Showing 117001 words to 120000 words out of 196911 words
Chapter 40 - A RUBUCE TA KE book 1 Completed Huguma .txt
Koda aka tashi daya daga cikin qawayenta ta bata ajiyar hausa novels
"Ki ajjiyemin don allah widad,yayana yazo gutu,doke sai ya koma zan karba,hanani karatun yakeyi,kada yaje garin bincike bincike ya ganosu na shiga uku" a karba din ta tafi dasu gida,da daddare ta buda jakarta bayan ta gama wani assignment zata maida jakar don kada ta manta idanunta suka gano mata litattafan,saita jawosu ta buda tana kallo tare da mamakin meye a ciki da za'a hanata karabtawa,don ita kallon normal kowanne littafi take masa,taji sha'awar duba meye a ciki,ta dauki daya part one ta buda ta fara karantawa.
Ko page daya bata dauka da niyyar karantawa ba,sannu sannu sai gashi har tajai page na wajen biyar,ta saki murmushi saboda labarin yaja hankalinta,saita kife littafin,ta wuce kitchen ta zuba abinci ta dawo taci gaba da dubawa.
Sannu a hankali sai gashi ta raba dare tana karatun,sam batasan dare yayi haka ba,don hatta da wayarta ta manta da ita,taje ta samu miscall na abbas kuwa harda sms guda daya,dare yayi don haka bata kirashi ba,sai tayi addu'a ta kwanta,amma kuma bacci ya qauracewa idanunta,tanata bitar abinda ta karanta din cikin kwanyarta,da gaske akwai soyayya irin haka?,soyayyar jaruman littafin ya tafi da ita,ta dinga kwantanta kanta dasu,kunya ta kamata ita akdai cikin dakin,saita kifa kai tana murmushi.
Washegari babu makaranta good friday ce,wuni tayi tana karatun,wanda a ranar ta gama da part 02 ta shiga 03,sai data qare littafin a ranar ma sannan ta kwanta,nan dinma dai dukka labarin ta dinga tunawa,yadda jarumar ke gudanar da rayuwarta
"Kamar ni da uncle kenan?" Ta ayyana a ranta,da sauri ta girgiza kai,kai anya?,ita kanta wasu abunuwan cikin labarin kunya suka dinga bata,first night dinsu ya dawo mata a rai,sai tsoro ya shigeta,itama wataran haka uncle din nata zaiyi mata?,amma wannan ai iskanci ne,to amma dama akwai ranar da wannan abun zai tashi daga sunan iskanci?,ta tuna haihuwar da jarumar tayi,suna nufin kowacce mace ta haka take haihuwa?.
A daren qwaqwalwa da tunanin yarinya kala kala ta dinga yi,abubuwa da yawa ta watsar dasu tana ganin bazai yiwu ba,ta rungumi abubuwa da yawa da syka dinga burgeta,har ta dinga kwantata gwadawa.
Da safe kuwa ta gwada abunuwa da yawa da ta karanta din,duk da tana wasu qarawa tayi,ta gama komai ta hada breakfast dai dai cikinta,din me tayata kwana gari na wayewa take komawa cikun gida tayi ayyukanta,bata dawowa sai wani daren,ko idan bata da abinda zatayi ta leqota su gaisa sannan ta koma,mayar mai gadin gidan ce,tana da matuqar kirki sosai.
Tana cikin yin breakfast taji sha'awar kiransa kamar yadda taji jarumar littafin tana yi,gabanta ya dinga faduwa sabida rashin sabo,ta dinga jin tsoro tana ganin kamar ba wani abun burgewa bane,saidai duk da haka bata fasa kira ba.
Lokacin ya shiga wanka,hafsat na zaune daga gefan gadon nasa tana dakon fitowarsa,da sauri kamar wadda aka kirayi wayarta ta dauki wayar tana duba mai kiran
"Weedad" ta maimaita sunan data gani a rubucen cike da mamaki,kanta ya daure da kyau,ita dince ke kiran ko kuma dai idanunta ne,ko wata ce mai irin sunan,saita daga kawai kai tsaye.
Shagwababbiyar muryarta data zame mata jiki,ta kuma saba magana da ita,da ita tayi sallama
"Ke tsaya" hafsat ta fada da sauri dai dai sanda take ficewa a bedroom din don kada ma ya jiyota.
Wani mugun faduwa gaban widad yayi jin muryar mommy hafsa
"Ina kwana mommy"
"Da ban kwana na zaki jini?,wa ya sakaki kiransa ko shi din sa'anki ne?" Mamaki ya bayyana a fuskar widad din,ta dauka ba komai,ta dauka momy din zata ce ta kyauta,saita kasa gane yadda abun yake
"Kiransa nayi mu gaisa mommy,jiya ya kirani ban dauka ba" tashin hankali!!, Ta fada a ranta tana jin yadda fuskarta ta dauki wani irin zafi,zazzafan kishinta da taketa qoqarin dannewa ya taso mata
"Yanzu ke har kisan ki kira d'a namiji kusan sa'an babban wanki koma babanki,ashe baki da kunya kwata kwata,to ba sa'anki bane,idan kika sake kiransa ko kuma ya sake kiranki kika daga saina miki mugun duka,ke bakya tsoron abinda zai sameki?,na gaya miki ba'a sakar musu fuska ko jiki,so kike yayi miki ciki ki mutu ko?" Karon farko taji maganar mommy hafsa din banbarakwai,sai taji kanta ya kulle
"Karna sake ji kuma kada na sake gani,kina jina?" Ta tambayeta a tsawace
"Tom" ta amsa mata jiki a sanyaye,sai hafsat din ta katae wayar tana jan tsaki,taso yarinyar na gabanta,amma bari ya fita,zata sake kiranta ta sake jadda da mata.
Jiki a sanyaye ta ajjiye wayar, kwanyarta ta shiga rububin lissafin maganganun hafsat din,zuciyarta taqi amincewa da hakan jikinta yaqi karba kuma ranta yaqi gamsuwa,saboda aduk abubuwan data karanta bataga ta inda aka nuna abune mara kyau ba da har mommy hafsat din zata dinga mata fada haka ba,kusan minti goma ta kasa samun nutsuwa,sai tunani yazo mata,sai kawai ta kira anty deena tace bari ta tambayeta.
KI KULANI miss xoxo
DAUDAR GORA Billynabdul
RUMBUN K'AYA hafsat rano
IDON NERA Mamuhghee
A RUBUCE TAKE huguma
_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_
_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_
0022419171
Maryam sani
Access bank
Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070
*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261
*Al'ummar nijerπ³πͺπ³πͺπ³πͺ zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63
*Thanks for choosing us*π₯π₯π₯π₯π₯π₯[3/13, 12:54 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:huguma*
Page 61
Kiran farko aka gaya mata user busy,tadan dakata na wasu mintuna sannan ta qara kiranta,cikin sa'a kuwa ta shiga
"Aah,kaga amaren kaduna" anty deena ta fada cikin tsokana,da yake idan taso tsokanarta haka take ce mata,dariya ta danyi ta gaidata tambayarta yaranta,ta amsa mata da suna lafiya,suka dan taba hirar data shafi gda sannan daga bisani shuru ya biyo baya,sai anty deena dince tace
"Kina bibiyar kuwa karatun da ake a groups din nan,kinsan kudi na biya kada ki sakani nayi asarar kudina" dariya ta danyi
"Inabi Allah anty,a ciki ma naga wani abu,nayi kuma to mommy hafsa tanata fada,nace anty ko banyi dai dai bane?" Ta qarasa fada a shagwabe
"Me kikayi kuma?" Antu deena ta tambayeta,bata boye mata ba ta gaya mata komai,anty deena tayi shuru tana nazarin maganar cikin ranta,zuciyarta na hasaso mata wani abu,amma kuma nataso ta dora nata tunajun ko tunanun yarinyar akan hakan,tunda dukka dan adam ajizine,zai yiwu ajizanci ne da kuma yanayi ma kishi da zai iya motsawa kowacce mace a kowanne lokaci
"Bakiyi abu mara kyau ba widadun ummu..."
"Ba wani widad din ummu yanzun fa anty deena ta daina sona,su Aafiya tafiso,kullun mukayi waya sai tace zatazo amma taqi zuwa" murmushi ya kubce mata
"Zatazo weedad,kullum ummu cikin zancanki take,amma kafin sannan.....inaso kome kika gani ance ayi kiyi qoqarin yinsa,zaki yi?" Ta tambayeta,saita gyada kai
"Eh anty deena"
"Yauwa widad dinmu,sannan ko meye kika gani baki gane ba ko ya faru ki kirani,koni ko anty madeena ki tambayemu,ba komai ne idan mommy hafsa tace kiyiwa uncle din naki zaki dinga yi ba kinji ko?"
"Tom anty deena" sun dan jima suna waya tana sake wayar mata da kai a fakaice sannan sukayi sallama,koda suka gama wayar litattafan ta debo ta sake zabo wasu a ciki ta dora da karatunta,itama tama manta d batun mommy hafsa da duk matsalolinta.
Rai bace hafsat din ta goge kiran da widad din tayi masa,sannan ta koma dakin ta maida wayar ta ajjiye ta kamar yadda ta ganta taci gaba da zaman jiransa,amma kuna qasan ranta a quntace yake da abinda ya farun,tana zargi da kuma tuhumar kanta,kwana biyu ta watsar da kiran yarinyar bare taci gaba da saita mata hanya,amma fa tana tsoro,kada ya zamana ta hadu da gogaggu kima wayayyun da zasuyi mata karatun da yafi nata shiga,tunda kaduna badai hadakar gamayyar mutane daga gari da qabila kala daban daban ba,amma zata kira ta binciki hajiya amina taji dawa dawa take hulda.
Koda ya fito daga wankan baisan anyi kiranshi ba,saboda qarar shower ta hanashi jin ringtone din,yana goge ruwan jikinsa tana binsa da kallo,jikinsa luwai luwai, fatarsa mai santsi da taushi sai daukar idanu takeyi, muscles din a hade alamun ya samu kyakkyawan training,ta hadiye wani abu da qyar saboda kishinsa daya tsarga mata.
Waiwayawa yayi suka hada idanu da ita,saiya dauke kansa yana cewa
"Ya akayi?,me yake faruwa?" Qaqalo murmushi tayi sannan tace
"Har yanzu banji kace na fara hada kayana ba"
"Zuwa ina?" Yayi mata tambayar bayan ya isa gaban madubi yaja lotion dinsa zai fara shafawa,wani abu ya tsarga mata amma ta dake
"Umara mana" sai daya kalleta ya kuma ci gaba da shafa mansa sannan yace
"Ban shirya wannan zuwan dake ba,babu kudi a hannuna,ina cewa ma ko wata shida bamuyi da zuwa ba ko?"
"Eh amma ai musulmi baya gajiya da zuwa" kai ya gyada
"Haka ne,amma yanxun bani da kudin da xamu iya tafiya mu duka,ke ni da hajiya" ranta ya baci sosai, zuciyarta tayita qissimata mata abubuwa da yawa da zata gaya masa,a fakaice dai hajiyan kusan duk shekara saiya kaita kenan,tunda itama ai baara iwar haka taje
"Aure ya cinye maka kudin kenan?" Ta tambayeshi tana tsareshi da ido,ya sake waiwayowa ya kalleta,ya kuma karanci yanayinta cikin sakanni,sai ya kuma dauke kansa ya maida ga abinda yakeyi,bayason doguwar magana,hakanan baya qaunar mita da qorafi
"Idanma hakanne ba mamaki bane" tofa,baki yasan me zai fada amma baisan me za'a mayar masa ba,saita miqe a mugun fusace
"Allah yayi mana arziqin da zamuyi ta zuwa babu mai hanamu" sai tayi waje fuuuu kamar zata tada iska.
Ransa ya sosu,amma ko iskar data kwasota bai kalla ba,yaci gaba da shirinsa,kafin ya sanya kayansa ya tsaya ya tsaftace sassansa,ya kuma dafa coffee yasha sannan ya qarasa shiryawa ya fice abinsa,yasan bazai rasa abinci gidan hajiya ba.
Tun daga wannan maganar ta dauke masa wuta gaba daya,shima kuma ya tattarata ya watsar ya baiwa banza ajiyarsa,yana ganin guga koda baiyi tsiran komai ba yayi na igiya,ta yaya zatayi kishi da mahaifiyarsa ko nawa kuwa zai kashe mata?,ita din ai ba tsararta bace.
Duka kwanakin da yayi kowa sabgarsa yake,amma hafsa din ta fishi damuwa,saboda tana da buqatar kudi a wajensa,baya ga haka tanason ya dawo da widad din har su dawo daga tafiyar,a wata dayan da zasuyi tasan zata moreta sosai,zata kuma dora mata karatun da zai zauna daram a kwanyarta,amma girman kai da jin tafi qarfin tayi qasa yasa taji gwara tayi shuru duk abinda ma ya yanke shikenan.
Ta bangaren widad kuwa cikin kwanaki qalilan karatun hausa novels ya shigeta sosai,idan tana karantawa tana jinta ne kamar a wata duniyar ta daban,yana debe mata kewa,tana kuma ganin abubuwan da suke bata mamaki,duk kuwa girki ko drinks din data gani saita gwada,a lokacin kitchen dinta yaga rayuwa,saidai duk abinda ta gwada din idan taga yayi farinciki cikata yakeyi,mai aikin maama(hajiya amina) ke tayata wani bin,tana ganinta kamar latifa saboda kirkinta.
Ranar da zai baro kadunan zai biya ta gidan hajiya ya daukota su wuce,har ya kammala shirinsa tsaf a sassansa tana nata sashen tana baccinta,don tun daga waccan ranar basu qara hada makwanci ba,tana sashenta yana nasa,yaci alwashin ko meye zatayi badai shi da qafafunsa ya bita yayi begging nata ba,yasan abinda takeso kenan.
Tare dasu mimi suka fito,a wajensa yaran suka kwana,tsaf dasu don su kansu sai daya shiryasu ya kuma gyara sasssan,suna riqe da hannunsa ya tura ya shiga,falon a hargitse kamar wanda aka tashi taron biki,harsa pampers din nawwara da yayi imanin idan bana shekaran jiya bane na jiya ne
"Ku zauna nayi sallama da mamanku" ya fada yana kallonsu,sai suka amsa suna hayewa saman kujerar,ya ajjiye luggage dinsa ya nufi qofar bedroom dinta,don ko takalminsa bai fidda ba saboda tsaftar tiles din ma bata gamsheshi ba,duka yayi rod'i rod'i kamar an watsar da ruwan tea ya fara bushewa samansa.
Sau uku yana knocking sannan yaji ana tambayar waye da cunkusashiyar muryar bacci,gyaran murya kawai yayi,ta taso tana turbune fuskarta daya kacame saboda bacci ta buda qofar.
Ido hudu sukayi, doguwar rigar wata kodaddiyar atamfa ce a jikinta da aka yiwa adon net,net din har ya soma bubbulewa alamun dake nuna ya fara gajiya da aikinsa,kanta gashinta ne him daya hautsine kamar ciyawar da aka tara za'a ciyar da dabbobi,abinka da baqar fata idan bai shafa mai ba....duk jikinta yayi fari fari,dakin yana fidda irin abinda jikinta ke fiddawa,da alama ya kama ko ina.
Kansa ya dauke,don takaicinta bazai kasheshi ba,ya fara gajiya da al'amuranta da kullum babu gyara sai gaba da abun yakeyi,ya sanya kai cikin dakin,dole ta kauce masa ya rabe ya shige,sai ya kasa zama,yana kallonta ta tsince pant dinta da bra dake watse a qasa
"Ina kwana?" Ta gaisheshi murya a cushe
"Lafiya....mu zamu wuce" ya bata saqo a gaggauce,saboda qagauta da yayi da wanzuwarsa cikin dakin,ya zura hannunsa a aljihu ya fiddo rafa na kudi ya matsa gefanta ya ajjiye mata yana cewa
"jibi zamu tashi,zamuyi sati uku idan ta kama har hudu ma,saboda inaso zamu tsaya egypt hajiya zataga likita,duk yadda ta kama dai....shikenan babu wani abu?" sai a sannan ta dago ta sake kallon sa
"Daa ka sani ma baka shigo ba,inda wucewarka kayi da hakan yafi" tsareta yayi da idanunsa yana mamakin furucinta
"Hafsa.....magana nake miki ta zanyi tafiyar da babu lallai na sake dawowa fa" gaba tayi tana qoqarin komawa cikin bargonta
"Allah ki yaye hanya" ta fada cikin nuna halin ko in kula taja bargo ta rufa abinta,saidai tuni idanunta sun cika da hawaye,banda qin Allah,da kudin da zataga likitan basai ta haqura ba a biya musu tare,idan suka dawo taga likitan a nan ba,ai duka daya ne,to amma a'ah,wai dole sai an nuna maka iyakarka.
Sai daya bata kusan mintuna a tsaye yana kallonta ta cikin bargon,zuciya na hasalashi amma ya hadiye ya juya a hankali ya soma fice daga dakin.
Wuf tayi ta yaye rufar ta kuma sauko daga gadon,da gudu tasha gabansa
"Au tafiyar zakayi?" Ta fada hawaye yana layi kan fuskarta,kallo daya yayi mata ya kauda kansa,saboda yadda zuciyarsa ke azalzalarsa
"Tun ba yau ba nasan baka damu da damuwata ba dama,ba abinda ya shafeka da baqinciki na ko walwalata,to kaje,amma ka sani akwai hisabi tsakanina dakai,Allah bazai taba yafe maka ba idan ka zalunceni" ido ya runtse yana jin zafin maganganunta,ya budesu a hankali sai suka kan yaransu,mimi da nawwara suna tsaye daga bayanta sunyi carko carko,da alama sun fahimci wani abune mara dadi yake faruwa.
Maganganu ne da yawa a ransa da amsoshin da zai bata,amma sai ya hadiye,muryarsa a sarqe yace
"Naji,Allah ya saka mikin,matsa ki bani hanya" jagale tayi tana kallonsa,sai kuma ta saki qofar ta koma ciki da gudu ta fada gado tana sakin kuka,baiko waiwayeta ba ya matsa zuwa gaba,ya sunkuya yayi kissing goshin yaran sannan ya kama hannunsu zuwa falo ya kunna musu cartoon yayi musu dabara ya fice.
Har suka kama hanyar kaduna ransa a bace yake amma yaketa dannewa saboda kada hajiya ta fahimta,yasan yanzu zata gaza nutsuwa.
Sai da suka shiga garin kaduna sannan ya fara tunanin yadda zasu samu widad ita kuma,abinci da zasuci da sauransu,yau dai ba makaranta yasan tana gida,to amma abinci bashi da tabbacin zasu samu,tunda ga wadda a haife ta haifeta ma bata da wannan tunanin,ina ga ita?,ya yanke kawai idan sun isa yana kai hajiya ciki ya koma ya siya musu abinda zasuci ya hada musu da order din abincin dare,gobe kuma ya samu time yayi musu,da wannan tunanin suka shiga unguwarsu.
[3/13, 12:54 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:huguma*
Page 62
Tun jiya da ya kirata yace mata gobe zasu taho da hajiya,tayi murna sosai saboda zaman kadaicin ya isheta amma bata kawo wai ta tanadi komai ba,ta dauki littafinta taci gaba da karatunta,tana tsaka da karatun taga inda jarumar littafin ke shirye shiryen dawowar mijinta daga tafiya,abun sai ya burgeta sosai,ta idar da sallah azahar tana saman abun sallah abun ya sake fado mata,saita dauki wayarta ta kira anty deena tana labarta mata
"Kema irin hakan zakiyi, bakiga abincin da aka kiya jiya ba a group?" Kai ta gyada
"To haka zakiyi,ki shirya shi kamar yadda aka koyar ana shirya abincin mutum" daga kan abun sallar kuwa bata koma yin komai ba ta fara practicing abincin,datayi kuma yayi mata yadda takeso,suna da komai ba abinda zata buqata,saita fara shirya komai tun a ranar.
Washegari gari yana yin haske ta gyara gidan,dama ta saba wannan ya fara zame mata jiki,saidai yau har dakinsa ta gyara kamar yadda anty deena tace mata,tana yi tana kiran anty deena ita kuma tana qara mata haske,tana aikin suna video call da anty deena ta watsapp,sannu sannan sai gashi har girkin ta gamashi tsaf,ta kuma zuba a warmer,ta jera,anty deena ta kalla ta cikin wayar,cikin farinciki tace
"Well done qanwata,yanzu saura abu daya"