Showing 189001 words to 192000 words out of 196911 words
Chapter 64 - A RUBUCE TA KE book 1 Completed Huguma .txt
da dama,gaba daya sai wuta ta dauke mata,taci burki tana kallonsa kamar wata zararriya riqe da kumatunta
"Don kina iskanci da rashin mutuncinki kina ganin kamar bazan iya daukan mataki a kanki ba kin yaudari kanki,sassauci na da dauke kan da nake miki inason na zama mafi alkhairi ne ga iyalinsa,amma ke gaba daya tosashiyar kwanyarki ta kasa gano miki hakan,to wallahi wallahi kinyi na farko kinyi na qarshe,bazanci gaba da dauka ba,ki bacemin daga wajen nan tun ban bi ta kanki ba!!!" Ya fada da wata irin rugugin tsawa,ba hafsat dake tsaye a wajen ba,hatta da widad dake daga cikin falon saida cikinta ya juya, tsoron sosai ya kamata,ta koma ta zauna saman daya daga cikin kujerun dake dab da qofar,karin farko da taji sautin fushi da bacin rai daga gareshi kenan.
"Ko meye zaka ce, kuma ko me zakayi bazan fasa fadin cutata da kakeyi da cin zarafina ba,yarinya qarama ta mallakeka sai yadda tayi dakai,sai abinda tace,kanata zalunta ta,bazna yafe ba wallahi,sai Allah ya sakamun,kai da ita dukanku bazan yafe muku ba" cikin fushi ya sake daga hannu sai kuma idanunsa suka sauka kan cikinta,ya janye hannun yana qoqarin hadiye fushinsa,bai taba dora hannu a kanta ba sai yau,sai ya kama hannunta ya saita mata hanya yana gaya mata cikin tsawa ta bace masa a wajen.
Jinta take kamar ba'a tsaye take saman qafafunta ba kamar akan iska take haka ta juya ta fara barin wajen, hannunta har yanzu akan kuncinta,idanunta na malalar hawaye masu zafi da quna,yau ita abbas ya mara?,wannan shine mummunan abun tarihi na farko daya faru a iya zamansu da ba zata mance dashi ba.
Ido ya zuba mata cikin fushi har ta bace a wajen,sannan ya juya ya bude qofar,wanda tuni widad dake zaune saman kujera ta miqe tana dakon isowarsa,saidai zuwa yayi ya wuceta abinsa yana wani irin huci,kaman zai zauna akan kujera amma sai ya kasa,ya dinga kai komo widad din tana kallonsa tana kuka qasa qasa
"Shut up" ya fada mata da wata irin tsawa data sakata qanqame jiki waje daya hadi da runtse idanunta,bayason jin kukanta ne kwata kwata,tana qara hasala masa zuciyarsa ne ba tare data sani ba,a cikin yanayin da yake kuma a yanzun bazai iya lallashinta ba,sai kuma ya koma ya zauna bayan ya sakar mata tsawar,jikinsa yana mutuwa,qaramin sautin kukanta yana sake ratsa falon.
Kusan minti talatin suna a haka,ta kasa shuru shi kuma ya kasa lallashinta,sai da suka doshi minti arba'in sannan ya miqe ya fice,ba jimawa ya dawo dauke da hijab dinta da wayarta ya miqa mata,sannan ya isa gaban freezer dinsa ya ciro ruwan gora mai sanyi ya bude ya miqa mata,tasa hannu ta karba tana satar kallonsa,idanunsa ba'a kanta yake ba,wani gurin daban yake kalla,sai takai ruwan bakinta ta fara sha,ya fara sauka cikin cikinta yana ratsa qirjinta dake suya,yana kuma rage mata radadin da takeji.
Kusan rabi tasha sannan ta miqa masa,sai ya sake saka hannu ya karba ba tare daya kalleta ba,bakinsa yakai ya shanye sauran yana yin gaba,ya cillar da robar yana cewa
"Wuce muje" bayansa tabi ba tare da tasan ina suka nufa ba,motar sa ya bude tun kafin su qarasa da remote control,ya isa seat din gefan driver ya bude mata ta shiga ya mayar ya rufe,sannan ya zagaya shima nasa bangaren ya shiga ya tayar da motar suka bar gidan.
Lamo tayi cikin motar,ta kwantar da kanta a makarin kujerar tana 'yar sheshsheqar kuka,idonsa ya dinga runtsewa,sautin kukanta yana qonashi da yawa,basarwa ya dinga yi yana zaton zai iya daurewa amma sai ya kasa,tausayinta ya lullubeshi,yadan daki kan motar,sai ya gangara gefan hanya yayi parking ya juyo sosai ya zuba mata ido yana hadiye bacin ransa da qyar
"Why widad.....why.......me yasa kika biye mata?" Idanunta dake jiqe da hawaye ta daga ta kalleshi
"Amma uncle.....itace ta fara fa" kai ya jijjiga
"Na sani,amma kina zaton zan tsaya ne a wajen ina kallo ta cutarmin dake?" Kai ta kada a hankali alamun a'ah
"So kike ki koyi irin abinda takeyi?,kinaso na daina samun walwala gaba daya?" Kai ta girgiza nan ma sabuwar qwalla na sauko mata
"Kayi haquri uncle......am sorry" a hankali ya lalubo hannunta da hannunsa guda daya ya hadesu waje daya yana hadiye wani bacin rai daya tsaya masa
"Am sorry too baby,na miki tsawa,it was not intentionally.......hankalina ne a tashe,raina a bace,banason kema ki koma wani abu daban"
"Bazan sake ba uncle" ta kuma fada hawaye na sake balle mata
"Kina qonani baby doll,kina qona zuciyata,ki daina wannan kukan" ya fadi yana kamo fuskarta cikin hannunsa,tare da zaro handkerchief dinsa ya soma goge mata fuskar cikin wani irin salo na tausasawa da nuna zallar qauna,hausawa sukance gaida mai gaidaka ko bazai amsa ba,ko meye zai mata idan tana cikin bacin rai bai fadi ba,widad ce kadai ke fahimtar ransa a bace yake ko yana fushi,saita tabbatar tayi abinda zai samu sassauci kota saukeshi daga fushinsa,duk da kusan ba itace sila ba.
Saida suka shiga unguwar ta fahimci gidan hajiya ya kawota,bashi da wani solution illa hakan,saboda yasan kwana zatayi kuka ita kadai,babu lallai ta saki jikinta,a nan ne kawai zata sake tayi baccinta.
Mamaki ya kama hajiya lokacin data gansu tare,baice ma hajiyan komai ba ya barta a nan ya koma setting room din qofar gidansu suka shiga meeting din da suka shirya yi din.
Itama batace komai da hajiyan ba,saidai hajiya ta fuskanci sanyi jiki kadan tattare da ita,tanata kallon widad din,canzawar da tayi tayi yawa,ta kasa cinyewa wannan karon bayan sun gama meeting din ya shigo gidan,widad din ta tafi kawo masa abincin da bai samu ci ba tace dashi
"Anya abbas ba juna biyu yarinyar nan take dashi ba?" Ido yadan lumshe yana sakin qaramin murmushi,hasaso 'yar rigimar tashi da ciki kawai yakeyi,inda hakan zata kasance da yafi kowa farinciki,amma fa yasan daru ne za'a shashi
"Banjin haka hajiya"
"Bata amai bata yawu,ba zazzabin dare?" Dan jim yayi sannan ya girgiza kansa
"Babu hajiya"
"To ma sha Allah,Allah ya kawo nagari masu albarka"
"Ameen ameen" ya fada cikin dan jin nauyi.
Muneera ya nema yace ta gyara daki daya widad din zata kwanta a ciki,ba jimawa muneera ta gyara din,don dama ba dakin da hajiyan ke barinsa da dauda.
Yana zaune ta wuce dakin,hajiya tace taje ta kwanta,taga kamar tana alamun bacci a idanunta,ta yima hajiya sai da safe,ta juyo zata masa sallama suka hada ido,sai ta basar tace
"Sai da safe"
"Allah ya bamu alkhairi" ya amsa ta yana binta da kallo,inda suna kaduna waye zai shiga tsakaninsu a irin wannan lokacin,kaf rayuwarsa yana qaunar dare yayi,saboda lokacine da zai rabi jikinta sosai ya kuma kwana yana jin duminta hadi da shaqar tattausan qamshinta.
"Ba yanzu zaka wuce bane" hajiya ta tambayeshi ganin goma da rabi na neman gotawa,agogo ya kalla sannan yadan dubi hajiyan
"Wannan program din nake jira su gama saina wuce" ya bata amsa yana maida dubansa ga tv din,saidai a zahiri gidan ne baya qaunar komawa,idan ya tuna abinda hafsat din tayi sai yaji ransa ya baci,yana so ya sake hucewa ne kafin yakai ga shiga gidan,bayason komawa da zafinsa shaidan ya ingizashi ya yanke mummunan hukunci.
"To bari na shiga na kwanta nidai" sukayi sallama da hajiyan,amma yace idan ya gama zai wuce zai mata magana.
Ido yabi hajiyan dashi har ta shige daki,sai yayi zumbur ya miqe yana zuba hannuwansa a aljihun rigarsa ya wuce dakin widad.
Tunda ta shiga dakin tana kwance ne kawai amma bacci bai zowa idanunta ba har sannan,har yanzu zuciyarta a bace take kan abinda hafsat din tayi mata,tunda take ba'a taba yi mata makamancin abinda hafsat din tayi mata ba,gaba daya kimarta babu ita a idanunta,duk wani sauran mutunci nata da take gani a yanzu babu shi,to me tayi mata da har take yunqurin dukanta?, tabbas inda ta dora hannunta a kanta babu abinda zai hanata ramawa kowa kuwa gemunta na jan qasa ne saboda girma da shekaru,tunda ai bataga abinda tayi mata ba.
Sallamarsa tasa ta daga idanunta zuwa fuskarsa,ta zuba masa ido na wasu sakanni,haka kawai taji tausayinsa ya kamata,tausayin da batasan na meye ba,ya tako a hankali zuwa gaban gadon,sai ya matsa jikin switch na fankan yana rage gudun fankan dakin,sannan ya dqwo gefan gadon ya zauna yana cewa
"Wannan iskan ai tayi yawa"
"Zafi nakeji" ta fada muryarta qasa qasa,ya waiwayo yana dubanta cikin mamaki,don garin a sake yake da iska, baice komai ba yakai hannunsa jikinta ya taba,da gaske gumi takeyi,sai yasa hannu ya dagota gaba daya yana zare mata rigar jikinta,ya barta daga ita sai farar vest me siririn hannu, idanunsa suka sauka a qirjinta da suka cika suke a tsaye kyam,sai tayi hanzarin jan bargo zuwa qirjin nata ta koma da sauri ta kwanta tana boye fuskarta.
*H A F S A T*
Kuka ta zauna tana yi sosai kamar zata fidda zuciyarta,ba zafin marin ne yafi damunta ba,wadda aka mareta ta sanadinta ne damuwarta,hannun abbas yau da yakai fuskarta ya daketa saboda widad din?,takai ta kawo,ta kasa zama tana jin kamar abinda yake cikinta zai fito a yau.
Tana tsaka da wannan taji tashin motarsa,da sauri ta daga labulenta tana leqensa har ya fice, zuciyarta ta dinga qissima mata abubuwa da yawa,shi da waye?, abinda yafi tsaya mata a rai kenan,sai kawai kuka ya qwace mata,ta dauki wayarta da hanzari ta danna wa mamanta kira,tana jin baqinciki kamar zai kasheta,ba zata iya hadiyar wannan bacin ran ita kadai ba.
Ashar mamanta ta dinga zundumawa
"Saboda baisan darajarki da mutuncinki ba?,cikin daren nan,da tsohon ciki a jikinki zai kamaki ya daka?"
"Ni umma anya wannan hanyar tana aiki kuwa?"
"Bana shakka akai,saidai kice wani abu da ya kawo tasgaro ya faru,amma koma meye ki daga waya ki gayawa uwarshi abinda yayi miki,yadda yasa kika tasheni a bacci itama ki tasheta" akan wannan suka rabu,ba tare da wani dogon tunani ba kuwa ta laluba number hajiya ta kirata.
Dai dai lokacin da dattijuwar ke saman abun sallah tana shafa'i da wuturi taji qarar waya
"Subhanallah" ta furta bayan ta gane number wadda ke kira,tabbas matsala ce ta faru ta tabbatar,don ba zata iya tuna sanda taga kiran hafsat din a wayarta haka siddan ba tare da komai na matsala ya faru ba.[3/22, 9:37 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*
Page 99
"Hajiya ina wuni"
"Lafiya alhmdlh,ya nauyin jiki?"
"Lafiya lau" ta fada a gaggauce,sannan ta zauna ta fara rattabo mata abinda ya faru.
Fiye da rabin maganar ta canzata, hajiyan tayi shuru tana saurarenta har ta gama fada sannan ta rushe da kuka
"Ya isa,kiyi shuru haka ki daina kukan ko don abinda yake jikinki,zan laluba gaskiyar maganar,indai na sameshi da laifi saina bata masa,ki kwanta kiyi bacci zan nemeki in sha Allah" a haka suka rabu da hajiyan,can qasan ranta tana jin haushi haushi,wai zata bincika taji,itama ta fara canza hali kenan.
Ajiyar zuciya hajiyan ta saki
"La haula wala quwwata illa billa" ta fada a fili,qaddarar abbas kenan shi kuma,kalar tasa jarrabawar rayuwar kenan,yunqurawa tayi ta miqe tana fatan ta sameshi a falo,duk da sha daya na dare ma ta gota,amma yace zai mata magana idan zai wuce.
Murmushi ya bita dashi sanda ta koma ta kwanta tana boye fuskarta,sai yaja mata bargon sosai,ya sunkuya yayi kissing dinta lightly,sannan ya motsa bakinsa zuw kunnenta cikin rada yace
"Kiyi bacci mai dadi babyn uncle" a dole murmushi ya subuce mata,hakan yayi masa dadi,sai ya rage mata hasken dakin sosai,ya sake lullubeta ya fice yaja mata qofar.
Dai dai lokacin hajiya ta fito a dakinta,sai sukayi kacibus,kunya ta dan kamashi,sai hajiyan ta kauda kanta
"Yanzu nake shirin shigowa muyi sallama" ya fada yana shafa kansa
"Gwara da baka wuce din ba ai,zo ka zauna muyi magana" tuni jikinsa ya bashi tayi halin,ya dawo gaban hajiyan ya zauna
"Matso" tace dashi,sai ya dawo saitin qafarta
"Wanne abu ne ya shiga kanka da zaka saka hannu ka mammari matarka da tsohon ciki?" Kansa ya saddar qasa na wasu sakanni,sannan ya dago
"Hajiya na fara gajiya da hafsat,na gaji da halayenta,inajin taqi kadan ya rage mu rabu"
"Aah,kada ka sake fadin haka,yanzun me ya hadaku?" Bai boye mata komai ba ya gaya mata,tayi shuru abun na tsumata,ko yaushe abun na hafsat gaba yake ba baya ba?
"Iya qoqarina hajiya inayi,ina dannewa,ban taba kai qararta ba,amma kome nayi ita bata gani,da qyar wani lokacin nake iya tanqwara zuciyata akanta,tana kaini bango,bani da guarantee din abinda zai iya faruwa gaba"
"Haquri zaka ci gaba dayi,ko don albarkacin zuri'a data ratsa tsakaninku"
Duk da ita kanta hajiyan abubuwan sunata kwance mata,to amma ita din uwa ce,duk yadda uwa take da juriya aka santa,ba yadda zataso abbas din yayi wani abu na rashin dadi ko kyautatawa,har abada da naka yayi cuta gwara shi a cuceshi,baki ta dinga baki da nasiha cikin hikima ta dattawan mutane masu hankali da sanin ya kamata,taga bacin rai da damuwa masu yawa a idanunsa
"Ku shirya gobe ku koma inda kuka fito kawai abbas,banason wannan tashin hankalin,mun yafe bikin" statement din hajiya na qarshe kenan,don shine kawai mafita.
Kamar dama ta shiga xuciyarsa,don darajarta ce kawai take sanyashi yawancin lokutta yake zama a garin har yayi kwanaki idan yazo.
Sha biyu da minti goma ya isa gida,tana falo zaune don ta kasa runtsawa,ta kuma ji shigowarsa,sai taci gaba da zama tana tsammatar shigowarsa ganinsu mimi,amma har aka qara mintuna talatin shuru babu shi babu bayaninsa.
Shikam sashensa ya shige,ya fidda kayan jikinsa yayi wanka,sannan ya shirya kayansa waje daya kafin nan ya kwanta.
Har qarfe daya na dare tana zaune shuru,ranta yana sake baci,zuciya na mata saqa iri daban daban,yana nufin har kwanan nata ma ya saraya kenan?,idan bai shigo yanzu ba ta tabbata da safe zai shigo,zata ga da wanne ido zai kalleta.
Daga sallar asuba ya zarce da wanka,kafin qarfe shida ya gama shirinsa tsaf,ya fidda luggage dinsa ya saka a mota.
Sale ya barwa envelope yace ya bawa matar gidan,kudaden hidimar gida ne a ciki,ya zare dukkan wasu kudade daya saba bar mata wanda suke kyautatawa ce kawai bawai na haqqin dake wuyansa na shari'a ba.
*********Da farko ta watsar dashi kamar yadda ya watsar da ita,don ba qaramin shaqar takaici tayi ba sanda ta karba saqon ta hannun sale,ya rasa wa zai bawa aiken kudin amfanin gidanta sai salen?,bata sake shiga rudu ba sai dataga kowanne kudi ya fadi na meye,babu ko qarin sile akan abinda ya saba bata,gashi buqatar kudin take da gaske saboda fara adashin asara data yi,ko cikin satin ummanta tace lallai lallai ta tanadi kudi,saboda ba zasu taba bari sakaci ya shigo cikin aikin da aka fara ba,wannan ya sanya ta sake qullatar widad din qwarai,a duniya idan aka bata bindiga akace ta kashe mutum daya widad din zata fara harbewa.
Yadda ya dauke mata wuta abin ya fara damunta,gashi tana fuskantar EDD dinta yana sake matsowa,wata zuciyar tana ta kirashi wata tana ta shareshi,a haka kwanakin suka fara tafiya, dole daga bisani ta karya billent ta kirashi,ta kuma maida komai ba komai ba,don lallai tana buqatar kudi.
*B a y a n wa t a u k u*
Bayan watanni uku hafsat din ta sauka,ta sake samun baby girl,zagayowar kwanaki hudu abbas ya dauki excuse don zuwa ganin baby,dole widad ta soma shirin binsa itama,don rabonta da bauchi tun wancan lokacin da suka samu sabani da hafsat,duk sanda zaije weekend tabar binsa,saidai yaje yayi kwanaki biyu ya dawo Kaduna,hakan yafi mata kwanciyar hankali,har ya zamana koda wasa batason taji ya ambaci xuwa bauchi da ita,yanzu zataji hankalinta ya tashi.
Ta shirya tsaf tayi sabbin dinkunanta,gyaran gashi zuwa lalle suka wuce bauchi,ranar ta shiga sassan hafsat din,wanda rabonta dashi har ta manta.
Ba wani mutane bane sosai, kasancewar ita din dama bata mutane bace,mai zuwa mata sha'ani sai wanda ya dubi Allah,anty ummee ce sai wasu baqi mata biyu sai 'yar yayarta data dauko saboda aikace aikacen gidan,sai hajiya habiba.
Ciki ciki hafsat din ta amsa mata barkan data mata,itama sai bata saka kanta can ba,ta zauna daga hannun kujera,anty ummee ta miqa mata baby da aka gama yiwa wanka tana qarewa widad din kallo tsafff tana kaduwa da yadda taga ta sauya,ta karbeta tana jin sha'awar yarinyar har cikin zuciyarta,kasancewarta mai son yara sosai.
"Uhmmm.....ko a bar miki ita ne?,naga