Showing 3001 words to 6000 words out of 52544 words

Chapter 2 - MAKAUNIYA CE BOOK COMPLETE HAUSA NOVELS BY Jidda s Mapi.txt

29 Oct 2025

542

baya nan zata saida alalenta hankali kwance,
Latif ne yakaraso wajen yace "kanwata yau zanci alalenki, kisamin na ɗari uku"

Waro manyan Eyes nata tayi cikin mamaki tace "na ɗari uku? Kaida wa zakuci?"

Latif ne yayi dariya sosai yanda ganin yanda ta waro idonta yace "kanwata ai saikisa na tsorata, wannan idon naki ay zasu ruɗa mutum, Nikaɗai zanci.

Dariya tayi wanda yasa gefen kumatunta lotsawa Tace "to ay bazaka iya cinye na ɗari uku ba, guda sha biyar fa"

Yace eh zanyi sadaka da sauran, tace tom.

Roba taɗauko tasa mishi na ɗari uku hadda kyautan biyu tace gashi,
Karɓa yayi yaciro ɗari biyar yace ga kuɗinki.

To ay ba canji cewar Minal,
Latif ne yace kiɗauka duka nabar miki, tace Aa banaso kabari agida za'a min faɗa, yace to kirabarwa mutane na ɗari biyun, tace to.

Ɗaukan roban tayi, takira almajirai tafara raba musu.

Almajurai ne suka taru akanta suna wawa, garin zata kwace roban wani Almajiri ya tureta, ai kuwa sai gata akasa dama jikinnata kamar karkashi, wawa suke suna tattaka ta.

Da sauri Madina takaraso wajen tana turesu.

Daidai lokacin motar Bilal ta danno kai, ganin yanda almajirai suka taru awajen suna wawa yasashi fita amotar da sauri.

Karatawa yayi wajen yana san jin meyake faruwa?

Ganin Minal kwance tana ihu ne yasashi tsayawa yana kallonta, yanda taje birgima akasa kamar 'yar shekara biyu.

Takaici ne yakamashi ganin yanda jikinta yayi datti.

Tsaki yaja azuciyarshi yace "Allah yasa karsu barta haka saitaji ciwo, yajuya yayi tafiyarshi"

Dakyar Minal tasamu takarɓi roban tafalfala da gudu tabar cikin company ɗin.

Shikuma Bilal yana shiga yaga Latif da roban alale yana ci,
kallonshi Latif yayi yace "you are wellcome, meyasa yau kayi letti"

Amaikon Bilal ya bashi amsa, sai yace "aina kasayi wannan abun?"

Awajen Minal cewar Latif

Wace Minal?

Latif yace "yarinyan dakake wulaƙantawa"

Dagudu Bilal yashige cikin toilet na office ɗin yafara sheƙa Amai, gashi ba abunda yaci yau da safe.

Mamaki ne yakama Latif, daga cewa awajen Minal saiya fara Amai?
Kai ina ganin ba lafiya ba!.


_✅ote Comment and share_


✍🏻 *Jiddah S Mapi*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸

*Written by*
Jiddah S Mapi


*بسم الله الرحمن الرحيم*


*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*

_wannan littafin sadaukarwa ne ga yayata Maryam S Mapi_

*WATTPAD*
_Jiddah S Mapi_


*Page* 3

"Latif ne yabi bayan Bilal, yana shiga toilet ɗin yaga Bilal yana sheƙa Amai kamar zai amayar da kayan cikinshi, mamaki ne yakama Latif yatsuguna yana tambayan Bilal bakada lafiya ne?"

Bilal ne yaɗago kanshi a zuciye yace "kai wani irin mutum ne Latif? Tayaya zakaci abinda yafito daga hanun wannan ƙazamar? Yanzu fa ina zuwa naga almajirai sun taru akanta suna wawa, shine zaka iya cin abincinta?"

Knocking na kofar office ɗin sukaji anayi, Latif ne yace waye?
Daga waje naji muryar wani yana cewa ku buɗe kofar.

Bilal ne ya umurci Latif dayaje yabuɗe kofar dan yanajin muryar kamar na Daddy, Latif ne yaje yabuɗe kofar, yana buɗewa yace sannu dazuwa Daddy, mutumin baiyi mishi magana ba yawuce ciki, Latif ne yace "to Allah yasa lafiya"

Ina Bilal? cewar mutumin, Latif ne yace "yana toilet Amai yakeyi tin ɗazu"

"Meya sameshi?" cewar mutumin
Latif ne yayi mishi bayanin duk abunda yafaru tsakanin Bilal da Minal.

Numfashi mutumin yasauke sannan yace "kana nufin kacemin yarinyan ma ta tsaneshi?"

Latif ne yagiɗa kai yace "kwarai kuwa Daddy ni abunda yafi damuna shine yanda yake wulaƙanta yarinyan a idon kowa, inda Allah yataimaka yarinyan bata bari itama"

Daidai lokacin Bilal yafito daga toilet yace "sannu dazuwa Daddy ga wajen zama"

Mutumin ne yanemi waje yazauna yana fuskantar Bilal.

Bilal meyasa kake wulaƙanta Afrah?
Katunafa Afrah 'yata ce tacikina,
Inason Afrah yanda bakayi tsammani ba.
Sanin kanka ne ciki ɗaya muka fito da Babanka, inada tabbacin da babanka yanada rai da tuni kadaɗe da Auren Afrah.

"Agaskiya Daddy bazan iya Auren Afrah ba!
Sabida ni amatsayin kanwata naɗauke ta, hasalima ni halin Afrah sam beyimin ba"

Daddy Afrah ba kalar macen dazan Aura bace, ninafi son mace wanda idonta be buɗeba....
Ya isa Bilal, kadakata haka!

Agabana kake cewa bakason 'yata?
To bara nafaɗa maka ko ubanka ne be isa nace "Eh" yace "Aa" ba.

Yaushe aka haifeka?

Daddy nima inada tabbacin da Mahaifina yanada rai bazai taɓa yimin abu dole ba.

Daddy yace nika faɗawa haka Bilal?
Bilal yace "ka gafarceni Daddy"

Fita daga office ɗin mutumin yayi azuciye.

Latif ne yazauna a inda Daddy ya tashi yana fuskantar Bilal,
Yace "Bilal kayi babban kuskure! Meyasa zakace bakason 'yarshi a idonshi? Ai kobaka santa to be kamata kafaɗa mishi ba, Bilal mutane yanzu anaso kabisu ahankali ne badan kana tsoronsu ba".
Saidan bakasan zuciyar wani ba.

Bilal ne yace "Latif lamarin gidanmu ya isheni, su basa duba abinda nakeso kansu kawai suka sani, gara nafito fili nafaɗa musu abinda yake raina, domin ko sama da kasa zasu haɗu bazan Auri Afrah ba".

Latif yace "hakane Amma karage nuna tsanan dakake mata afili sabida tsaro ba tsoro ba"

Bilal yace "ok zan duba nagani"

_Minal_
Sauri take ta iso gida dan jikinta raɗaɗi yake mata ko ta ina, duba hanunta tayi taga yanda yayi jaa, sai kawai tafashe da kuka, gani take kamar bazata iso gida ba.

Wani me Napep ne yace "ina zuwa hajiya?"

Minal tace "bayan kasuwa"
Yace shiga mutafi.

Minal ce tashiga Napep ɗin suka tafi.
Suna isowa bayan kasuwa daidai kofar gidansu tace "anan zaka saukeni"
Me Napep yana sauketa ta ruga dagudu tabar wajen.

Ke ke ke tsaya kibani kuɗina, ina zakije?
Kafin yakarasa Minal tayi kwana, yanemeta sama da kasa be ganta ba,
Idan nakama ta saita yabawa aya zakinta cewar me Napep.

"Minal kuwa gudu take harta isa gida, tana zuwa ta tsaya abakin kofa tagyara jikinta tsaff kafin tashiga gida,
Tana shiga tasamu Umma tana tsince shinkafa,
Zama tayi agefen Umma takwantar dakanta ajikin Umma,
Cikin shagwaɓa tace "Umma nagaji wallahi"

Umma ce tace "sannu Minal tawa, insha Allah gobe zaki huta, Minal tace "Umma idan nazauna agida ban fita talla ba me kike ganin zamuci?"

Umma ce tayi shiru sabida tasan Minal gaskiya take faɗa,
Tashi kije kicire kayan jikinki sai kiyi wanka,
Minal tace "to Umma amma fa yau nagaji saide kimin wankan"

Umma ce tazaro ido tana kallon Minal tace "yanzu Minal kina katuwa dake zanyi miki wanka?"

Tashi kibani waje,
Minal ce ta tashi tana wani shagwaɓewa, tace Umma to ai har yanzu ni yarinya ce.
Shiru Umma tayi tayi mata sanin halin Minal na shagwaɓa.

_Washe gari_

"Bilal Ne yake lulluɓe cikin bargo, kanshi yana kallon sama, tunani yake.
Tayaya za'ace ya Auri Afrah? Anya wannan ba shiri bane akeson ayi mishi? Ya tabbata da Daddynshi yana raye bazai taɓa yadda ya Auri mara tarbiya ba".

Yana cikin wannan Tinanin yaji an buɗe kofarshi ko knocking ba'ayi ba,
Afrah ce tashigo da gudu tafaɗa jikinshi tana kuka.

Tureta yayi ajikinshi yace "ke bakida hankali ne? Meyake damunki ne? Ko aljanune dake nikam?"

Afrah ce tafashe da kuka tace "yaya Daddy ne yace nahakura dakai"

To sai me dan yace kihakura dani?
Ai gaskiya yafaɗa miki.
Look idan baki tashi kin fita aɗakinnan ba, zanyi maganinki yanzu.

Bilal saide ka kasheni wallahi amma bazan daina cewa ina sanka ba... Mari Bilal yasauke mata afuska yace "get out"

Yaya nika mara? Cewar Afrah.

An mareki ko zaki rama ne?

Yaya tinda na nuna maka "so" baka gani ba, kuma na nuna inasan ka Aureni kaki, duk na hakura.

Amma tinda kaɗau
Hannu kamareni, nibazan iya marinka da hannuna ba, sabida har yanzu ina sanka,
Amma kasani saina mareka da abinda yafi hannu ciwo,
Tana faɗan haka tajuya tafita a ɗakin.

Bilal yace "idan kin fasa ba'a haifeki ba"

Riga yaɗauko acikin kayan wani lemon colour, sawa yayi ko tsayawa yin wanka beyi ba,
Makullin motarshi yaɗauko yafice aɗakin.

Daidai zai fita a falone yaji Hajiya tana kiranshi.

Bilal tsaya.

"Tsayawa yayi yana kallonta harta karaso"

Bilal dama hakuri nakeson baka akan abubuwan dasuke faruwa agidannan, shima Alhajin yace in baka hakuri sabida bayajin daɗin yanda kake zama cikin takaici kullum, dan Allah kayi hakuri.

Bilal shiru yayi yana kallon Hajiya wato mahaifiyar Afrah, yace ba komai hajiya, ai Afrah kanwata ce, komai tayi nasan yarintane.

Hajiya tace to Bilal an gode,
Bilal besake cewa komai ba yajuya yayi tafiyarshi.

Amaikon yashiga mota yatafi sai naga yabi wani hanya daban dake cikin gidan, wani waje me kyau naga yashiga.

Lambu ne me ɗauke da kayan itatuwa daban daban, plastic chair ɗaya nagani daidai wajen wani bishiyan Mango, iskan wurinne yake shiga jikinshi ahankali yafara samun nutsuwa, jingina yayi ajikin chair ɗin, yaɗaura kafarshi ɗaya akan center table ɗaga kanshi yayi yana kallon sama.
Hawayene yafara fita a idonshi zuciyarshi tana mishi raɗaɗi.

Aduk lokacin daya tuna rayuwarshi nabaya, sai yaji yana tausayin kanshi, sai yaji inama daba'a haifeshi ba, runtse idonshi yayi yana tunanin rsyuwarshi nawasu shekaru dasuka wuce.


_wanene Bilal_

BILAL IBRAHIM USMAN shine asalin sunanshi, Yarone ga Alhaji Ibrahim me gold.

Alhaji Ibrahim asalin bafulatani ne ɗan garin Gombe ne, iyayenshi masu kuɗi ne, yagaji saida gold awajen mahaifinshi Alhaji Usman me gold,
Alhaji Usman me gold yanada arziki sosai, mata biyu ne dashi Hajiya rukayya dakuma Hajiya salamatu,
Hajiya Rukayya itace uwar gida, Allah bai baiwa hajiya Rukayya haihuwa da wuriba shikuma Alhaji Usman ganin Irin dukiyar daya tara ace bashida ɗa ko ɗaya? Hakanne yasashi kara Aure, shine ya Auri hajiya Salamatu, bayan Aurensu da shekara Biyu ne hajiya Salamatu tahaifi ɗanta, murna awajen Alhaji Usman baya misaltuwa, tun daga ranan da Hajiya Salamatu tahaihu tin lokacin hajiya Rukayya bata kara samin farin ciki acikon gidanba, wulakanci kala kala take gani agidan.

Bayan wasu shekarune itama hajiya Rukayya Allah yabata ciki, murna Alh Usman yayi sosai tindaga ranan tazama 'yar gata awajen Alh Usman, ranan suna yaro yaci sunan mahaifin Usman wato Ibrahim.

Ibrahim kyakkyawa ne sosai, hakan yasa Alhj Usman idan ze tafi office to Ibrahim yana gefenshi, abun yana kona ran Hajiya Salamatu, hakan yasa taɗauki karan tsana taɗaurawa Ibrahim.

Alokacin da Allah zai ɗauki ran Alhj Usman, tara iyalanshi yayi yace "kunga yanda nake ciki rai ahanun Allah, addu'arku nake nema, kona mutu kada kudaina yimin addu'a".

Kafin yarasu saida tarabawa kowa gadonshi.

Bayan rasuwarshi ne hajiya Salamatu mahaifiyar Umar, tasace takaddan wani company wanda yake mallakin Ibrahim ne,
Hajiya Rukayya tanaji tana gani aka hanata hakkin ɗanta, hakuri tayi taci gaba da zama agidan.

Kwatsam wata rana sai aka wayi gari Hajiya Rukayya ta tashi da tsananin ciwon ciki, kiran Ibrahim tayi, tayi mishi nasiha sosai tare da faɗin "Ibrahim kaga ka mallski hankalinka, inason idan namutu karka zauna agidannan katara dukiyanka kagudu sabida tsaro kaji?"

Ibrahim ne ya giɗa kai yana kukan tausayin mahaifiyarshi, haka har Allah yakarɓi ran Hajiya Rukayya, Ibrahim yayi kuka kamar ranshi yafita, haka aka ɗau gawan aka tafi da ita.

Adaren Ibrahim yatattara komai nashi yabar gidan,
Wani unguwa yakoma yasayi gida ysci gaba dazama aciki, yana kasuwancinshi yanda yaga mahaifinshi yake,
Har wata rana aka wayi gari yazama me kuɗin gaske,
Abokinshi ɗayane wato Alhaji Kabeer "Mahaifin Latif"

Alokacin dayayi kuɗi lokacin yahaɗu da mahaifiyar Bilal wato Khadija, Khadija tanada nutsuwa sosai gata da kyau kamar me, itama fulana ce 'yar asalin garin Gombe,
Anyi Aurensu suna cikin kwanciyar hankali.

Haka har Allah yabasu Haihuwan ɗa namiji, murna awajen Alhaji Ibrahim sai godiya, ranar data haihu saida yabawa mutane kyautar kujeran hajji.

Ranan suna yaro yaci sunan Mahaifin Alhaji Ibrahim wato Usman Amma suna kiranshi "BILAL"

Bilal yarone kyakkyawa wanda yake kama da mahaifinshi kamar an tsaga kara, hakan yasa Alhj Ibrahim ɗaurawa yaron "so" fiye da tunanin me karatu,
Bilal yasamu gata,
Alhj Ibrahim bayason yaji kukan Bilal ko kaɗan, hasalima akan Bilal suna iyayin kwana uku basuyi magana da Hajiya Khadija ba.

Idan tace "Alhj karage son yaronnan sabida ze iya zama maka damuwa idan baya tare dakai"

To ranan zaiyi zuciya, wai tana cewa yadaina son ɗanshi, ita kuma sai tace Allah yabaka hakuri.
Bayan wasu shekaru ne Allah yakara bawa hajiya Khadija ciki, makka Alhj Ibrahim yakaita yace tahaihu acan.
Bsyan tahaihu ne tadawo da 'yarta fara sol me kama da ita,
Bilal aduniya ba abinda yatsana kamar yaji kukan kanwarshi wato "Nabila" idan tana kuka sam baya gane hankalinshi.
Sun shaku da Nabila sosai, zaman jin daɗi da kwanciyar hankali ake agidan.

Kwatasam sai wata rana aka kira Alhj Ibrahim cewar Matar Yayanshi wato Alhj Umar tarasu,
Gani yayi bazai iya fasa zuwa ba, cewahajiya Khadija yayi kishirya muje mugaidasu keda Nabila, shikuma Bilal zan ajeshi awajen aiki.

Hajiya Khadija ce tace "haba Alhj Kadubafa kaga Bilal yanda yagirma, be kamata ace har yanzu kana kaishi office ba"

No hajiya wannan tsakanina da ɗana ne,
Hajiya khadija taja baki tayi shiru.

Ahanyansu nazuwa ne Bilal yake cewa "Daddy nima zanje nizan jamu amotar"

Aa Bilal kabari kawai gobe sai kaje amma yau inason akwai aikana dazaka karɓamin a office,
Bilal yace to Daddy.

Nabila ce tace "yaya yau zaka siyamin icecream irin najiya?"

Dariya Bilal yayi sannan yayi mata kiss agoshi yace "insha Allah my lovly sister"

Dariya tayi ta rungumeshi,
Hajiya Khadija ce take kallonsu haka kawai taji zuciyarta tana bugawa.

Alhaji ko zamubar Nabila ce suwuce office da Bilal?
Alhj yace Aa hajiya barshi yahuta,
Hajiya tace to.

Suna sauke Bilal yayiwa Nabila kiss agoshi, Daddy yace "ni bazakamin ba?"

Dariya Bilal yayi ya sumbaci Daddy agoshi, yajuya yace "Mommy saura ke"

Hajiya tace ban roka ba,
Dariya sukayi duka kafin Bilal yasumbaci Mommy yawuce office,
Juyawa yayi yace Daddy kayi tuki ahankali dan nasan kafara tsufa,
Harara Daddy yayi mishi yace "ja'irin yaro"

Hajiya khadija tace "karka tsufar min da miji"

Dariya yayi yawuce yatafi yana mejin farin ciki aranshi.

Da yamma Bilal suna zaune a office shida Latif abokinshi tin suna yara, yaji karan wayanshi, numban Daddy yagani yaɗaga yace "Daddy na, kun dawo ne?".

Muryar wani yaji yana cewa "Wannan mutanen motar sun mutu tasanadiyar hatsari dasukayi, babu wanda yafito da rai acikinsu,
Yanzu gawansu yana Federal center azo aɗauka, ɗitt aka kashe wayar.

Bilal ya bushe awajen, wayan yafaɗi ahanunshi Amma har yanzu hanunshi akunnenshi,
Latif ne yake tambayarshi meya faru?

Kaini Federal center shine abinda Bilal ya iya faɗa.

Latif ne yaja hanunshi yayi hanyan waje dashi,
Amota yasashi kafin yashiga motar suka fice da mugun gudu.

Duna zuwa Asibitin faderal center, wani doctor ne wanda yasan Bilal yayi musu iso Zuwa wani ɗaki,
Suna shiga ɗakin Bilal ne yafara hango mutane uku kwance an rufesu da farin kyalle.

Saurin karasawa yayi,
Yana zuwa yafara kokarin buɗesu.

Fuskar Daddy yagani wanda duk ya ɓaci da jini an rufe da bandage,
Yabuɗe ɗayan yaga fuskar Mommy ma babu kyaun gani,
Rufewa yayi da Sauri yabuɗe na Nabila,
Saurin rufewa yayi, yasa kanshi akan Nabila hanunshi rike dana Daddy da Mommy, ihu ya kwala yana buga kanshi jikin Nabila.



_✅ote comment and share_


✍🏻 *Jiddah S Mapi*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸

(An heart touching story)


*Written by*
Jiddah S Mapi

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*

_wannan littafin sadaukarwa ne ga yayata Maryam S Mapi_

*WATTPAD*
_Jiddah S Mapi_



*Page* 4

"Latif ne yafita dagudu kiran likita,
Atare suka shigo cikin ɗakin da Bilal yake kwance babu alaman motsi atare dashi"

Kiran sauran Ma'aikatan sukayi,
Aka taru aka ɗauke Bilal awajen.

"Anje an birnesu Bilal be sake ganin fuskarsu ba, yana kwance luff baya hayyacinshi"

"Tin daga wannan rana Bilal yadaina dariya, yadaina kula mutane idan zaku shekara awaje tare bakayi mishi magana ba, tofa shi ko kallo baka isheshi ba!

Jinya yake a asibitin bayason cin abinci ya rame yayi haske sosai, idan anayi mishi magana sai Eh Aa yake iya faɗa.

Baban Latif da Latif ne suke jinyarshi,
Yau kwanansu Uku kenan a asibiti, doctor ne yashigo yace musu ba wani matsala zasu iya tafiya,
Godiya Baban Latif yayi suka fara tattare kayansu,
Alhaji Umar ne da mamanshi Hajiya Salamatu suka shigo ɗakin,
Cewa sukayi saide Bilal yakoma gidan Alhaji Umar dazama, da farko Bilyaki yadda saida Baban Latif yasa baki kafin ya yadda.

Bilal yakoma gidan Alhaji Umar dazama,
Amma yana cikin takura, Afrah ta takurawa rayuwarshi, gashi Alhaji Umar yanason sashi yin Auren Dole.

Hajiya Salamatu kuwa (mahaifiyar Alhaji Umar) banda harara da tsaki ba abinda yake shiga tsakaninsu dashi.

"Alhaji Umar yanada yara Uku, Hafiz, Sabir, sai Autarsu Afrah takwarar hajiya Salamatu,
Hafiz yatsani Bilal, hasalima bayason ko ganin Bilal ne yayi,
Tinda Bilal yagane haka saiya fita a harkarshi,
Yaran haji Umar an sangartasu, sam sam basusan darajar mutum ba!
Sabir ne kaɗai yafito me hankali, shine wanda mamanshi tarasu Daddyn Bilal sukaje gaisheshi,
Bilal jiyaje azuciyarshi yayi Babban rashi, tinda yarasa iyayenshi da kanwarshi"

_cigaban labari_

"Tissue yaciro a aljuhun rigarshi ya goge hawayenshi,
Jiyayi an dafa kafaɗarshi, be ɗago ba sabida yasan Daddyne ko Latif zasu iya zuwa inda yake kai tsaye"

Kayi hakuri Bilal nasan yanda kakejin zafi azuciyarka, hakika rashin iyaye bakaramin rashi bane, amma ahalin yanzu ba kuka yakamata kayi ba Addu'a yakamata kayi musu, kaji?
Cewar Latif

Bilal ne yace "bazan iya ba, wallahi Latif bazan iya ba, iyayena suna matukar sona! Ina dana sanin rashin binsu gidan rasuwannan danayi. kuma wallahi ko mata sun kare aduniya bazan taɓa Auren Afrah ba,
Na rantse akan na Auri Afrah gara na nemi 'yar kauye wanda batasan komaiba in Aura, yarinyan Da idanunta abuɗe yake, tasan komai na jikin namiji,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login