Showing 30001 words to 33000 words out of 52544 words
Chapter 11 - MAKAUNIYA CE BOOK COMPLETE HAUSA NOVELS BY Jidda s Mapi.txt
d'akin nan"
Cikin tsiwa da rashin kunya Afrah tace "bazan fita ba yaya saidai kayi abinda zakayi"
"Okay bazaki fita ba?"
Afrah tace "Eh"
Bilal bulalar daya siya ya d'auko ya nuna mata k'ofa yace "get out of this Room"
Cikin tsiwa tace "bazan fita ba"
Bulalar ya watsa mata, ihu tayi tace "bazan fita ba ko zaka kasheni"
Dukanta yafarayi kota ina da Bulalar, tana ihu.
Hajiya babba wacce ta sake kunnuwa ne taji ihun Afrah, da gudu tanufi d'akin, tana zuwa taga Bilal yana dukan Afrah kamar shiya haifeta.
Cewa tayi "kai bakada hankaline? Da zaka kama yarinya kayita duka haka?"
Bilal dama haushin Hajiya babba yakeji, yasan duk iya shegen Afrah to da bakin Hajiya babba,
Bulalar ya watsa mata abaya daidai lokacin data k'araso wajensu.
Ihu Hajiya babba tafara tana Sosa bayanta, Bilal cigaba yayi da zabga mata Bulalar.
"Hajiya Babba k'ofar fita ta nufa tana k'ok'arin bud'e kofa, Bilal yabita da gudu yakara zabga mata wani, Sosa bayanta take sosai.
Da karfi tace "Bilalu bani bace, gacan Afrah a bayanka"
Bilal zabga mata Bulalar yake tsakani da Allah, da kyar Hajiya babba ta kwaci kanta, tabud'e kofar, tana fita tafad'i akasa, da rarrafe ta isa d'akinta
Bilal Jan Afrah yayi Wanda duk jikinta yayi tsami, ya wullata waje yarufe kofarshi.
"Hajiya babba tana zuwa d'aki tasa sakata, toilet tanufa da kyar tasamu tayi fitsari, tana sauke nunfashi kamar wacce tayi wasan tsere.
Minal kwance take akan gadonta, tana tunanin Abinda yafaru tsakaninta da Bilal, tunawa tayi da yanda yake fitar da numfashi lokacin dayake kissing nata, yarrr taji ajikinta, " Auzubillahi" shine abinda tafurta.
Lumshe idonta tayi daganan bacci ya d'auketa.
_Asuba tagari_
Daddy ne ya lek'o d'akin Bilal yace "Bilal kasameni a falo"
Bilal yace "to Daddy"
Bayan Bilal yaje falon ne yaga Afrah da Hajiya babba, sai Mommy da Daddy,
Gaishe da Daddy yayi Amma Daddy yaki Amsawa saima tambayar daya bishi da ita na "Bilal meyasa ka daki mahaifiyata?"
Bilal yace "nifa daddy ban daki Hajiya babba ba, Afrah kawai na daka, itama Dan tayimin laifi ne"
"Wani irin laifi tayi maka da zakayi mata wannan dukar, kuma ai koba komai ita kanwarka ce"
Bilal yace "Daddy Afrah tana shigemin sosai, ya za'ayi ta shigomin d'aki da daddare, cikin k'ananan kaya? Kuma tasan matata bata nan, idan wani Abu yafaru laifin wa za'a gani?"
Daddy cikin Mamaki yace "Bilal? Ya akayi kasan tasa kananan kaya? Bacin kai ba gani kake ba"
Bilal jin tambayar da Daddy yamishi saida zuciyarshi tabuga, yarasa wace amsa zai bashi..
_✔ote & Comment_
Jiddah S Mapi
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 26...
*___________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
Shiru Bilal yayi dan baisan Amsar dazai bashi ba.
Daddy yakara cewa "Bilal tambayarka fa nake ya akayi kasan kananan kayane ajikinta?"
Bilal yace "Daddy jikina ne yabani, sabida nasan sune kayan datake sawa, maganar duka kuma nasan Afrah kawai nadaka Amma ban tab'a Hajiya babba ba, Daddy inada haukane zan daki Hajiya babba?"
Hajiya babba ce ta harzuk'a tace "yo hauka na nawa kuma? Kana mak'aho ina zaka sani? Yanda kayita zabga min bulala abayana kamar kasamu jaka, tin jiya Addu'a nake yanda kayita zabga min bulala, Allah yasa mala'iku suyita zabgawa Uwarka guduma"......Bilal da ranshi ya b'aci yace " Hajiya babba kada ki kara sa uwata a wannan lamarin, sabida tana kabari batasan meyake faruwa ba"
"Kabaro Bilalu ba Kabariba, ai nima Uwata tana kabari kuma ka zage kayita jibgana"
Bilal bai k'arayi mata magana ba, kawai yatashi yafice a d'akin.
Gidan ma gaba d'aya yafita mishi arai.
Yana shiga d'aki yafad'a akan gado, cikin zuciyarshi yace "yanzu da Minal tana nan koba komai zan kalli fuskarta inji dad'i, to Amma meyasa takemin haka? Wata zuciyar tace mishi "kodai Dan kaki ka kaita India aduba mata idonta ne take wannan fushin?"
Wani tinani yayi kafin yatashi da sauri yanufi wardrobe ya d'auko Riga da wando yasa, makullin motarshi ya d'auka, tareda barin gidan gaba d'aya.
Gudu yake shararawa akan kwalta, bai tsayaba saida ya iso kofarsu Minal, yana zuwa dab yaji jikinshi yayi sanyi, duk zafin daya d'auka.
Yana zaune kusan minti talatin, harya cire ran zata fito, sai kawai yaga Madina tazo wucewa harta shiga gidan, "Alhmdllh" yace sabida yasan dolene tafito yanzu tinda ga kawarta.
Saida yakara kusan minti talatin akalla yayi Awa d'aya zaune awajen, kafin ya hangosu sun fito daga gidan, Madinace agaba sai Minal dake bin bayanta, tana kokarin sa hijabi.
Saida yabari suka wuce motarshi kafin yabud'e yafito.
A hankali yafara bin bayansu, cikin sand'a yasa hannu ya d'auke Minal,
Minal kuma jin an d'agata sama yasa tafara kiran "Madi....kafin tak'ara ya rufe bakinta da hannunshi, saida yakaita motar kafin yasake mata baki.
Minal da duk ta tsorata tace "wayene? Dan Allah kuyi hak'uri ni makauniya ce"
Shiiiiii Bilal yafad'a, "karki sake magana anan idan bahaka ba saina kwakule idonki nakaiwa kare ya cinye"
Minal takara mugun firgita muryar Bilal, tasan zai iya tunda ya tsaneta, jikinta ne yafara Rawa,tace "Dan Allah yaya Bilal kayi hakuri wallahi bazan kara aika maka bak'ar magana ba na tuba, nabi Allah"
Bilal kunna mota yayi yad'au hanya da mugun speed, kamar zai tashi sama.
Minal Addu'a tafara afili tace "Subhanaka inni kuntu minazzalimeen".
_✔ote & comments_
Jiddah S Mapi
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 27...
*___________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
Banda Addu'a babu abinda Minal takeyi,
A b'angaren Bilal kuma dariya ma take bashi, bai wuce ko Ina ba sai Airport, parking na motarshi yayi kafin yaja hannunta suka fito, Minal tana ta rok'anshi Dan Allah kar yayi mata komai, ticket ya yanka musu kafin yawuce da ita wajen jirgi, yana zuwa yace kitsaya anan kar kiyi kuskuren fita sabida nan ba gidanku bane kinaji?
Gyad'a kai tayi tace "Dan Allah yaya Bilal karka cutar dani"
Bilal ko kallonta baiyi ba, yawuce yaje ya siyo abinci da drinks.
"Oya kici"
Minal kuka tafara tace "banajin yunwa ka maidani gida kawai"
Bilal yace "ok karki ci kizauna da yunwa, nidai nafita a hakki"
Kuka Minal tafara, kamar anyi mata mutuwa.
Daidai lokacin aka fara announcing cewa jirgi yakusa tashi kowa ya shirya.
Minal kukanta ne ya tsananta jin hardasu jirgi,
Bilal zama yayi a gefenta yana kallon yanda take kuka kamar anyi mata mutuwa, dariya ma abun yabashi, saida yayi daidai son ranshi kafin yariko hannunta yace "haba mana beauty meyasa kike kuka haka? Nifa gidan yankan kai kawai zan kaiki a kasar waje, kinga ai addu'a zakiyi ko?"
Ihu Minal tafara tana bubbuga kafarta a kasa, tace "nashiga Uku na lalace nahad'u da d'an yankan kai, shikenan nawa yakare, Umma ki yafeni na saci kud'inki na siya awara a makaranta"
Bilal dariya yake harda rike ciki, wayarshi yad'auko yafarayi mata video.
Lokacin da jirgi ya tashi, wani irin runguma Minal tayiwa Bilal tsabar tsorata, jingina jikinshi yayi da kujerar shima ya rungumeta sosai ajikinshi.
Minal baccine ya d'auketa.
Bilal tausayi yarinyar take bashi, ganin da tana ganin komai amma yanzu bata ganin komai sai duhu, yanason ya tambayeta meya sameta har idonta ya makance Amma yana ganin kamar bazataji dad'i ba.
6:30Pm daidai suka sauka a kasar India.
Hotel Bilal ya kaisu a kwalkwata.
"Inane nan yaya Bilal?"
"Wajen yankan kai ne, Akwai matsala ne beauty?"
Bata kara magana ba.
Bilal hannunta yaja har zuwa d'akin daya kama musu.
Suna shiga yace "oya cire kayanki kiyi wanka"
"Ni bazanyi wanka ba a wanke nake"
Cikin tsawa Bilal yace "tashi kiyi wanka nace, umarni nabaki ba ra'ayinki na tambaya ba"
Ta tsorata da maganar tashi, dama gata gwanar tsoro, ka kaini toilet d'in tafad'a cikin cikin tsoro.
_✔ote & comments_
Jiddah S Mapi
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 28...
"Janyota jikinshi yayi ganin yanda ta tsorata"
Yace "beauty kidaina janyo ina miki tsawa wallahi banason wani yaji tsorona ko kad'an"
Jikinta rawa yake sosai tunawa datayi, akwai watarana da Madina tace mata idan mutum yana binka a hankali to akwai abinda yake bukata,
Azuciyarta tace "nashiga uku yau na lalace, Ashe da gaske yankani zaiyi? Subhanaka inni kuntu minazzalimin"
Bilal janta yayi zuwa cikin toilet yahad'a mata ruwa me zafi, yace "shiga kiyi wanka ina zuwa"
A tsorace takeyin komai harta gama wankar, Bilal ne yashigo da towel babba da karami, d'aura mata yayi kafin yariko hannunta yakaita cikin d'akin, mai yashafa mata tareda sa mata sleeping dress yace "ki kwanta kihuta kafin gobe muje Mumbai Dan acan me yankan kai yake zama"
Firgita tayi zata tashi Bilal yayi saurin maidata yace "haba beauty ina zaki? Kefa bakya tsoro kin manta lokacin da kike min rashin kunya a Company? Ai dama barinki nayi sai yanzu zan rama"
Minal sai kikkifta idanu take, jin yace zai rama abinda tayi mishi, cikin murya me sanyi tace "yaya Bilal na rantse da Allah Madina ce take zugani Amma bazan kara maka rashin kunya ba Dan Allah kayi hakuri"
Kiyi kwanciyarki nidai bazan hakura ba, yana fad'an haka yashiga toilet d'in shima yayi wanka daganan yayi Alwala yazo yayi sallah raka'a biyu kafin yashafa lotion nashi mai kamshi, taje suman kanshi yayi, shima yasa rigan bacci yahau gadon tareda rungumeta, Minal tanajin ya rungumeta tafara mutsu mutsu Amma yaki sakinta saida ta hakura Dan wuya.
_Asuba tagari_
"Acan gidansu Bilal kuma hankalin Sabir ya tashi sosai ganin Bilal bai kwana agida ba, zuwa d'akin Daddy yayi yace " Daddy banga yaya Bilal ba bai kwana agida ba, ko kasan inda yaje? Hankalina duk ya tashi"
Daddy yaji maganar kamar Almara, "badai Bilal yayi zuciya bane yabar gidan? Nashiga uku ina yakai takaddun gidajenshi da company nashi?"
Cikin firgici yacewa Sabir "kadubashi a garden?"
Sabir yace "babu inda ban dubashi ba Daddy"
Daddy yace "OK kacewa duk mutanen gidan damasu aiki su had'u a babban falo ina zuwa"
"OK Daddy"
Da ma'aikata da mutanen gida duk sun taru a babban falo, kowa yana addu'an Allah yasa lafiya,
Daddy ne yashigo falon yasamu kujera ya zauna, gyaran murya yayi yace "a cikinku wayasan inda Bilal yaje?"
Shiru falon yayi babu Wanda ya Amsa,
Cikin tsawa Daddy yace "ba tambayarku nake ba?"
Baba me gadi ne yace "Alhaji jiya da safe naga yad'au motarshi yafita".
What?
Yafita da mota?
Kai wani irin jahilin me gadi ne?
Kana sane da shi Makaho ne kuma kabarshi yafita?
To duk inda yake kaje ka nemoshi Dan bar shirya rabuwa dashi yanzu ba"
Baba me gadi ne yace "Alhaji Dan Allah ayi hakuri zan nemoshi"
"Karma ka nemoshi"
Cewar Daddy.
Kowa ya watse a falon ana tirr da halin Daddy na rashin girmama na gaba dashi.
Bilal kuma da Asuba ya tashi Minal yace "oya tashi kiyi wanka mutafi don mutane dayawa suna zuwa"
Minal zuwa wannan lokacin ta Riga tabarwa Allah komai, wankan dayace tayi shi tayi sannan ya taimaka mata tasa kaya,
Shima yayi wankar tareda sa kaya me kyau,
Sallan Asuba sukayi kafin Bilal yariko hannunta yace "muje ko?"
Binshi tafarayi kamar statu.
Motar haya Bilal yakama musu zuwa kwalkwata, sun sauka a City Hospital Kwalkwata dake cikin Kasar India,
Hannunta Bilal yarike suka shiga wani babban office, Sallama Bilal yayi kafin suka shiga, wani Ba indiyene zaune akan kujerar doctor, ganin Bilal yasa yafara murmushi tareda mikewa yace "you're welcome Mr Bilal"
Bilal dariya yayi yace "thank you Dr Shekhar"
Dr shekhar ne yace "namastey Mr Bilal"
Bilal yace "namastey"
Juyawa yayi wajen Minal yace "namastey ma'am"
Minal jin yaren take kamar na jinnu, lalub'o Bilal tayi ta b'uya a bayanshi.
Tace "yaya Bilal Dan Allah kabasu hakuri banajin yaren"
Dariya Bilal yayi yace "to ai saiki fad'a musu ko?"
Dr shekhar yace "have a sit"
Zama sukayi Bilal yayi mishi bayanin duk abinda yafaru da harshen India.
Suna gama maganar Dr shekhar yakira wata nurse yace mata Asawa Minal uniform yanzu za'ayi mata aiki sabida idan an ba'ayi da wuriba zai iya zama babban matsala.
"Okay sir"
Shine abinda Nurse d'in tafad'a,
Tareda riko hannun Minal tace "let's go ma'am"
Minal taki sakin Bilal sai kuka take da rokanshi Dan Allah yabarta araye.
Dariya kawai yske, dakyar ta sakeshi suka tafi da nurse d'in.
_✔ote & comments_
Jiddah S Mapi
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 29...
"Suna fita aka kaita wani babban d'aki me d'auke da na'urori da dama, uniform nurse d'in tabata karb'a tayi tasa, daganan suka kara fitowa zuwa wani d'aki d'an karamin da wata karamar gado, nurse d'ince tacewa Minal " sleep"
Minal tace "zan baki wasiyya idan kun kasheni kufad'awa Umma cewar yaya Bilal ne yakashe ni, sannan kifad'awa yaya Bilal yabawa Umma dubu ishirin acikin kud'in dayayi dani, Allah yasa in cika da imani"
Nurse tsaya tayi tana kallon Minal yanda take surutu babu Tsayawa gashi bata jin yaren datakeyi, batayi mata magana ba ta kwantar da 'ita tareda yi mata Alluran da zatayi kwana d'aya bata tashiba harsai angama Aiki.
Bacci me Nauyi ne ya d'auke Minal, wasu manyan doctors ne suka shigo suka fara mata aiki, bayan Bilal yayi sign yabiya kud'in.
_Nigeria_
"Umma da Madina sun nemi Minal sama da kasa basu ganta ba, iya tashin hankali Umma tashiga, kuka take ba kama hannun yaro, " ina kika shigane Minal? Kinsan banida kowa sai ke ya zakimin haka?"
Madina ce tace "Umma ko zamuje gidansu Bilal ne mu tambaya?"
Da Sauri Umma tace "Dan Allah muje"
Tafiya sukayi gidan Alhaji Umar,
Suna zuwa lokacin Daddy yana waya da 'yan sanda akan aduba mishi duk inda Bilal yake, su Ummane suka tsaya agefe suna jiran yagama wayar, yana kashe wayar yace "Ku kuma me kuke buk'ata?"
Umma ce tace "Alhaji nice maman Minal matar Bilal, tin shekaran jiya muke nemanta Amma bamu ganta ba shine mukace bari muzo mu tambaya ko Bilal yasan inda take"
Daddy yace "amma bakuda hankali, an fad'a muku nan gidan b'arayi ne masu satar mutane? To bari nafad'a muku nima banga Bilal ba tin shekaran jiya, na kira layinshi akashe, sabida haka kubar gidannan before I loo
Loose my temper"
Da kuka suka bar gidan Umma tana cewa "Dana sani da ban yadda da wannan Auren ba" Madina tanata bata hakuri.
_India_
"Anyi Aiki lafiya ansa mata bandage a idon sabida sai gobe around 2:30Am cif zata tashi"
Bilal ne ya kwana a gefenta yana me tausaya mata.
_washe gari_
2:30Am cif hannun Minal yafara Motsi, Bilal ne zaune agefenta yanata Addu'ar Allah yasa anyi a sa'a, ganin hannunta yana motsi yasashi kara kaimi wajen yin Addu'ar, wani doctor ne yazo daidai wajen yana son ya gyara mata kwanciyar sabida yaga tana motsi, da sauri Bilal yariko hannunshi yace "nahi" wato Aa.
Tashi yayi yagyarata me kyau tareda riko hannunta yana wasa dashi, baifi da minti biyar ba Minal ta tashi afirgice tace "Dan Allah karku kasheni".
Bilal ne yariketa yace " ke tsaya babu Wanda zai kasheki yanzu sai anjima tukun"
"Doctor ne yazo da gudu yafara kwance mata bandage d'in, yana gama kwancewa Minal taga wani haske acikin idon ta, da sauri ta runtse idon, Bilal yace " bud'e idonki ki kalleni"
A hankali tafara bud'e idon harta saukeshi akan Cute face nashi me d'auke da murmushin jin dad'i,
Takasa koda motsi sai kallonshi take kamar statu, hura mata iska yayi a ido yace "kallonfa Hajiya? Ko na miki ne?"
Batayi magana ba har yanzu mamaki ne a ranta, Tashi Bilal yayi zaije yakarb'o maganin,
Yaji an rungume shi ta baya sosai, murmushi kawai yayi Dan yasan itace, a hankali tace "yaya Bilal idona yana gani?"
Cikin wasa yace "Aa idona ne yake gani"
Sakinshi tayi tadawo ta gabanshi ta rungumeshi sosai kamar zata mayar dashi ciki, "Ash karki karyani Malama, jeki kwanta zan karb'o magani"
Tace "zan bika mu karb'o tare ina son ganin ko dagaske na warke"
Dariya yayi yariko hannunta yace "to muje hajiya me idanu"
Suna fita tafara ganin indiyawa sai kallonsu take baki bud'e har suka iso cikin office d'in, Wata doctor ce mace zaune kan kujera, tana ganin Bilal tafara dariya tareda wani yauk'i tana kwarkwasa, tashi tayi tabasu Maganin, kafad'ar Bilal tariko tana mishi bayani da harshen turanci,
Minal ce abin yabata haushi tace " Madam bakya ganin tareda matarshi yake ne?
Bilal yaji abunda tafad'a Amma be kulata ba, ganin sun shareta yasa taja hannun matar tace "ba magana nake miki ba?"
Matar tace "what are you saying?"
Minal tace "oho dai kifad'a da Hausa kiga ikon Allah"
Bilal yace "batajin Hausa kiyi mata magana da turanci"
Minal tace "oho, you mata, ni dashi we are mata da miji, Aure d'aurawa ni dashi, sabida haka I will tell you"
Da Bilal yafara dariya saida tafara mishi kuka kafin ya daina, hannunta yariko yace "karkiyi kuka Mrs Bilal muje amiki Allura saimu tafi ko?"
Minal taki yin magana har suka je akayi mata allura da kyar ta yadda, ana gama yi mata Bilal yakarb'i takaddan sallama, suka nufi Hotel, Minal ido tazuba tana kallon kasar India a zuciyarta tace "idan nakoma gida zan fad'awa Madina duk abinda nagani"
"Chungathara" wani Babban Hotel ne dake kasar India acan suka sauka, Bilal yace "oya jekiyi wanka kifito zamuyi magana"
Minal tace "to"
Wanka tayi ta d'aura towel Amma towel d'in yayi mata karami, tsayawa tayi a toilet d'in takasa Fita, Bilal ne dayaga ta dad'e yace "Me kikeyi ne?"
"Yaya Bilal towel d'in yamin karami ka taimakamin da babba"
"Ni sa'anki ne dazaki aikeni, idan bazaki fito ba kizauna haka"
Dataga ba sarki sai Allah kawai ta mazge tafito tana kakkare jikinta da hannu, Bilal dayake zaune akan gado hankalinshi yana kan chatting, sai jin kamshin turaren wanka yayi, data lura baya kallonta tafara tafiya cikin sand'a tanason d'auko kaya tasa, d'ago kai Bilal yayi caraf idonsu yahad'u dana juna, da sauri ta d'auke kanta tafara Neman kayan dazata sa, saidai tana bud'e wardrobe d'in taga wayam ba komai, durkushewa tayi awajen, shikuma Bilal yakasa d'auke idonshi akanta, Minal ganin yana kallonta sosai yasa tace "yaya Ka daina kallona haka"
Har yanzu idonshi bai bar kanta ba, zuwa lokacin har idonshi yafara sauya kala, sabida ganinta haka ba karamin rikitashi Tayi ba.
_✔ote & Comment_
Jiddah S Mapi
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 30...
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
"Runtse idonshi yayi bai kara bud'ewa ba, Minal ganin yarufe idonshi yasa tayi tsalle ta d'ane gadon, ta lullub'e jikinta da bargo,
Bilal dayaji ta kwanta sai ya bud'e idonshi a hankali, Ya sauka akan gadon"
Wata babbar jaka ya d'auko ya bud'e yaciro kayansu jerawa yayi a wardrobe.
Yana gamawa, Toilet yanufa yayi wanka yayi Alwala.
Yana fitowa yayi sallah raka'a biyu, hawa gadon yayi shima ya kwanta, Amma bacci yakasa d'aukanshi, sai juye juye yake, sab'anin Minal datake baccinta cikin kwanciyar hankali,
Yaye bargon nata yayi yajata jikinshi yarungumeta sosai, mutsu mutsu tafara Alamun ya saketa,
"Ke Kidaina abinnan idan ba hakaba ranki zai b'aci"
Cak Minal ta tsaya bata kara koda motsi ba.
A rungume da ita yayi bacci.
Lab'ewa tayi saida taga