Showing 27001 words to 30000 words out of 42609 words

Chapter 10 - A BAKIN AUREN KI Complete Writing by Feenah.doc

30 Aug 2025

1318

mana da hannun
agogo baya,ina ta murna komai ya wuce ashe
albarkar ciki ne yasa ki zaman dole. Ganin
kukanta na karuwa yasa ya fice ya koma d'akin
Bintu. Har da bawa kura ajiyar nama,wai duk
randa Salma ta fita dan Allah karta 6oye mishi.
Tun daga ranar ya sauya mata,sam in ya shigo
sai dai ya d'au ya'rshi ya fice,itama daga
gaisuwa shikenan ta gama,dan a ganinta
wulakanci ne wannan babba. Ga wani fi'ilin
mutunci da Bintu ta koya da kissa,kullum faram
faram take mata,harda gaisuwa in antashi. Ta
d'au Miemie ta goya a bayanta in Baban ya
d'akko ta. Ba karamin dad'i kwa Ja'afar din yake
ji ba,dan yana karrama mai son Miemien shi,ita
kam Salma nata ido,sai ta dukufa gun kai
kukanta ga Allah. Dan tabbas tasan tai saken da
har mijinta yai mata mummunan tambari. Bintu
kuwa kullum rokon ta Allah duk wani sharrin da
take nemanta dashi Allah ya mayar mata kanta.
By Feenat Ja'afar.
9/29/16, 9:20 AM - Queen Safiyyert???a: [8/2, 2:29 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
30_Sai ya huce kamar sati ana mutunci da ta
tambayi fita unguwa zai kicin-kicin,yace tai son
ranta,haka zata hakura tanaji tana gani,in ya
dawo kuma tasha fad'an da batasan laifi ba.
Kawai Allah ya d'aura mata wani irin hakuri,daga
Ja'afar din har Bintun ido tasa musu kawai.
A haka har Miemie tai wata hudu Salma na
zaman hakuri, musamman ga saurin fushin
Ja'afar gareta,ga tai alkawarin daina kai kara gun
kowa sai gurin Allah.
Ana haka Maman Abba ta haihu.
Ganin yau y'an mutuncin na kanshi yana zaune
ya shagala da yiwa Miemie wasa tana wage
mishi baki tana dariya.
Da fara'arta ta zauna kusa dasu tana k'allonsu.
"Abban Miemie...
K'allota yayi tare fad'in yana jinta,cigaba yayi da
wasan su.
"Inda hali dan Allah zani barkar Maman Abba yau
kwananta hud'u da haihu banje ba.
Kai ya kad'a, "wace Maman Abba?..
Da zumudin zai batta ta sanarshi makociyarta ta
unguwar su ta da.
Abinda yake ya t'sagaita yana k'allonta ba koh
kiftawa.
Tuni ya zata an rufe babin y'an tsohowar
unguwar su a gidan,ashe har yanzu tana makale
dasu.
Bazai manta dasu ba,dan sune ummul aba'isin
wargaza gidanshi.
Kai ya girgiza mata,
"Kiyi hakuri ba halin zuwa..
Baki ta sake tana K'allonshi, a gaskiya bazata
zuba ido tai ta zaman gida na y'anci ba,da takura
gaskiya.
Amma sai ta bishi da lallami.
"Dan Allah ya Ja'afar ka barni naje,nima dana
haihu fa sau biyu tazo min har suna uku,kaga ba
dad'i ace ni koh sau d'aya banje ba barka ba sai
suna.
"Sunan ma ki fidda a ranki,dan inda mu'amular
dana fi tsana,toh mu'amular ki da y'an unguwar
chan ne,kin gane ai?.
Kasa tai da kai,sosai take d'aure irin halin da Ya
Ja'afar ya tsiro mata,yanzu da ta kara tambaya
zai ce tai gaban kanta,hakan yasa tai shiru.
Shi kuma yadda yaga batai gardama ba yasa yai
tunanin zancen bai shige ta ba ne.
Miemie ya ajiye kusa da ita ya bar mata d'akin.
A hankali ta zame ta kwanta,sai ga hawaye ya
zubo mata.
Zaman gidan nan ya fara isar ta,hakurinta ya
fara karewa.
Tana ji yai ma Bintu sallama ya fice,kawai sai ta
sau kuka a hankali marar sauti.
Wato a dake ka a hanaka kuka?.
****
Tun bayan fitarshi bayan ta gama kukanta
Miemie ta fara,kukan har ya wuce kima, komai
tayi taki shiru,kawai sai ta goyata tasa hijab akai
suka fita t'sakar gida dan sanyin magriba.
Bintun na t'sakar gida tana saita abin fad'i kan
Ja'afar ya dawo tambayar Salma koh ta fita,dan
komai a k'unnenta ya wakana.
Jijjiga ta take tana yawo daga t'sakar gida zuwa
zaure da ita,tasan Miemie ba mai rigima bace,
tabbas da abinda ke damunta yau,yawan kukan ji
take kamar itama tasa kukan koh taji sa'ida.
Dak'yar ta samu tai shiru,sai ajiyar zuciya take
halamar tai bacci.
Buta ta d'auka ta shiga band'aki kenan sai gashi
kamar an hulloshi gidan,fatanshi yau ya rit'sata
garin satar fita.
Bintu ya kalla wacce ke murmushin ganinshi,sai
taunar cingam take tana kas-kas,kai da ganinta
da yanayinta kaga na mai shirin kulla wani
sharrin.
"Sannu da zuwa..
Kai ya daga mata, kamar kullum zai tambayi
Salman sai yaji bud'e band'aki.
A fusace ya kallo Bintu, "bayan fita ta Salma ta
fita?.. Ki fad'an t'sakani da Allah.
Kwai tayi kan ta fasa tare da yin kas dashi,
"Eh ta fita,mey ya faru? Yanzun bud'e dakinta ta
shiga band'aki ka shigo.
Gadan-gadan Salma tayi kanta da butar data cika
zatai alwala anjima,kansu farga ta rot'sa mata
aka tana huci,bai isa ba ta rufeta da duka baji ba
gani,fad'i take
"Sharrin naki ya wuce bayan idona yanzu a
gaban idona ma yi..
Mari ya d'auketa dashi shima yana fad'in ta sake
ta.
A fusace tace bazata saka ba,ita kam tamkar
wawiya ta bari Salman na jibgarta,ganin da gaske
take yasa da sauri ya finciko Bintun tare da kara
mata wani marin.
Kunci ta rike tana K'allonshi, "ki sani na gaji da
halinki a gidan nan, karan nan zan d'au
mummunan mataki akanki wall...
"Ka sallame ni in ka gaji dani Ja'afar.. Dan ni tuni
na gaji da zaman gidan ka, ka sallame ni ka huta
toh..
"Haka ki ka ce?..
A fusace tace "eh haka nace..
Tuni shedan ya shiga cikin zuciyar
kowa,musamman Ja'afar da ya rufe ido tamkar
bashi ba.
"Ki je gida sai na neme ki toh...
Cikin kuka tace
''Ban isa zuwa musu ba sheda ba,dole ka bani
sheda..
Ba tare da jin komai ba mugu(shedan) yasa ya
rufe ido.
"Kije na sake ki toh..
Chak! Taji kukan ya t'saya sai na Miemie data
tashi dan hayaniya.
Baki sake take k'allonshi fuska wanke da
hawaye.
"Ja'afar ka sakeni kace fa?.. Muryarta na
ka'rkarwa ta tambaya.
Da sauri ya bud'e ido ya dawo hankalinshi kanta.
K'allon-k'allo suke ma juna cikin rashin sanin
abin fad'a, musamman Ja'afar dashi ya furta.
Ido ta rufe a hankali, sai ga hawayen da ya
makale sun zubo.
A hankali ta bud'e idon ta k'alli Bintu.
"Allah ya biya ki da dai-dai abinda ki kamin
Bintu.. Ki sani,sharri kare ne,ko yayi nisa zai
dawo gun maishi..
Jiki a sanyaye ta juya gun Ja'afar.
"Shikenan abin nema ya same mu Ja'afar.. Aure
ya kare a t'sakanin mu..igiya uku ka rusheta
Ja'afar.. Ka rushe su..
Hannu tasa ta share idonta.
"Ba ka da bukatar na t'saya maka bayani yanzu
kam,dan ka zuba katanga a t'sakanin mu.
Cikin nut'suwa tai hanyar waje ba tare da ta koh
waiwayi d'aki ba.
Da k'allo ya bita, ilahirin jikinshi ka'rkarwa
yake,ya kasa tattara kalma daya da zai ambata,
har Salma ta 6ace wa ganinshi.
'By
Feenat Ja'afar.
[8/2, 10:40 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
31_"Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'un.. Allahumma
Ajurni fi Musibati,wakhluf li khayran minha...
"Salma ki ce min ba gaskiya ki ke fad'a ba
Salma?.. Dan Allah ki ce wasa ki ke..
Murmushi take,wanda da zatai kukan zai fi mata
alkairi, amma ta kasa,tun zuwanta gidan Aunty
A'i ido ya kafe,tunani ya t'saya.. Dabara ta ka
re,sai kallo da ido da murmushi da yafi kuka
ciwo.
Waya Aunty A'in ta d'auka dan kiran Ja'afar,
tayuwu koh shi ya mata bayanin da zata gamsu
tunda Salma ta zama kurma.
"Ja'afar..
"Bashi bane.. Tsam tayi dan tasan Bintu ce ta
d'auka.
Da karfin hali ta tambayi in yana kusa ta bashi
man, t'saki tai mata kamin ta kashewar.
Kasa tai da wayar tana mai tabbatar da kalaman
Salma na aure babu,ya ka re.
A hankali ta sakko ta t'suguna gaban Salman
tare da dafa kafafunta.
"Salma kimin magana ba shiru ba dan Allah.. A
dunkule kika bani, dan Allah kiyi magana, shin da
gaske ya sake ki cikon na ukun?..
K'allon Aunty A'in take cikin ido,tabbas wannan
kalmar ita ta 6acewa tunaninta.
Kan ta ankara ta sau mata wiwi,baji ba gani.
"Bintu ce... Wallahi itace.. Ban mishi komai
ba..ya raba aurenmu.. Allah banyi komai ba
karan nan Aunty A'i,ki yarda dani dan Allah, koh
su Abba baza su yarda ba...
Kamar karatun yara haka take had'a kalaman
cikin kuka.
Jiki a sanyaye Aunty A'in ta tashi tazo kusa da
ita,sosai ta gane sambatu take,cike da tausayin
y'ar uwartata ta rungumo ta, ta abu daya take
gane gaskiyar Salma tun a yarinta, shine fad'in
abin da batai ba cikin kuka.
"Na yarda Salma,na yarda dake karan nan.. Ki
bar kukan haka, Allahu yasa shi yafi zama muku
alkairi.
Ita dai kukanta take.
Ina Ja'afar ya gano abinda Aunty A'i ta sani
game da rayuwar Salma, da bai bawa CID na fitar
ta ba, da ya fuskanci ta sauya tun sa'ilin da in
yace ta fita take kuka,da ba ayi hakan ba.
*******************
"Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'una... Ja'afar mai ya
kai ka wannan yanke d'anyen hukuncin kan ku?..
Mey ya kai ka?.. Abinda ya faru yake sanar
mishi,gaba daya ya rasa abin yi.
"Shin ka tambayi ta fitan koh bata fitan ba?.. Koh
har yanzu kai baka hango hankalin Salma ba ne..
Kai ya k'ada mishi
"Ba wannan ne karon farko ba,ni nasan Salma
fiye da zaton ka..
"Ka kuma yarda da Bintu fiye da yarda ka bawa
Salma yarda koh ka ke nufi?..
Murmushi yayi na takaici, "Ja'afar bakasan sharri
irin na mata bane.. Da baka ba Bintu amanar
aurenka sukutum ba Allah. Tayu ka tafka babban
kuskure na fahimtar Salma karan nan.. Amma ka
yi bincike, shine t'sarin Shari'a.. Ni na shiga gida.
Da kallo yabi bayan Garban, duk maganar shi
gaskiya ce,kuma ba daya daga ci da ya aiwatar
kamin komai.
Yau daya yaga fushin Garba karara kwance a
fuska,tabbas haushin shi yake ji shima,kamar
yadda shima yake jin haushin kanshi da kanshi.
Jiki ba kwari ya tada machine yai gida.
Dole ya tit'siye Bintu ta sanarshi gaskiya.
Bata d'aki,ga nan wayarshi da ya manta da tata
akan gado halamar tana sana'ar tata ta charting.
A garin ya d'auki tashi ya danno screen na
Bintun, haske ya baiyana halamar tana ma kan
charting din tai wani waje.
Kwanciya yayi da bayanshi jiki duk a
sanyaye,bazai iya bawa wannan ranar suna ba.
Ido ya kura ma wayar Bintun kirar _Techno_, zai
so yau yaga mey ke debe hankalin ta zuwa
Facebook.
*Bintu U*.
_"ke an saki shegiyar fa,ki tayani murna zan
sakata in wataya_..
*Shining star*:
_"Kai matar nan baki da dama,a bani satar amsa
dan yanzu na dawo makarantarki_..
Da azama ya mike zaune dan ganin charting din.
*Binta U*
_"Hhhhh,tuggu dai kamar kullum nayi,sai dai na
yau mai zafi ne,dan jiya an bani sa'a har gida,
take ina fad'in ta fita ya d'anna mata saki,baiwar
Allah harda dan guntun wa'azin ta ta min
hhhhh_..
*Shining star*
_"ina ma zan iya irin wannan sharrin naki dana
huta, sai dai tawa tasan takan duniya,ina mata
take dawo min da abu na_..
*BINTU U*
_"ba gari daya muke ba,da wallahi taci karya,ni
zan baki maganin y'ar banza_...
"Ya Allah... Kai shafo cikin ranar jiki hawaye na
zuba, da sauri ya d'anna _previous chat_
Sai gata kamar an jehota da buta a hannu tana
zare idano na munafukai.
Sam bataji koh dirin machine dinshi ba,sai
arbawa tai da takalmanshi.
Da d'ukkan hannu biyu ya dafe kanshi yana
hawaye,mey zai ma Bintu ya huce da bala'in da
ta jawo mishi?..
A hankali kalaman Salma ya dawo mishi,
_"Allah ya biyaki da dai-dai abinda ki kamin
Bintu..Ki sani,sharri kare ne,ko yayi nisa zai
dawo gun maishi_...
Gashi tun kan a kwana ya dawo ma Bintu bata
shirya ba...
"Ka dawo..yaushe ka shigo..ban banji shigowar
ka ba..
Da in'ina take maganar, ganin yadda hawaye ke
diga a kafafunshi ga kuma wayarta a hannunshi
tasan yau karya ta kare.
Ido ya goge kamin cikin nut'suwa ya ajiye wayar
kan gado ya k'allota.
"Tabbas kinyi nasarar rabani da d'ukkan farin
cikina Bintu.. Kinyi nasara,tanan kam nasan kin
ma Salma fincinkau,dan ita bata sharri..
"Na baki d'ukkan wata amana,ki mayarni
shashasha.. Ki nunan yau abinda Salma take
gudu a kishiya,"makirci"..
"Amma ki sani,wallahi!,wallahi!!.wallahi!!!
Uku,yadda kikai sanadin 6allewar aurenmu da
Salma kinyi naki.
"Kamin nan zaki ji jiki kamar yadda ki ka sa taji
t'sawan zaman ku..
Kan tai kwakwaran mot'si ya hard'o ta, ta ko'ina
mari yake bata iya karfinshi tana ihun jama'a su
ceceta..
Sai da tabbatar ya taga wuta dan mari kamin
yana haki ya nuno ta.
"Kije kema,na yanke igiyar aurena dake kanki har
guda uku... "Tun kan ki kwana maganar Salma ta
kar6u gun Allah...
Ihu ta saka tana bashi hakuri kan ta daina, "dan
Allah karka sake ni...
Hanyar waje yayi yana sa waya a aljihunshi.
"Ki tabbatar baki kara awa d'aya cikin gidana
ba,dan saki uku na furta.
Waje yayi ya ja ya t'saya a zaure,tamkar wani
yaro ya rushe da kuka mai tsanin ciwo..
Yayi kuskuren da dak'yar ya g'yara shi cikin
rayuwarshi.. Yayi kuskuren da ya bari Salma tai
mishi nisa...
Yayi kuskuren kin kar6ar shiryiwar Salman sa..
Tabbas ya tafka babban kuskure a rayuwa.
"Allah ya isa t'sakani na dake Bintu... Ubangiji
yai ma Salma sakayya akanki daga yau har ranar
sakamako... Allah ya isar mata cikin sauri..
Ganin hakan ba mafita bace gareshi yasa ya
d'akko waya hannu na ka'rkarwa zai nemo Garba
yaga kiran Aunty A'i na dazu.
Garban ya kira,dole ayi wacce za ai,Aurenshi da
Salma mutuwa ce kadai zata raba.
Da Allah ya had'ashi cikin muryar kuka kan yazo
gidanshi yanzun nan..
"Isha'i ake kira fa Ja'afar..
"Dan Allah kazo,in bakazo ba komai zai iya
faruwa...
Ba'a fi minti goma ba yazo,fatattakar arziki yai
ma Bintu ta bar gidan ya rufe ya fad'a mota.
Da t'sananin mamaki yake k'allon abokin nashi, a
iya abotarsu bai ta6a ganin koh da hawaye na
Ja'afar ba bare kukanshi mai sauti irin haka.
Dan Ja'afar namijin duniya ne,Jarumi, kuma
jajirtacce, yasan komai ya sashi kuka ayau ba
karami bane.
"Gidan Aisha zaka kai ni yayar Salma..
Baki sake yake k'allonshi,
"Yayar Salma kuma?..
Ido jajir ya kalloshi ba halamar wasa,dole ya tada
mota suka d'au hanya.
Waya yai mata kan ta fito yana kofar gida.
"Malam mijina ya fita..kai hakuri.. Kit ta kashe
wayarta,yau Aunty A'i ta d'au zafi ya sani,tabbas
kuma Salma na gidan..
Murfin motar ya bud'e a fusace ya fice Garba na
kira.. Kofar a bud'e take,kawai ya tura ya shiga,
nufinshi a d'aureshi bayan yaga Salman.
"Salma!,, Salma!!.. A tunzure Aunty A'i ta fito a
parlourn dan tsayarahi shiga mata parlour.
Yadda taganshi bata isa hana shi ba ganin
Salman, dan g'wiwa biyu ya zube gabanta tamkar
yaga Salman.
Hanya ta bashi ba musu,da zafin nama ya mike
ya shiga parlourn, bata zata ba taga mutum a
kanta,da sauri ta zabura ta mike tana kwad'a
kiran Aunty A'i da sauri.
Bata nufa ba taga mutum zube a gabanta kanshi
a kasa.
Ido ta rint'se tare da kawar da kanta,koh kadan
bata son kara ganin Ja'afar a rayuwarta Abadan.
Juyo wa tai da niyar surfa mishi ruwan bala'in da
ba shiri zai bar gidan,sai dai mey?
Da t'sananin mamaki take kallonshi tana k'allon
Aunty A'i.
Hawaye ke malala a idonshi kamar wanda ya
rasa jin dad'in rayuwarshi,abin g'wanin ban
tausayi.
Ja'afar?.. Kuka ma?, a namey toh?.
"Salma gani gabanki, a matsayin wanda ya tafka
miki laifi cikin rashin sani,da kuma sharrin
Bintu..Salma kiyi hakuri,wallahi _am really really
sorry.. Kar ki barni dan Allah.. Zan tagaiyyara
Salma.. Zan zauce.. sharrin Bintu ne,kuma itama
ta amshi hukunci,dan na saketa kamar yadda ta
jawo mana,
_please_ Salma _forgive me_... Wallahi _I can't
live without you anymore_,ki tausaya ma mijinki
uban yaranki...
Baya taja da sauri ganin yana kara kusantota.
Da sauri Aunty A'i tai waje jin kuka zai kubce
mata.. Dole haka zata kasance dasu Salma,ranar
rabuwa, rabuwar da ba a da tabbacin za'a dawo
ta.. Tabbas tausaya wa rayuwar su,dan a irin
soyayyar nan ita ce ake kira *Mutu ka raba*..
Gashi yanzu K'ADDARA ta raba masoyan biyu.
By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 9:24 AM - Queen Safiyyert???a: *A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
32_Kuka take yanayi iya karfinsu, tabbas
K'ADDARA ta rigayi fata, duk kuma yadda ka
t'sara rayuwarka sai ka ga ba haka ya tafi
ba,tabbas ta Allah itace daidai. Baya tai ta zube
kan kujera da6ar.. Duk sunyi kuskure, kowa na da
laifi,meyasa ma tace ya saketa?.. Mey yasa?..
Le6e ta cije tana mai sa d'ukkan hannunta biyu
zuwa fuskarta, kuka kam yau har sunji ba dad'i.
A hankali ta dago tana K'allonshi ido yai luhu-
luhu,duk ya marairaice mata hawaye na zuba, tafi
tausayin kanta sama dashi, Kokarin magana take
su Aunty A'i sukai sallama ita da maigidan da
taima waya. Fuska Ja'afar yai saurin gogewa
ganin yadda Abban Aslam ya sau baki yana
kallonsu,bai tunanin abin ya kai haka ba, kuka a
gaban mace da zubewa g'wiwa biyu?.. Lalle
yasan abin babba ne. "Innalillahi Wa'ina
Ilaihirraji'un... Itace kalmar shima da ya fad'i
bayan yaji mai ke faruwa.. "Dole aje gida kowa
ya samu labari,dan wannan ba abin a 6oye bane
koh da za'a nemi sulhu,saki ya cike na uku abin
yafi karfin zama anan Ayush.. Zamu tafi da
Salman kai Ja'afar sai ku taho da abokin ka. Har
kusan goman dare ana abu daya akan zancen
saki. "Ka ce kayi saki,ita tace ya zama uku,
sannan kana zancen ai sulhu koh? Kai ya daga
da sauri, murmushi Abban yayi,abin yaso ma
bashi dariya, "Wato Ja'afar... "Malam Umar
wannan zancen ba zancen da za'ai wa sakwakwa
bane,kan Ja'afar ya dawo. "Kai kuma in dan baka
tashi mun wuce ba zan mugun sa6a maka
yanzun nan.. "Kana hauka ne?.. A wane garin ka
ta6a jin anyi saki d'ai daya har uku kuma ana
neman sulhu?.. "Ai baka fara ganin komai ba
Ja'afar, ba dai zuciya ba?.. Za ta sa ka dana
sani, "Malam Umar ai hakuri bisa wannan
K'ADDARAR da ta sakko mana,zamani ne yanzu
muke ciki da yara basu dauki saki a bakin komai
ba.. Tashi yayi yana bawa Abban Salman
hannu,kan ya kallo Ja'afar,har yanzu sautin
kukan su ke fita shi da Salman. "Muje koh?..
Salma ya dago ya kalla da sunkuyar da kai,
"Salma dan Allah ki basu hakuri kar su
rabamu,kin san bazan iya rayuwa ba ke
ba,Abadan Salma...Please. Kuka ta kara saka
mai karfi, t'saki Abba yayi ya karkade riga yana
nuno shi cikin fad'a. "Hauka kenan wannan, dan
koh a musulunce Salma ta haramta a gare ka..ta
haramta har abada,dan kai kam ka nuna mana
bazaka ta6a iya rike aure ba, saki tamkar wasan
yara? Itama waccan wai ka mata saki uku?.. Toh
koh aure Salma tayi na fad'a maka ta haramta a
gare ka har abada,kaje kaci zuciya. Da gudu
Salman ta tashi tai d'aki tana kuka.. "Haba
Alhaji, abin bai kai haka ba,kuskure ne kowa yana
iya tafkawa a rayuwa.. Anji bai k'yauta ba,amma
kar hakan yasa kai mishi baki,kai hakuri. "Hakuri
shine ya biyo ni yanzun nan.. Wace iriyar
haukace wannan kamar a jahiliya?.. Wani yai
mishi sakin?.. Haka Ja'afar naji na gani yai waje
yana waiwayen dakin da Salma ta shige yana
hawaye. Tun daga ranar duk suka zama sakwa-
sakwa, barin Ja'afar da baida kuzari,ga Abba ya
sako shi gaba ta ko'ina.. Dan har gida iyaye
Bintu suka zo sukai ma Abba rashin k'yauta wa
akan yadda bayan saki uku sai da aka
kumburawa ya'rsu fuska,harda ikirarin
koto,dak'yar aka basu hakuri kan suka debe
kayanta, ranar Abba yayi takaici har yaji ina ma
da ya barma Umman shi Ja'afar,kila da baici
karo da bacin ranshi ba. Sai dai yace kayan
Salma koh sama da kasa zasu had'e ba mai diba,
ashe ma in ya bari aka diba sun rabun kenan...
Ja'afar mat'sala. Anyi ban baki, Abba yayi fad'an
ya dawo lallashin amma Ja'afar ba sauki,kawai
sai Abban Salma yace a rabu dashi,dole in ta
tashi aure zai bari a diba da kanshi. Kullum ta
Allah yana kan jelar gidan su Salma,a wata guda
har kama ya sauya,ba aski,ba g'yaran fuska,ya
zama tamkar zararre. Sosai Abba yake tausaya
mishi,Mama kadai ke shafawa idonta toka ta
hana ya ga Salman,sai dai a bashi Miemie, haka
zai gaji har ya tafi,sai dai tai ta ganin text na ban
hakuri,gobe ma zuciya zai dawo. ***************
*************** Rayuwa irin ta kunci kam sun
ganta a wata hudu da ta gabata. Salma ta
saduda sosai akan Ja'afar,dan har yanzu shi
yana kan bakar shi. Sam in ka ga Salma ta
sauya,ta dawo shiru shiru sosai,kullum zaka
same ta a daki,koh ta dukufa tunani, koh tana
k'allon Miemie tana hawaye. "Salma... Gefe tayi
da sauri da kanta tana goge hawayen jin
maganar Mama akanta. Dole yau ta kawo
karshen matsalar nan. Zama tayi a gefen gadon
tana kare mata kallo. "Rayuwa fa kullum sauyi
take Salma,amma banda taku, ni dai ban ta6a cin
karo da kulafucin D'a namiji irin naki ba, wata
hudu ba kwana hudu bane Salma.. "Lokaci yayi
da za ki cigaba da rayuwarki ki manta da kashin
Ja'afar.. Ki d'auka Rabon Miemie kawai ya had'a
ku,ki manta da rayuwar da,dan ta wuce,ki
fuskanci zahiri a rayuwar gaba Salma.. Fad'a
Mama ke ta mata tana kuka, taya zata mance
Ja'afar?.. Taya zata mance zaman su?..Soyayyar
ta da Ja'afar had'i ne na Allah a ganinta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login