Showing 3001 words to 6000 words out of 30605 words

Chapter 2 - ME YA JAMIN NEW BOOK COMPLETE BY OUM HAIRAN.txt

bayanta da kallo tare da taɓe baki.
Turus taja ta tsaya saboda ganin yanda parlourn yayi kaca² yaran duk sun ɓatashi da gudu Jannat ta nufota ta ɗauke ta tana juyawa da ita tanayi mata dariya yarinyar ma na dariya daidai lkcn da Salma ta fito Anam bataji tahowarta ba kawai sukayi karo aikuwa ta angajeta bisa tsautsayi ta faɗa kan cup ɗin glass ɗin ɗaya fashe a parlourn aikuwa ta fasa ƙara saboda nitsewar da kwalbar tayi a goshinta jini yayi wata irin tsartuwa ya fallatsa har jikin Aliyu dake tsaye tun lkcn da Anam keyima Jannat wasa.








Da gudu ya ƙara so kanta ya ɗagota gabaɗaya jini ya wanke mata fuska yace “subhanallahi Salma bakida hankali ne wasa fa takewa ƴarki shine zaki ture ta har kiji mata ciwo haka kefa kika dameni naje na ɗaukota yara sun dameki dama abinda kika shirya yi mata kenan?"
Yana mgn yana tare jinin da hannunsa inda ita kuma Anam taketa jijjiga kanta daya ɗaure da wani mugun ciwo, taɓe baki Salma tayi tace “to ko zaka rama matane Aliyu naga alamun kaji ciwon kaima a jikinka" kallon Salman yayi rashin lkcn bata amsa yasashi kama hannun Anam yace “Sannu Kharimatu tashi muje ayi miki dressing na gurin" miƙewa tayi tana layi saboda ba ƙaramin jini ta zubar ba motar yaja a mugun guje suka fice daga gdan suka nufi wani asibitin kuɗi a cikin unguwar ta Yankaba tasha wahala kafin su zare kwalbar sukayi dressing gurin likitan ya dubesa yace “zatayita fama da ciwon kai dole ta rinƙa samun hutu" jinjina kai yayi ya biya su suka fito har yanzu kuka takeyi bawai na zafin ciwon bane a'a tunawa da tayi cewa da mahaifinta yana raye qila duk da haka bata rinƙa faruwa da itaba.








Sau ɗaya yace mata sannu har sukaje gda wani abin mamaki Salma Bata gyara gurin da jinin ya zuba ba balle ta gyara parlourn Suna shiga Anam ta ɗauki tsintsiya zata share parlourn ya dakatar da ita yace “kije ki kwanta kawai" aje tsintsiyar tayi ta nufi ɗakinta ta kwanta nandanan kuwa zazzaɓi ya rufeta me zafin gaske a daren taci wahalar zazzaɓin batayi tunanin zatakai safe ba hakanan dai ta rinƙa addu'o'in da suka sawwaƙa a bakinta har zuwa wayewar gari da safe da wuri ta tashi domin shirya yaran zuwa makaranta ta kamasu tayi musu wanka tanayi tana duba breakfast ɗin data ɗora harta gama ta haɗa masu gdan basu sauko ba ta zauna tana rawar sanyi tana bama yaran abinci zazzaɓi na ƙara ƙarfi sanyin A.C na haɗa ta ita ba abin ta kasheba matar gdan ta nakasata.
Gama sallamar yaran tayi takaisu ga driver ya tafi makaranta dasu hadda jannat dake itama ansata juma'a ne bata zuwa ta dawo a wahalce ta rinƙa gyara gdan ta kusa gama parlourn taji sun sauko ta durƙusa cikin ladabi ta gaishesu Salma ta ɗauke kai sai Aliyu ne yace “ya jikin...." Kafin ta bashi amsa yaga yanda take rawar sanyi yace “ko zazzaɓi kikeyi ne?" Ɗaga masa kai tayi ya matsa ya taɓa jikinta yaji zafi zau ya dubi Salma yace “ki ɗauki key na motarki ki tafi zan Kaita asibiti" wani malolon baƙin ciki ne ya cika zuciyar Salma ta kuwa taso masa da cewa “haba Aliyu wannan ai wulaƙanci ne akan wannan ƙazamar talakan zakace naje nayi driving bayan kasan banason......."








Ɗaga mata hannu yayi ya dubi Anam yace “Ɗauko hijjab ɗinki Kharimatu" da sauri ta miƙe domin shiga ta ɗauko hijjab ɗin jiri ya ɗebeta ji kakeyi tik ta zube a ƙasa ya isa da gudu ya ɗagota ya fice da ita yasata a mota suka fita suna zuwa aka bata gado tsoron kira yake ya faɗa yasan masifar Granny Indai tasan dalili to ba Salma ba shi kansa ya kaɗe har ganyensa.
Ganin lkc na tafiya gashi yanada taro 9:30am yasashi yin shahadar kiran wayar Mama Yabi ta ɗaga suka gaisa ya faɗa mata abinda ke faruwa aikam ta ruɗe tace “bansan yaushe Kharimatu zatayi hankali ba kawai saboda sakarci taje zata illata kanta ganinan"
Ajiyar zuciya yayi ganin ya ɗorata ta ɗoru yaci gaba da zama gurin Anam tare da zubanta ido yanda take kwance da drip a hannunta baccin wahala ya ɗauketa kanta sanye da hula fuskarta wasai ga ɗaurin dressing ɗin da akayi mata jiya a hankali ya gangaro zuwa gangar jikinta yana ƙare mata kallo tunda yake baitaɓa tsayawa ya ƙarewa Anam kallo ba sai Yau Nazeer abokinsa yana yawan faɗa masa wato Aliyu babyn nan ta gdanka Anam tana matuƙar burgeni ɓoyayyen kyaunta yana ruɗani bantaɓa gajiya da kallonta ba nikam da zan samu dama zanso abani wannan yarinya matsayin mata nasan zanji daɗin hakan" taɓe baki yayi ya miƙe yana ƙare mata kallo yace “kai kasan wani ɓoyayyen kyau Nazeer Ni bayyananne na sani".......






_Zaku iya samun damar cigaba da karanta wannan littafi kan ₦300 kacal tura ta acc 0255526235 Gtbank ko kati MTN ta whattsAp number 09013718241_






*Oum Hairan*
[11/6, 7:22 PM] Oum Hairan&Affan: ME YA JAMIN?




~Paid book~




Oum Hairan




7-8




Kiciɓis sukayi da Mama a ƙofar shiga ɗakin suka gaisa ta shige ciki ta zubawa ƴartata ido cike da tausayi ƙarasawa tayi gabanta ta riƙo hannunta daidai lkcn data buɗe idonta tace mata “sannu Kharimatu ashe haka tsautsayi ya faru dake kema kin cika gaugawa ki rinƙa bin abubuwa a hankali kinji" lumshe idonta tayi tanajin ɗacin abinda ya faru da ita a ranta Aliyu ya shigo da sallamarsa a ƙasan maqoshi ya ajiye ruwa da magunguna yace da Mama “tunda kinzo zanje office inada Meeting zuwa tara da rabi" kuɗi ya zaro ya ajiye a gefen gadon tayi masa gdy ya fice a ɗakin batare dako inda Anam take ya kalla ba.
Bayan fitarsa Mama ta haɗa mata shayi me kauri da madarar daya kawo ta zauna tana bata tanaci daƙyar abincin ɗaci yakeyi mata a baki hakadai ta rinƙa turawa harta ƙoshi jefi² suke yar hirarsu da Mama Anam ta kasa jurewa ta faɗawa Mama asalin abinda yaji mata ciwo har ya haifar mata da zazzaɓin sosai Mama taji babu daɗi amma a fili sai tace “babu komai akwai Allah da talaka da mai arziƙi duka wanda yayi su son abinsa yakeyi saboda haka komai yayi farko zaiyi ƙarshe"








Ba haka Anam tasoba domin zuwa lkcn hƙrnta da zama a gdan Salma ya ƙare burinta kawai barin gdan saidai batada wata hanya ta barin gdan dole saida shahalewar Mama, yini sukayi a asibitin da yamma Aliyu ya dawo shida Granny tanata zubawa Anam sannu likitan yazo ya sallameta yayi Hamdala domin bayaso asirinsu ya tonu yafiso ayi a lulluɓe mgnr ɗebe kayan sukayi suka zuba a mota bayan sun shiga Granny tace “Ali wannan yarinyar gda zata wucce gurin uwarta idan ta warke ta dawo wannan kasaltacciyar matar taka me shegen son jiki ba ƙyaleta zatayi ta warke ba"
Bayason jan maganar dole ya amince saboda gudun tujarar Granny suka wucce Ɗan ladi nab Sidi zuciyar Mama da Anam wasai suna zuwa ya zubesu ya juya ya nufi gdansa. A falon ya tarar da Salma taci uwar kwalliya ta harɗe tana kallo tanacin donnut ya dubi yaran yagansu da kayan islamiyya yace “ya haka Salma gobe babu makaranta ne?" Ɗagowa tayi tace “kayan naji suna tsamin gumi shine nabarsu idan kun dawo waccen yarinyar ta wanke" jinjina kai yayi lallai Salma batada imani wato wadda aka sallamo a asibiti take tsammanin tayi mata wanki lallai Granny tanada hangen nesa.








Samansa ya haye yayi wanka ya fito ya zauna a dinning ya buɗe abinci ya faraci baici na kirki ba ya miƙe ya nufi waje ya zauna a kujerun dake cikin flowers na gdan yana duba jarida
Bai koma cikin gdan ba sai bayan yayi sallah Magrib da isha sannan ya shiga ya nufi saman ya shiga ɗakinsa ya sake watsa ruwa ya kwanta shiru yana jiran Salma har dare ya tsala yaja tsaki ya juya lamarin Salma ta fannin kula da shimfiɗarsa yana bashi tsoro kullum ita cikin uzuri take yau aiki gobe ciwon mara jibi zubar jini idan bataga damaba sai su shafe satittika a haka babu ruwanta shikuma ga miskilanci Indai bata kawo kanta ba ya daina kiranta.
Wayewar garin ta shirya tsaf tana mita ta shirya yaran suka fice suka tafi aiki sukuma yaran aka wucce dasu makaranta a mota take tambayarsa wai meye ya hana Anam dawowa? A gajarce yace “ganin dama" daga haka tayi masa shiru shima yayi mata ya ajeta a ma'aikatarsu ya wucce Campanynsu.








Kwanakin da Anam tayi tare da Mahaifiyarta abin gwanin daɗi ji takeyi kamar karta koma.
Ranar data cika sati tana ɗakin Granny sunata shirmensu Suka tsinkayo sallamar Aliyu saida gabanta ya faɗi ya shigo ɗakin idanunsa na kanta hakanan ya riski kansa da wata muguwar faɗuwar gaba lkcn da ya sauke idanunsa akanta cikin sati gudan da baya ganinta sai yaga gabaɗaya ta canza masa tayi wani haske fuskarta tayi fiyau da ita, janye gashinta tayi daga hannun Granny da take daure matashi tana ranƙwashinta tana cewa “ni banda tsiya Allah yayi miki yalwar suma ki rinƙa neman lalatata da shirme idan tayi fushi ta kaɗe ai naga da uwar da zakiyawa mijin da kishiyar gwalli"
Turo baki tayi tace “tabdi lallai ma Granny nikam ki dainamin fatan kishiya wlh ko sunan banson ji" ba Granny ba hatta Aliyu saida ya zare tabarau ɗin idanunsa ya kalleta tayi ƙasa da kai ganin irin kallon da yakeyi mata yasata jan mayafinta ta fice sumsum har taje bakin ƙofa yace “ki shirya zamu tafi gdan babu kowa Salma ta tafi Ziyarar aiki Sokoto sai yara"








Amsawa tayi cikin ladabi duk da bataso hakan ba amma ya zatayi ta fice ta nufi cikin ta ishe Hajiya Muniba a parlour tayi mata sannu da gda ta amsa mata a yatsine ta wucce ta tarar Mama hatta haɗe mata kayanta dauka kawai tayi tana hawaye ta fita daidai lkcn da yake fitowa a sashin Granny ya shiga gdan bai jima ba ya fito ya shiga motar itama ta shiga suka wucce.
Yaran sai murna sukeyi ta dawo itakuma tana ƙunci sarai Aliyu ya lura bataso dawowar ba daga yanayinta baisan dalili ba duk sai yaji ya tsargi kansa da takura mata to amma ya zaiyi zaman gda daga shi sai yara bazai yiwu ba itakuma Salma yanayin aikinta yana yawan sasu yawo.
Kayanta ta ɗauka ta shige ciki yabita da kallo shi kansa baisan meye yake kallo a jikinta ba amma tabbas yasani ba tun yau ba wani abu yana burgeshi game da yarinyar a hankali batare daya sani ba ya kira sunanta taja ta tsaya cikin fargaba tare da juyowa shikansa baisan dalilin kiran ba yace “am ki dafamin coffee ki kawomin ɗakina" saida taji wani ras da yace ɗakinsa domin a tarihin zamanta na gdan batajin ta taɓa shiga ɗakinsa yananan bai bata dama ba har marinta saida yayi akan aikenta ma da Salma takeyi tun lkcn ta daina gigin zuwar masa ɗaki........








_Zaku iya samun damar cigaba da karanta wannan littafi kan ₦300 kacal tura ta acc 0255526235 Gtbank ko kati MTN ta whattsAp number 09013718241_






*Oum Hairan*
[11/6, 7:22 PM] Oum Hairan&Affan: ME YA JAMIN?




Paid book




Oum Hairan




9-10






Shiga tayi ta aje kayan ta fito ta nufi kitchen yaran suka biyo ta musamman Farooq yana ce mata “nifa yunwa nake ji daddy indomie kawai ya bamu" jinjina kai tayi ta kunnan kan Gas biyu ɗaya ta doransa coffee ɗaya ta ɗora abinci ta riga gama dafa masa coffee ɗin ta ɗauka ta nufi ɗakin nasa ta ƙwanƙwasa yana zaune ya zuba uban tagumi baisan abinda zuciyarsa take shirin aikatawa ba amma tabbas tana tunzurashi ya aikata wani abu saidai shi kansa yanajin faɗuwar gaba idan ya tuna abin mai wahalar yuwuwa ne bayan haka ma zuciyarsa kamar ba adala bace a cikin sati guda tunanin nan ya fara bijiro masa wanda ya ɗarsu domin nemawa yaransa mafita shin tayaya ma Anam zata amince da wannan shirin nasa? In itan ta amince mahaifiyarta da mahaifansa zasu yarda? Musamman ma Hajiya Muniba.






Ya jinjina wannan lamari yafi a ƙirga kafin ya ankare da taɓa ƙofar da akeyi yabata izinin shigowa ta buɗe ta shigo da sallama a bakinta amma kanta a ƙasa yake ta ajiye masa flat ɗin data jero kofunan ta miƙe zata fita yace “am bakiji ba...." Tsayawa tayi tare da juyowa ta koma ta tsugunna tace “Na'am" zubanta ido yayi ya kuma kasa cewa da ita komi har saida ta gaji tace “Abinci na ɗorawa su Farooq zai iya ƙonewa"
Numfashi ya sauke ya bata izinin tashi ta miƙe ta fita ta koma kitchen ɗin ta tace shinkafar data ɗora ta zuba musu miyar data dumama ta ɗauka suka fito Parlourn tana bawa jannat Muwaddat da Farooq sunaci yanda yaran sukecin abincin zai tabbatar maka da gaske yunwa sukeji.
Sunci abincin sosai ta gyara gurin ta jasu ɗakinsu ta kwantar dasu bayan tayi musu wanka itama tayi tayi sallar Magrib da isha da bata samu tayi ba ta kwanta a cikinsu tana rungume da Jannat tayi musu Addu'a bacci ya ɗaukesu dukkansu.








Fitowa yayi domin duba yaran ya buɗe ɗakin ya shiga tare da kai hannu ya kunna glub gabansa ya fadi ganinta kwance tsakiyar yaran ya daɗe tsaye yana kallonta luguden zuciyarsa na ƙaruwa a kallo na zahiri baya hango wani abu dake burgeshi ga Anam Amma ya fahimci zuciyarsa ta jima da sanya masa wasu alamomi masu neman fassara.
Juyawa yayi ya fice zucciyar tasa cike da tunanin ta inda zai fara aikinsa tabbas lkc yayi da ya kamata ya samawa yarinyar yanci wanda ya farajin ɗarsuwar dacewar sa daga tausayi, ya ɓata dogon lkc yana tunanin rikicin da yake shirin ɓallowa kansa da Anam Amma zuciyarsa taƙi karaya a ƙarshe wayarsa ya ɗauka ya turawa abokinsa Nazeer cewar gobe su haɗu a office yanason su tattauna. Hakance ta faru washegarin kamar yanda Anam ta tashi da wuri haka shima ya tashi lkcn daya fito tana kitchen tana haɗa abin karin safe tana goye da Jannat da tayima wanka ta juyo ta ganshi tsaye a ƙofar kitchen ɗin ta sunkuyar da kanta tare da gaisheshi cikin ladabi ya amsata yace “ina sauri ne" daga kai tayi tare da ɗaukar kayan data gama dasu takai dinning ta dawo ta gyara kitchen ɗin ta shirya yaran ta miƙawa driver su ya tafi kaisu makaranta hakan yabata damar sake kwanciya.






*********




Duban juna sukeyi da Nazeer kowa yana sauke numfashi inda Nazeer yake goge zuffa ya ɗago cikin tsananin mamakin abokin nasa yace “ƴar aikin gdanka kakeji kanaso kuma so na aure? To ya kuma zakayi da masifaffiyar matarka me baƙin kishin masifa?"
Ajiyar zuciya ya sauke ya aje biron da yake wasa dashi a hannunsa yace “abinda nakasa samun amsarsa kenan am ni Ina ganin idan harsu Hajiya sun amince bazai zama matsala ba asanya rana gajeriys cikin sirri zanyi ƙoƙarin nema mata gida ƙarami nasata a ciki kafin komai ya daidaita bansan meye yake damun mata ba sun gaza ta ɓangarori da dama na auratayya amma daga lkcn da namiji yayi niyyar ɗauko musu wacce zata tayasu sai suyi tsalle suce basusan zancen ba duba dai Nazeer kaga rayuwar gdana nasani duk da cewar Salma Bata cikin matan da zaayima tambarin ƙazanta Amma fah da taimakon Anam kullum kaje gdannan Anam Bata tsaye bata zaune itace kula da yara gda da masu gda to inda zata iya ɗaukar wannan aikin meye yasa bazan gayyato ta tazo ta tayamu rayuwar har abada ba? Am Bama wannan ba Nazeer duk da cewar Ni bana cikin jinsi na maza masu takura ko yawan buqata hasali ma ta wannan fannin inada rauni amma fah a hakan duk lkcn dana buƙaci Salma sai ta kawomin uzuri kuma fah duk da haka cewa takeyi Ni ragone"






Shafa ƙeya Nazeer yayi yace “hakane
saidai kasan tunanin mata ya bambanta da namu sukan a ɓangarensu wannan babban abin kunya ne zaka aikata tabbas za'ayi surutu Bama iyakar surutu ba harda abinda yafi surutu to amma dake ka shirya saika fita da qwanjinka idan rabone sai kaga ka dauka"
Miƙewa sukayi tare suka fita sun jima jikin mota suna ƙara tattaunawa sannan sukayi musabaha suka rabu kowa ya shiga motarsa lkcn da yaje gda bai iske kowa ba a parlour ɗakinsa ya shiga ya cire kayansa ya watsa ruwa ya sanya jallabiya ya sauko ƙasan ɗakin Anam ya nufa ya ƙwanƙwasa ta miƙe a gyaran wardrobe ɗin da takeyi ta buɗe yana tsaye da cup a hannunsa ya zubanta idanunsa masu kama da wanda kejin bacci ta sunkuya cikin nutsuwa tace “barka da dawowa" lumshe idonsa yayi yanajin muryarta na ratsa sassan jikinsa yace “ina yaran nan?" Sunkuyar dakai tayi tace “dake juma'a ce Zeeze tazo ta ɗaukesu wai Aunty Salma tace tazo ta ɗaukesu suyi weekend acan"








Jinjina kai yayi yace “ina buƙatar abinci" yana faɗin haka yayi gaba ta koma ciki ta ɗauka hijjab ɗinta ta fito ta shiga kitchen ta haɗo masa abincin ta kawo masa ta miƙe zata tafi yace “bakiji ba" tsayawa tayi yace “ki haɗa kizo ki zauna inason mgn dake ne" dawowa tayi ta zauna ta fara haɗa masa a zahiri zakace wayar hannunsa yake kallo amma Anam ya zubawa idanu yana nazarinta sanyin yanayinta yafi komai burgeshi a ƴan kwanakin nan mika masa flat ɗin tayi cikin natsuwa yasa hannu ya karba tare da saukowa ƙasa ya zauna ya tanƙwashe ƙafarsa yanacin abincin yana satar kallonta, duk ta tsargu so take ya sallameta ta tafi gashi taga alamun bashi da niyyar bata izinin tafiya.
“Ranar da naje ɗaukoki a gda naji kinyi mgn lkcn da Granny take Miki faɗan gyara gashi kince ta daina yi miki fatan kishiya ko zan iya sanin dalilinki?"
Kanta na ƙasa ta ɗago ta sake sunkuyar dakai bazata iya jurewa irin kallon da yakeyi mata ba hakan yasa duk ta takura
Alamu yaga na bazatayi mgn ba yasashi cewa “ok amma zaki iya auren me mata?" Ɗagowa tayi da mugun sauri tare da girgiza masa kai ba tare da ta san tana girgiza masan ba kafeta yayi da idanunsa cike da faduwar gaba yace “why?" Maimakon ta bashi amsa sai kawai yaga ta fara share hawaye ya sake zubanta ido yace “talk

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login