Showing 33001 words to 36000 words out of 42609 words

Chapter 12 - A BAKIN AUREN KI Complete Writing by Feenah.doc

30 Aug 2025

1309

Hajiya
ta k'arfen.
Tunda suka rabu tazo gida tana tuna abu uku,
tabbas a yanzu bata da ra'ayin auren mey
mata,dan taga aya akan Bintu.
Sannan bata son mutum mai irin kud'in Alhaji
Usman sam a rayuwarta.
Gwara ma Kamal dan shi matashi ne kamar su
Ja'afar, kuma yafi kwanta mata a rai,gashi da
saukin hali da saukin kud'i.
"Oh ni y'an nan,ashe arziki ke binki Salma a
rayuwa?..
K'allon Maman take yadda take daga abubuwan
da Alhaji ya bata,ita dey nata ido.
"Bana jin koh lokacin y'an matancinku kun ta6a
had'uwa da irin wannan, babbar harka ai tayi y'an
nan...
"Mama ni fa mutumin nan bai kwanta min ba
sam Allah,gashi har ya fara maganar aure tun
yanzu,ga yana da mata fa,ga ni sam irin kud'in
nan baya...
Baki sake Mama ke k'allonta,tuni ta tsayarta
cikin fad'a.
"Rufe baki ni sauraniyar y'an iya t'sari, ashe har
yau kina nan da halin nan Salma? Arziki na binki
kina zura da gudu?..
"Ina ruwanki da matarshi?.. Koh a kanta zaki
zauna?..
Kai ta girgiza zatai magana ta dakatar ta.
"Koh dai Salma hudubar yaron chan tai tasiri
akanki?..
Kai ta kad'a,
"Allah Mama ba haka bane,ni ina tsoron kishiya
ne,kinaji fa wai aurenshi uku suna rabuwa sai ita
ke zama...
"Sai mey toh?.. Kar ki bada mata mana Salma?..
Baki sake take k'allon Maman,kamar ba ita ke
fad'in ba mai zama da kishiya ba a yaranta tunda
itama bata zauna ba,wace daga ce ba'aci ba
lokacin auren Bintu da Ja'afar amma yanzu kud'i
ya warware Mama?... Kat'seta tai,
"Saboda haka komai yace ki ce toh, in ma ita ke
fidda su toh ke zama daram,dan wannan ba
gidan fita bane in an shiga...
Hawaye ke zubar mata yayin da tazo k'wanciya
tana tariyo zancen Mama, dole in dai tana son
faranta mata wai ta ba wa Alhaji dama.
Waya ta d'auka jin shigowar text message,tasan
na Ja'afar ne.
_"Salmatee,remember, a heart dat truly loves
never loses hope..but always believes in d
promise of love,no matter how long d time and
how far d distance,at d right time,love will fine a
way".._ ki rike alkawarin ki,love you..
*Ja'afar*
Kukanta ne ya karu sosai bayan ta gama
karantawa, tabbas in ta cigaba da sauraran
kalaman Ja'afar zasu sa ta karaya har ya ci
galaba akanta..
"Bani da kamar ka har kullum Ya Ja'afar, sonka
gareni ba mai misaltuwa bane,amma kai kaja
mana koma meye...
Fuska ta goge sakamakon jin tahowar Mama da
Miemie na kuka.
Washegari kanta t'saye ta bawa Alhaji damar ya
turo magabatanshi kawai koh ta huta da
dawainiya da son Ja'afar.
Sabon sim ta siya tasa a sabon wayar Alhaji da
ya bata,a haka suka raka wata kusan biyu, duk
da tai kewar text da kiran Ja'afar din.
Shikam yana chan hankali tashe na rashin samun
wayar Salma, ga Abba ya sanarshi kar ya sake
ya dawo sai an nemeshi a makaranta,
Duk da an sanarshi ana kawo Miemie gidansu ta
yini.
A jikinshi yaji abu na faruwa,duk sai yaji bai da
nut'suwa sai ya je gida dan tabbatar da
zarginshi.
***
Tunda daga d'anno kanshi layin su Salman ya ja
ya t'saya. T'saye take da dan murmushi a
fuskarta, sanye cikin favorite dinshi riga da skirt
na atamfa purple, tai kyau matuka gyalen nan a
kafada,daga inda yake zai iya gano bakin
gashinta a tufke ta chan kasan dankwalinta,
tasha ado tamkar zata party.
Wani abu ne yazo dai dai makogwaronshi ya
tsaya,kishi...
Bai san ya isa gun ba sai da yaji ana "lafiya?..
Kallo shi yayi, duk sai yaji yau baida ma k'warin
g'wiwar fad'a,Salman ya kalla,da sauri ta kawar
da fuskarta gefe ta had'e rai.
Sai ya dawo kan Alhajin,tsaf sai ya haifi
Salma,sai t'sabar kud'i da jindadi da suka 6oye
shekarunshi.
Kallonshi yake tun daga sama har zuwa kafa, so
yake ya gano ta inda ya fishi har Salma ke mishi
murmushi haka. A zuciya yace
"Babu... Sai dai kud'i kawai da sa kaya masu
t'sada.
"Kai fa,daga ina ba koh sallama?..
Cike da haushi ya kallota, "baki sanarshi ko ni
waye ba ne?.. Kan Alhaji ya dawo,ba shakku
yace "matata ce ita,zaifi mana k'yau in ka daina
zuwa gunta Alhaji.
Murmushi yayi Alhajin,kan ya kallo Salman, "sai
kinji ni kawai.. A takaice ya k'alli Ja'afar din,ba
sai an fada mishi waye ba,halamu ya nuna
tsohon mijinta ne,har zaga wa tai ta rufe mishi
tana daga mishi hannu d'auke da murmushi, har
ya kule tana daga mishi hannu kan ta d'au
kayanta koh ta kanshi bata tai hanyar gida,da
zafin nama.
"Wato abinda ki ke kenan tun bayan tafiya ta
shine yasa ki ka kashe waya? Salma mey yasa
kike son ki 6ata min rai wai?.. Jibi fa shigar ki,ji
gashi a waje,wace iriyar rayuwa ki ka za6a
mana?
Cike da fada tace
"Wace iriyar ka za6arwa kanka dai Ja'afar.. Ya
zaka zo kana fad'an wata iriyar magana mijin da
zan aura?.. Karan nan bazan dau abinnan naka
ba wallahi, aure zamuyi dashi nan da wata biyu...
Sai kayi abinda zaka yi.
By
Feenat Ja'afar.
[8/7, 11:07 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
36_Kan yai k'wak'waran mot'si ta shiga gida tare
taru kofa harda sa sakata.
Jiginna tai hawaye na neman zubo mata,daga
yar bular dake jikin kofar ta leka waje,kofar gidan
yake kallo jiki a sanyaye kamar yasa kuka,juyawa
tayi hawayen dake makale mata ya zubo,dak'yar
ta seta kanta ta shiga ciki rai cike da tausayin
Ja'afar.
Kusan kullum zai zo ba zuciya dan bata baki
akan Alhaji tana mishi wulakanci,shi kam Alhajin
har dariya yake bashi wani sa'in, dan baijin da
abinda zai iya rabashi da Salma a dai dai lokacin
nan,sai dai jin saki uku ne kawai sai ya bar jin
komai,iyaka ma yai ta tusa ma Ja'afar din bakin
ciki in ya gansu da kalamai ma Salman.
Biki ya karato ga makaranta,amma haka duk
week end daga Zaria zai zo kan batun Salma ta
janye zancen bikin nan.
Duk ya fita a hayyacinshi duk akan auren Salma.
Da halamu ya fara hankalin daina zuwa gun
Alhajin,sai dai in yazo ya tsaya chan gefe sai
tazo shiga ya tare ta da magiya.
Yau saura k'wana biyu biki, sai gashi shi da
Garba,dawowarsu daga gidan g'yaran jiki kenan
ita da Ummi.
Turus ta ja ta t'saya ganin Ummi ta wuce ita ya
tare mata hanya.
"Ka ga yau bani da lokacin jin wannan
mahaukatan zantukan naka,jibi iyanzu na d'aura
aure, ya kamata kasan inda dare ya maka,
sabuwar rayuwa zan fara,saboda haka kai yanzu
ya rage ma,danni yanzu baka gabana...
Kai ya kad'a mata,
"Karan nan bazan hanaki aure ba Salma,sai dai
ba da Alhaji ba.
Baki sake take kallonshi, Garba ya nuna,
"Garba zaki aura Salma,kimin wannan alfarmar.
Kai ta dauke daga kallonshi ta k'alli Garban
wanda shima ya cika da al'ajabin kan maganar
Ja'afar.
Sai ta girgiza kai da murmushin takaici.
"Tanan kuma ka bullo min?.. Auren kisan wuta
Ja'afar? Lalle kayi nisa ba zakaji kira ba.
Bayab hannunta tasa tana goge hawayen idonta.
"Wai ka zata ni din auren kisan wuta zanyi da
wanda zan aura?.. Kai ta kara kadawa,
"Kai kuskure toh,dan ni aure zanyi na tsakani da
Allah,ba wai nayi na fito ba Ja'afar..
"A'a Salma,ba haka ne nufi na ba.. Da muryar
kuka ta tareshi,
"Hakane man,haka kake nufi,wato ka kawo min
abokin ka na aura bayan wani lokaci ya sake ni
sai ka halartawa kanka ni koh?..
Baki sake duk suke k'allonta,ganin yadda hawaye
ke zubar mata.
"Jahilcina bai kai nan ba Ja'afar, a bazan ta6a
abinda ka ke so ba, a gareni yanzu k'allon Yaya
nake ma,da kuma uban yarinyar dana haifa,
bayan haka.. Kai ta girgiza, kan tace "you mean
nothing to me a yanzu kam..
Jin baice komai ba yasa taci gaba.
"Banzaci haka daga gare ka ba Garba,a ganina in
shi ya 6ata kai mey dawo dashi kan hanya ne,
wallahi auren t'sakani da Allah zanyi, ku sani
kuma auren so zanyi,wanda nake fatan mutu ka
raba ne,dan Allah,dan kaunar ka da Allah ka bar
bibiyata,dan Allah..
Shiru tai dan ganin shima idonshi ya taru da
hawaye,da sauri ta shige gida tana goge
hawaye..
Har ta shige yana binta da ido ba magana, sai
hawayen da ya zubo mishi shar, da sauri yasa
hannu ya share.
Kafad'arshi Garba ya dafa, "kaji zancenta, tai
mana fassara baibai,ya kamata kai hakuri ka bar
kulata in har kana wa Allahn data had'a ka dashi.
Kai ya daga, "InshaAllah..
~~~~
Taro ne iya taro,taron shedar auren Salma da
Alhaji Usman, daga inda yake t'saye a chan nesa
da kofar gidan yana k'allon komai har aka shafa.
Juyawa yai da jaka biyu hannunshi tare da sanya
bakin glass dan 6oye sirrin dake idonshi.
Yasan yanzu kam Salma ta mishi nisa.
"Mama taki ta bud'e dakin fa,daga ina jiyo sautin
kukanta Allah.
Ta window Ummi ta leka,gata k'wance ta tasa
tsohuwar wayarta a akan fuska tana razgar kuka,
So ba karya bane Salma.
By
Feenat Ja'afar.
[8/7, 11:08 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
37_Har aka kai amarya gidanta bata bar kuka
ba,dayawa sun zata kukan na Mama ta cire
Miemie ne, dan basa ji koh auren farkonta tayi
haka.
Kowa ya wat'se sai ita kad'ai, ko'ina take kallo a
dirare, gida ne iya gida,tun bata fita ba ta
zaga,yau gata a gidan da ba Ja'afar, ba kuma
Miemie,tuni ido ya cika da kwallar tuna baya.
Anya tai ma Ja'afar adalci kuwa?.. Anya bata ci
amanar so ba kuwa?.. Ta sani da takai Ja'afar
bango,hakan yasa bai kara waiwayarta ba,ta
yuwu yai zuciya... Ido ta goge da sauri jin motsin
za'a bud'e d'akin.
Ango ne yasha babbar bunjima da rike da leda,
bakin nan har kusan kunne,jan mayafinta ta kara
yi ta rufe fuska.
"Amarya! Amarya!!.. Ba k'ya laifi wai koh kin
kashe dan maigida koh?..
Murmushi ta k'akalo mishi, zama yayi a gefenta
tare da ajiye ledar a gefen bedside, bata aune ba
taji ya yaye mata g'yale yana kallon fuskarta.
Alwala yace ta d'auro suyi nafila,dan wai
agareshi babbar kyauta ce ita daga Rabba.
Sun gabatar da duk wani al'ada,sai dai har ango
ya d'ane gado amarya tana t'saye a gaban
madubi
sai sininiki take,gabanta sai mugun fad'uwa yake
tamkar wacce tai auren fari.
Murmushi yayi da kanshi ya taso ya karaso har
gaban madubin tare da kamo hannunta.
"Muje ki kwanta haka dare nayi sosai..
Kamar yarinya ya kwantar ta gefen shi yana kallo
da murmushi.
Salon ya sauya,tuni ta fara digar da hawaye,shi
kadai yake kid'anshi yana rawarshi,sai dan sautin
kukanta dake fita kad'an-kadan,wanda a gareshi
tamkar zigi take mishi.
Kai ta juya ta kallo Alhajin dake bacci
hankalinshi k'wance,abu uku sun hanata bacci,na
farko kukan zamanta ta wani ba Ja'afar ba,na
biyu tunawa da Miemie, na uku minsharin Alhaji..
Har gari ya waye bacci sai jefi-jefi-jefi ke
dibanta,sam taki jinin minshari kusa da ita,tsaf
yake hanata bacci.
Shikam da farin ciki ya tashi irin na sabbin
ango,ita kam da ido kawai take binshi.
Tara sai ga yaron uwargida ya kawo abinci,da
fara'a ya gaida ta,kanshi ta shafo kan tace ya
sunan shi?
"Sunana Ja'afar".... Kallonshi take da mamakin
jin sunanshi, koh dai bataji dakyau bane?...
Kat'seta yai da fad'in
"K'anwata kuma Nabila,Umman mu tace sai
anjima zamu shigo kar mu tashe ki a bacci.
Murmushi tai mishi yace ya tafi.. "Ja'afar...
Ido ta rint'se jin maigidan ya kira sunan,ba shiri
ta d'au abincin tai kitchen.
Bayan sun gama komai yace suje bangaren uwar
gida zai magana dasu.
Batai zatan da kishiyoyi masu kaunar kishiyar su
ta ra6e su sama da matar Alhaji ba,sosai tai
mata bazata,tun tana d'ari-d'ari har ta saki jiki da
ita da yaranta, musamman Ja'afar..
Yau Miemie ce tazo mata,sai murna take taga
Auntyn ta.
Duk babyn ta rame,yaye bai amsheta ba.
''Miemie, ga nan Abdul yazo ku tafi gun Mama
koh?...
Kafad'a ta make halamar taki tana neman kuka,
"Yi hakuri gobe zanje gida mu taho koh?..
Kuka ta saka mata baji ba gani, sai mak'e
kafad'a take tana ita "um-um.
Sai ta sallami Abdullahi kan gobe yazo ya d'auke
ta, har ya jima da tafiya Miemie bata bar kuka
ba.
Sai um-um kawai take fad'i, suna haka Alhaji ya
shigo,duk yai kicin-kicin da fuska, cikin fad'a-
fad'a yace ta lallasheta man,shi baison hayaniya
bare ta yaro...
Baki sake take kallonshi,kaya ya ajiye ya juya ya
fice harda dan tsakinshi,toh mey yake nufi?...
Y'arta ta d'auka ta sa6a a baya sukai kitchen
tana fad'in tai shiru ba inda zata toh,kan aje
ko'ina sai ga nan Miemie harda dariya tana bata
labarin Mama cikin gwaranci.
Har dare ba Alhaji ba duriyarshi,abinci ma sai
Ja'afar ya turo ya d'auka.
Suna k'wance Miemie sai k'allonta take,gani take
kamar guduwa zata yi ta barta.
Kanta ta shafo tana mata murmushi,
"Yi baccinki my Miemie, ina nan fa tare da ke
kinji?.
Kai ta daga mata tana k'allonta.
"Antee...
Kai ta dago kan tace
"Na'am Miemie nah...
"Abba...
Tsam tai tana k'allon Miemien,Abba? Ta nanata a
ranta.
Murmushin dole ta k'akalo tana fad'in Abba yana
nan Miemie,bata aune ba taji ta kara fad'in
Abba...
Hawayen da take makalewa ne suka zubo
mata,da halama yanzu Miemie ce matsalar
ta,dan zata dawo mata da hannun agogo baya.
Da dabara ta d'auke hankalinta daga tunanin
Abban ta hau lalla6ata har tai bacci.
Photocopyn Ja'afar ce Miemie,barin yanzu data
kara girma, tunani take koh dai Ja'afar har yanzu
baya zuwa gida, laifinta ya shafi Miemie?
Dan tasan sai Miemie ta kwana biyu bata ganshi
ba take nemanshi haka.
Tana nan har maigidan ya shigo,sai wani k'allo
yake aikama Miemie wanda ta kasa fassara shi.
Tun daga ranar ya zamana in dai Miemie zata
zo,toh fa zata rasa gane kan maigidan, ta rasa
dalili, musamman in tai la'akari da hadithn
hausawa na Duk mai son uwa toh yaso d'iyanta.
Ranar har ta kasa d'aurewa tai mishi magana,
amsar da ya bata ta jima tana sata hawaye.
Ga Miemie da kulafuci bare tace kar a sake kawo
ta,asalima duk randa tazo fara'arta karuwa take.
Sa6anin in tazo mata,data gane sai take d'akko
ta duk randa bata da girki su k'wana, ranar da
maigidan yake da ita su wuni ai rabuwar kuka
har uwar.
Allah yaga Miemie kadai take gani taji sanyi a
ranta.
Ranar suna fira a bangaren uwar gida take mata
korafi kan halin maigidan akan Miemie.
Murmushi tayi kamin tace
"Sai kinyi hakuri da halin Alhaji Salma,ba tone-
tone ba,a'a kawai dai ya kamata ki sani, Alhaji
sam baya son yara,musamman hayaniyar
su,hakan yasa ya d'aurawa kansa kin haihuwar
k'arfi da yaji, nayi ta zaman takaicin halin nan na
Alhaji har t'sawan shekara bakwai,a lokacin aka
tada kayar baya kan sai ya kara aure tunda ni
sun zuba ido shiru.
"Hanna ta shigo itama ta shekara biyu shiru, ni
dai nasan kusan kullum yakan tasa ni da Hanna
dan shan maganin daukan ciki.
Ana nan ranar wata kawar Hanna tazo suna
jajanta ko dai matsalar gun mijin ce,toh a ranar
dai asirin Alhaji ya tonu,dan kawar Hanna taga
magani tace na hana d'aukar ciki ne.
"Ranar muka mishi tawaye har Hanna,in takaice
miki yace shi bai shirya haihuwa ba yanzun,anan
sukai baram-baram da Hanna ya bata takardar
ta.
"Haka sauran mata biyun kowa tazo zai fad'a
mata ra'ayinshi, da taga bazata iya ba zata fice,
duk kuwa da tarin arzikin shi,a lokacin muna da
shekara kusan sha uku da aure,koh mai zaiyi na
daina shan magani, hakurina ya kare,nan na kai
kara gun Hajiyarshi.
"Ya saduda muka haifi Ja'afar, yace daga nan ta
isa haka,wai incigaba shan magani,a gabanshi
zanyi kamar nasha, daya kauce zan zubar.
Koh shekara Ja'afar bai ba na samu cikin
Nabila,cikin da a kullum sai naga tasku gun
Alhaji,gar da gar zai nuna bai kaunar su,barin in
Ja'afar na kuka,haka nai ta hakuri har na haifi
Nabila.
"Yanzu kam magani sai dai shi yai tasha,amma
banda ni,kinga Nabila har ta shiga shekara ta
biyar.
Tsam tai tana tunani bayan kammala bata labarin
waye Alhaji, ita ba kullen ne yafi damunta ba
sama da rashin son haihuwa..
A kalla yanzu ta doshi wata na biyar a gidan nan
amma ba bayani,sam bata kawo wani abin
ba,ashe wannan ne dalili?..
Bazata iya tuna ranar fitarta ta karshe a gidan
nan ba,tun kwa bayan aure sau daya taje gida sai
dai aukin waya koh azo mata, lalle duniya labari.
"Zaman hakuri kawai zamuyi Salma,sai adu'ar
shirya in da rabon zai gane, amma shawarata
gareki ki rike y'arki, dan kar kiyi sakiyar da babu
ruwa tun kina yarinyar ki dake,shi ba ruwanshi.
Kai ta kad'a mata,Allah sarki Ja'afar, ta tuno
lokacin data fara period tana kukan samun ciki
yana murna.
Ta tuno da abinda yace mata
"Allah sa Miemie ta samu k'ani a kusan nan...
Ta tuna data hau bori ya hau lallashinta,
harda alkawarin shi zai mata reno in bata shirya
ba...
"Ba kuka zakiyi ba Salma,muyi ta adu'a.
Hannu takai fuskarta, ashe kuka take bata sani
ba.
By
Feenat Ja'afar.
[8/7, 11:08 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
38_Ranar sakwa-sakwa ta yini tana tuna halin
Alhaji, bai da mugun hali koh daya sai na bakin
kulle da kin yara,bayan nan baza tace ga mugun
halinshi ba.
Zataso sanin wane hali Ja'afar yake ciki a
yanzu,dan tabbas tasan ya zuciya da ita,tunda
gashi ance koh wajen Miemie baya zuwa sai
aike?..
"Mey nai kenan?.. Mey nayi ni Salma?.. Mey yasa
ban iya jure zama ba aure ba a rayuwa kamar
yadda yaso muyi..mey yasa?..
Juyi tayi tana hawaye,
Kila rabon Miemie kadai take dashi a
duniya,tasan kuma aure dai ana yinshi ne dan
abu biyu,samun zuri'a na daga ciki, gashi ita
anan ana son a haramta mata.
Tabbas d'aukar y'arta shine babban mafita a
game da yadda take jin son ta haihuwa a yanzi..
Wayarta ce tai ruri, a hankali ta goge hawayenta
ta tashi,
"Billy" taga a rubuce.
Da sauri ta saita kanta kamin ta daga.
"Sarauniyar kirki kina gida ne?...
Dariya ta danyi kan tace tana nan..
"Toh ina kofar gidan ki yanzu haka.
Da sauri ta tashi dan g'yara fuska tana fadin gata
nan zuwa.
Sai da ta tabbatar da ba mai gane tai kuka kamin
ta fita kofa shigo da Billy.
"Matar nan kinganki kuwa?.. Kin zama big
madam da gaske fa.
Murmushi tayi tana kar6an Ilham.
"Kai Billy banda fa sharri..
Dariya tai tana "ba wani sharri, koh dai mun
karu?.. Miemie tayi k'ani?
Shiru tayi tana murmushin iya le6e.
Bayan sun gaisa take ce mata ai daga wajen
Miemie suke,tai ta kukan zata zo tana jin tace
gun Auntyn ta zata.
Murmushi tai tai kasa da kai,Allah sarki Mimi.
"Yau Miemie aka kaima ziyara kenan?.. Murmushi
Billy tai kan tace "ai duk sati sau biyu Abban
Ahmad (Garba) ke zuwa dan dubo ma Abban
Miemie lafiyarta.
"Shine yau muka je tare,Miemie akwai
wayo,kusan wata shida amma bata manta
Abbanta ba,tana jin muryarshi a waya ta fara
murna..
Shiru tai tana nazari,ba dai ace tun tafiyar
Ja'afar ya zuciya ya bar garin nan ba?..
"Ja'afar kanar wasa,kinga wata shida muke nema
yaki waiwayo mu,sai kulafucin a dubo mishi
gudan jininshi... "Rayuwa kenan fa,kana naka
Allah na nashi,in kai hakuri sai ka ga na Allahn
ne dai dai a gare ka.
"Amma Abban Miemie namijin duniya ne,mai
ra'ayin kanshi,tunda ya jima haka nasan alhinin
aurenki ne bai sake shi ba.
Shiru tai tana jinta,a hankali ta fara jin nadamar
wulakancin data kartawa Ja'afar, Abban y'arta.
Yau Billy ta kawo fitina,dan har ta tafi bata da
sukuni,har sai da ta tiki kuka son ranta taji
dad'i,yanzu burinta Miemien ta dawo gare ta.
Koh da maigidan yazo yaga yanayinta yasan
tasha kuka,da ya tambaye ta sai tace Miemie
take son gani ta d'akko ta.
Anan ya tada mata bori,har sai da tai da na sanin
maganar Miemie.
Ba abinda yafi kona mata rai sama da yadda
tanaji tana gani yai mata haramiyar
makaranta,sannan Mama ta goya mishi baya,abu
goma da ashirin sun had'e mata.
Adaddafe akai shekara, lokacin tuni ta jima da
d'akko y'arta,dan bazata iya da rashinta ba a irin
yanayin da take na son yaran nan.
Sai sai wani abu,fur Miemie taki jinin Alhaji, ko
abu take in zai kwan dubu yana ta bari bazata
koh k'alleshi b??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a,asalima har wani kumbura baki
take in ta ganshi,Salma tai magana tasa mata
kuka,ga bala'in Alhaji na wai yarinya tun kan ta
girma ta rainashi shi da gidanshi, har harara wai
take mishi...
A tunaninta kamar Miemie wane harara ta sani
bare wai kumbura mishi baki?.. Amma dan a
zauna lafiya yasa kullum take kwa6ar ta.
A gaban kowa har su Nabila zatai wasa harda
k'yak'yatawa, amma fa koh a nan bangaren taci
ka'ro da Alhaji zata d'unkume,tamkar ba ita
ba,shima kwa da harara zai bita, wani sa'in harda
t'saki..
By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 9:33 AM - Queen Safiyyert???a: *A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
39_"Aunty A'i na rasa yadda zanyi ne,yadda yake
nuna t'sanar Miemie karara yafi damuna,abu
kadan tayi sai ya hantara,t'sawa, ga kullum yai
ta surutun wai tana hararar shi,koh fa wai turo
mishi baki,nawa take fisabilillahi?... "Allah bansan
haka agolanci yake sai gun Miemie. Murmushi
tayi "bari muga,ke dai sa ido... ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login