Showing 39001 words to 42000 words out of 42609 words

Chapter 14 - A BAKIN AUREN KI Complete Writing by Feenah.doc

30 Aug 2025

1307

yake a t'sawan shekara guda da
d'auri. Sai dai har ta gama leke bata koh hango
mai kamar Ja'afar fa sai sawun mota. Zaure ta
koma tana lumshe ido tare da dafe kirjinta. Babu
makawa Ja'afar ya shigo zauren nan.. Dan ga
nan kamshin turarenshi ciki tana iya shakarshi.
Jiki a sanyaye ta juya ta koma cikin gida, a chan
d'akin Mama ta jiyo karad'in Miemie na ba ma
maman labari tana dariya. Da murmushi ta samu
ta dan dosana tana kallonsu kamar ta sa kuka.
"Na fuskanci yarinyar nan in dai tai arangma da
Abbanta tana kwanan murna, haka kwanaki
dak'yar na ban6areta jikinshi ashe bata manta shi
ba tana kuka,shima harda y'ar kwalarshi yana
daga mata hannu... Ido ta kurawa Maman ba koh
kiftawa.. Ba dai Mama na nufin Ja'afar yana
zuwa garin nan ba kuma har gidan nan?... Mama
ce ta kat'se mata tunani da fad'in "Ban tunanin
yaron nan koh a hanya ya ganni zai gaidani ba
sam bayan aurenki, duba ga yadda na rika mishi
fatattakar arziki.. Zuwan shi biyu gidan nan ashe
makaranta ya koma kinji.. Murmushi tai Maman
da iyakar shi le6e tare da daga kai. Tuni ta
zurfafa tunani,har bata jin mey Mama da Miemie
ke fad'a,kan ta farga har idonta ya cika da
kwalla,da sauri ta juyar da kai tare da goge wa
kamin su gani. Sakkowa tai tana taya Miemie
rad'awa teddy suna suna dariya. Kallonsu kawai
Mama take tana wani tunani, kai ta kad'a kamin
ta tashi ta basu gu dan tasan Abba yana gaf da
zuwa. Washegari da yamma tana kokarin shiga
wanka akai mata sallama. Hijab ta zira harda
shafa powder da zumudin Ja'afar ne ma,kila ya
samu labarin tana gida. Turus tayi tare da
chunno baki kamar Miemie ganin Alhaji da
abokinshi. Baki ya washe mata yana fad'in ta
karaso man kusa... Murmushin mugunta tai kan
ta kalloshi "Dan bani minti biyar na fito a gida...
Kai ya daga yana mata murmushi, ashe bazai yi
wahalar shawo kan Salma ba kamar Halima.
Ruwan da ta zuba na wanka ta d'auka da wani a
buta dan tsarkake kai in tai wankan t'sarki. Tana
yi tana murmushi har ta gama. D'aki ta shiga ta
tsane kanta da towel kan ta dan shirya a
gaggauce ta fita. Yadda take murmushi ne yasa
Mama tambayar waye yazo, a tunaninta koh
Ja'afar ne,tana cewa Alhaji ne ta 6ata rai. "Ki dai
kama kanki ki saiwa kanki mutunci,dan sam
mutumin ba nagari bane,kinjini ai? Kai ta kad'a
tana murmushi, lalle Mama, yau Alhajin guda?..
Sai ta kad'a kai, "adu'a bata fad'uwa kasa banza.
Bayan sun gaisa yake zungurar abokin nashi
sarkin iya t'sari, duk tana jinsu tana murmushi
dan feleke harda tambayar Miemie,sai da suka
gama tass tana jinsu tana kad'a kai. "Ai yanzu na
fita sahun matarka Alhaji,sai dai kabi sahun
zawarawa na..dan nayi iddah ni... Fuska ya
g'imtse yana kallonta, "haba kar muyi haka dake
man,ina fa lissafi,yau watanki biyu da kwana uku
rabonki da gida na, kinga ai bakiyi wata uku bare
ace kinyi iddah koh ba haka ba abokina? Kai ya
jijjiga yana fad'in "kwarai kuwa,dan haka muka
sani a al'adan ce. Kai ta kad'a tana murmushin
takaici, wato ga babyn roba,a hular a lokacin da
akaso a d'auka a randa aka ga dama.. 6aro-6aro
tai mishi dalla-dalla kan ita ai duk bayan sati uku
take period, kuma ya sani sai dai ya take. A fafur
yace shi baisan zance ba,kawai ya maida ta
dakinta. Juyawa tai ta koma gida,tana ji sai
kwad'a mata kira yake tai mishi banza. Da farin
ciki ta shiga har baya misaltuwa, dan da yanzu
dabarar yin wanka ba tazo mata ba da tuni
ansha da ita an gama. "Ba dai ya maidaki ba
naga kina murna tun yanzu Salma?.. Yanzu ke
bazakiyi kishin kanki ba har kin bada kai daga
fita bori ya hau?.. Ina laifin ya samo Abbanki da
maganar in dai da mutunci aciki... "Au dariya ma
na baki koh Salma?.. Ga shash.. "Mama ni fa ba
aure a t'sakanin mu da Alhaji yanzu,dan tau nai
iddah ta.... Baki sake take kallonta,dariya tasa ta
bata labari,sai ga Mama na tikar dariya. "Lalle
yarinyar nan da wayo ki ke,kwarai kinyi dabara,
dan sam mutumin ya sane min, dan ban fad'a
miki bane,ba'a fi sati da dawowarki gida ba muka
had'u da dan talikinnan,d'auke kai yai kamar bai
ganni ba fa,bayan sarai mun had'a ido.. "Shi yasa
yaron nan Ja'afar nake ganin kimarshi har
kullum,dan koh bayan rabuwarku yana daraja
mu,musamman zai sa azo har gida abokinshi yai
mana goma ta arziki in sun d'au Miemie... Shiru
tayi tana sauraran maganar Mama, wai Ja'afar
take ma ya6o haka da kirari?.. Farin cikinta a yau
bai misaltuwa,ina Miemie na nan ta rad'a mata
itama suyi tare,tasan dai duk inda take yanzu
tana neman gida,dan tun dazu tai mata kwalliya
da kayan Abbanta kaninshi yazo ya d'auke ta.
Murmushi tai tana jijjiga kai. Lalle ne *Duniya
Labari ce* By Feenat Ja'afar. feenat-jafar.my
wapblog.com
Feenat Jaafar's Mobile Blog
feenat-jafar.mywapblog.com
Like ? 2 ? Reply ? Report ? Aug 9
Feenat Ja'afar Novel's
*A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
43_Waya yake d'annawa a nitse yana duba sakon
waya kamar bayaso,kamili ne,da hasken
shi,sajenshi a yanzu shine sirrin 6oye kyanshi na
ainashi, sanye cikin kananan kaya da glass
manne a idonshi,da gani yana ji da ajinshi a dai-
dai lokacin nan,dan miskili ne yanzu na karfi da
yaji. A yanzu ne yake tsone idon y'an mata
musamman na jami'a, dan ya iya t'sare kai da
tsare gida. Rayuwarshi ta sauya,dan ya dawo
ainashin halaiyar shi ta da,koma yafi da din,
Ja'afar kenan,namijin duniya. Dago kai yayi yana
duba yanayin garin da yadda kowanne shago
suke hadahadarsu,sai ya sauke kai kan Abdull
mai tahowa dauke da baby a kafad'a tana ta
washe baki tun kan ta karaso. Tuni fara'a ta
maye g'urbin rashin walwalar shi,kashe wayar
yayi tare da ajiye ta gefe dan tarar gudan
jininshi,duk Abba dake gefe kad'an yana kallo.
"Abbaaa... Miemien ta fad'a lokacin da yake
k'ar6ar ta,murmushi yayi mata tare da shafo
fuskarta "Na'am Miemien Abba.. Sai ta washe
baki. Ciro changi ya mika ma Abdull, "Kan
magriba kazo ka maidata kaji?... Kai ya kad'a
tare da amsa yayi godiya. Zama yayi tare da
d'aura ta cinyarshi, Tasha kwalliya da rigar da ya
yo mata tsaraba cotton ja da pink,kan nan kamar
an mata shampoo sai kyalli yake yasha ribbons..
Hannu yakai kan dan beauty point nata ya latsa
sai ta sa mishi dariya. A hankali shima yayi har
hakorinshi suka baiyana. Tashi yayi zuwa gun
Abba dan mishi sallama,kai ya kad'a Miemie na
mishi bye-bye tana dariya. Kamar kullum nai yai
ta yawo da ita suka sai ice cream suka nufi
gidan Garba nan suka yada zangon su. Miemien
Garban ya kallo yadda take tsalle kan Abban nata
shikam sai murmushi yake mata. "Abokina ina so
yau dai daya ka saurare batu na,sama da wata
hud'u dana fara ma magana zaka ce a'a kai baka
so.. Kallonshi yake jin inda yake neman dosa,tuni
ya fara sauya kama. Ba tare da yabi ta kanshi ba
Garban yaci gaba "Salma fa au... Cikin t'sananin
fushi ya rufe ido tare da daga mishi hannu. "Dan
Allah ka d'aina dawo min da hannun agogo
baya,ina a cikin farina yanzu,banson jin sunan
wata Salma chan.. Gefe yayi da kai yana
chunkune fuska,kai Garban ya kad'a kan yai y'ar
dariya, "Karyar banza kenan,yanzu da zance
Salma tana gida an sakota da nasan ba wanda
zai farin ciki a yau,kaine fa.. Baki sake yake
kallonshi, "kana sanin abinda zaka fad'a man
malam.. Matar mutanace fa yanzun. Murmushi
yayi yana mishi k'allon bakasan komai. "Toh
auren Salma ya rabu tun wata hud'u da ya
wuce,sai ka kurbi ruwan sanyi ka huce.. Baki
sake yake kallonshi ba koh kiftawa. Baya Garban
yayi da kai yana shafa ha6a tare da daga mishi
gira,ya dan jima a kame kamin ya d'auke tare da
wayance wa. "Wannan bazai sauya komai ba
kama ji da wai,dan ban manta abinda ta dirka
min ba a baya.. Kama d'aina wata dariya..
Kafad'a Garban ya make,kan yace "Daga baya
kenan kuma,chan ta matse ma,dan nasan yau sai
kafi kowa farin ciki a garin nan,karyar kawai.
Tashi yayi yana daukan Miemie tare da hararar
shi, "Kanka ake ji,ni nayi kaga tafiya ta.. Dariya
yai kan ya mike dan sauke su, "Kaima an kusa
jin naka soon. Harara ya sakar mishi kan suka
fice yana ta mishi t'siya. ***** "Mama zan tafi,a
min adu'a Allah yasa kar na samu mat'sala
kamar yadda principal yace.. "Amin kam, in Allah
ya taimaka zasu karbi uzirin.. Kai ta kad'a, ''Amin
toh, na tafi kan wannan ta farka. Da sauri ta fice
ganin zatai latti. Allah yasota tana zuwa wata
Napep zata tashi ta d'au wani da dan sauri ta
t'sayar ta shiga ba tare da ta dubi na ciki ba.
"Dan Allah ka taimaka school of... Shiru tai jin
wani kamshi da ya bigeta,turaren da koh ajikin
wani taji,toh mutum daya ke zuwa ranta. A
hankali ta waiwaya dan ganin waye masanyin
turaren. K'yam tayi tana kallonshi da murmushi
ba koh kiftawa, shima hakan take,kan da sauri ya
d'auke kai kamar ma bai ganeta ba yake nufi..
Dad'i ne..koh farin ciki a ranta a safiyar yau..
*Ja'afar* Wannan shine yaushe gamo. Kokarin
mishi magana take yace da mai Napep ya t'saya.
Ba musu yaja ya t'saya, da mamakinta taga yana
kokarin sauka a Napep d'in, da sauri mai napep
yace "Kazo gaba toh. Ba tare da ya kalle yace
"Kai hakuri,bana shiga keke da mata... Gaba yai
ya batta baki sake.. Kuturu,wa ya ga turnuku...
Ji tai tamkar ta d'aura hannu a ka ta kurma
ihu,wai ita Ja'afar zai haka?. By Feenat Ja'afar.
9/29/16, 9:44 AM - Queen Safiyyert???a: Feenat Ja'afar Novel's
*A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
45_Washegari kowa da farin ciki ya tashi kamar
ma ance an shirya. Yau tana son ta koma
Salmanta ta da ne. Yau shima yana son komawa
Ja'afar d'inshi na Salmateen shi,dan haka tun
wuri yaje yai g'yaran fuska,ya rage sumar kai,tuni
ya hasko kamar zamanin angoncinshi da Salma.
Gun Garba yaje yasha kwalliya kamar wani sabon
ango. "Ya mutumina nayi kyau kuwa?%??? banda
shakiyanci pls. Daga sama har kasa yake
kallonshi,yai kokakarin 6oye dariyar shi. "Kayi
man,ina zuwa haka da sanyin yammacin nan
haka?.. Da zumudi yace "gun Salmatee hayatee
man. Da rashin fahimta yace mishi "wace haka?..
Harara ya sau mishi tare da fad'in "Ban sani ba,
kaima ramawa zaka yin?.. Dan Allah ni taso
muje.. Kai Garban ya juyar yana fad'in "ba inda
zani bansan mace ba, haka kawai, Da zumudi
yace "Salma ta fa,kar kace baka gane ba mana
mun dinke.. Kunu yasha yace "ban gane
ba,yaushe aka dinke?.. Koh ka manta
kalamanka?.. Lallami ya fara yana kasa da
kai,tuni Garban ya ware yana dillika mishi dariyar
mugunta. Shi dai yau bata tashi yake ba,burinshi
kawai su isa ga Salman shi. Yau d'aya ta zauna
zaman kwalliya duk da bata da tabbas din
ganinshi,har Mama na mata t'siyar ina zuwa?.
Murmushi kawai tayi ta ciro wani arnan purple
swiss tana kallo, shafashi tai tana tunano colorn
da Ja'afar yafi kauna ya gani ajikinta. Riga da
zani ne single, dinkin yai mata kyau tsam ya
kama jikinta, da gaske yau ta fito a Salmanta.
Tana daga d'aki ta jiyo yaro yazo wai Salma
tazo,tana jin Mama na fad'in inji wa?.. Bataji
amsar yaron ba taji Mama tace kace tana zuwa.
G'yale ta rufa fari da ratsin flower purple tana
k'allon kanta a mudubi,ina ma Ya Ja'afar ne
man... "Ki fito ana kiranki a waje Ja'afar yanzu...
6ata rai tayi tana gunguni, "Ja'afar kuma
Mama?.. Ni fa ba danshi zan fita ba fa.. Harara
ta sakar mata,kan ta juya tana fad'in
"magulmaciyar kawai,ni zakiyiwa alaye?.. Da gani
shigar Ja'afar daban take gunki ai... Dariya ta
kunshe kan ta kara k'allon kanta a madubi ta
fita. Suna tsaye sun rike hannun Miemie da suka
dakko chan gidan su jaafar suna mata y'ar dage
tana dariya. Murmushi ta tsaya yi musu da
sallamarta. Ido ya zira mata,yayinda itama take
kallon sauyawarshi a yau kadai kamar sabon
ango. Murmushi ya sakar mata yana daga mata
hannu halamun tayi k'yau, da sauri ta d'auke kai
a kallonshi tana cinkune fuska. Kai ya kad'a yana
murmushi, karya kuma ai ta kare, tunda har
shigarshi an mishi. Ha6a Garba yake shafawa
yana kallon wani fulakon karya gun Salma da
Ja'afar. "Kaganta ni dai ya kamata nayi fushi
bisa abinda ta dibga min,amma kaga an dakeni
an hanani kuka... Harara ta sau mishi,kan ta kau
da kai, "lefinka ai dayawa,bar tunatune kawai.
Kai Garba ya kad'a,kan ya kallo Salman. "Salma..
Kalloshi tai,bata tunani ta ta6a ganin Garba ya
zama serious haka, hakan yasa ta bashi
hankalinta gaba daya. "Nasan nima har yanzu
kina ganin baki na sakamakon zuwanmu na
karshe gunki. Rantsuwa ya mata,kan yace
"Ja'afar baizo ranar gunki da neman auren kisa
wuta ba sam,asalima yazo ne danya sadaukar
miki da farin cikinshi gare ki sakamakon sanin
waye Alhaji Usman.. Kai ta dago tana kallonshi.
Sai ya kad'a mata kai, Ja'afar din ta kalla,shima
itan yake kallo. Yacigaba, "yana son ki samu
farin ciki ne Salma,wanda yasan a gidan Alhaji
dak'yar ki sameshi,dan kaf halin Alhaji ba wanda
ba'a karanto mana ba,hakan yasa ya gwammaci
ya baki ni,duk nai imani sai ya fi mishi ciwo
sama da auranki a waje.. Ya kallo Ja'afar da
murmushi, "nasan abuna. Murmushi sukai ma
juna,tabbas hakane,dan da Garba ya auri
Salma,da yana gani bashi ba sake ganinshi bare
hulda da gidanshi. "Dan haka banajin da wanda
ya kai Ja'afar son farin cikin ki,ki d'aure ki bawa
abokina second chance a zamanku ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?kamar yadda
bukaci haka. Nan yai ta musu fad'an rayuwa sai
y'ar hakuri ce,da sanya tsoron Allah a
lamari,gashi sunji dad'in tawakallin tunda suna
fatan in Allah yaso su maida aurensu. Kan Garba
ya tafi sai da ya tabbatar kowa ya yafe. Zaure
suka koma ta sa musu taburma. Kallonta yake
suna ma juna murmishin so cikin kauna. Sai wani
dan sinke kai take halamar kunya. Hatta Miemie
ta gane iyayen sun dinke, sai kallonsu take tana
murmushi. "Assalam Alaikum.. Kai suka
dago,Ja'afar ya amsa. "Aunty Salma wai ana
kiranki a waje.. Kallon Ja'afar d'in tayi, Shima ita
yake kallo,sai yai mata murmushi. "Tashi muje
naga wane tsageren ne wannan... Miemie ya
d'auka itama ta tashi tana murmushi suka fita.
Alhaji ne yasha gayu da babar riga da wata
katuwar mota yana murmushin ganinta. Fuska ya
tsuke ganin fitowar Miemie da Abbanta suna
wasan su. Tana ganin Alhaji Miemie ta g'imtse
fuska,murmushi Ja'afar ya mata tare da shafo
fuskarta suka karasa. Hannu ya bashi dan su
gaisa Alhaji ya juyar da fuska gefe. "Gunki nazo
fa. Kallonshi tayi tana murmushi, "toh
Alhaji,gamu ai.. Da halamar tambaya ya k'alleta.
"Ban gane ga ku ba?.. Kina nufin dashi zan
ganki?.. Ja'afar d'in ta kallo tare da Miemie dake
kallon Alhajin duk rai had'e daga shi har y'ar.
Murmushi tayi tare da matsawa kusansu suka
jeru mishi a gaba. "Alhaji, kai hakuri, kai
hakuri,ka daina zuwa,InshaAllah aurenmu zamu
mayar da Abban Miemie.. Ka d'auka zaman mu
yazo karsh.. ka d'auka rabuwar aure na da kai da
auran duk had'i ne na Allah... Ja'afar ta kalla tai
mai murmushi tare da shafo fuskar Miemie. "Kai
hakuri na na zauna da iyalina, ka yarda sune
farin cikina, ni ce tasu,kai hakuri pls... Kai ya
kad'a,tare da kallonsu,duk daga gani suna a farin
ciki.. Tabbas yasan yai sake,gashi ya tashi a
tutar babu,ba Halima ba Salma,ba su Nabila ba
Miemie... Wa zai gane a jiya yayi nadama?.. Ya
zasu gane yasan dad'in jin motsin D'a kusanshi a
yanzu?.. Wa zai gane ya hakura yanzu kam yana
son zuri'a?.. Murmushi yayi yana d'auke kai,kila
haduwarshi da Salma sanadin shiryuwarshi
ne,koh yanzu ya gode Allah. Kai ya kad'a tare da
masu fatan alkairi, k'warai tai mamakin jin harda
mata godiya a bisa gaskiya da take tsage mata.
Hannu ya mikawa Miemie fuska d'auke da
murmushi. Kafad'a ta mak'e tare da lafewa a
kafad'ar Abbanta. Mota ya shiga tare da fitowa
da leda cike da shopping na chocolate da ice
cream.. Alawa daya ya fito dashi tare da fad'in
"Zan baki sweet fa,zo mu gaisa mana Miemie..
Salma ta kalla kamar mai jiran umarninta.
Murmushi tai mata tare da daga mata kai,abin
kai sai taje ba musu,yau sai ga Miemie harda ma
Alhaji dariya. Da zai tafi hannu ta daga mishi
tana mishi bye-bye tana dariya. Duk sai Alhajin
ya bata tausayi Alhajin,har Ja'afar na daga mata
gira halamar tambaya. Marairaicewa tayi tare da
shagwa6e fuska. "Y'arka ta rabani da Alhajina
shikenan kunji dad'i.. Harara ya sakar mata
kamin yace "toh bishi, Allah yai ma y'ata albarka
yarinya mai kishin Abbanta koh? Kai ta daga
mishi tana dariya,da murna ya shillata sama ya
chafe suna dariya. Gwalo yai ma Salman,sai
Miemie ma ta hau mata,tuni ta fara chunno
musu baki suna cikin shagwa6a. By Feenat
Ja'afar.
Like ? 2 ? Reply ? Report ? Aug 11
Feenat Ja'afar Novel's
*A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*. 46_Ba
sauran jira,dan karara suke nuna ma fitsara a
gidan Mama, su Ja'afar abin nema ya samu,ba
guntun fulako,ba shiri ta bama Abba shawarar ayi
a mayar da auren nan. Wata daya aka sa suka
sha biki kamar ba gobe.. Nan take jin labarin
auren Bintu a gidan mai mata uku,tana chan ta
zama bora. Su Maman Abba duk sun halarci bikin
nata,nan take tsurkuta mata labarin Maman
Ummi kan ranar ta fita gantali miji ya
dawo,bayan ta dawo yace ta nemi inda dare ya
mata,karshe dai akai saki. Murmushi tayi,tasan
Allah ba azzalumin sarki bane,dole yadda taga
tasku Maman Ummi tagani itama. Jingina yayi a
jikin bango yana kare mata kallo,fuska rufe ruf da
g'yale,murmushi yayi dan tunawa da daren
farkonsu a wanchan gidan. Karasawa yayi tare
da g'yaran murya kad'an yana leka fuskarta.
Zama yayi tare da sauke ajiyar zuciya. A hankali
ya kai hannunshi tare da daga mayafin da ta rufe
fuskar. Tsam yayi yana kallonta ido cikin ido,tuni
ya marairaice mata fuska,kuka fa?.. Hannu yasa
yana share mata wani na zubowa,duka ya hayo
gadon tare da janyota yana shafo bayanta
halamun tai shiru. Sai da tai shiru kan ya dago
kanta. Ido suka zuba ma juna ba koh kiftawa.
Chan ya nisa cikin murya kamar mai jin bacci
yace "Kin tuna kalaman da na ta6a turo miki na
karshe cikin text message dina kuwa?.. Tunowa
ta fara,sai yai murmushi tare da zamewa kan
katifa da ita a kafad'arshi. Ajiyar zuciya suka
sauke tare da kamo y'atsunta. "Na ce miki _" a
heart dat truly loves never loses hope..but
always believes in d promise of love,no matter
how long d time and how far d distance,at d right
time,love will fine a way".._ "Hope kin yarda da
maganar ba wai soki burutsu Masoyinki bane?.
Kai ta daga mishi halamar ta yadda,tunda ga nan
K'ADDARAR wani zama ya kara had'a su waje
daya. Yau kam ya gama gasa mata jiki da
d'anyun kalaman da ya tanadesu kawai da
Salmanshi,fatanshi Allah ya kare sa6ani a
tsakani. Washegari da t'sant'sar farin ciki suka
tashi,suna kitchen had'a break fast sai nannan
yake da ita. Tashin Miemie suka ji tana kiran
Aunty cikin kuka taga sabon waje. Ganin iyayen
waje daya ita kanta sai binsu take da kallo,
mot'si kad'an ta kallesu,kamar wacce bata so su
rabu da juna suyi rayuwarsu tare. ********** Yau
ziyara aka fito ta sallah ita dasu Ummi, Sun zaga
duk inda ta tambaya saura gida 1 taga sun
karkata zasu shiga gidan kawunsu wanda jiya
sunje. Ja tai ta tsaya tare da ce musu su shiga
su fito dan yau bata tambayi nan ba. Murmushi
Aunty A'i tai tare da kad'a kai,a lalle kullum
Salma hankali na kara zuwar mata. Tuni Ummi
kam tai gaba tana t'saki. Tana nan tsaye
kawunsu ya fito a gidan,bayan sun gaisa yace
mata ya bata shiga ba ga y'an uwanta suna ciki?
Kai a kasa tace "Abba ban tambayi nan ba
ne,dan jiya munzo yini. Murmushi yayi na jin
dad'i, "hakane kinyi tunani mai kyau,Allah ya miki
albarka. Kai ta kara kasa kamin ta amsa. Kud'i
ya ciro daga aljihu ya kirga dubu ya bata,dan
sosai Salma tana wa mutane bazata,yana
matukar son mutum mai gyara kuranshi. "Sannu
da jira uwar y'an ka'ida... Juyawa tayi daga
kallon wani a mota sun tsaya da Kawunsu da ya
wuce yanzu,sai dai kan ta tantance su Ummi sun
fito. Murmushi ta mata tare da basar da zancen
suna tafiya. "Wannan ai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login