Showing 174001 words to 177000 words out of 196911 words

Chapter 59 - A RUBUCE TA KE book 1 Completed Huguma .txt

daya ya dage mata tare da kashe mata ido,abun ya bata kunya sosai,sai ta rufe fuskarta da hannuwanta tana dariya,shima ya tayata dariyar idanunsa na kallon titi.


Ko wanka bata tsaya yi ba,saboda tana ganin kamar zai bata mata lokaci ne kawai,ta canza kaya ta canzawa nawwara pampers,ta kada kan yaran ta zubasu a motarta suka wuce gidansu.


Kallonta kawai mamanta takeyi sanda take gaya mata duk irin abubuwan da suke faruwa


"Amma su uwa sun ha'inceni,keda duk da wadan nan matsalolin cikin gidanki amma kike zaune haka kina amfani da gurguwar shawarar ummee?,don ta kai mata ke lallai ne takai mikin?,bari na kira hajiya shuwa naji wanne malamin zata hadaki dashi" ta cire wayarta dake kusa da ita a chargy ta soma neman number din.


Kamar hafsat tace abarsa,duk ds yadda matsalar take damunta,amma dai sai ta kanne tana sauraren mamar tata sanda suke gaisawa da hajiya shuwa din.


Tana zaune tana sauraren umman nata tana yiwa hajiya shuwa bayani,bayan ta gama suka shiga tattanawa,kusan minti talatin sannan sukayi sallama,ta dubi hafsat


"Baki da wata matsala,itama kanta fadan zaman da kikeyi takeyi,tace yanzu ai ba'a zama,kada kiga wai yarinya qarama,idan batayi ba magabatanta zasuyi mata,bare sadakar yalla?,ai sai addu'a kawai,shu'umai ne" kai ta jinjina tana jin abun yana damunta har cikin zuciyarta


"Yanzu kudi kawai zaki fito dasu,sai mu saka rana mu sameta,tunda baya gari ma komai zaizo da sauqi"


"Kudi kaman nawa?" Ta tambaya tana duban umman nata


"Daga dai dubu dari zuwa sama"


"Za'a kaiwa malamin?" Hafsat ta tambaya tana dan riqe da habarta


"Eh,har miliyoyi ma ai kashewa akeyi,ita ranar biyan buqata rai ai ba'a bakin komai yake ba" janye hannunta tayi tana gyara zamanta,itakam bata jin ko naira dubu goma zata iya fitarwa,kudin da take fadi tashin tarawa rana daya ta wafci wani abun a ciki ta fara kaiwa wani suna raba dai dai,koma ya fita ci


"Shikenan umma,ki bari idan na shirya sai ayi mata magana sai muje" wani kallo uwar ta watsa mata,dama tuni labarin yadda ta baci da son abun duniya yake zuwa mata


"Kudin ne ba zaki iya fitarwa ba kenan?,ko a jikinsa ba zaki tarasu ba hafsatu?,gwara ki zauna da damuwarki kenan?" Kai ta girgiza


"Ni ba haka bane umma,kawai dai matsalar batayi girman da zan kashe wadan nan kudaden ba,mu bari kawai anty ummee din tazo nasan tabbas akwai mafita daga wajenta,basai an kashe komai ba" haushi takaici da baqinciki suka cika umman,saita dauke kanta gefe tana cewa


"To ai shikenan,sai kici gaba da zama har sai sanda matsalar ta girmama ta zama babbar".


***********Tunda suka koma ta tattara ta watsar da batun mommy hafsat din ta shiga sabgoginta,sosai ta maida hankalinta ga karatunta koyon girke girke online da kuma practical classes da akeyi cikin garin kadunan.


Cikin lokaci qalilan ta zama expert,hannunta ya sake fadawa,ta kuma qware da kalolin abinci masu dama.


Zamu iya cewa batason so ba,amma tana jin wani abu mai qarfi akan uncle din nata,wanda inda da cikakken wayo kai tsaye zata fahimci soyayyarsa ce ta fara kafa kanta a zuciyarta,sam bata iya wuni guda cikin nutsuwarta muddin baga ganshi ba,kowanne lokaci burinta shine tayi abinda zaice


"That's my baby.....ma sha Allah baby wannan yayi......baby doll inason abu kaza,babyn uncle wannan yayi dadi ko yayi kyau" wannan ya sanya ta sake zagewa da dukan iyawarta ta haddace abinda tasan yafiso yafi muradi,gefe guda anty deena da anty madeena harda hajja sun zage sosai suna wayar mata da kai dai dai gwargwado.


Ta gefan abbas kuwa abun har baya faduwa,wani irin wawan kamu soyayyar widad tayi masa,ta yadda shi kansa yake mamakin kansa,zuciyarsa ta koma sabuwa,tamkar bai taba qaunar wata halitta ba cikin rayuwarsa,yarinyar ta tafi da dukka zuciyarsa,ta kuma shiga rayuwarsa fiye da kima,har bayason wani abu da zai kawo su nisanci juna,duk da yana fama da shagwabrta sakalci da kuma wauta amma hakan sai ya zame masa kamar wani abun debe kewa,ya kuma zame mata ado,kasancewar bai saba ganin wannan ba.


A koda yaushe hafsatun na masa magana ne a tsaitsaye,tana kuma nuna masa ita din me wayo ce,bata da lokacin shagwaba ko karya murya,kamar yadda take ganin bai kamata ace mutum yana da wani choice a rayuwarsa ba na tsafta abinci turare sutura da sauransu ba,banbancin ra'ayi me girma da kuma tarin yawa ne a tsakaninsu.


Sabanin widad,da komai nata nashi ne,komai zatayi tana duba zai burge uncle?, uncle zaiji dadi?,hatta da shopping tana yinsa ne base on his choice,komai ta dauka saita tambaya cikin shagwabar nan tata


"Uncle yayi?" Wani lokaci yace baiyi ba,wani lokaci kuma ya barta da zabinta,ya zuwa yanzu bayajin akwai wani abu da zai iya shiga tsakaninsa da widad din,ta shiga rayuwarsa fiye da kima,ta samu gurbi a zuciyarsa sama da yadda kowa yake hange.


Tun daga wancan ranar ta rage binsa weeknd bauchi kwata kwata,koda ta bishi ma raba kwanan take tsakanin gidan hajiyan da kuma gidansu,dukkansu shi da hajiyan da suka fuskanci hakan yafi samar mata da nutsuwa sai suka rabu da ita.


Hafsat na gama kwananta baya iya jurewa,haka zai je gidan hajiyan da kansa yayita raragefen daukarta saboda kunyar hajiyan,abinka da uwa,takan bishi da murmushi ne kawai sannan ta sanya widad din shiryawa ta kuma bishi,a yanzun duk duniya tafi kowa samun farincikin canjin da abbas din ya samu,idan ka kalleshi da kyau zaka fahimci hakan,don har wata murjewa yayi,yayi 'yar qiba,ba shakka ko ta iya fannin abinci kawai dole rayuwarsa ta sauya,saboda shi din mutum ne da baya wasa da cikinsa,sai Allah yasa widad din bata da wani fatinciki itin ta ganta cikin kitchen tana sarrafa wani sabon abu da basu saba ci ko basu taba ci ba,koda yaushe hajiyan godewa Allah takeyi da sauyin da abbas din ya samu,nutsuwa sosai tazo masa,duka matsalolin hafsat ma sai suka rahe damunsa,tunda ko ba komai akeai gefen da yake samun nutsuwa gamsuwa da kwanciyar hankali,inda widad din yakeso takai wanda bata qarasa kaiwa ba yanata qoqarin horar da abarsa cikin soyyaya qauna kulawa da kuma nutsuwa.


Gefe daya hafsat din itama bata sake tayar da zancan ba,saboda anty ummee ta kwabeta kan ta barta haka,kada a fahimci takunta,saidai akwai sabbin hanyoyin da zasu sake dubawa.


_wannan kenan_


*Masu karatu muje zuwa,akwai sinqi sinqin CAKWAKIYA a gaba*[3/20, 8:54 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*


*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*


Page 91


Sassanyan qamshi parlor din yake fitarwa baya ga wani kwantaccen yanayi da duk wanda ya shigo ciki sai ya burgeshi,awa guda kenan da gama dukka aikinta,ta kuma shirya kanta cikin wata gown ta yadin chiffon mai qaramin hannu,plain ne black babu digo ko adon komai a jiki,ta matse gashinta da jiyan abbas ya kaita da yammaci aka gyara mata shi,yana daya daga cikin abinda yakeso,shi yasa shima yake bashi kulawa har fiye da yadda ita ke kula da sumartata,duk sanda take kwance a jikinsa zaka samu hannunsa saman kanta yana yamutsa sumartata mai tsaho da santsi,abinda yake yawan haifar mata da kasala,saita lafe a jikinsa.


Hankalinta ya dauku ga wayarta sosai,tana karanta wani hausa novel mai suna HANGEN DALA,labarin ya tafi sosai da hankalinta,ya kuma fara ankarar da ita matsayin hafsat a wajenta.


Ya dauki mintuna kusan uku tsaye a bakin qofar yana qare mata kallo ba tare data sani ba,hancinsa kuma yana shaqar daddadar iskar da parlor din yake fitarwa.


Tayi masa wani mugu mugun kyau,cikin kwanakin gaba daya wani kyau take qarawa,ga wani irin fari data sakeyi kamar ka sanya hannu jini ya fito,ta kuma qara qibar data sakata murjewa,alamun hankali da girma sun fara nunawa a jikinta,qibar tayi mata wani irin kyau dake dimauta masa tunani,shi kansa wani lokaci yakan tuhumi kansa


"Abbas anya baka zauce akan yarinyar nan ba?" Bai sani ba ko zaucewar yayi,amma shi kansa yasan yana mata wani irin so da bazai misaltu ba,baya gajiya da kallonta,baya gajiya da ganin shirmenta,baya gajiya da sauraren hirarta,ko ba komai zai samu nishadi irin wanda duk duniya idan ba wajenta ba babu wajen wanda yake samunsa.


Yaga alamun hankalinta yayi nisa sosai,don haka ya sanya qafarsa cikin tattausar muryarsa yayi mata sallama,suna hada ido ta miqe da sauri bayan ta watsar da wayar gefe,ta kuma tako da sassarfa yadda ta saba yi masa ta dane shi,ya sanya dukka hannayensa ya tarbeta,ya kuma dauke abarsa cak ya aza a jikinsa yana aika mata kisses ta ko ina,laushin fatarta da qamshinta kamar zai zautashi.


Kamar ko yaushe ta sunne kanta tana jin kunyarsa,ya saki qawataccen murmushi yana shiga cikin falon sosai da ita hadi da cewa


"Gayamin.....me zanyi na qarasa cire kunyar nan baby......tana qwarata wani lokacin fa" ya fada murya qasa qasa kamar su da wani ne a falon,saita sakar masa murmushi tana shigewa jikinsa.


A hakan yana dauke da ita suka shige bedroom dinsa tana masa sannu da zuwa


"Yau anyi zafi,wanka zan fara yi baby,ba wani abinci yau" dariya ta sakar masa,sannan ta wantsalo daga hannuwansa zuwa qasa,ya tareta da sauri yana cewa


"Yi a hankali,wai bakiga kin fara zama 'yar lukuta ba?,inajin na kusa fara kasa daukarki" baya taja tana bata fuska


"Ka kusa daina daukata kuma uncle?" Ta fadi tana bubbuga qafa a shagwabe,yasan yanzun zai ballowa kansa ruwa,sai yayi saurin yin kwana


"Wasa nake miki fa babyn uncle.....amma fa wait.... seriously kin fara zama 'yar lukuta,ban yarda ba akwai abinda yake faruwa,me kike ci bakya sanmin?" Siririyar dariya ta saki


"Uncle ka fini ci fa,saidai wanda nake ci da daddare kana bacci" kai ya gyada yana dariya


"Harda rabona kike ci ai,kuma ban bayar ba,saina fanshe abuna,zo nan" ya fada yana takawa gabanta idanunsa a narke a kanta,ta saki dariya taa fadawa toilet da gudu.


Tsayawa yayi ya bita da kallo har ta shige,qugunta ya bude sosai,qirjinta ya fara cika irin yadda yakeso,abinda yake sake dimautar dashi a kanta koda yaushe,saidai har yau 'yar shagwabar tasa kukan amarci takeyi bata daina ba,hakan baya damunsa,hakan ma burgeshi yakeyi,ya zauna ya lallashi kayarsa.


Gaban mudubi ya taka ya zuge jakar daya shigo da ita yana duba takaddun daya shigo dasu,ya sake sakin murmushi yana tunanin irin yadda zataji idan ya gaya mata komai na tafiyar ta saudiyya ya kammala,yana tsaka da dubawar kuwa ta fito tana goge ruwan hannunta da qaramin towel


"Uncle ka shiga na hada" ajjiye su yayi,ya matsa zuwa gabanta,a tausashe ya kamo qugunta ya hade da nashi yana duban qwayar idanunta,itama shi take kallo,tana samun kanta cikin wani irin yanayi a duk sanda irin hakan zata faru,tana ji da ganin wani abu na musamamn cikin idanuwansa


"Amma dai na gaya miki,indai kina yin wankanki bakya jirana,zaki dinga wanka biyu ko?" Fuska ta narke masa sannan ta turo masa dan qaramin bakinta


"Uncle saina zauna ka dawo kaga qazantata?" Bin siraram lips dinta daketa qyallin lip gloss yayi da kallo tsigar jikinsa na zubawa,sannan ya dauke ya maidasu cikin manya kuma fararen idanuwanta,har cikin zuciya da ruhinsa yana yaba mata,yadda bata qaunar ya ganta ba wanka,naturally haka take,sometimes kafin ya dawo daga salla tayi wankanta


"Okay,tunda haka ne zaki biya ladan qin jin maganar uncle" bai barta ta samu damar cewa komai ba ya hade bakinsu waje daya ya shiga aika mata da wani zazzafan kiss da ya sanya taji kwanyarta tana yamutsawa,cikin lokaci kadan ya sauke mata wani saqo mai nauyi daya sanya jikinta saki gaba daya,yayin da ilahirin nashi jikin ya dauki rawa gaba daya,kusan ta saba da wannan yanayin nasa,tun tana tsoro harta saba gani,ta saba ganin wannan romance din mai zafi daga wajensa,fice mata a hayyacinsa yakeyi cikin lokaci qalilan,wannan yake rudata itakuma tayita masa kula,kukan da baya samun damar lallashinta sai bayan komai.ya kammala.


Yau dinma daga bata ladar rashin jin magana ya zarme,shi kamsa baisan me yakeyi ba,illa dai zuciyarsa da qwaqwalwarsa yaji sun kasa jurewa,bai kuma barta ba sai daya isa ga muradinsa duniyarsa qarshen farincikinsa.


Tana a jikinsa tana masa 'yan koke koken data saba,hannunsa cikin sumarta yana yamutsata,idanunsa a rufe,lips dinsa kawai ke motsawa suna fidda sautin wasu kalmomi masu zaqi da kwantar da rai,yayin da zuciyarsa tayi nisa wajen son gano iya matakin matsayin da widad ta tsaya a ransa,ko yaushe yana jin kamar a ranar ya fara saninta,tana da wata irin baiwa da bai taba tsammanin za'a sameta jikin kowacce diya mace ba,a duk sanda ya kasance da ita burinsa na sake kasancewa da ita baya raguwa saidai ya qara hauhawa


"Uncle wayo" ta fada a shagwabe da siririyar muryarta, murmushi ya kubce masa,hakan take yawan gaya masa duk sanda irin hakan ta faru


"Kiyi haquri dani babyn uncle,na jarabtu dake har bansan iyaka ba,am sorry....but I have something special for you,muje muyi wanka ki gani".


Tare sukayi wankan duk da tana dan zuzzulle masa,suka shirya ta gabatar masa da abinci yaci cikin nutsuwa da kwanciyar rai,best taste for ever a wajensa.


Bayan ya kammala ya jingina bayansa da kujera qafafunsa a miqe harde wajen guda,yatsun hannunsa ma a hade yana dubanta,kamar cin abincinta yadan ragu,tun ranar nan ya gani,amma kuma bai sakashi damuwa sosai ba,ganin bata canza ba,saima murjewa da jikinta yakeyi,hannu ya miqa mata alamun ta taho,saita maqale kafada


"Uncle wayo" ta fada tana dariya,bai shirya ba dole shima dariya ta kubce masa,a baya yakan jima baiyi dariya irin haka ba,amma a yanzu.widad ta maidata abu mai sauqi a wajensa idan yana tare da ita,dukka tsare gida shan kunun nan da kamewa sun koma office da sauran guraren aiki


"Kizl ki karba albishir din naki,ba wayo bane yanzu" matsawa jikin nasa tayi,ya kuwa riqeta gam yana fidda takaddun ya fara mata bayani.


Ruqunqumeshi tayi da kyau cikin farincikin da batasan yawansa ba tana sake tambayarsa


"Uncle da gaske?"


"Na taba yi miki qarya?" Kai ta girgiza


"Baka taba uncle" ta fada hawayen farinciki yana sauko mata,saiya bata fuska kadan


"Kuka?,noo baby,don't cry mana" ya fada yana janta jikinsa hadi da dan bubbuga bayanta alamun lallashi.


Irin godiyar data dinga masa sai daya ji qwalla ta sauko masa,godiya ce da bai taba jin irinta daga bakin hafsat ba,duk kuwa da ya kaita gurin da yanzun widad din zata je a qalla sau uku kenan,sai ya saka hannuwansa yana sake lullubeta cikin jikinsa da kyau,yana sake jinta tana shiga rayuwarsa da gasken gaske.


A ranar ta dinga kira waya tana shaidawa kowa,ummunta mommynta da abbanta sune farko,sannan uncle muhsin anty madeena anty deena dasu hajja,kowa yaji dadi ya kuma yi farinciki da wannan labari,ya kuma tayata murna qwarai, uncle muhsin ya kirashi yayi masa godiya,kai kawai ya girgiza


"Bakasan wacece widad a wajena bane muhsin,she meant alort to me,bansan ya zan fasalta maka ba" yayi furucin tun daga qasan zuciyarsa.


Murmushin jin dadi uncle muhsin ya saki,amma a fili sai yace


"Easy sir.....surukinka nake fa kaketa fallasamin sirrin zuciyarka" sai suka sanya dariya a tare.


Cikin satin yace ta shirya zasu wuce bauchi,batajin son zuwa bauchin sam,amma tana son ganin hajiya dasu mimi,don ta kwana biyu bata je ba,bata nuna masa komai ba,cikin karsashi ta shirya musu dukka jakankunansu,ta kuma siyawa su mimi da hajia tsaraba,bayan tace ya turo rose ko samuel su kaita kasuwa,sai gashi ya kashe aikinsa da kansa yazo ya kaita ta siya duk abinda takeso,don yanzun ba kasafai yake bari wani ya kaita wani waje ba,idanma ta kama to saidai ya turo mace.


**********Tunda sale ya bude gate din gidan ta gane motarsa ce,amma data fahimci bashi kadai yazo ba saita ci gaba da zamanta saman plastic chair din da take zaune a kai,ta jibge kayan da take siyarwa tana faman lissafi,gefenta su mimi ke wasa kamar ko yaushe futu futu abinsu,kai bakace akwai interlock cikin gidan ba.


Widad dake bacci abinta cikin motar ko shigowarsu cikin gidan bata san dashi ba,ya waiwaya yana mamakin nauyin baccin da takeyi a 'yan kwanakin nan,fuskarta tayi wani mugun fresh hasken fatarta ya kashe masa idanu,ya daga hannu da nufin tashinta,saidai mimi da nawwara sun rage masa aiki,don tuni suka fara kiran sunanshi suna rige rigen isowa,muryarsu ta sakata bude idanunta a hankali,ta saki murmushi tana kallon yaran har suka iso garesu.


Ita dashi aketa rige rigen tarbarsu,tayi nasarar riqe mimi shi kuma ya dauki nawwara,daga inda hafsat din take kamar zuciyarta zata fado,ta janye idanunta tana jin kamar zuciyarta xata fashe,ta gaji da jiran da anty ummee tace tayi,sai take gani kawai ta soma gajiya da lamuranta,tunda ta nemi aron dubu dari biyu bata bata ba.
[3/20, 8:54 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*


*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*


Page 92



Kasa ci gaba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login