Showing 48001 words to 51000 words out of 59266 words
Chapter 17 - MAJANUNI Book by Binta Umar Abbale.txt
mutu! ta gaji sosai! sai addua take Allah ya sa su sauka lafiya! ko ta samu ta mi'ke k'afafunta!
Matar dake kusa da ita ta bata pure water "Kar'bi ruwa 'yan mata naga kamar kin gaji."
Ba ta ji maganarta ba kawai dai ta ga tana mi'ko mata ruwa.
Da sauri tasa hannu ta kar'ba ta bud'e baki za tayi magana, ya juyo daga mazauninsa wata muguwar harara ya daka mata fuskarsa a mugun had'e!
Sai tayi saurin sunkuyar da kanta gabanta na wani irin fad'uwa ta mayarwa da matar ruwan da sauri! jikinta sai rawa yake.
Matar ta bi ta da kallon mamaki! sai kuma ta ta'be bakinta ta ajiye ruwanta da fadin."Kin yi wa kan ki."
A galabaice suka isa abuja! yanda ta fahimta kamar tafi kowa galabaita watakila saboda rashin sabo ne.
Ya riga ta fita daga motar yana tsaye yana jiranta ta fito. a gajiye likis ta fito, nan ta ga yanda ya sa bakin gilashi a idonsa tare da rufe kansa da bakar hular sanyi. ta dan tsaya a gefansa tana bin tashar da kallo! ga rana ta k'wallare! jama'a kowa na gabatar da abinda yake gabansa.
Hannunta ya ri'ke! ya jata suka nufi wata rumfar kwano gurin wata mai sayar da abinci bayerabiya. cikin harshen turanci suka gaisa kafin ya shedawa matar cewa ga ajiyar yarinya ya kawo mata ta bata abincin da zai isheta anjima zai turo a d'auke ta, wanda zai zo ya d'auke ta sunansa Sule."
Ta Amsa da "to
kafin kalle ta da fad'in." Zo ki zauna." tana nuna mata wata kujera.
Gabanta ya dinga duka yana daka! hawaye suka ciko idonta! ita dai ba ta ji abinda suke cewa ba amma ta fahimci kamar barin ta zai yi a gurin ganin yanda matar ke kallonta tana nuna mata gurin zama.
Ta ri'ke hannunsa tana girgiza masa kai! wasu zafafan! hawaye suka kufce mata.
Saurin d'auke kansa yayi ya cire hannunsa daga nata ya kalli matar da fad'in." Tana da matsalar kunne ba sosai take ji ba."
Da kansa ya ja hannunta ya kai ta ya ajiye a kan kujera, fuska a murtuke ya ce" Zan je wani guri ne shiyasa na kawo ki anan na ajiye amma zan turo a dauke ki kada ki damu."
Bai jira tace wani abu ba yayi saurin barin gurin ko waiwayenta be yi ba.
Duk kyawun abincin bai bata sha'awa ba, gabadaya ma ba ta cikin nutsuwarta, tsoro da fargaba sunyi mata dabaibaiyi, tunani ma ta rasa wane kala za tayi, sa'i da lokaci ta ke share hawaye tana bin tashar da kallo da nazarin wace rayuwa za ta fuskanta a nan gaba.
Ekeke matar dake sayar da abincin kenan, ta kalleta a karon da ba zai lissafu ba, domin tun tana lallabata ta ci abincin har ta gaji ta zuba mata ido! sai dai haka kawai take tausaya mata idan ta tuna cewa kurma ce ba ta ji sosai, ta yi tunanin abubuwa da yawa akan yarinyar, ta tunanin mutumin yayi kawalcinta ne domin ya dinga biyan buk'atarsa!
Sai daf da magariba Sule ya je domin d'aukarta!
Ko kusa ko alama bai gane ta ba ballantana yayi tunanin wani abu, ko da yake can baya da ya je binkice lokacin da abin ya faru duhun dare ya shigo da kuma cikowa ta mutane shine dalili.
Su ka gaisa da Ekeke kafin ya sheda mata shine Sule ya zo tafiya da yarinyar."
Ta ce." To kud'in abinci dubu biyu sai kudin jira dubu uku, duk da ba taci abincin ba ita wannan ba damuwarta bane. Sule bai ja doguwar magana ba ya ciri kudinta ya bata.
Jiki a sanyaye take binsa tana ta addua a cikin zuciyarta. ba ta 'kara firgita ba sai da ta ga shirgegiyar motar da ya bude mata wai ta shiga.
Ai sai hawaye suka fara zuba kuka sosai take! tana waiwaye a gurin, ta tsorata don gani take kamar sa ce za ayi."
Yayi -yayi da ita ta shiga amma fafur! ta' ki shiga sai kuka take tana nema ta tara musu mutane a gurin.
Wayarsa ya fito da ita ya kira maigidan nasa ya sheda masa halin da ake ciki.
Ya ce ya bata wayar su yi magana.
Nan ma da kyar ta karbi wayar jikinta sai rawa yake.
Da muryar da ya aro yayi mata magana da k'arfi yanda za ta ji. "Shahida ki shiga mota Sule zai kawo ki gidan da nake aiki wato gidan maigidana kamar yanda nayi miki bayani a can baya. zamu zauna a gidan ne a wani sashe da aka ba mu, ina nan ina jiran zuwanki."
Hankalinta ya kwanta jin muryarsa, a sanyaye ta ce." To." ta mika masa wayar tana godiya a cikin ranta domin wallahi tayi tunanin Sule sace ta zai yi.
*Normal group #500 Vip group 1k via 0542382124..Binta umar gtbank. idan kati za a turo sai ayi mini magana ta WhatsApp 07084653262...Mutanan Nijar za ku turo dala dari katin airtel. Vip gruop jakka daya.*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K7QH4idftZS5fSw7m2Rueb
*MAJANUNI!*
(The Unknown Rich Man)
NA
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
MANAZARTA WRITES ASSO..
_____
*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE🌳*
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_
_*infection*_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_
51&52
Girman gidan da tsaruwarsa ya firgitata sosai, sai ta 'kara shiga rud'ani zuciyarta ta cigaba da yi mata tunane-tunane marasa kyau! wani 'bangaran na zuciyarta na nuna mata cewa Baban- Baba mutumin arziki ne ba zai cutar da ita ba.
Tafiya mai tsayi su kayi a cikin gidan domin kwalta ce a shimfid'e har sai da suka kusa kai wa karshen gidan, sannan taga yayi parking, sai ta dinga kalle-kalle a gurin, tsit! sai shuke-shuke da kukan tsintsayen dake sauka a kan ciyayi gabanta ya cigaba da fad'uwa, cikin zuciyarta take ta nanata innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! ya bud'e mata 'kofar motar, alama yayi mata ta fito da hannunsa.
'Kin fitowa tayi ido jawur! take kallonsa kafin ta bud'e baki cikin yanayin maganarta tace." Ina ne nan din.?
Ya ce." Gurin da zaki zauna ne maigida ne ya ce a kawo ki nan"
Sai ta kasa fahimtar inda maganarsa ta dosa. kawai dai ta zuba masa ido tana ayyanawa abubuwa da yawa aran ta.
Cikin wayo da dubara ya ce." Ai yana ciki yana jiranki kamar yanda ya fad'a miki a waya." shima ya fadi maganar ne kawai! ba tare da ya san abinda ke faruwa ba.
Jin abinda ya ce yasa ta d'an ji 'kwari a jikinta, ta fito daga motar, yayi mata jagora zuwa wani ke'bantaccen sashe, ya bude mata ta shiga da bisimillah a bakinta! tare da jin fad'uwa gaba a tare da ita.
Tana shiga ya mayar da k'ofar ya rufe da key. ya bar gurin da saurin gaske.
Shuru falon babu alamun motsi! sai dai tsaf ko'ina a tsare babu datti a ko'ina.
Falo ne mai girma da kujeru masu kyau da labulaye! sai dak'in bacci guda biyu da kicin da bandaki duk a falon. a hankali ta zauna kan kujera mai cin mutum d'aya tana sake nazarin falon, gefe guda kuma zuciyarta sai bugawa take, shin ko daga ina mijin nata zai fito oho!
"Yallabai komai ya kammala, yarinyar tana wannan sashen daka umarce ni dana ajiye ta."
Sule ne ke wannan maganar lokacin da yake zaune a gabansa.
Ya cire farin gilashin dake sakaye a idonsa ya kalleshi sosai kafin ya ce."Matata ce Shahida."
Da sauri Sule ya kalle shi da dumbun mamaki a tare dashi ya ce." Matarka Yallabai?"
Yayi murmushi da fadin."Kwarai kuwa a jiya nan aka daura min aure da ita, itace yarinyar mutumin nan da nasa kayi min binkice a kansa."
Sule ya dinga jinjina al'amarin ya ce." Wallahi Yallabai ban gane komai ba, ita kanta yarinyar ban gane ta ba, sai dai nayi ta mamakin dalilin da yasa ka 'kebance ta a gidanka, sai na ce to ko da wani abu ne wanda kake shiryawa."
Ya ce." K'warai kuwa Sule kai din yaro na ne amintacce wanda na yarda dashi, nasan cewa ba zaka mance wahalhalun da nasha a can baya ba, auren farko ban yi dace ba, na biyu ma haka, wannan dalilin yasa gabad'aya nake tsoron duk wata 'ya mace saboda kaidi da sharrinsu, da yawa 'yan uwa da abokanan arziki suna fad'in ai ba duka suke da mugun hali ba, bahaushe yace wanda maciji ya sara idan ya ga bakin tsumma dole ya razana! a cikin zuciyata na cire aure gabad'aya daga raina! sabida samun zaman lafiya na, daga baya surutai na jama'a yayi yawa a kaina cewa ba girma na bane na zauna babu aure! wannan dalilin yasa na janye kudirina, auran wannan yarinyar nayi shi ne da manufofi da yawa. saboda haka kai kad'ai ne a gidan nan kasan wannan yarinyar matata ce, akwai wani shiri da nake akan lamarin duk don na gwada ta, da tarbiyarta." numfashi ya sauke kafin ya cigaba da cewa." Matata ce, amma za ta zauna a matsayin matarka na d'an wani lokaci, ina nufin ko da wani daga cikin iyali na zai tambaye ka sai ka amsa da cewar matarka ce, shikkenan, amma babu ruwanka da zuwa sashen, sai dai idan ni na aike ka gurinta."
Sule ya sauke zazzafar ajiyar zuciya, a sanyaye ya ce." To shikkenan Alhaji Allah ya sa a dace da tagari, ina yi maka fatan alheri ubangiji Allah yasa anyi kenan."
Ya amsa da "Ameen ya rabbil-alamina Sule za ka iya tafiya sai na neme ka."
Godiya yayi sosai kafin ya tashi ya tafi cike da mamaki a tare dashi, ko da yake bai ga laifin maigidan nasa ba, duba da cewa a can baya mata sun wahalar dashi don yayi hakan ba laifi bane.
Kuka taci sosai! ganin duhu dare ya shigo gashi babu haske a falon, ko'ina yayi duhu! sai labulan tagogin dake falon ta janye haske ya shigo, hakan yasa iskar sanyi ta dinga shigowa, jikinta ya dinga kyarma! da sauri ta takure jikinta akan kujera tsoro na sake kanainaye ta, bud'e tagogin da tayi sai idanunta ya dinga yi mata gizo ta dinga ganin gilmawar abubuwa da yawa. da sauri ta je ta sauke labulayen ta koma ta zauna, babu abinda ya fi damunta irin sallar magariba da isha'i! ga yunwar da take mugun sasakarta!
Jin motsi kamar ana ta'ba 'kofa ya sa gabanta ya tsananta fad'uwa! ta tsirawa kofar ido! duk da bata da tabbacin ganin fuskarsa saboda duhu amma a jikinta take jin shine zai shigo.
Ya shigo da sallama ciki-ciki. ba ta ji ba amma ta ga inuwarsa.
Tsaye ta mi'ke! har yanzu jikinta bai dawo daidai ba.
Ya kunna hasken 'karamar wayarsa, nan ya hangeta a tsaye ta tsura masa ido, lokaci guda ya fahimci firgici da tsoro a tare da ita.
Sunanta ya kira babu walwala a fuskarsa.
Ta amsa cikin rawar murya.
Ya ce." Zo ki kar'bi wannan ledojin kayanki ne a ciki."
A sanyaye ta 'karasa kusa dashi tasa hannu ta kar'bi manyan ledejojin dake hanunsa.
Bayansa ta bi ganin ya nufi d'aya daga cikin d'akunan dake falon.
Ya juyo ya kalleta, babu yabo babu fallasa ya ce." Nan d'akina ne kuma ina bukatar sirri! ki d'auki wancan dakin ya zama naki." ya fada yana nuna mata d'aya dakin. Yana gama maganarsa ya bud'e ya shiga ya barta a tsaye da ledoji a hannu.
Ta jima a tsaye a bakin kofar dakin tana tunane-tunane! daga bisani ta fara laluben hanya tunda ya shige dakinsa da hasken sai falon ya dawo inda yake duhu sosa! ta nemi kan kujera ta zauna ba tare da tayi tunanin shiga dakin ba, saboda tsoro take ji tana ganin gwara ta zauna a falon shi yafi mata alheri, amma haki'kanin gaskiya Baban-Baba yayi mata bazata! ba ta ta'ba tunanin zai mata wannan wulakacin ba, hawaye masu tsananin zafi suka shiga kwaranya a saman fuskarta.
Fitowa yayi daga d'akin ya ji shashshekar kukanta!
Tausayi ta bashi amma bai nuna ba, ya d'aga muryarsa sosai!" Ke menene? ki ke wa mutune kuka"
A zabure! ta juyo tana kallonsa! sai kuma ta sunkuyar da kanta amma ba ta fasa zubar da hawaye ba.
Ya ja tsaki! da fad'in." Ko yunwa ki ke ji ?"
Kai ta daga masa alamun hakane sannan tayi namijin 'kokarin fad'in." Ina so nayi sallar magariba da isha'i."
Ya ce." To waye ya hana ki? da duk zaman da ki ke a gidan ba kiyi sallar ba?"
Ta ce." Duhu ko'ina babu haske."
Ya ce." Ki bud'e wannan ledojin da akwai fitila da batiri a ciki sai ki kunna."
Da sauri ta fara dubawa, ya kunna mata hasken wayarsa har ta saita fitilar ta kama, sannan ya kashe wayarsa, ya kama hanyar fita, ta bishi da wani irin kallo zuciyarta sai bugawa take.
Tana d'aura alwala a bandakin dake cikin falon ta dinga jin motsinsa kamar yana shigowa da abu, sai da ta fito ne ta fahimci cewa kayan abinci ne.
Nan falon ta gabatar da sallolinta, ta jingina jikin kujera tana kallon shiga da ficensa tsakanin kicin da dakinsa.
Gani tayi ya zo ya zauna a daya daga cikin kujerun dake falon, ido ya zuba mata, sai ta kasa jure hada ido dashi, domin yanzu gabadaya tsoro yake bata, ya sauya sosai! ya dawo Baban-baba na asali wanda ta san shi a lokacin da yake kwanciya a 'kasan mota!
Gyaran murya yayi kafin ya kira sunanta yanda za ta ji.''
Ta amsa ba tare da ta kalleshi ba.
Ya ce." Nan ne gurin da maigidana ya bani domin na zauna da iyalina. bayan haka kuma sa'i da lokaci za ki dinga zuwa kina gaisawa da kakarsa wacce take zaune a cikin gidan, za ki dinga taimaka mata da wasu abubuwa duk da cewa akwai masu aiki amma kema zaki shiga sahun su, akwai kayan abinci a kicin komai da komai na bukata maigidana ya bani kudi nayi miki sayayya! a cikin ledojin nan akwai kayan sawarki kala hud'u da mai na shafawa da sabulun wanka da wanki da sauran tarkacen ku na mata, abinda babu kada kiyi 'kwaron baki sai ki sanar dani, amma ina so ki zauna da masu gidan nan lafiya! mussaman maigidana domin shi ya mayar dani cikakken mutum kamar kowa, wannan dalilin yasa nake so kiyi masa biyayya kamar yanda za kiyi min, duk wani abu da yake bukata kiyi masa.''
A sanyaye ta ce." Insha Allahu zanyi iyakar bakin kokari na, ni dai buri na ka ri'ke ni amana kamar yanda kayi alkawari!
Tsaki ya ja kafin ya mi'ke tsaye ya ce." Wace amana kuma? ki daina wannan maganar, domin kada ki manta fa ke kamar siyan ki nayi a gurin mahaifinki, saboda haka ki daina wannan maganar."
Wani irin kallo take masa tana jin maganganunsa na amsa kuwwa! a kunnanta "Kada ki manta fa ke kamar siyan ki nayi a gurin mahaifinki, don haka ki daina maganar amana." Wannan magana ta jima tana yi mata yawo a k'wa'kwalwarta.
Jin yunwa na nema ta halaka ta yasa babu shiri ta dauki fitila ta nemi hanyar kicin ta je tana laluben abinci, aikuwa ta samu fulas cike da dambun shinkafa wanda yaji kayan had'i! ga ledojin ruwa nan pure water ta dauka ta fito da fulas din abincin a hannunta.
*BINTU*Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K7QH4idftZS5fSw7m2Rueb
*MAJANUNI!*
(The Unknown Rich Man)
NA
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
MANAZARTA WRITES ASSO..
_____
53&54
A ta'kaice dai Shahida ita kad'ai ta kwana, domin tun da yayi fitar nan, bai dawo ba, tun tana jin tsoro har ta hak'ura ta barwa Allah al'amarin, sai dai bakinta bai daina addu'a ba har san da bacci 'barawo ya sace ta.
Motsin shigowarsa da asubah ya tashe ta, sai ta mik'e zaune da sauri tana laluben fitilar da gurin bacci ta fad'i a gurin, batiran duk suka watse
Shigowarsa yayi daidai da lokacin da ta gama gyara fitilar haske ya mamaye falon.
Ya kalle ta babu walwala a tattare dashi ya ce." A nan ki ka kwanta ne?"
Kanta ta daga masa alamar ."Eh." ya kama hanyar d'akinsa ba tare da ya sake wata magana ba, wannan ya sake tabbatar mata da cewa ba a gidan ya kwana ba.
Jiki a sanyaye tayi alwala ta fito anan falon dai ta gabatar da sallah, ta jima tana addu'a tana kuka sosai take neman sassauci a gurin mai duka domin ba ta ta'ba tunanin cewa zata fuskanci irin wannan matsala ba.
Sai da gari ya waye sosai ya fito cikin shiri ya d'ora rigar sanyi babbah da sabuwar hula irin ta sanyi ya rufe kunnuwansa sannan