Showing 87001 words to 90000 words out of 102653 words

Chapter 30 - YAR TALLAH Book Complete Document by Jamila .txt

18 Dec 2024

5928

samu Faridat ta qara gyara gadon har
ta ciro mata kayan da zata saka don haka
Saudat ta nufi inda sallaya ta ke ta yi sallar
magriba ta zauna, har lokacin isha ya shigo
sannan ta yi sallar tare da shafa’ i da wutiri
wadda Momy ta . koya mata tare da wasu daga
cikin ayyuka na addinin musulunci tana idarwa ta
mike ta nufi kan gado inda Farida ta ajiye mata
kayan da za ta saka, wasu lallausan yadi ne
kalar baki mai taushin gaske wanda aka kawata
shi da wasu fararen duwarwatsu masu haske.
Saudat ta saka yadin a jikinta Wanda aka yi'wa
dinkin riga da siket yadin ya bi jikinta ya lafe a
farar fatarta. Farida ta shigo tare da ‘yar siririyar
-sallamarta hannunta na rike da wani
madaidaicin faranti da ke dauke da ‘yan wasu
kananan kwanuka ns tangaram. Ganin Saudat ya
sa ta ta saki murmushi, “Yauwa Aunty Saudat k0
ke fa? Ki dan yi make up k0 ya ya ne Murmushi
kawai Saudat ta yi ta nufl gaban ,dressing mirro
ta ja kujera ta zauna tana kallon gaban madubin
.wanda ke shake taf da kayan x kwalliya irin na
wayayyun mata da suka san kansu.
Body lotion kawai .Saudat ta dauka ta murjawa
jikinta, sannan ta murza wa fuskarta wata yar
karamar hoda wadda ta ida fito da tsabar kyawun
fuskarta, sannan ta shafa wa laBBanta wetlips
gloss, sai da ta Kara gyara gashin kanta ta dame
shi da farin ribbon kwara guda ta sake shi a baya,
sannan ta yi sassaukan daurin kallabi a kanta
wanda ya Kara fito da ita, ta dauki ‘yan qananan
‘yan kunnayenta da sarqa na diamond ta maqala
a kunnenta ta 'saka ‘yar qaramar sarqa ta dauki
turarenta body spray ta mammatsa a‘ gaBObin
jikinta, ita kanta ta san ta yi kyau irin wanda ke
nutsar da zuciyar maigida, ta juyo ta nufo inda
Faridat ke tsaye tana tattara ‘yan komatsanta.
Muryar Saudat na rawa ta soma fadar,“ina kuma
za ki je don Allah : naga kin yi lullubi kina tattara
jaka?”
Faridat ta mike tana kallonta da murmushi a
kan fuskarta, “Maigida ya yi kira Saudat, amma fa
kin yi kyau sosai, nasan yayana zai yaba don
Allah kada dai a yi masa rowa". Tayi maganar
tana dariya tare da shafar beauty point din
Saudat din ta juya a gurguje ta fice tana fadar,
“Don Allah ki ci abin da na hado miki, please
Auntyna".
Saudat da ke tsaye ta bita * da , idanunta masu
kama da madara harta ta fice ba
yadda ta iya haka ta sadakas ta koma da baya ta
zauna a kan gadon nata wanda kr fitar da ,
sassanyan Kamshin bed freshner Ta miKa hannu
ta janyo tiren da Faridat ta ajiye mata ta soma
dudduba abin da ke cikin‘ yan kwanukan da
kofinan, na farko gasasshen nama ne wanda ya ji
kayan yaji, sai na biyu wani' irin nama ne Wanda
aka yi wa 'wata irin dahuwa mai danko, sai' kofi
na farko tsumin markadaddun ‘ya'yan itatuwa ne,
dayan kuma danyar madarar shanu ce , mai kyau.
“ Duk da ba ta fahimci amfanin abubuwan a gare
ta ba, ta daure ta ci sosai kamar yadda Faridar
ta roKa. Ta dauki tiren ta fice da shi ta mayar da
shi a kicin da ke falonta na biyu, ta tsaya tana
kallon kicin din, komai na ciki tsab.tsab gwanin
kyau, ko falon wani mai kudin sai haka, don haka
maimakon ta bar kayan a haka, sai ta soma tara
ruwa ta wanke ’su cike da sha’awar komai na
kicin din Ba ta ji motsin shigoWar mutum a kicin
din ba sai dai ta ji an rungumo kwankwasonta ta
baya. * ” Ta fasa wata razananniyar Kara tare da
juyowa hakan ya ba shi damar rungume ta .
gabadaya a jikinsa tare da lalubar kunnceta cikin
’ sanyin muryarsa ya soma rada mata ‘yan
guntayrn ~kalmomin da ta rinka jinsu tamkar a.
cikin mafarkinta.
Cikin sanyin jiki ta soma Kokarin zame‘ jikinta
hakan ya sa shi rike hannayenta duka biyun
'yana fadar, “Sauara tsaya ki ji, bakinki kawai za
ki ara min just minti biyar kawai’
Wani kallo ta watsa masa a razane tare da fizge
hannunta za ta tsere ya yi'saurin damko ta yana
dariya ya ce “Ke da wasa fa nake miki, wallahi a
gajiye ma nake ba kiji gaBobina ba gaskiya na
samu Saudat da wahala, mu tafl ki taya ni na
watsa ruwa”.
Duk yadda ta so ta kwace abin ya faskara
saboda irin kyakkyawan rikon da ya yi mata a
dole ta bi shi. ‘
Kai tsaye dakin baccinta ya nufa da ita, ya dire ta
a kan gadonta yana fadar, “Zauna nan, bari na
watso ruwan na flto” '
Ba ta tanka masa ba ya juya ya nufl wurin shiga
bandaki ya latsa ya shige _ ita dai kallonsa kawai
ta ke amma da
shawararta yabima da bai cire baqin yadin da ke
jikinsa ba, don ba Karamin kyau ya yi masa ba
abinka ga farar fata. Ta lumshe idonta ta bude
lokaci guda tare da komawa. da baya ta kwanta a
kan gadon, hakan ya yi daidai da shigowar Asma
’cikin dakin. Kirjin‘ Saudat ya yi wata. mummunar
bugawa tamkar saukar aradu, don dama tun dazu
ta kasa nutsuwa tunda ta fahinci a gidan Asma
aka
kawo ta
Asma ta shigo falon sosai tana kallon Saudat . ta
kada kai tare da maida murfin kofar ta rufe tare
da murza key, abin da ya ida firgitar da Saudat ke
nan ta tashi zaune cikin matukar rudani tana
kallon Asma wadda ta jingina bayanta da kyauren
shigowar tana kallon Saudat bakinta dauke da
wani malalacin murmushi mai cike da mugunta,
sannan ta soma nufo inda Saudat din take zaune
Cikin tsananin firgici da rashin sanin abin yi
Saudat ta soma ja da baya. Asma ta ja ta tsaya
tana fadar, “Ina za ki je ‘yan mata? Da ma kin
tsaya don kashe ki zan yi wannan shi ne
huquncin kuskuren da ki ka aikata '
wannan ranar ta yau za ta zamo darasi ga
sauran ‘yan aikin da ke kokarin auren mazan
iyayen
gidansu. Wallahi yau zan kashe ki kuma na kashe
banza, duk duniyar nan babu wanda ya isa ya bi ‘
miki hakki”.
“ Kafin Saudat ta yi wani yunkuri tuni har A‘sma
ta» kai mata cafka tana kokarin Shakar wuyanta
kamar wadda ta sha wani abin maye, kira ' ta ke,
“Yanzu zan kasheki sai dai yazo ya tarar da
gawarki; amma ba dai ke ba don Asma tafi karfin
‘ ‘ ta. hada miji da kaskantacciya, wulakantacciya
~ matalauciya wadda ta yi gadon ;siya da
talauci”.
Kokawa ce ta kaure tsakaninsu, Asma na qokarin
kama makasar Saudat,’ ita kuma Saudat na
qokarin kwatar kanta sai dai qarfin badaya ba
don Asma tafi Karfln Saudat k0 daga yanayin jiki
ma tafita qiba, tunda ita har yanzu ba ta da
Kwari kamar a kama a karya, don haka Asma ta
samu nasarar kayar da ita ta janyo filon da ke
kan gadon abin da ya jazawa Saudat kurma wani
uba-uban ihu kenan, sai dai za mu iya cewa
ihunka banza, kururuwarka wofl don kuwa babu
wanda zai iya juyo ta.
Tana qokarin danne fuskar Saudat da filo, ita
kuma tana kokarin kwatar kanta tana ihu, a haka
Dr. Ahmad ya fito daga bandaki yana dame da
tawul da wani dan karami a hannunsa yana tsane
jikinsa, idonsa da kunnensa suka yi mummunan
gani da ji cikin kidima ya yi kukan kura ya dira
inda suke, ya fincike Asma da
Qarfinsa, amma har a lokacin ba ta daina boren
sai ta cafko Saudat ba.
Abin da ya sa shi kifa mata wani zazzafan marin
da ya sa ta dafe kunci kenan cikin tsananin
kidima don har wata wuta ta ga ta gifta mata
cikin tsananin takaici da zafin zuciya ta ke kallon
Dr, din da idanunta da suka ciko da hawaye
jikinta ya yi sanyi matuka ta soma magana cikin
muryér kuka.
, “Ahmad ni ka mara? Ni ka mara saboda wannan
abun? Lallai ka tsokano wa kanka tsuliyar dodo
dan na“ rantse maka da Allah sai na halaka
yarinyar‘ nan, sai na ga bayanta, sai na kawar da
ita daga doron qasa. Kai in ban da ma asiri ya
rufe _maka idanu wannan har mace ce wadda za
ka 'wulakanta ni a kanta”.
Ta ja kwafa tana girgiza kai, “Tabbas sai ka yi
dana sanin abin da ka aikata min banza, butulu,
mayaudari ai da ma duk dadinka da jaki watarana
sai ya yi maka tutsu don da ma dan halas ne
kadai ke maida halarci. . .”
“Shut up! You are very stupid, get out! Sakarar
banza na ceki bar nan”.
Duk Dr. Ahmad ne’ ke maganar cikin
tsananin fushi tare da nuna mata hanyar fita. _
Tsananin baqin ciki da takaici suka sa Asma yin
wani malalacin murmushi tana kallonsa cike da ‘
qunar zuciya ta girgiza kai ' “ ba zan yi mamakin
duk abin da ke fitowa daga bakinkaba Ahmad,
amma ina so ka sani na shirya daukar dukkanin
tashin hankalin da ka ke ganinka iya kuma ni din
nan wallahi sai na sa ka zubar da hawaye, sai
kayi nadamar sanina a rayuwarka.. “It is enough
Asma I say get out!!” Ganin yadda idanunsa suka
birkice ta san
komai zai iya faruwa idan har ya yi irin wannan
fushin don haka ta ja kwafa ba tare data sake .
magana ba ta bude qofarta fice tana murza
yatsunta alamar za ya gani ke nan. Tana fita ya
maida Kofar ya kulle sannan ya nufo inda Saudat
ta ke kwance tana faman shesshekar kukanta.
Dr. Ahmad ya zauna bakin gadon tare da
janyo ta jikinsa ya rungume ta sosai da‘yar
sanyayyar muryarsa ya soma lallashinta, “Ya isa
haka nan Saudat, kada kanki yazo yana ciwo, ki
yi haquri kinji, duk abin da ta fada karya ta ke ba
za ta iya ba”.
Saudat ta dago kanta da sauri tana kallonsa
cikin idanunta da ke zubar da hawaye ta ce
“Yanzu abin da ta yi bai tabbatar maka da zata
iya aikata abin da ta fada din ba?”
Dr. ya Kara rungumrta, “Ki kwantar da ,
hankalinki zan Kara ja mata kunne sosai kin ji
k0?”
Ba ta iya ce masa komai ba sai ma ta mayar da
kanta a kirjinsa tana kukanta kasa-qasa, Dr. ya
tallafo kanta da hannunsa ya soma bin fuskarta
yana lasar hawayen da suka Bata mata fuska, a
hankali ya soma zarcewa har zuwa kan Wuyanta
da‘ Kirjinta ya rinka bin gabobin jikinta har zuwa‘
tsakiyar kanta yana sinsinar lallausan gashin
kanta wanda ya sha gyafa, sai daukar ido yake.
Saudat ta tSinci kanta cikin wani irin yanayi ’
wanda bata taba tsintar kanta a cikinsa ba
tsawon
rayuwarta, ita kuka shi kuka duka an rasa mai
rarrashin wani, kiran sallar farko shi ya dawo da
Dr daga duniyar rudanin da ya shiga, iya jarunta
da hakuri Saudat ta yi shi, sai dai duk yadda ta
zata abin ya wuce tunaninta. Ta yi kuka har
muryarta ta dusashe don ta azabtu ta kuma sha
wahalar da ba zata misaltu ha, shi kansa ya rude
ganin yadda ya wahalar da ita, don haka ya sure
ta ya nufi bandaki da ita da kansa ya tara ruwa
masu dumi a bahu ya gasa mata jikinta, sannan
ya sa ta dauki niyya ta yi wankan janaba, ya
taimaka mata suka flto daga bandakin kai tsaye
saman gadonta ta haye, saboda yadda jikinta ke
faman kwankwatsa. Cike da tausayawa ya raBa
gefenta Ya shiga mammatsa mata jiki yana
rarrashinta da kalamai masu dadi, har ya samu
bacci ya yi awon gaba da ita, sannan ya mike ya
nufi bandaki ya yo wankansa ya dauro alwala
yazo ya zura jallabiyarsa sannan ya fito inda
shimfidar sallarsa ta ke ya rinka. jera nafilfilu, ,
sai da ya ji ana kiran sallar asuba sannan ya
sallama ya yi addu,o in da zai yi na godiya ga
Allah, ya maida sallar asuba. Yana gamawa ya
mike ya nufi inda Saudat ke kwance tana kukanta
yana son tayar da ita. amma yana tsoron ya
tsokano wa kansa rigima ba yadda ya iya a dole
ya tayar da ita din yadda ya . zata kuwa hakan
ya kasance don tana farkawa kuka ‘
ta sa masa ya samu ya rarrashe ta da
taimakonsa ta dauro alwala ta yi sallar sannan Dr
ya sure ta suka koma kan gadon suka kwanta
yana rarrashinta tare da rirrike ta tamkar tsoka
daya a miya
Karfe sha daya daidai Saudat ta farka daga
baccin da ya kwashe ta, ta bude idanunta sosai
babu Dr. a gadon don haka ta lallaBa ta mike ta
nufi bandaki don watso ruwa, sai da ta tara
rowan dumi ta gasa jikinta sosai sannan ta yi
wankanta sosai ta fito ta ja kujerar dake gaban
madubi ta
zauna. Ta janyo lotion ta murza wa jikinta, ta
dauki
kayan kwalliya ta yi ‘yar sassaukar kwalliyarta, ta
qara gyara gashin kanta wanda ta cude da
mayuka masu laushi, ta sa ribbon kwara daya ta
daure gashin kanta ta fesa masa hair freshner, ta
mike ta nufi wurin wardrof ta bude ta ciro wani
swiss lace mai sulBi irin mai rawa-rawa kalar
jinin kare maroon an masa adon' fulawa light
pink dinkin riga da siket, Saudat ta saka kayan a
jikinta wanda suka .dace da kalar farar fatarta.
“Dinkin ya hau jikinta matuka ta nufi gaban
madubi ta kafa daurin kallabinta sannan ta saka
dankunne da sarka fashion kalar pink ta dauki
body spray ta bi jikinta ta mammatsa ta nufi
cover
din ,da aka tanada dan ajiye takalma ta soma
tunanin kalar da za tasaka.
‘ Dr. Ahmad ya turo qofar ya shigo da sallamarsa,
Saudat taji tamkar ta aza da gudu don idan
akwai wanda ta ke jin kunyarsa to bai wuce Dr‘.
Ba a yanxu, shi kuwa kai tsaye inda ta ke ya nufa
fuskarsa dauke da fara’a yana fadar, “Kai babyna
wannan kyan fa duk nawa ne?”
Ya ida maganar tasa tare da dora kansa a
kan bayanta yana sunsunar kamshinta.
. Saudat ta yi saurin zamewa za ta ruga ya sa
dogon hannunsa ya riko ta yana dariya, tare da
fadar, “Lallai yarinya kina tunanin za ki iya tsere
min ke nan?” *
Saudat ta sa tafukan hannayenta ta rufe
Fuskarta da su tana jin tamkar Kasa ta tsage ta
shige
ciki, Dr. ya sa hakoransa ya cizar mata ‘yan
yatsu
abin da ya sa ta saurin bude fuskar tare da ‘yar
siririyar Kararta cikin shagwaBa kenan ya lakace
mata hanci yana fadar, “Marowaciya Allah da kin
Kara hana ni kallon kwalliyarki sai na cinye miki
bak8” ’ Saudat ta yi rau-rau da idanu tana kallon
inda ya cizar mata. Ya yi saurin rike hannun yana
fadar, “Ayya
'am sorry dazafi ko?’
Ba ta tanka masa ba ta zame hannayenta zata
wuceshi ya yi saurin. cimmata yana fadar, ' '
“Tuba nake ‘yan matana mu je ki karya kin ji”.
Bai saurari abin da za ta ce ba ya riqo ta suka
nufi kicin, ya zaunar da ita a kan daya daga cikin
kujerun da suka zagaye Katon dinning table din
glass, ya cr“Zauna a nan yan matana, me za a
kawo miko?”
Saudat ta dago tana kallonsa sai a lokacin ta
lura da shigar da ke jikinsa, baqin wando ne jeans
da Karamar T.Shirt sai apron da ya daura fara
tare da zungureriyar farar hula irin ta kuku,
Saudat ta yi murmushi ta ma rasa abin da za ta
ce masa.
Ya dan matso daf da' ita, “Ina jinki Madam, me
za kici?” ‘
Saudat ta dauke kanta tana fadar, “Ni fa da ,
kaina nake son in girka”.
, Shi ma ya kwaikwayi maganar tata ta hanyar
fadar, “To ai ni ma tuni na hada miki wani special
girki wanda zai gargade miki kunnuwa”
Dariya Saudat ta sa sosai, saboda salon da ya yi
maganar da shi, shi kuma ya dauki faranti da
serving spoon ya bubbude food flask din da ke
saman tebur din ya kalle ta, “Me za a. zuba wa
, Hajiyar , akWai soyayyar agada plantain, akwai
pizza akwai soyayyen kwai, akwai sandwich tare
da
Lol ga asma ga saude akwai rikicifa
[9:08AM, 07/02/2017] 🙆🏼‍♂@lh@ji🙆🏼‍♂: YAR. TALLA
CHAPTER 33
da soyayycn kifi gasassun kaji a side kuma
tafasasshen ruwan zafi ne me zan zubo wa
gimbiyar tawa?”
‘ Saudat ta yi murmushi tana kallonsa ya riqe
_ ludayin zuba abincin sai ka rantse wani
kwararren
. kuku nr ta lumshe idanunta ta bude lokaci guda
tare da fad'ar, “Ni dai kunu nake son sha”. . ‘
Dr.ya ware ido cikin firgici yana fadar, ’ “‘Kunu
kuma baby? Karfa kice min an karBi 'takardun
ajiya ta jiya har an yi min sing?’ » . Saudat ta
zumburo baki tana fadar, “Ni dai *wallahi bana
so”. ‘ Ya langwaBe kai yana‘kwaikwayonta, “Ni
dai wlh baba so”. Dariya ta Kwace wa Saudat
harda kyalkyalawa, duk yadda ta ke Jin nauyin Dr
sai da
ya kangarar mata da idanu, har ba ta san lokaCin
da .
. ta saki jiki da shi ba a dolenta. Sun yi break
dinsu sosai don da ya lura ma «Saudat
tsattsakuran abincin take mikewa ya yi tsam
ya janya ta jikinsa ya zaunar da ita ya shiga ba
ta
‘ abincin da kansa
Tun tana turjewa har ta gaji ta saki jikinta, saida
ya tabbatar ta qoshi sannan ya kyale ta ya ja "
hannunta suka mike suka nufi falo inda suka baje
.inda yaketa Koqarin ya ga ta saki jiki da shi “
Karfe biyar na yamma taga ya yi shirin; fita
zucayarta ta yi mata wani iri ta zuba masa idanu
ba tare da ta iya tankawa ba Dr yana lura da
yadda yanayinta ya sauya lolkaci guda, amma sai
ya mika mata hannu, “Taso mu je Madam in
zazzagaya dake kiga Bangarenki ki kuma gaisa
da ' ma,ai katanki” ' Ba musu Saudat ta mika
masa hannun nata ya janyo ta suka fice daga
falon sai da suka ratsa 'faluka kusan hudu
sannan suka hau matattakalar .bene suka sauka
falon qasa; sannan suka koma falon da ya’ fi
kowane girma a cikin gidan, a cikinsa kuma ke
da Bangaren ma’aikatan har su'uku ‘yan mata
biyu dattijuwa guda, sai kicin wanda yakr ta
' ,waje, nan kuma akwai mutum biyu masu girki
kwararru mace da namiji. Sai da ya zagaya da ita
ta ko’ina na Gangarenta wanda tsarinsa ya yi
matukar burge Saudat komai na ciki ya yi mata,
musamman wuraren shakatawa da wurin
hutawarta. Suna gama zagayen gidan ya ja ta
waje har inda harabar motocinsa suke da sunan
rakiya, ai ' suna isa wurin motarsa ta tubure sai
ya tafi da ita ' Dr ya riko hannunta yana fadar,
“Tsaya kiji bafa dadewa zanyi ba, just minti
talatin na dawo su Momy kawai zan je in gaisar,
insha Allahu ba zan jimaba
Saudat ta kWantar da murya kafin tace “Allah ya
kiyaye” hanya Dr ya dan zuba idanu kafin ya ce
Kinmin izini da gaske har cikin zuciyarki na tafi
karfa sai na dawo in fuskanci fushinki” ‘ ' Saudat
ta dan yi dariya tana fadar, “Haba ni na isa? Ai
sai”
Bangazar da akai kai mata ce ta katse maganar
da take qokarin yi, ta yi taga-taga ta fada ‘_ kan
motar da ke gabanta, kanta ya bugi motar,
Saudat ta dafe goshi ta waigo tana ganin mai
,wannan aikin, ba ta yi mamakin ganin Asma ba
wadda ta sha gaban Dr; har jikinsu na gugar
juna.
Saudat ta ji wani irin abu ya dakar mata zuciya
tamkar saukar guduma, musamman yadda taga
ya kafe ta da fararen idanunsa ba ya k0 son
kiftawa, yana kallon yadda take magana cikin
kissa da gadara
“Zan yi magana da kai?”
Ya mantar da tasa muryar kasan tata, “To ga shi
kuma fita zan yi yanzu a yi haquri sai na ‘ dawo”.
, .
Ta watso masa wani fari mai kama da harara '
sannan ta juya a fusace ta nufi inda sabuwar ’
motarta ta ke mai baqin gilashi “ta fada
mazaunin dircba tare da dagawa escort
Dinta hannu ; ta ja abinta a guje ta fice
DR Ahmad ya yi wani dan gajeran murmushl tare
da kallon inda Saudat take wadda . tsabar takaici
yasa ta wasu siraran hawaye suka biyo kuncinta,
Dr. ya yi saurin janyo ta jikinsa yana fadar, "Am
sorry tawan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login