Showing 3001 words to 6000 words out of 42609 words

Chapter 2 - A BAKIN AUREN KI Complete Writing by Feenah.doc

30 Aug 2025

1305

ciki take ciki na ganin Ya Ja'afar
d'inta yau. Sai murmushi take saka cike da
kunya ita kad'ai kamar yana ganinta. A haka har
Ummi ta cimmata, dan harara ta sakar mata
gami da had'a rai. "Yanzu Ummi kinyi dai dai
kenan? A y'atsine ta k'allo ta tana ninke g'yale,
"da nai miki mey? Iya jaraba.. Kai Salma ta k'ada
kan tace "dan t'sabar wulakanci ashe Ya Ja'afar
yasha zuwa gidan nan nema na in yazo gari
muna sa6ani sau biyu yana fad'a miki amma
koda wasa baki fad'an ba? Allah kin ban haushi..
"Mtsww.. T'saki Ummin tai kan ta ta6e baki,tuni
Salma ta kule,sam ta t'sani t'saki, bare ga Salma
K'anwar ta. "Na zata wani abin kirkin ne wallahi,
toh meye nawa dashi da zai mayarni y'ar aiken
shi?.. Anki a fad'a miki d'in ki d'au mataki toh.. A
tunzure Salma ta tashi tayo kan Ummin sukaji
Mama na magana a kofar d'aki, "Kun fara cin kan
koh? Yara kamar masu ganin hanjin junansu?
Baya Salma tai tana harar Ummi, "Mama kimin
tsakani da ita toh,ta fita harkata dan bata da
kunya sam wallahi.. A y'atsine Ummi ta harare
ta,"ka ga kunya manya,akan wannan mai dan
uban d'acin ran kike wannan kumfar
bak'in?...baki ta ta6e kan tace "Kin k'wa kama
abga in dai Ja'afar ne.... "Ke Ummi... Bana son
fit'sara fa,kullum ina sanarki Salma yayarki
ce,dole ki bata girma, koh nai mugun sa6a miki..
Maza bata hakuri. Tana chunno baki ciki ciki ta
bawa Salma hakuri,ita kam har ta fara hawayen
bak'in ciki. "Toh fito ki biyoni.. Mama ta nuna ma
ummin kofa da hannu.. *By* *Feenat Ja'afar*
Like ? 1 ? Reply ? Report ? Jul 20
Feenat Ja'afar Novel's
*A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
7_Washegari ma ta fito zata makaranta sai gashi
shi da abokinshi Garba suna tafiya. Ido ya kura
mata ganin tai kasa da kai tana murmushi. Sai
ya k'ada kai suka karasa,cikin sanyin murya ta
gaida su,Garba kad'ai ya amsa,shikam Ja'afar
k'allonta kawai yake yana murmushi, kamar mai
son sai sun had'a ido. "Malama Salma fa kar tai
latti a mata bulala abokina.. Kasa ta kara da kai
tana dan dariya, shikam gogan sai binta yake
kawai da k'allo,kan ya nuna mata hanya kan wai
su rakata hanya. Ba musu ta wuce suka
jera,Garba sai shakiyanci yake zuba
musu,murmushi kad'ai ne nasu har suka zo bakin
_gate_ d'in islamiyar. Ka'ro na farko suka k'alli
juna cikin ido,da sauri ta K'awar da kanta tana
murmushi, shikam harda k'ada kai, tuni Garba ya
harbo jirgin nasu,sai ya hau shafa ha6a yana
k'allonsu,musamman abokinshi da yace bai san
so ba.. Hannu Ja'afar ya kai aljihu yana lalube,ita
kam sai ta hau satar k'allon shi ganin mey zai yi.
Da mamakinta k'wa sai gashi ya fito da naira
ashirin yana mika mata. K'alloshi tai tana kunshe
dariya,sai ta k'ada mishi kai, "Kud'in tara ne fa
Salma, ki k'ar6a ki sai hambididi... Dariya Garba
ya fara harda rike ciki,itama wacce take rikewa
ta fito fili, sai ta sa hannu a baki dan rufe sautin
ta.. Shikam Ja'afar kawai sai ya hard'e hannu
yana K'allonsu, musamman Garba yadda yake
k'yak'yata dariya. Shikam ba kasafai ya iya
dariyar keta ba irin ta Garba,shi yasa wataran
yakan kularshi a abu. "La Malam Ja'afar......
Gaba d'ayan su suka juya k'allon mey magana.
Ja'afar take k'allo tana murmushi halamar jin
dad'in ganin shi, shikam tuni ya had'e rai yana
k'allon ina ma ya santa. Kamar tasan mey yake
tunani tace *"Bintu*(Na Rufaida Omar) ce,dalibar
ka a day... Salma ya k'alla wacce itama ke kallon
Bintu,kan ya k'ada kai, "toh Bintu.. Salma Bintun
ta k'alla jiki a sanyaye ganin ko in kulan da
Ja'afar ya mata,"shiga za kiyi ne Salma? kai ta
kada mata, jiki a sanyaye tai gaba Salma ta daga
musu hannu halamar sai anjima tana murmushi.
Da k'allo ya bita cikin wani yanayi, da ko shi
kanshi bazai iya fassara wa ba. Kai ya k'ada kan
ya k'allo Garba wanda k'wachokam ya maida
K'allonshi kan abokin yana dariya kasa-kasa.
Harara ya maka mishi kan ya juya,sai k'wa
Garban ya kara sa dariya yabi bayanshi. "An
fad'a tarko makal ana hura mana hanci,sai anyi
magana kace wani "mey nene so? Ni ban sanshi
ba.. Karyan kawai,koh makaho ya laluba yaji ka
afka so ai yanzu kam. Chak! Ja'afar ya t'saya
tare da juyo wa gun Garba. "Mey kenan haka ke
nufi?.. Harara Garban ya k'wada mishi kan
yace"kar ka maida ni yaro fa malam,kana nufin
baka san kana son Salma ba ko mey?.. K'allonshi
kawai Ja'afar ke yi cike da mamaki,a hankali ya
furta *"SO"*?... Hararar shi Ja'afar ya kara,gani
yake kamar ya raina mishi hankali ne. "Kaga
Malam kawai kai saranda haka,tuni tun yadda ka
ke ta yawan fad'in Salma nasan a rina,ka bar
wani k'wane-k'wane. Shi dai Ja'afar ya
t'sunduma tunani maganar Garba,wai So? Salma
kuma?. *By* *Feenat Ja'afar* ?^NWA.
9/29/16, 8:56 AM - Queen Safiyyert???a: [7/21, 12:28 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
8-Har Ja'afar yazo k'wanciya yana tunanin
kalaman Garba,tabbas biri yaso kama da mutum,
dan yana jin sauyi tun ranar farko da ya dora
idonshi a Salma bayan dawowar shi.
"So"... Ya furta a hankali, murmushi yai kan ya
k'ada kai,dan yana da aiki a gaba,dan bai san
kom ba game da lamarin.
Tun daga ranar ya zamto kusan kullum da
yamma yakan raka Salma islamiya,koh da yana
shago zai zo ya ganta kawai,hakan na sashi
nishad'i, yau da gobe har ta fara sakin jiki dashi
a karo na biyu.
Sai ya zamana itama in bata ga Ya Ja'afar a
ranar ba batajin dad'i sam,haka zata k'wana
sukuku.
Shirye-shiryen bikin Aunty A'i suke,duk sun shiga
_busy_.
Da yamma sun fito bak'in shagunan su Abba
siyayyan kayan fitar biki, tasan kuma d'uk layin
ba inda ya kai shagon su Ya Ja'afar kawo kayan
k'yali, amma da tayi magana Ummi sai ta tanka.
Kai duk'e yana duba takaddu,kamar
_papers_,chak ya t'saya da abinda ya yake yana
murmushi kai duk'e, ajikinshi ya ji kamar Salma
na kusan shi,itama dai satar k'allon shi take,tana
ganin zai dago tai sauri ta juyar da kai tana
murmushi.
Fara'ar shi ta karu dan hango Salman.
A hankali ta dan kara K'alloshi,sai k'wa suka
had'a ido,da azama tai kasa da kai tana
murmushi har suka karaso.
Tuni Ummi ta had'e rai ganin Ja'afar a shagon,a
takaice ta dan harari Salman ganin sai wani
munafukin murmushi suke sakar ma juna,baki ta
ta6e kan a ciki ta gaidashi tai cikin shago ta
barsu nan.
_"My_ kanwa,.. Kai ta kara duk'ar wa tana
gaidashi,sai ya k'ada kai,ya rasa irin kunyar
Salma gare shi yanzu,abu kad'an duk'ar da kai.
"Biki ya karato ba? Kai ta daga mishi tana dan
k'allon _net_ d'in gefenshi da murmushi.
Tashi yai zuwa gun inda take k'alla ya fara
saukar mata dasu.
A hankali ta tako gun dan zabi,d'uk sun mata
k'yau.
Sai ta dan kallo shi, "malam Garba fa? Murmushi
yai yana k'allonta, "yaje inda aka tura shi
_service_ nashi yaga gun,gobe zaki ganshi.
Kai ta k'ada, d'uk sai taji ta kasa za6a ganinshi
kusa da ita.
Kamar ya sani ya kara s'akko mata da wasu.
"Bari na tayaki za6a.
Kai kawai ta k'ada mishi tana k'allon kayan,kan
wani _purple_ idonta ya kai,a hankali ta kai
hannu zata ja shima ya kai zai d'akko shi yana
fad'in
_"purple_ zai miki k'y... Shiru yai ganin itama shi
ta rike,ya rike rabi ta rike rabi.
D'uk sai suka k'alli juna ba koh kiftawa da wani
yanayi...
Tamkar wanda aka lika _poster_ a gun haka suka
kame da k'allon juna.
Ummi ce ta kat'se su da fad'in
"Ga nan wasu materials y'an leda Salma masu
kaman _lace_....
Shiru tai ganin wani ikon Allah,baki sake take
k'allon su,tuni Salman ta sakar mishi tai baya
tana sunke kai da murmushi tare da amsar kayan
hannun Ummin tana sunyi k'yau ba dan ta gani
ba.
Murmushi ya sakar mata shima,har yanzu yana
rike da _net_,ya rasa mey ke damun
K'wak'walwar shi akan Salma.
*By*
*Feenat Ja'afar*
[7/21, 8:05 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
9_Baki ta dan ta6e,kan a y'atsine tace ma Jafaar
d'in "mun zabi wannan, zamu nuna ma Baba sai
ya bada kud'in.
Murmushi yai yana k'allon gun Salma,itama
idonta na kusan hannunshi.
"Koh na tafi ne Salma? K'allo Ummin tai,kan ta
k'ada kan suka yi hanyar fita a shagon,a hankali
ta dago mishi hannu halamar _bye_.
Kai ya k'ada mata shima ya dago mata nashi.
Tai k'walli da Ja'afar ta ji dad'i,har aka je gida
bata umm ba um um,sai Ummi ke ta zuba kamar
kanya, yadda zata zuba wanka a bikin Aunty A'i
har ta kule.
Da dare sai ga yaro wai ana kiran Salma.
Rai had'e ta k'allo yaron, "je kace bana nan...
Shiru tai ganin yadda mama ke mako mata
harara, "anya yarinyar nan kalau kike kuwa? Wato
sai dai ai ta min asarar hoda da kazal a banza
ina tufka kina min warwara koh?
"Farin jini Allah ya bayar kina ma kanki bak'in
ciki? Haka zan ta barar miki ni baki ban bare na
maida g'urbin abinda na fitar Salma?..
Maman ta k'allo da mamaki,toh rokon samari
mama take so ta fara komai? Allah yaga ta t'sani
fita zance.
Amma ganin yadda mama ke wanke ta yasa ba
shiri tace ma yaron "yace ma waye?.. Kai ya
daga mata,"wai ince inji
"Ja'afar in kin tambaya... Ai koh karasa wa nai
ba ta mike,tuni murmushi ya maye g'urbin 6acin
rai, da k'allo mama ta bita, kamar ba ita ce
yanzu ba.
Yau kam ga su Salma harda mit'sika hoda da
_lips stick_ har ta d'au hijab ta kara k'allon
madubi,kawai sai ta janyi g'yalen Ummi tai waje.
Shine kuwa yana jingine da gidan,wani murmushi
ta saka na farin cikin kara ganinshi a daren.
Da sallama ta karasa d'uk da ba wani haske gun
sosai,amma sai dan sinke kai take kamar rana.
Bayan sun gaisa kowa yai shiru kamar basu abin
fad'a.
Chan dai ya nisa ya miko mata ledar hannunshi.
Kamar mai neman ba'asi ta t'saya bata k'ar6a
ba.
"Ajiya na kawo kimin zuwa gobe ne,ba wani abun
ba naga kina tsoro.
Murmushi tai kan ta amsa tana k'allon Ummi
zata wuce,koh ci kanku bata ce ba ta shige gida.
D'uk sai Salman taji wani iri,Ummi sam taki jinin
Ja'afar ta rasa dalili.
Ba jimawa yai mata sallama dan ya rasa abin
fad'i shima.
Dama da Garba ne yau kam da zai iya fad'in
komai ga Salma.
***
Tunda daga lokacin Ja'afar ke zuwa gun Salma
jefi-jefi,d'uk da har yanzun bai furta mata so
ba,amma ita a ganinta d'uk acikin so ne.
A k'wan a tashi gashi har ta kammala secondary,
wannan itace tafiya mafi tsawo da Salma tai bata
ga Ja'afar ba,kusan wata bakwai.
Tun tana damuwa har ta hakura ta rungumi
karatun ta na fita.
Gasu yau sune a gida,d'uk an rame anyi baki.
By
Feenat Ja'afar.
[7/21, 10:10 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
10_Babban tunaninta bai wuce d'uk t'sawan
lokacin nan da aka diba ba Ja'afar ba labarin shi
ba,tasan yakan je mata ziyara makaranta koh a
t'satt'saye ne,ga ita ba waya ba balle ta neme
shi koh lafiya?
K'wana biyu da dawo wa yau d'ai ta kudiri niyar
fita jin ba'asi,koh Garba in ta gani.
Hijab d'in _mss_ d'inta har kasa ta sa harda
nikaf.
Sai d'ai har ta gama zagayen layin ba wanda ta
gani ciki,kawai burinta ganin Ja'afar ne.
Iyanzu kam tasan tai nisa kan sonshi ba kad'an
ba,sai d'ai ita yanzu ta fara tantama.
Har zata juya ta tuna da shago,d'uk da tasan
yanzu ba kasafai yake zama ba tunda ya samu
g'urbin koyarwa.
Sai dai tai chan d'uk bata tunanin ganin nashi.
Daga d'an nesa ta t'saya kusa da wata bishiya ta
d'an kare ba mai ganinta, da sauri ta juya tare da
dafe kirji,zuciyar ta sai bugawa take da k'arfi.
Yanzu ta samo amsarta da kuma kokwantan ta
da ya zama gaskiya... Bata aune ba sai jin
hawaye tai na bin kuncinta cikin nikaf d'in.
A hankali ta fito daga bayan bishiyar tare da kara
k'allo shagon.
Murmushi yake harda darawa, ita kuma budurwar
sai washe mai baki take tana ta mai zuba,rike
yake da hannun wata y'ar k'yak'yawar yarinya
fara kamar yayarta.
Ji tai wani abu ya tokare mata kirji,da sauri tasa
hannu ta dafe gun,ga hawaye yaki ya d'aina
malala.
Lalle tai wautar kin kula kowa sai Ya Ja'afar da
bai furta mata so ba.
Ido ta rint'se ganin ya d'akko mata wani
had'adan net purple yana bata,wato har kalar da
yasha sanar mata yana so ya bata?
Tai imani mai irin wannan zankadediyar budurwar
fara ba abinda zai da ita Salma baka.
Hannu tasa ta cikin nikaf d'in tana goge hawayen
dake zuba mata.
K'allo sun da zatai taga Ja'afar ya zuba ma inda
take ido,har budurwar na k'allo itama,da sauri ta
juya gabanta na fad'uwa, kar dai ace ya gane ta?
Tab,da k'wa ta bada kanta wallahi.
Juyo wa ta kara,sai karaf suka kara had'a ido da
Ja'afar. Ba shiri ta tare mai adaidaita ta
shige,tana k'allo ya bi napep d'in da k'allo yana
girgiza ma budurwar kai.
Kawai sai ta sa kuka mara sauti tare da cire
nikaf d'in.
Lalle tai wautar zurmuwa ga soyayyar Ja'afar,??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
soyayyar da ba'a ma bayyana mata ita ba... Ya
Ilahii.
**************************
"Oh! Man Ja'afar, dama kana k'allon mata har
haka? Bafa koh kiftawa?
Murmushi yai mata tare da girgiza kai, "Hala tai
kama da Salma ne? Danma da hijab ga kuma
nikaf..
"Kusan hakan ne, jikina ya bani kamar Salman ce
kam..amma nasan ba ita ba ce ma.
Dariya ta danyi har hakorinta farare suka
baiyana,kan tace "sannu _Romeo_ toh, ni
sallameni kan Amal ta fara neman mamanta,
amma ina mamakin yadda ka iya zaben kaya da
color, halama kana son _purple_? Murmushi
kawai yai mata,kan ya k'ada mata kai halamar
eh.
Ita kam Salma tana zuwa gida ta taho da yaro a
kofa ya kaima mai Napep kud'in shi.
Allah yaso ba kowa t'sakar gidan mama na d'aki.
A katifa kawai ta zube ta sau kuka,sai da tai mai
isarta tai shiru tana maida numfashi.
Chan kuma kamar wacce aka t'sikara ta mike
zaune.
Tabbas Ja'afar bai ta6a nuna yana sonta ba
kam,d'uk zuciya ke yaudarar ta.
Asalima da "K'anwata" yake kiranta, kila hakan
ne tun da,ita kad'ai ke kidanta, gaba d'aya ta
gama kore masu sonta ita a dole ta riki Ja'afar.
Hawaye ne ya kara zubo mata tunawa da yadda
yake washe ma budurwar nan baki.
Tasan yadda Ja'afar yake a gaban mata baya
wargi,baya sake fuska ma bare har yai musu irin
wannan tad'in.
"Tabbas budurwar sa ce,nai wauta ni Salma...
"Lafiyar ki kuwa kike maganganu ke kad'ai ya
sabuwar kamu?
Kai ta dago jin batun Ummi tana wannan y'atsine
matan.
Sai dai ganin irin yadda idon salman yadda yai
ja,ga kuma hawaye yasa ta mat'so
"Mey ya faru kike kuka haka?.. Ai kamar mai jira
a ta6ota ta kara sa wani kukan mai sauti.
Tuni kuma sai Ummin ta zauna tana lallashi da
fad'in lafiya?
Ita de sai kukanta take baji ba gani.
Tashi Ummin tayi,"bari na fad'o ki da mama
toh,kila k'ya fad'a mata ita... Da sauri ta rike
mata riga, "ni ba komai.. Marata ke ciwo da
bayana kawai.
T'saki Ummin tayi, "Allah kina da aiki a gaban ki
Salma,kukan jinya sai kace wata yarinya.
Ita dai tana jinta ta karaci kardinta tai waje,a
hankali ta zame ta k'wanta,sai sauke ajiyar
zuciya take.
*By*
*Feenat Ja'afar*
?^*NWA*
[7/22, 12:02 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
11_Kan safiya har ta gama tunanin abin da zai
fisshe ta.
Hakan yasa t'saf ta tashi kamar ba ita taci kukan
nan ba. Aunty A'i yau za'a kaima wuni,tun (12)
suka fice ita da Ummi.
Chan suka yini har dare,a kafa ta ratso ita kad'ai
sakamakon Ummi da ta biya kar6an _style_.
Tunda tazo layin su Ja'afar d'in taji gabanta na
fad'uwa, duk da bata koh k'alli hanyar gidan ba.
"Abokina ina ka tafi ne daga lissafi kai shiru?
"Ba kaga kamar Salma ba waccan mey tafiyar?
Ido Garba ya k'wara, da mutum,amma a duhun
nan bazai tantance ba,kawai sai ya k'ada mishi
kai,
"A cikin duhun daren nan ne har zaka gane wake
tafi.... Shiru yai ganin Ja'afar d'in yai gaba,da
sauri yace "wai mey ke damunka ne? Ina za
ka?.. Binshi yake shi kuma yana bin mai tafiya a
duhun.
"Salma"... Chak! Ta t'saya dan jin kamar an kira
ta,a hankali ta juya,da dan tazara a tsakanin su
kad'an, amma hakan bazai sa ta kasa gane ya
Ja'afar ba koh a cikin dubu,hakan yasa cikin
sauri ta juya ta chigaba da tafiya,har dan gudu-
gudu sauri-sauri take.
"Mey zai fad'a min kuma? Ta fad'a cikin ranta.
Har kusan layinsu ya bita, tsammanin shi koh
tsorata tayi,amma tabbas wannan Salma
ce,kawai sai ya t'saya a dai-dai layin nasu yadda
bazata ganshi ba,da hasken inji a layin, yana gani
ta t'saya ta waiga,kan da sauri ta shige gida.
"Amma fa baka aiki sam Jaa, wai har nan ka
biyota kage ma koh aljana ce a daren nan?
Juyawa yai yana girgiza mishi kai,"Allah Salma
ce,toh yaushe ta dawo?.. Baki sake Garba yace
"hadda rantsuwa? In Aljana ce fa mai siffar ta?.
Harara ya sakar mishi kan ya juya suka tafi.
Ita kam tana zuwa gida Abba da Mama suna
t'sakar gida ta shigo sai haki,tuni k'wa Abba
fad'a ya karu, kan mey yasa sukai dare?
Tuni tai zuru zuru,fad'a sosai tasha,saura
Ummi,d'uk da laifin Ummin har sukai daren.
Washegari kusan yamma sai ga nan yaro kan ana
kiran Ummi da Salma inji su isma'il.
Harara Salman ta k'wada ma Ummi, kan tace
"yanzu sai da kika fad'i ma mutanan gidan mu
kika huta koh? Allah ban san yayi6e ni.
Hararar itama Ummin tai mata,"arziki na binki
kina guduwa,kowa yazo kice bai miki ba,ki mayi
karatun ta nut'su wallahi,dan aure zanyi ni ba
jira..
"Keai Kowanne dan chaburos ma yazo Ummi a
shirye kike, toh ba dani ba.
Yankan farcen Ummin ta bari tai hanyar d'aki
tana fad'in"sai kiyi ta zama kar kiyi aure,har
mahadi ya baiyana.
Cikin kuluwa zatai magana sai ga Mama ta fito a
d'aki, ashe d'uk tana jin su, "toh k'wa maza ki
wuce ki je tun kan na sa6a miki,daga yau na
d'aina zuba miki ido ba fus bare ass Salma...
Yarinya sai taurin kai,ace koh kishin yadda y'ar
uwarki take shiga take fita da y'an k'wabai ba
kiyi? Toh na gaji da gafara sa dan ban hangi
kaho ba... Maza ki shiga daga ciki ki g'yara ki
wuce...
Kai kasa Salma tace "toh.. Ita kam tana
mamakin halin Mama har kullum akan su,sai dai
tana tuna Ja'afar tuni taji tana da muradin
fita,tunda wanda take danshi bai ma san tana yi
ba.
G'walo Ummi tai mata,kan tai waje tana sai ta
fito.
Bata aune ba taji mama a d'akin nasu, bani waje
ki ga,da kaina sai na g'yara ki...
Baki sake take k'allon Maman,aikwa ta zage ta
hau cha6a ma Salma k'walliya irin wacce bata
ma san mama ta iya ba.
Fad'i take "na rasa gane wace iri ce ke
Salma,arziki na binmu kina zura da gudu,d'uk
wani buri da na sa kanki kin rushe shi, in banda
haka a jiya kad'ai kina ga irin bajintar da Ummi ta
shigo dashi daga gun isma'il yake ko wa?
"Haba k'alle ki a madubi man,san kowa kin
wanda ya rasa... Tana yi tana g'yara mata
d'aurin dank'wali.
"Maza ki fita kan Abban ku ya dawo ya hana
ruwa gudu..
Kai ta daga zata d'au hijabi,da sauri Mama ta
warce, "g'yale zaki sa matar Malam,koh a
Shari'ar a haka ake son a ganki,ta ina za'a yaba
in kin maka hijabin? Toh ba walima nace kije ba..
Kai ta k'ada, ta zama tamkar rakumi da akala,sai
yadda mama tace.
"A'a, ko ke fa,k'alli kanki a madubi ki ga man,ai
da banbanci, maza je ki... Kai ta kara k'ada
mata, har zatai waje da sauri Mama ta kara
kiranta.
Turare ta fesa mata,kamar tace ba k'yau
mama,sai dai taja tai shiru.
"Ki murmusa man Salma,haba..murmushi ma ado
ne ga fuskar Y'a mace...
A yadda maman take yi bata ma san sanda abin
ya bata dariya ba.
Allah ya gama su da uwa "LASHE MONEY", har
ta fita kuwa tana murmushi, mama sai barta.
Suna t'saye gaban wata jar _CRV_ tare da
Ummi,d'uk dinsu sun zubo mata ido.
Ita kanta tasan tayi ne, fari da manyan ido kawai
budurwar Ja'afar zata fad'a mata tasan.
Doguwa ce ita dai dai misali,farin jinin samarin
zamani,fatarta a goge take mai launin Wankan
Tarwada(black beauty), tana gashi ga gashin
ido,gata fuska doguwa,gata tana da diri dai dai
so,d'uk komai ya ji ba bau ba.
Ya dace kam tai amfani da lokacinta tun yanzun.
Cikin takun da ba irin na Salma ta da ba ta
karasa gun su Ummi,ga murmushin nan dan
_beauty

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login