Showing 162001 words to 165000 words out of 196911 words

Chapter 55 - A RUBUCE TA KE book 1 Completed Huguma .txt

haduwa,yasa hannu a hankali ya janye hijabinta baya,kyakkyawar fuskarta ta bayyana,ya sanya hannu ya kamo tafin hannunta ya saka cikin nasa yana ci gaba da kallonta


"Fushi ake dani baby?" Ya tambayeta yana narkewa kamar shima zai sakar mata kukan,kamar jira takeyi ita saita rigashi,ta sakar masa nata kukan qasa qasa


"Ba kaine ba......shine ka yimin wayo,saboda kaga ka girmeni" tayi maganar tana mele baki,kaman zaiyi dariya amma sai ya danne


"Am sorry,nima fa ba'a son raina ba,bansan nayi ba sai daga baya"


"Kuma fa gidan nan kasan akwai baqi,yanzu idan mom ahmad ta gane me zance mata?" Dariya sosai ta sake kamashi kamar yayi me,amma ya tabbatar idan yayita yanzu zai jama kansa jagwal


"Waye yace miki ana ganewa?, ba'a fa ganewa kayi,kuma ma....." Sai yayi qas sosai da muryarsa,ya sake matsowa da fuskar sa dab da ita kamar zai shige cikin hijabin


".....kowa yanayi,itama nasan sunyi jiya......." Bata barshi ya qarasa ba ta cure waje daya cikin hijabinta


"....don Allah uncle" a wannan lokacin kasa boye dariyarsa yayi,ya dora fuskarsa saman qafafunta yayi dariyarsa sosai yana jin nishadi yana wanzuwa a rayuwarsa.


**********Sati guda daya rak amma dai dai yake da wasu shekaru a wajensa,sati guda daya daya canza rayuwarsa da tunaninsa,tayi wani mugun tsayawa cikin rayuwarsa,ta kuma barma zuciyarsa wani babban tambari da yakejin har duniya ta nade bazai taba goguwa ba.


Jinta yake sosai a ransa,wani irin ji da yake ratsa zuciya matuqar ratsawa,tattali qauna da soyayya yake nuna mata irin wadda idanuwa basu saba gani ba,wasu abubuwan shi da kansa baisan yana yinsu ba,ta mantar dashi dukka wata damuwa tasa da matsalar da yakejin yana ciki.


Duk da bata gama sakewa dashi gaba daya ba,amma zai iya cewa ya samu fiye da rabin abinda yakeso,ya sani cewa da zarar ta sake sanin darajarsa ta kuma sake hankali da wayo,zai shiga sahun mazan da sukayi sa'ar matana aure a duniya,wani irin qauna da kimar hajiyarsa ke sake kwaranya a zuciyarsa,uwa uwa ce......uwa daban take,ashe irin wannan take ta kwadayin samar masa shi yasa ta dage cikin qanqanin lokaci sai data shigo da widad din cikin rayuwarsa?.


Ta fannin widad din ta sake zama wata tabararriya ta gaske,shagwabarta take zubawa yadda taga dama,biye mata yakeyi,ta koma tamkar su mimi,ko tari tayi sai ya tambayi ba'asi,duk wani koke koke da take masa a duk sanda ya samu yadda yakeso sam basa damunsa,yasa hannu ya karbe ya kuma shnaye dukka rigimarta,hasalima shagwabarta na daya daga cikin abubuwan dake saurin kunnoshi da rura wutar soyayyarta a zuciyarsa,wannan ya sake haifar da shaquwa tsakaninsu shi da ita,duk da har a lokacin yana tantamar tasan kalmar so?,abu na qarshe da yakeson ya gina gini mai ingancin da bazai rushe ba cikin zuciya dama rayuwarta gaba daya.


A qarshen watan ya gama yanke shawarar meye mafi girman tukuci da zai bawa rayuwarta?,yana tsaka da wannan tunanin saiga kyautar kujerar hajji har guda biyu daga wajen tsohon governor ya bashi kyauta,yayi masifar jin dadin aiki da abbas din,kuma har yau yana yaba masa,wannan yasa time to time yake tabo abbas din,inda tason ran Excellency dinne da tuni abbas din ya koma aiki qarqashinsa,saidai shi bashi da wannan interest din,dole ya haqura ya qyaleshi,amma lokaci lokaci yana taboshi akan wasu harkokin tsaro da suka shafeshi,kamar yanzun da zaiyi tafiyar,yaji ba wanda ya dace ya tafi dashi da yafi abbas din.


A lokacin babu wanda yaga ya dace da wannan tafiyar sai widad din,don haka ya karba daya yasa sunanta a daya ba tare da tasan ma da kujerar ba,aka soma processing na tafiyar,wadda zasu yita ne in group cikin tawagar his Excellency din.


Cikin sati na gaba suka shirya zuwa bauchi,tun bayan zuwan da sukayi suraj da matarsa sukazo musu basu sake zuwa bauchi ba sai a yanzu.


*********Karon farko data zauna ta hadawa abbas din kayan tafiya bauchin,a lokacin ya fita office,baisan ma ta hada din ba,sai daya dawo daga aiki,ya buda akwatin,ya jima tsugunne yana kallon luggage din, murmushi yana kubce masa,yadda ta shirya masa komai kamar shi da kansa ya shirya kayan nasa,ya girgiza kai ya miqe yana jin qaunarta tana sake ninkuwa cikin ransa,tasan buqatarsa,tasan choices dinsa tun yanzu.


Kai tsayr toilet ya shiga ya gama wanka ya fito,yana tsaye gaban mirror yana tsane ruwan wankan dake jikinsa,wanda ke fidda qamshin daddadan turaren wankan daya cakuda dana shower gel dinsa,fuskarsa yake kalla,cikin kwanakin har wani canzawa yaga yayi,kuzarinsa ya qaru,kamar yadda yaga yadan sake cikowa,fatarsa kuma ta qara haske kamar mai amfani da wani mai na daban.


Ana taba qofar ya maida idanunsa ga bakin qofar,ya kasa ya tsare yana jiran shigowarta.


Da sallama ta shigo cikin siririyar muryartan nan,sanye take da wata fara sol don smoked gown,kanta babu dankwali sai farin ribbon data matse sassalkan gashinta,fuskarta fes yau babu digon komai saina man lebe da ya sanya siraran lips dinta suketa qyalli,ba shiri ya saki comb din ya waiwayo harde da hannayensa a qirji yana qare mata kallo.


Shigar yau ta fidda asalin tushenta wato larabawa,kamar diyoyin larabawan da suka samu kyakkyawan kulawa,rigar ta karbeta,haka gyaran data yiwa gashinta wanda gaba daya wani abune da bilkisa ta koya mata kafin su tafi


"Bakison kiga uncle din yafi ji dake akan kowa?,to haka zaki dinga yi,ma sha Allah,inda nice da wannan jikin naki da wannan gashin.....ai da tuni na kori hafsat" ta fada tana qyalqyala dariya,don dama sam babu jituwa tsakaninta da hafsat din,duk da amintakar dake tsakanin mazajensu, bilkisa bata daukar raini ko wulaqanci,hakanan dama tun usul ita bata jituwa da marowacin mutum,wadan nan siffofi kuwa dasu hafsat tafi shuhura,wannan dalilin yasa matan abokansa da suke manyan mutane masu manyan muqamai iri daban daban a gwamnati suka janye jiki daga matarsa da gidansa,don babu wadda kejin dadin mu'amala da ita,idan sunzo gidan sai dole,kamar haihuwa da sauransu.


Dukka hannayensa ya bude mata,yana mata alamar ta taho,saita tsaya daga bakin qofar ta noqe kafada tana tura baki gaba,tana tuna azabar da tasha daren jiya a hannunsa


"C'mon mana baby doll,nayi alqawari fa bazan sake ba har sai kin yarda"


"Promise?" Kai ya jinjina yana murmushi sannan yace


"Amma kada ki manta,kema kinyi alqawarin zaki barni nayi komai banda wannan abun dai....." Yadda yayi maganar a narke shi kansa zaka dauka yarone dan shekara tara ko goma,abun ya bata kunya sosai,ta sanya zara zaran fararen yatsunta ta lullube fuskarta tana dariya,sannan ta fara takowa a hankali zuwa gabansa,yayin da shi kuma ya kafeta da ido yana jiran ta qaraso,bugun zuciyarsa na daduwa,yanajin kamar tana ja masa aji ne,kamar bata sauri.


Taku biyu ya qara ya cimmata a hanya,ya durqusa gabanta ya lullubeta cikin ingarman qirjinsa dake cike da muscles da gargasa suka yiwa tufa,haka qirar jikinsa yake tun asali,wannan ya qara masa interest na shiga aikin police.


Cikin abinda baifi second goma da shiga jikinsa ba dukka jikin nasa ya dauki rawa,ya cusa kansa a wuyanta yana shaqar qamshinta da har yanzu bai sake jin wani qamshi da yake burgeshi kamarsa ba,yadda bugun zuciyarsa ya qaru haka speed na fitar numfashinsa,banda girman alqawarin daya dauka babu abinda zai hanashi karyashi.


Tayi lamo a jikinsa ita kanta,tana jin yadda numfashinsa ke kewaye fatarta yana ratsata har cikin qashi,ko qwaqwaran motsi batayi ba,wani yanayi yana sauka a jikinta,har ya haqura don kansa,ya daga kansa a hankali zuwa ga fuskarta yana riqe da fuskartata a tsakanin hannuwansa


"Ki rage tsoro don Allah baby.....i love you" murmushi ta saka a kunyace tana son sake boye kanta,sai ya miqe yana cewa


"Nooo.....wannan kwalliyar na siyeta har fuskar,zan biya.....don Allah a barni na kalla" cak ya dagata ya azata saman madubin,ya jawo dressing chair ya zauna akai ya buda lotion dinsa ya fara shafawa,yana shafawar yana duban fuskarta hadi da tsokanarta ta hanyar tuna mata da abinda ya faru daren jiya.


Kukan shagwaba ta sakar masa tana bubbuga qafafunta


"Nidai Allah uncle......Allah.....Allah" dariya ta dinga cinsa,irin abinda bata taba gani ya sake haka yana dariya ba


"Shikenan.....wasa nake miki,na daina,amma bakiji bane?,nima fa na kira hajiya har bansan adadi ba,na dauka mutuwa zanyi,yarinyar nan haka kike da......" Ba tare data shirya ba ta saka hannunta ta rufe masa baki idanunta dukka a waje,tana jin kamar qasa ta tsage ta shige,sai kawai ta nemi silmiyowa daga saman madubin,cikin zafin nama ya tareta da cinyoyinta,sai gata zaune sosai a samansu


"Yarinya kin kawo kanki" ya fada a tausashe murmushi na kubce masa.


°°°°°°°°°Karfe goma na safe suka fito shi da ita,kallo daya zakayi musu kaji sunyi mugun burgeka,kamar hadin baki,shi da itan duka shigar sky blue sukayi,shi shadda ainihin gezner ya saka,ita kuma wani lace ne cotton mara nauyi.


Yau din bai nema wani dan rakiya ba,shi da kansa yayi driving nasu daga kadunan zuwa bauchi,duk da jirgi ma yaso subi,amma sai yaji yana da muradin awannin da zasuyi a tare cikin motar waje guda kafin su isa kadunan,don yasan dole kuma ya bawa hafsan lokaci kodon fita hakki,amma for now ya fara tunanin yadda zai dinga raba musu kwana duk lokacin da suka je bauchi,musamman idan zaiyi kwanakin da yafi biyu.
[3/18, 4:01 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*


*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*


Page 85




Yau din tunda suka tashi daga kaduna basu tsaya ba,don bata jima ba bacci ya dauketa,don dama yawanci saboda ita yakan tsaya din,ya samar mata wani abun da zataci,to har suka je inda yakan tsaya din suyi sallah da sauransu tana baccinta,don haka ya wuce abinsa kai tsaye,lokaci lokaci yana waiwayawa ya kalleta,yana monitoring baccin nata.


Bata farka ba sai da suka shiga unguwarsu,tadan kalleshi,suka hada ido,yasan me takeson cewa,gidan hajiya takeson zuwa,to amma bayajin zai iya barinta,tunda duka duka kwana hudu zasuyi su juya,suya saki murmushi kawai ya shafi gefan fuskarta


"Ba kwana gidan hajiya wannan karon,i need you by my side" shuru tayi kawai,ta langabar da kanta gefe guda ba tare data ce komai ba,duk da ba haka taso ba cikin ranta.


Yana gama parking kusa da motar hafsat din data dauki qura mimi na shigowa ita dame daukota daga makaranta,ganin motar babanta ya sanyata tahowa da gudunta tana kiran sunansa,ya dagata ya rungumeta yayi kissing dinta,saita zame daga jikinsa ta koma wajen widad.


Ta yima widad din nauyi,amma saita riqe hannunta tana tsokanarta hadi dayi mata waqar 'yar makaranta,tana ta dariya,dadi ya cika yarinyar,ko banza tana samun nishadi kulawa da kuma canjin rayuwa a duk sanda baban nata da antyn nata sukazo.


Kamar sama sama take jiyo muryar mimi din tana kiran sunan baban nata,sai taja tsaki ta share,a ranta tana jin haushin yadda yarinyar keda qulafucin ubanta,tana tsoron gaba kadan ma zaiyi wahala idan batafi sonta akan uban ba,saita ci gaba da lissafin kudinta,amma kuma jin shiru bata ji motsin mimin ba,saita ajjiye wayarta da take lissafin a ciki ta miqe tana gyara daurin zaninta,ta sako kai zuwa harabar gidan.


Dai dai sanda sale ke cire kayansu a booth din motar,abbas din yana gaya masa kada yayi nisa zai kaishi kasuwa.


Cikin wani mugun mutuwar jiki ta sauke hannuwanta data tokare bakin qofa dasu


"Kanbun bal bala'in bala'i!" Bakinta ya furta duk da batasan yaushe hakan ta faru ba,daga inda take tsaye tana iya hangen widad wadda ke riqe da hannun mimi,fuskarta kwance da murmushin daya qarawa fuskar tata kyau da kuma kwarjini


"Wanne irin girma ne haka cikin wata guda kacal?" Ta tambayi kanta da kanta,har yanzu idanunta na saman fuskar widad din,ko sau daya ma bata waiwayi inda abbas din yake ba.


Takawa ta soma yi zuwa inda suke tsaye a hankali tanason sake gasgata abinda idanunta ke nuna mata,saidai duk taku daya idan tayi bugun zuciyarta sai ya qaru,kyau da yadda girma ya fara nunawa a jikin widad din suka soma bata mamaki.


Qaramar jakarta abbas ya dora mata saman mota bayan ya kulle motar


"Keda mimin banga marabarku ba" yayi maganar yana kafeta da idanu hannayensa duka biyun cikin aljihun rigarsa.


Dariya ya bata,tadan juya ido cikin irin nuna mamakin nan,saidai hakan batasan mugun kyan da ya qara mata ba


"Uncle kace na girma fa?" Har tsakiyar zuciyarsa ta aike da saqo,bayason yayi saurin bada kai tun yanzun,tunda dai nan ba kaduna bace


"Yes.....amma ga jakarki nan,ki dauka sai mu gani" ya fada tsadajjen murmushin nan nasa yana fita daga fuskarsa.


"Uncle itama wannan din da nauyi don Allah....." Widad ta fada cikin shagwabar data saba yi masa


"Ya salam" ya fada yana miqa hannu hadi da dauke jakar,yayin da hafsat taji tana shirin faduwa,sai takai hannu tana neman abinda zata riqe gudun faduwa,hannunta ya sauka kan kyakkyawar luggage din widad guda daya da tayi saura sale bai dauke ba.


Hannunta ta janye,mamaki yana sake kasheta,gata kusa da wajen amma cikinsu ba wanda yama lura da wanzuwarta a wajen,wani tunani yazo mata,tayi qoqarin saita kanta ta hanyar yin gyaran murya kadan,abinda yasa duk suka waiwayo


"Sannu da zuwa,saukar yaushe?" Tayi maganar tana tsare gida hadi dayin kicin kicin da fuska,sannan ta miqa hannu tana son karbar jakar widad dake hannunsa a zuwan tasa ce


"Yanzu ne,ko kayanma ba'a gama daukewa ba"


"Fitar wuri kukayi kenan" ta sake fada tanason calling attention dinsa,sai ya dan gyada kai,abun nata nayau yana dan bashi mamaki


"Ina wuni" widad ta fada ba tare data dubi sashenta ba,haka kawai takejin wani abu mara dadi yana dan taba zuciyarta,taji kuma.ba zata iya gaidata yadda ta saba ba,sai hafsat din ta waiwaya tana kallonta,sai a lokacin ta sake ganinta sosai


"Oh..... amarya lafiya lau" can qasan ranta tana dan mamakin yanayin data gaisheta dashi,ba haka ta saba gaisheta ba dashi,ta saba ta gaisheta tana fara'a bayan ta rusuna mata,sa'an nan idan tayi kamar bata ji ba sai ta sake maimaitawa


"Ba jakata bace ta qanwarki ce" ya fada yana kulle motar sanda yaga tana nufar sashensa da jakar


"Oh, okay" ta fada tana dawowa baya inda widad ke tsaye da mimi,kai tsaye ta miqa mata jakar,don dama abinda takeso kenan ta karba kayarta.


Ba tare da nufin komai ba ta kalli abbas din a shagwabe


"Allah uncle da nauyi,kuma kace zaka kaimin fa"


"Bance na fasa ba ai" ya fada yana miqawa hafsat hannunsa,kamar sakarya ta sakar masa jakar,xallar mamaki yana cikata,ta bishi d kallo sanda yake cewa


"Muje na ajjiye miki"
Su ukun suka juya zuwa sassanta,mijinta..... diyarta ta bisu da kallo,me yake shirin faruwa ne wai?,ko kuma tace meye ne ya farun?.


Kamar wadda aka tsikara saita kasa tsaiwa,ta daga qafarta da hanzari tabi bayansu,ta cimmasu ya karba keys din ya saka yana bude mata qofar sassan nata,sai ya waiwayo yana duban hafsat din da tayi tsaye a bayansu,ta kasa ta tsare tana dubansu,ya dauke kai ya qarasa buda qofar ya matsa mata gefe ta sanya kai ta shige ita da mimi da suketa surutunsu ko a jikinsu.


Cikin falon ya ajjiye mata jakar,sannan ya juya ya fice daga falon yana tsokanar mimi,a sannan hafsat din tana qifar parlor din bata shigo ba,saidai tana jin zuciyarta na mata wani iri,ta kasa tuna komai bare tayi tunanin me ya kamata tayi,jikinta yayi mugun sanyi,zuciyarta kuma tana bata akwai wani abu.


Kallonta ya sakeyi sanda ya fito,tana tsaye qyam kamar wadda aka bawa gadin qofar falon,yadan kalleta sai kuma ya wuce,ta taka ta bishi a baya,zuciyarta kamar sata fito daga qirjinta,tanason masa qorafi to amma kuma tace masa meye?,haka taci gaba da binsa a baya har zuwa sashen nasa.


Sanda ya bude waiwayowa yayi yana kallonta,qura fal sashen,wannan abu yana masa ciwo,baisan sai yaushe zai fara dawowa yana samun sassan nasa a tsaftace ba,suna hada ido ta kauda kai,tasan qorafi yakeson yi,amma ba zata bashi dama ba,zata gyara tunda ga widad tazo,wasu ayyukan zasu ragan mata ai,sai ta karba jakarsa ta wuce bedroom dinsa da ita.


*_BAYAN AWA BIYU_*


Yana zaune saman kujera take gyaran falon,tana aikin tana gyara daurin zaninta dake kwancewa,fuskarta sam babu walwala,tunani ne cunkushe fal a ranta.


Nawwara na zaune saman doguwar kujerar da yake kai,yanata bare mata chocolate tana sha tana masa surutu,lokaci bayan lokaci yakan daga kai ya dubeta,tun daga tsefaffen gashinta da yayi cibiri cibiri har zuwa qafafunta dake cike da kaushi,babu digo lalle ko kadan bare su samu arziqin suturta kaushin qafartata,brassiere dinta ta saki sosai,don kana iya hangota ta gadon bayanta.


Ya lumshe idon takaici yana cikashi,duk wani abu da diya mace zaga gyara a jikinta ya bada sha'awa hafsat din ta kauda shi da kanta da mugun qazanta da rashin sanin ciwon kanta,tattausan qshin widad ya tuna,babu sanda zata giftashi bakaji tashinsa ba daga jikinta,sabanin hafsat din da saidai yaji wani na daban bawai qamshi ba.


Ta gama gyaran tana jin tayi wani gagarumin aikin azo a gani,gaba daya qugunta har ya riqe,saita taka zuwa qofar fita,tanason kiran widad din tazo ta gyara mata kitchen hade da kayan miya zata dora girki,sannan ta kama sauran gyaran falonta zuwa sassan part din nata


"Zo mana" ya kira hafsat din yana sauke lallausar qafarsa a qasa tsigar jikinsa nadan xubawa,haka kawai yake ji gyaran data yiwa sassan nasa bai gamsar dashi ba,saboda ya riga ya saba.....muddin widad din tayi gyara to sai ka rantse da Allah wani engine akasa aka kauda qazantar waje.


Dan jim tayi don ta qagu ta kira yarinyar,tanason jin abubuwa da yawa daga bakinta ko zata samu haske kan zarginta,amma ganin ya kafeta da idanu yasa ta kasa bashi uzurin cewa tana zuwa din,ta juyo ta dawo ta samu waje ta zauna


"Meye da meye a kayan amfaninki ya qare?" Ya tambayeta yana hada hankalinsa sosai a kanta with seriousness,don shikam Allah ya sani,bayason ya zalunceta,amma muddin za'a ci gaba da tafiya a haka komai zai iya faruwa,zuciyarsa zata gaza daurewa hada waje da ita.


Sosai ta kalleshi,saita girgiza kai


"Babu komai" shuru yadanyi yana jinjina amsarta,sai ya miqe ya kama hannun nawwara


"Ban yarda ba,muje na gani", kamar zata fasa kuka haka ta miqe,shigarsa sassanta tasan ba abinda zai dadeta dashi wani bacin rai,bata da damar musu,haka ta miqe tabi bayansa.


Suna fitowa daga sashen sukaci karo da wata iska mai qamshi dake kadawa dukka ilahirin harabar gidan,yaja iskar sosai cikin hunhunsa ya fesar,a wajen mutum daya yakejin wannan qamshin,kuma ko yanzun ya tabbatar yana fitowa ne daga sassanta,kewarta yaji ta saukar masa,tamkar sun dauki wani lokaci mai tsaho ne basu tare,yayin da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login