ne ki shigo kema ki zauna, sannu a hankali za ki koma yanda muke ”
Sauran matan dai babu wadda ta tanka, harkar gabansu kawai suke. Saude ta sa takalminta dai ta yi waje, tana jin Garba ya biyo ta yana fadar.
“Tsaya Saudatu ki ga dakin ki.”
Bata tsaya kulashiba tayi gaba da hanzarinta sai sauritake dankokadan batasan ta hada ido dashi, munin shi da qazantar shi kadai ta isa tasa ta tsane shi, to balle ga shi tsohon najadu ga nakasa kai shi dai abun ya yi masa yawa.
Bata ankaraba tanata tafia cikin sauri tana zancen zuci, ba ta ji horn din da ake faman kwarara mata ba, saidai taji an hankadata gefe hankalin Hamid ya yi masifar tashi, ya yi saurin yin fakin din motarsa ya fito a guje: ya nufo inda take yana kokarin daga ta, Saude ta yi saurin mikewa dan gudun karya tabata shimaya dago da niyar yabata hakuri, su kai four eyes, ido hudu, wanda ya
haifarwa Hamid da bugun zuciya mai tsanani.
Cikin tsoro da rudewa Saude ta soma ba shi hakuri, kallonta yake ido cikin ido wani abu na faman zarya a cikin kirjin sa muryarsa a sanyaye ya ce.‘
Ai nine zanbaki hakuri nidana kadeki kiyi haquri wallahi ban lura da keba ne.”
Saude ta kada masa kai sannan ta wuce shi abin
ta.
Hamid ya yi saurin bin ta yana fadar, ‘Don Allah dan tsaya mana ‘yanmata.”
Saude ta waigo tana ’ kallonsa, ya dan gyara tsayuwarsa kafin ya ce ‘Don Allah idan ba za ki damu ba ki fada mini sunan ki.” .
“Saude.” Ta ba shi amsa a taqaice.
Ya girgiza kai yana fadar, “Na’am Saudat, don Allah idan ba za ki damu ba kimin kwatancen gidanku
Saude ta waro ido tana kallon shi, alamun mamaki bayyane a fuskarta ta kasa ma magana, ya danyi murmusa kafin ya ce, “Ki yi hakuri kar kice na fiya shishshigi da yawa;”
' Saude ta dauke kanta kafin ta ce, “Lafiya dai ko?
‘ “Lafiya kawai dai ina so inxo in Kara duba kine don ban sani ba ko wani abu ya same ki.”
Saude ta wuce shi tana fadar, “Ni babu abin da ya same ni.” Hamid ya yi tsaye yana kallon tafiyarta hatta kusa Bacewa ganinsa, ya ja wani taqaitaccen murmushi
murmushi mai sauti tabbas yau zuciyarsa ta samu abinda takeso,zaicigabada binta harya samu ya samo kanta. Ya juya ya shiga motarsa ya bi ta a baya harkofar gidansu ya rakota batasanai ba, sannan ya koma abin sa.
Saude nashiga gida, Laure ta bitada kallo kafin ta ce, ‘Wai kin je gidan nasu kuwa?”
Saude ta daga mata kai alamar eh laure ta yatsina fuska kafin tace “Amma abinda mamakine da akace min amaryarsa mugun kishine da ita aina dauka sai sun karya miki qafar baya.” Ta ja tsaki mts!
“Sai ki wuce kafin tallar yamma ta qarisa
Saude ta wuce dakinta simi-simi ba tare da ta sake tankawa ba. Tana shiga daki ta kwanta, wani irin abu ya tokare mata zuciya, ta lumshe idanuwanta fuskar mutumin nan ce ke mata gizo, har yanzu hancinta baidaina shakar kamshin turarensa ba mai sanyin kamshi.
Dama yace yanasonta tabbas da saitayi kukan dadi. Makaskanciya irin ta a ce irin wannan namijin yasota aidakamar wuya wai gurguwada auren nesa. K0 ‘Yar Baba da ta fita komai ba ta samu kamarsa ba, ballantana ita mafi kaskanciya mai tsananin rauni Taja wani gwauron numfashi tare da
saurin kawar da abin dake zuciyarta, don ta san k0 a mafarkinta hakan ba zai taba samuwa ba.
Washe gari Saude ta dawo daga tallar safen ta, sannan ta dauro alwala ta yi sallah; sannan ta fita’ tsakar gida ta zauna, Laure ta sauke alalar aka zazzage mata a bokiti ta dauka ta fice abin ta.
Hanyarta ta kullum yau ma ta ita ta bi idonta na saman hanya ta wuce ta qofar gidan Alhaji Bashir, Hamid da ke zaune saman teburin maigadi ya ga tahowartaya zabura ya mike, ya dubi Malam maigadi yana fadar.
“Ina zuwa Baba bari in dawo.” Bai jira abinda zai ce ba ya yi saurin bin ta dan kar ta Bace masa.
Saude ta tsinci muryarshi na fadar. “Assalamu Alaikum. ” Ta waigo tana kallon shi da mamaki a fuskarta ta
kasa bude baki balle ta iya furta wani abu, Hamid ya yi murmushi kafin ya ce, “Ruwan zuma ne ni ba madaci ba na kasance mai began ki tun a lokacin da na soma ganin ki ba wai sha katafi ba, mene na tunanin a kan hakan?”
Saude ta fara nutsuwa tana kallon kyakkyawar fuskarsa, wadda ta qawatu da dogon hanci da yalwatattun idanuwa wata nutsuwa 'ta dirar .mata muryarta a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login