Showing 18001 words to 21000 words out of 42609 words

Chapter 7 - A BAKIN AUREN KI Complete Writing by Feenah.doc

30 Aug 2025

1317

yau,dan ta saba, ga kafa sai ka'rkarwa
take. "Amma dan Allah wa zaka aura?.. Ba dai
Bintu ba?. A yadda ta t'sareshi da ido yasa ya
kasa magana,sai ya kalli Garba,kafad'arshi ya
daga mishi halamar ba ruwan shi. Sai da ta
maimaita kan ya daga mata kai. Murmushi tai da
yafi kuka ciwo,a hankali take neman juyawa wani
kanta ya sara gami da ganin duhu. "Kar ki min
fassara Salma,ba abinda ya had'ani da Bin... Luu
ta fara halamun zata fad'i, cikin zafin nama yai
taku daya ya taro ta. Gaba d'aya jikinta ya
saki,ga wani irin zafi kamar garwashi. "Salma..
Jijjiga ta ya fara,da sauri Aunty A'i ta shigo,sai
ga Mama na fad'in ta taimaka su sa Salman a
Napep gashi ta nemo.. "Mey zan gani haka... Da
sauri suka juya ganin Mama da tai turus ganin
yadda ya mammakale Salman,ita k'wa k'allonshi
kawai take hawaye nabin gefen idonta. Garba ke
mishi da hannu kan ya saki Salman amma kamar
yana zigashi,sai kara naneta yake. Gaida Maman
sukai da girmamawa tai banza dasu. Sababi
Mama zata fara Aunty A'i ta jata sukai waje.
Garba ne ya tsayarshi ganin yana neman cicci6ar
Salman. "Kasan dai yanzu ba a mat'sayin
matarka Salma take ba,kar ka nemo mana
magana dan Allah.. Harara ya sakar mishi,kan
cikin fusata yace "na mayarta toh.. Koh da
magana? Kai ya k'ada mishi, kan ya bud'e mishi
labule, "Dan Allah kaimu asibiti... "Auntyn mu..
Aunty A'i ya k'wada ma kira, da sauri suka fito
ita da Mama dake huci. "Asibiti zamu kaita, dan
Allah Mama ki yi hakuri na kaita.. Harara ta
sakar musu kamin tabi bayansu ta sallami mai
Napep sai asibiti. Murna ta koma ciki,da d'ukkan
hannu biyu mama ta dafe kai,jin rahoton likita
kan tabbatar da cikin Salma,dan haushi ba tasan
tai waje ba. Shikenan an 6ata mata shiri, ciki?..
Kai amma an sha da ita, sam ta zata fad'in A'in
ne dan a bar Salma. "Mama kiyi hakuri zata
samu lafiya,bari naje na siyo allurori mu dawo.
Kala bata ce musu ba, asalima ji tai kamar ta
rufeshi da duka koh ta huce. A gun Garba ya
k'ar6i kud'i,basu juma da tafiya ba sai ga Ummi
da Aunty A'i sun zo,tuni k'wa ta ware tana
surfawa Ja'afar Ummi na tayata. Kai Aunty A'i ta
k'ada, fatan ta a kullum Allah ya ganar dasu
Mama alkairin Ja'afar, alkairin da batajin koh su
wanda suka auri masu halin suna musu. "Mama
Salma fa matar Ja'afar ce har yanzun,don
musulunci ya mallaka mishi,matukar batai idda
ba,bare da kunne na naji yace ya mayarta
wallahi, dan Allah Mama ki sassauta, in har da
mey lefi aciki toh fa Salma ce.. "Ke dama ina
kika ga kishin kai?.. Ai guntunki ta tsotsa, shi
yasa sam kusan halin ku daya... Aure kuwa in dai
ni nai nakudar Salma toh ya kare ya gama.. Ba
ruwana da wani ya mayarta,sakaryan yaro
kawai,sam bai da zuciya wallahi. Ummi ce ta
amshe tana k'wafa. "Ai wallahi dad'i yake ji dan
yaga Abba na jibgarta,dama garin d'ukan yaja ya
rasa cikin ai da shi ya jiyo... "Ummi mey yasa ke
sam baki da mutunci ne?.. Baki Ummin ta turo,
"Ja'afar fa ba sa'anki bane,in bazaki g'yara ba
toh kar ki 6ata... Salma ita ta chanchanci komai
ba Ja'afar ba,gashi taja yace aure zai kara... A
zabure Mama ta jiyo, "Aure?.. Shine ki ke kuma
fad'a min ya mayarta?.. Kai ta k'ada, "eh lalle
Ja'afar, toh k'wa zama da kishiya ba dai y'ata
ba, karan nan zamu banje da Malam wallahi akan
maganar komen nan,sam naki jinin yaron nan
wallahi.. "Ni kam Mama bana ganin aibun Ja'a..
"Kimin shiru,kar ki gani din,amma aure angama.
****************************** Yau k'wananta
biyu aka sallame ta,fur Mama taki bawa Ja'afar
fuska,daga ina wuni lafiya shikenan. Su Abban su
Ja'afar harda y'an cikin gida sunzo sun jajanta
abinda ya faru. Kowa ya bawa bangarenshi
rashin gaskiya, take Baba yace ya mayarta. Kai
duk'e yace ai tun ranar chan ya mayarta,nan ya
ja mishi kunne kan sarar ki fita A BAKIN
AURENKI. A gaban su Abba ya kara tasa zancen
zai kara aure,cikin fusata Abbanshi yace "Ba mun
gama maganar nan da kai tun jiya?.. Wane aure
kuma bayan wannan da aka mayar? Kai yai kasa
dashi yai shiru, murmushi Abban su Salma
yayi,kamin yace "Kamin dai dai Ja'afar, fatana
Allah yasa auren shi zai zaunar da Salma a
dakinta ta rungumi ibada. Ja in ja sukai tai
t'sakanin Abban Salma da Abban Ja'afar, dak'yar
Abban Ja'afar ya yardewa Ja'afar kara aure. Ana
watse wa koh gama jan mota basuyi ba Mama ta
fara sababi,ita a fafur ba inda Salma zata,bata
zauna da kishiya ba,saboda haka ba mai zama da
ita a yaranta. Itade Salma bata um bata um-
um,sai hawaye kadai ke zuba,ita kad'ai tasan ya
zuciyarta take hautsina mata,ta faru ta
kare,tunda har manya sun amshi magana.
"Ja'afar? kishiya? Kuma da Bintu kawarta?.. Tab
da matsala. By Feenat Ja'afar
9/29/16, 9:10 AM - Queen Safiyyert???a: *A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
24_Daaga sosai akai da Mama akan komawar
Salma,sai da Abba ya bud'e mata uwata sosai
kamin harda Yayanshi ta saki aka ta koma din.
Ita kanta Salman yanzu ba kaunar komawar take
ba sai ta mot'so mata ga laulayi. Ga Ja'afar
tunda ya ji batun ciki ya kasa sukuni,kullum yana
zaryar dubiya da leda. Shi dai bai mat'sa da sai
ta dawo ba lokacin, dan g'yaran gida sosai yake
wanda Ummanshi ta bashi ya zauna aciki. Har
gida yau Abba yaje gun Abban sun kan lalle yau
Jafar yazo ya dau Salma. Da dare k'wa ta koma
dakinta. G'yaran nan gidan ya t'saya
chak,sakamakon aikinshi da aka mayarshi aka
bashi albashin da ya wuce shi,bai da mat'salar
kud'i yanzu,auren shi kawai yasa a gaba. "Ina
k'wana.. Cikin sanyin murya ta gaida shi kai
duk'e, kai ya daga kamin yace "ya jiki?.. Shiru tai
ba amsa. "Ki tashi ki zauna man.. Kai ta dago ta
k'alleshi kamin ta kada mishi, "A'a magana nake
son muyi da kai. Zama ya g'yara yana
sauraranta. "Mey yasa ka ke son auren Bintu?..
Da ido ta kafeshi tana jiran amsa. Murmushi yai
kan yai baya kad'an harda d'aura kafa daya kan
daya. "Saboda tana so na ne Salma.. Kai ta kada,
''kaima kana sonta?.. A bazata tambayar tazo
mishi,ga takafeshi da ido hawaye taro a idonta.
"Ki gane Salma, ba wai.. "Eh koh A'a?.. Amma
nake son ji kawai. Ba koh shakku yace mata "eh..
Amma.. Hannu ta daga mishi tana hawaye,
"Barni haka dan Allah,amma kasan Bintu k'awata
ce da koh?.. Ya zaka min haka? Kai ya kada
harda dariya, "A sani na banta6a ganin Bintu a
gidan ki ba,asalima... Sallamar Aunty A'i ce ta
kat'se mishi maganarshi,sai ya tashi dan dan
bud'e mata kofar,da kallo ta bishi tana mamakin
kalamanshi,sai kawai ta k'ada kai ta mike tana
goge ido. "Bissmillah mana Auntyn mu.. Yana
gaba ta biyoshi a baya, sosai suke dasawa da
Aisha,dan tasan abinda take sosai,shi yasa baya
6oye mata komai. Bayan sun gaisa ya mike yana
zai fita, kai kawai ta k'ada mishi,sai Aunty A'i ce
tai mishi a dawo lafiya. Zama Aunty A'i ta g'yara
tana ma Salman k'allon tuhuma. "Ashe Salma
baki fara g'yara ba har yanzun?.. Da rashin
fahimta ta k'allo ta tana hawaye, "Fita fa yayi
jiyan nan dawowarki amma har kin fara nuna
mishi baki sauya ba. "Aunty A'i ba abinda na
mishi fa Allah.. Katseta tai da fad'in "Amma zai
fita babu koh a dawo lafiya?.. Haba Salma,nan ki
ka dinga rantsuwar kin shiryu, koh har kin leka
makotar ne yau d'akko sabon darasi?.. Kuka ta
sa mata tana girgiza kai, "Haba Aunty
A'i,k'awata fa zai aura fa,taya bazanji zafinshi
ba?.. Da mamaki tace "wacce kawar taki? Cikin
kuka tace "Bintu,dalibar shi ce a Day school fa.
Ita dai ta hanga bata gano wace Bintu bace a
k'awayen,tasan sarai k'awayen Salma basu fi
biyu ba wanda tasan su. "Wace Bintu kuma cikin
k'awayen naki? Amma basan ta ba koh?.. Kai ta
daga mata, "islamiya mukai tare fa.. "Mtsww,
t'saki Aunty A'in tai tana k'auda kai, "har wata
kawar islamiya K'awa ce?, bana jin ko hanyar
gidan ku ta ta6a zuwa balle ta zama kawarki,
koh ta halarci bikin ki?.. Kai ta kada mata tana
goge hawaye. Cikin lallami ta fara lallashinta.
"Kar fa ki bari tun kamin ta shigo taci galaba
akanki Salma, yanzu ba lokacin t'sayawa kishi
bane a gunki, lokacin g'yaran kuranki na baya ne
Salma... Ki d'auka baki ma ta6a sanin wata Bintu
ba rayuwa,dan ba gaminki da ita sam. "Ki kuma
fidda zancen auren nan a ranki,dan koma meye
ke ce sila Salma. Nasiha tai ta mata tana kuka
har ta gamsu da bayaninta. Ta bata shawara
masu k'yau, ta kuma d'auka. Da ya dawo ya ga
chanji,sannan bata kara mishi maganar Bintu ba.
Yau satin ta daya da dawo wa,amma banda
Maman Abba ba wanda ya leko mata har Maman
Ummin, Ga sai wani kama mata kai Ja'afar din
yake bare tace zata leka,abu daya ta sani,shine
ta daina zuwa gidan kowa sai in ta kama.
Washegari har kofa ta rako shi zai fita tace zata
leka gidan Maman Ummi.. Yana fita yace mata
sai ta dawo kawai. Da k'allo ta bishi,sai ta ga
kamar gat'se ya mata,dan haka ta koma ciki tai
k'wanciyarta. Mukullin gidan da ake g'yara zai
fitar musu dashi sai ya dawo. A k'wance ya
sameta ido rufe a parlour,sai yai jim,ganin bata
fita ba har ya dawo. "Har kin dawo ne?.. Kai ta
girgiza mishi,sai yai d'aki yana tunaninta, haka ta
saba mishi kan gaba ta fand'are mishi,shi dai
yasan yai alkawarin mud'in ta tambaye shi fita
ya d'aina hana ta,yasan duniya makaranta,da
sannu zata gane abinda yake gujar mata. Koh da
zai fita sai ya kara nanata mata kan taje kawai.
Bai jima da fita ba ta fito,tana dan jin hayaniyar
su kasa-kasa. Har zatai Sallama sai ta ja ta
t'saya jin wata gulmar da suke. "Ai yanzu ya
zamarta mai gadinshi, tunda ta dawo ba inda taje
tana d'aka,koh duk sururin zai kara auren ne?..
Tana jin Maman Ummi tace "oho mata,ba ita
areni muje biki ba,mijina baya fad'a.. Muryar
Maman Abba tajiyo tana fad'in ''ni tausayi ma
take bani wallahi, ranar chan dana shiga duk ta
rame tai baki,kana yaronka da kai an ma saki
2.... Baya tai cikin sanda danjin wani na shirin
fitowa. Gida ta koma ta cire hijab tai dabar a
kujera, tun yaushe haka take faruwa da ita?..
Ashe ita k'allon mara wayo suke mata acikinsu?..
Kai ta daga sama, lalle ta gane mey Ja'afar yake
nufi da mutunci yake nemar mata.. Yau ta gane
ashe in an yi gulmar wani da kai yau gobe da kai
za'a kafa ai taka. "Allah na gode maka daka sa
na ji na kuma gani. Tabbas Ya Ja'afar babban
gata yai mata. Toh a ina ma suka samu labarin
za ai mata kishiya?..har dare tana neman amsa.
Ranar har kukan bakin ciki tai na taraiyarta dasu
Maman Ummi. Tuni ta tattare kowa ta wat'sar
shi,duk da ba duka aka taru aka zama daya ba.
Ranar Maman Waleeda da suke kira uwar tsoron
miji ita ta zo mata harda nasiha har gida,matar
da koh gidanta sai tai fita ashirin bata leka
ba,kuma makociya ta kusa,har misali tai mata da
Maman Ummi. "A kaf unguwar nan bana tunanin
da matar da take cikin takura irin na Maman
Ummi Salma, ke shaida ce,in kinji gidan yai shiru
ba koh tarin yaro kasan uban na gida. Sannan in
zai shekara ba taje ko'ina ba shine dai dai a
wajenshi,duk fita in zatai satar hanya take tasan
in ya fita da yamma sai dare,amma a gun kuri
tafi kowa iya dadin magana,da ina cikin su,daga
baya na gane taraiyyata baza tai dasu ba,sai na
zabi zaman gidana ya fiye min alkairi sama da
yawan gulma. "Ka'rkara in abu ya faru in leka a
tsatssaye in dawo, dan Allah ki iya kafarki
Salma,dan zasu kai ki su baro ne kawai. Kai ta
k'ada mata, "Na gode Maman Waleeda,Allah bar
zumunci,kuma InshaAllah naji bayanin ki,duk da
mun kusa tashi a unguwar ma duka InshaAllah.
Anan ta sanarta za ai mata kishiya,k'warai ta
jajanta mata kan ta kara da y'an shawarwari,tun
daga ranar mutunci da Maman Waleeda
suke,kusan duk yamma tana turo mata su
Waleeda taya fira,har lokacin tashinsu yazo.
***************************** Cikinta yana da
wata biyar lokacin auren Ja'afar saura sati. Sam
bazaka zata Salma bace, dan tamkar bai dameta
ba haka tai a auren. Har ranar Ja'afar yana fad'in
wai ta daina sonshi gaba daya,koh kishi bata yi
zai kara aure,murmushi kawai ta masa,dan tsaf
ta kula da rawar kan da yake k'wana biyu. "Ba
k'ya shirye-shiyen komai gashi lokaci ya taho
fa... Tamkar ya choka mata abu makogwaro taji
wani iri,kawai sai ta sa mishi ido tana k'allo.
Tabbas rawar kan Ja'afar karuwa take akan
auran nan,banda haka wani irin tambaya ce
wannan?... Shikam tunani yake yadda Salman ta
g'yaru har kullum,a ganinahi halin ko'in kula da
yake nuna mata ne akan fita. "In da hali zan fita
kar6o wasu kayana unguwar Ummi. Kafad'a ya
daga mata,kan yace "sai kin dawo... Yai waje.
Baki sake ta bishi,tun bayan dawowarta ta kasa
gane inda Ja'afar ya dosa,abu yake mata tamkar
ya kosa da zaman ta a gidan. Gashi tun kamin
amarya ta tare har ya sallamata,wai ko'ina nan
gaba in zata kawai taje,dan yanzu bai son 6acin
rana irinta da. Toh mey yake nufi? By Feenat
Ja'afar.
9/29/16, 9:11 AM - Queen Safiyyert???a: *A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
26_Kowa bin kofar dakinta yai da kallo, yana
murna ba'a rikicin mata biyu a gidanshi yau gashi
an fara,dole ne tun wuri yai ma tufkar hanci. Har
yayi dakin Salman sai ya t'saya, dole ne ya nuna
mata kuranta, in da tai mishi fitsara ya k'yale toh
yanzu bazai d'auka ba,dan ba ita kadai bace a
gidan,kawai sai ya juya dakin Bintu. Kuka take
yana ta fadanshi taki kulashi, chan kuma sai ya
sassauto, "Ni tashin hankali ne bana so a gidana
ne,tun wuri ma in zaku had'a kai ku had'a, dan
ba mai chazan hawan jini. Kai ta dago tana mishi
k'allon tuhuma, "Au shine dalilin da yasa ka fad'a
wa matarka baka so na?.. Ni nace ina son ka
koh?.. A haka za ai zaman lafiyan?.. "Ke kinga
bana son iyayi,dawa nai wannan zancen?.. Da
sauri cikin kuka tace "da matarka man,wato
harda fad'a mata kwantai nayi nai ma tallan
kaina.. "Ban san anyi maganar nan ba Malama,ki
ma cire zargin ni na fad'a mata, bari na je zata
fad'a min yaushe muka fara y'ar sharri da ita...
Waje yayi zuwa dakin Salman. Kai Bintu ta k'ada,
"ashe munafuka karya take dan ta had'ani fad'a
da Miji,toh karyarki taci karya,Allah sa ya k'wada
mata mari tukuicin sharri. Ita kam tanajin bud'e
kofarshi ta mike tare kama k'ugu ta k'ank'ance
ido. "Salma yaushe muka fara y'ar sharri dake a
gidan nan?.. Yaushe nace miki Bintu ce tai min
tallar kanta na aura?.. Harara ta sakar mishi da
k'allon kar ka rainan hankali. "Ka nad'e taburmar
kunyar ka man ta haka,wato kayi amarya shine
ka zabi ka tuzartani agunta,karafkaf abinda ya
faru ta fad'a mini,toh da ka fad'a mata saura
igiya daya ta aurenka a kaina sai mey?.. Baki ya
saka cike da mamaki,lalle ya shiga tarkon kaidi
na mata, wato kowacce sharri take neman k'ulla
mishi a gun y'ar uwarta ashe?.. Bai da tace wa,
kawai sai ya juya zai fice, da sauri tace "a ka
fita man,dan nayi imani bazaka karyata cewar ba
kai ka fad'i ba... "Idan kuma habaici da iyayi
kake neman matarka ta dinga min dan ka huce
haushinka na da toh bissmillah,dai dai nake dana
sa kafar wando daya da kowa a gidan nan
wallahi.. Juyowa yai yana kallonta, sai tai d'aki
ta barshi t'saye baki sake. Titi ya fice ko ya
samu sa'ida, lalle yau ya jinjinawa sharrin
mata,amma kaf yafi jin haushin Salma,dan sam
yanzu ya fuskanci fitsararta tafi ta da yawa. Tun
daga ranar ba jituwa t'sakanin matan, daya in
Bintu ta fad'awa Salma sai ta fad'a mata
dubu,daga karshe ta bige da kukan bakin ciki, har
mai gidan yazo ta kit'sa mai karya da
gaskiya,wani sai dai ya bata hakuri, dan a
ganinshi yanzu Salma tafi karfinshi,dan da ya
mata magana ita y'ar dika take,daga shi har
amaryar zata chake tass, sai dai yai abinda zaiyi.
Shi yasa shi kuma ya t'siri mata t'siya,in dai zata
kona mishi rai,toh shi kuma zai ta biyewa Bintu
suna ta mata feleke a t'sakar gida, daga karshe
kam sai yaci nasara,dan haka zata shiga d'aki tai
ta kukan bakin ciki,a nan zai ta mata dariyar
keta. ***** Sallama taji kamar ta Maman Ummi
da Maman Abba,lekawa tai ta window, sune
kuwa, "munafukan Allah ta'ala kawai... Ta fada
tana kokarin ta fito rai 6ace,dan tai imani duk
abinda take fuskanta yanzu da sa hannun su
aciki... Chak! Taja ta t'saya rike da labule a
hannu ganin Bintu ta fito da gudu danjin sallamar
su. "Sai yau Aunty Ladi zaki zo min? Har nayi
fushi ai.. Baki sake Salma take k'allonsu,tana
k'allon suna nuno kofar dakin da baki suna ma
Bintun kuskus tai baya da sauri. Ido ta rint'se
tare da cije le6e,lalle mutum mugun ice ne,yanzu
ta gane inda Bintu ta samo duk wasu
_information_ na zaman aure nata ba agun
Ja'afar ba,ido ta bud'e, ta d'au alhakin Ja'afar,
har rantsuwa yai mata amma taki yadda. Karshe
har raba shimfida tai dashi akan maganar har sai
da ya gamo ta da Aunty A'i aka shirya. Zama tai
tana jiyo shewarsu a dakin Bintun. Har kullum
bazata daina nadama akan taraiyarta dasu
Maman Ummi ba,tasan duk fushin Ja'afar ne da
t'sinuwar mala'iku ke bibbiyarta. ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Har hawayen
bakin ciki tayi yau,tai kuma alkawarin daina
sa6awa mijinta ko da taji haushin shi. T'sakar
gida ta fito bayan ta g'yara fuskarta, tai sa'a
kuwa sun fito zasu tafi suna ta dariya. Ganinta a
t'sakar gidan yai bala'in saita nutsuwar su,a
t'saye take k'yam tamkar wata soja ta had'e rai
tam,ido cikin ido take k'allonsu,tuni suka hau
inda-inda, "dama kina ciki?.. Sannun ku da gida..
Harara ta sakar musu,ba shiri sukai hanyar
waje,Bintu ce ta t'sayar su, "bari na raka ku
hanya Aunty,ina zuwa na kira mai gida izinin fita.
Duk tana k'allonsu,har tai ma Ja'afar waya wai
za tai rakiya waje ya bata izinin fita. Bokiti ta
zaburo da sauri tai hanyar fita,da sauri sukai
waje sun zata kansu zata iyo,kawai sai ta ja
t'saki ta shige band'aki. "A toh na zata koh rafka
mana zatayi ai,g'wara muyi ta kai ta kai,dan
wannan da gani zatai kishin hauka... Dariya suka
sa tana jiyo su ta band'aki daga zauren sunki
tafiya. Ruwanta na cika da ta tara ta bud'e
band'akin a hankali tai zaure, basu nufa ba sai jin
saukar ruwa sukai akansu har Bintun. Bokitin ta
d'auka tai kansu dashi a sukwane, da ture ture
suka fita waje da gudu. Tana haki ta leko kofar
gidan ''Ashe karyar munafurci kuke, da ku t'saya
na g'wada muku aikin mahaukaciya, shegu gadon
na aiya,a haka zaki kare Maman Ummi wallahi,
InshaAllah kema dubinki ta kusa cika. "Ke kuma
yau mai rabani dake a gidan nan wallahi sai
Allah, yau zaki ga karyar iskanci. Gida ta koma
tana hakin daga ruwa bucket guda da tsohon
ciki. A t'sakar gidan ta zauna tana maida
numfashi a hankali, ta jima da zama kamin taji
tafiyar Bintu cikin sand'a, kofar ta zubawa ido
tana harara, kai ta leko dashi dan ganin koh
Salman bata nan sai suka had'a ido. "Wallahi
baki isa ki ce zaki hanani shiga ba, in gaske ne ki
bari na shigo na shirya in fad'an ki ke nema dani
ba hauka ba. Murmushi tai daga inda take, "Lalle
kinyi kuskure in kina zatan zan iya had'a jiki da
karya irin Bintu,haukar nake son sauke miki aka
yau ai, gaba kin d'aina irin kuskuren nan ina zuba
miki ido kawai,yau dole na fidda ki cikin gona ta.
Like ? 1 ? Reply ? Report ? Jul 31
Feenat Ja'afar Novel's
"Karya ki ke wallahi ki iya koyan hankali Salma,ai
fad'a da makami tsoro ne,ki ajiye bokitin mu
gabza da hannu in kin is... "Meye hakan ke kuma
Bintu?.. Juyawa tai da sauri,tana ganin Ja'afar ta
sau kukan munafurci harda kank'ame shi,wai
Salma tace in ta shigo sai ta kashe ta da duka
da bokiti bayan ta jika

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login