Showing 6001 words to 9000 words out of 42609 words

Chapter 3 - A BAKIN AUREN KI Complete Writing by Feenah.doc

30 Aug 2025

1315

point_ din nan sai lot'sa wa yake.
Tuni ta kara tafiya da imanin Muzammil,har yake
ji kamar ya taro ta kan ta iso.
By
Feenat Ja'afar.
[7/22, 4:57 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
*o Feenat Ja'afar*.
12_Ita kanta Ummi tai mamakin Salma da
sakewar ta.
Sun gaisa da isma'il saurayin Ummin su kuma
suka zaga dayan bangaren motar,
Kusan kawai d'aurewa take tana mishi yake,
amma ita sam taki jinin saurayi mai shegen
surutun t'siya.
Hakan yasa d'uk taji ta gagu su k'auce, ga tasan
Abba gaf yake da zuwa da magriba tayi.
Kamar ance daga kanki, Ja'afar tagani kusan su
kad'an, tamkar gunki yaja ya t'saya, ga nan
wannan budurwar da ta ta6a ganin su itama tana
k'allo su,sai ta k'alli Ja'afar, kawai sai ta d'auke
kai kamar bata gansu ba.
Harda kara bawa Muzammil wani _attention_ na
daban tana murmushi.
Cikin sanyin jiki ya juya,tana dan satar k'allon
shi,a baya budurwar tabi shi tana waiwayen
Salman,ji tai kamar ta k'wada mai kira,So ba
k'arya bane Salma.
Da k'allo Ummi ta bisu lokacin da suka zago ita
da isma'il, sallama sukayi,suna kokarin jan mota
sai ga wata bakar mota ta _parker_.
Ganin su Garba yasa da sauri Salma ta daga ma
muzammil hannu tana mishi murmushi.
Ja'afar dake k'allonta ta glass din ya rint'se ido
da sauri.
Ganin zata juya yasa Garba fad'in "Salma" da
sauri.
Juyo wa tai lokacin da yake yafito Jafar da
hannu halamar ya fito.
Koh ta kansu Ummi bata bi ba tai gida.
Yake tai mishi lokacin da suke karasowa,sai dai
koh inda Ja'afar yake bata k'alla ba shi da
budurwar shi.
Cikin barkwanci Garba yace "duniya da alkawari
kuwa Malama Salma?.. Murmushi tai mishi iya
le6e, "ashe kin dawo amma koh mu sani..
Karon farko ta k'allo gun Ja'afar, idonshi k'wa a
kanta girrr...ba koh kiftawa.
Da sauri ta d'auke kai daga kanshi.
Gaidasu tayi,budurwar na mata an dawo. Lafiya?
A ciki ciki ta amsa,Garba yace "yaushe a gari?
An gama lafiya _hope_?
Da mamaki take k'allon shi,yanzu dama da
wanda zai ce bai san y'an makaranta sun dawo
ba?
Kawai dai sai ta maze, "yau kusan satin mu da
dawo wa.
K'allo Ja'afar d'in Garba yayi,kan ya dawo da
K'allonshi ga Salman.
Ba wannan dawowar ba,yau k'wana uku da
zuwan mu K'anwarki tace mana kinyi tafiya...
Da sauri ta dago kai da mamaki,tana k'allo gun
Ja'afar d'in ya d'auke kai.
Garba yaci gaba, "zuwan mutumin kenan daga
Zaria yace sai ya zo ya ganki ya miki murna,ashe
ke har kin ma fice a garin.
Batta bakin magana,dan bata san amsar basu
ba,amma Ummi tana mata daya a rayuwa..wai tai
tafiya?
"Ga nan mutumin jiya har sururu yake yaganki da
dare ina mishi t'siya, ashe ke ce.
Kai ta daga,kan ta kara k'allon Ja'afar, d'anna
wayarshi yake kamar bai wajen.
Cikin wasa Garba yace "toh ni zan gabatar mata
da ita ko mey da kai mikis?..kasan ba kunya zan
ba ni.
Murmushi budurwar tayi kai duk'e, dan sam bata
ga fuska gun Salman ba.
K'allon Ja'afar din take,yayin da yake k'allon
Garba yai shiru.
"Toh,mu bama sanya, sai ya juyo gun Salman,
"Salma ga nan budurwa,kuma matar... Da sauri
ta rint'se ido,kan ta karasa da "Ja'afar"... Na
sani Malam Garba...
D'uk ido suka zuba mata har Ja'afar baki sake,jin
shirun yasa ta bud'e ido akansu,yadda suke
k'allonta tasan tai su6ul da baka...
Cije le6e tai,amma ta bada kanta wallahi....
Dariyar keta Garba yasa harda k'yak'yatawa, sai
ta dago tana k'allonshi.
Sai da yai mai isarshi kan ya k'allo Billy,
"Haba,Yanzu na ji batu,ni fa naga kowa yana
sassahan kamshi,ashe-ashe...uhm uhm
_Jealousy_...
"Toh wannan Matar Garba ce bata Ja'afar
ba,sassauto madam.
Wani irin sanyi taji ya ziyarci zuciyar ta,har
batasan sanda murmushi ya su6uce mata ba.
A kunya ce ta k'allo Billy,sai ta mat'sa kusan da
ita kan tace "sannu da zuwa...
Dariya suka sa mata banda Ja'afar da ya dan
dara,idonshi kir a kanta,bazai iya fassara mey
hakan yake nufi ba, shin Salma na son sa da
kishin sa ne koh mey?
Ita dey sai dan satar K'allonshi take,amma
bazata iya fassara ina ya dosa ba.
Mota su Billy sukai suka barsu,ga nan magriba ta
gabato,gaidashi ta kara yi itama ciki
ciki,t'sayuwa ya g'yara kan ya amsa,tare da mata
murnar kammala karatu,shiru ba mai cewa
uffan,kowa miskilin kanshi,kawai sai sukai
sallama kan gobe zai zo.
Tana shiga gida dan takaici kasa ma Ummi
magana ta cikin fad'a."yanzu Ummi kina k'yauta
min kenan a rayuwa? Mey Ya Ja'afar ya t'sare
miki ne ki ka ki jinin shi?
Rai ta had'e, kan tace "oho,kawai bai min bane...
Ga nan sakon daga Muzammil,kinga in da ake
harka ai...
Kai ta k'ada dan takaici tai d'aki batabi koh ta
kayan ba.
Washegari dan kalata sai ga su sun dawo, ana
la'asar, mama ta fita unguwa.
Ado Ummi ta ciwo da tafi na jiya,sakare tai ganin
Salma koh mot'sawa batai ba.
"Koh ba zaki bane Salma?
A tunzure tace "ba zani ba..
Baki Ummin ta ta6e,kan ta daga kafada,
"mat'salar ki ce wannan kuma... Sai tai waje.
Aiko yaro sau biyu ana yi daga waje daga
Muzammil amma fur taki fita.
A ka'ro na uku ne yaron suka shigo da Mama da
ta dawo daga unguwa.
Dole ta tashi badan rai naso ba,sai dan ganin
Ummi ta shigo ta had'a ta da Mama kan taki
zuwa gun Muzammil.
Tana had'a rai ta fito,sai dai da mamakinta taga
Ya Ja'afar t'saye yana aiken yaro kan tazo. Da
sauri ta koma cikin zauren kan ya ganta.
Jim tai kad'an bayan fitar yaron kan ta fito,kanta
t'saye tai gun Ya Ja'afar, kan tace ya bata minti
biyu dan Allah.
Kai kawai ya k'ada mata,sai tai gun su Ummi,a
mutunce suka gaisa,kan tace da Muzammil
sakon shi sai gobe.. Bata jira amsa ba tai gaba.
Shi kam Ja'afar k'allonta kawai yake,amma tuni
har yazo wuya.
Tabbas dole ya bayyanawa Salma yau ranshi ba
sai an k'wana ba,dan wannan samarin tsaf sai su
iya kasa shi yana k'allo.
"Bissmillah, muje zaure... Bai yi musu ba yabi
bayanta.
Har ya dan saki fuska, dan sam ba kaunar zaman
ta a layi yake ba.
Bayan sun gaisa yake bata labarin abinda yasa
bai je mata ba.
"Kinsan Mamana tana a Zaria ne,sun rabu da
Abba tun ina dan shekara biyar,hakan ya zamana
Abba ya k'ar6e ni a dalilin tai aure,nakan kai
mata ziyara haka,sannan dan ita na zabi zuwa
Zaria karatu.
A _time_ d'in da za ai _visiting_ aka aiko bata
lafiya,chan naje har t'sawan wata uku.
"Taji sauki sosai,har tana ta fad'an na koma
bak'in aiki na,ana haka y'arta K'anwata ta dawo
sun gama makaranta,hakan yasa na tuna da
Salma.. Nan nai shiri na dawo,duk dan na
ganki,sai aka samu akasi, Ummi tace kinyi
tafiya... Shiru yai kai duk'e, itama tai tsam tana
sauraren shi.
"Salma"...kai ta dago ta dan k'alleshi, shima
idonshi a kanta. "Yanzu kam lokaci yayi da zan
sanar ki wani sirri,sai d'ai ina fatan wani bai
rigani yad'awa ba...
"Salma"... Cikin wata siga ya fad'i, kan yace "na
jima ina dakon son ki azuciyata,tun ma kan
Salman tasan itace...
K'allonshi take baki sake,shikam ya zage sai
tona sirrin ranshi yake a gare ta ido bud'e..
Dad'i, farin ciki har ya kasa misaltuwa a gun
Salma,So d'aya ne, tasan Ya Ja'afar tai ma.
By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 8:59 AM - Queen Safiyyert???a: *A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*. 13_Har
yai shiru ita kam idonta na kanshi,kan dafa bisani
tai kasa da kai cike da kunya,kawai shima sai ya
zuba mata na mujiya yana murmushi. Magana
suke jiyo wa kasa-kasa,duk sai suka zuba ma
kofar ido. "Ba mutunci ace kowa yana wuce wa
yana ganin ku a t'saye a titi, gaba na fad'a miki
ki nemi koh zaure ne koh cikin gid... Shiru Abban
yai dan ganin Ja'afar a zauren da Salma.
D'ukawa ya danyi kan yai ma Abban sannu da
zuwa. Cikin sakin fuska Abban ya amsa,Salma
ma ta mai kai duk'e. Sim-sim Ummi tazo ta
wuce,dan duk iskancin ta tana bala'in tsoron
Abban su sosai. Yana shiga gida shima yai mata
sallama da alkawarin gobe zai zo dan jin amsar
shi. Da t'sananin farin ciki ta shiga yau, haka
dashi ta tashi. Tun jiyan Ummi ke ci mata kunu,
tasan kuma d'uk akan Muzammil ne,shi yasa koh
bi takanta batai ba. Washegari tun kan Ummi ta
shiga wankan yamman ta na kullum Salma ke
gaban mudubi, sosai take k'yali, yau d'aya ta
bata lokaci dan Ja'afar d'inta. Ummi da tun dazu
ta fito tana jira ta ta6e baki, ''kiyi kare ni ki ban
waje na zauna Malama... Juyo wa tai da tana
yage mata baki, "dan Allah Ummi nayi k'yau?..
Bar zancen wasa. Baki ta ta6e kan ta juyar da
kai gefe, "oho miki ni kar ki daman. Murmushi tai
kan ta tashi ta bata gu. Bincike ta fara,a babu
babu Mama kala 5-5 ta musu kayan _candy_ na
ke ce sa'a, ciki masu ruwan _purple_ ne kusan
duk. Cikin nishad'i ta ciro attamfa wata mai
_purple_ da rat'sin _yellow_ riga da siket,
murmushi tai dan tuna wa da kalar da Ja'afar
yafi so kenan. Tunda ta zura kayan ta nad'a
d'auri take bin kanta da k'allo a mudubi ta gefen
Ummi. MashaAllah tai k'yau, gashin da ya fito ta
kasa take turawa cikin dank'wali,ta kai dubenta
ga Ummi wacce sai ko'k'arin fiddo nata take tabi
dank'wali ta kansu. Murmushi kawai ta
mata,tasan da tace ta mayar su ciki ma a iska.
Sai dai tana d'akko turare ta hau feeeee ba ko
kakkautawa. "Haba Ummi,turaren nan kinsan
haramun ne sashi ki fita koh?.. Ga gashi kullum
sai ance ki alkinta shi.. Allah kina *TABARRUJ*
da yawa.... Galala take k'allonta, kan ta ja t'saki
tai waje. Iya wuya Salma tazo, ta bala'in t'sanar
t'saki. Ba'a jima ba Ja'afar yazo.. Tabarma yau
ta d'aukar musu,shima yasha wankan farin kaya
da farin takalmi _half cover_ sosai yai mata
k'yau. Yadda yake fara'a da bin k'allonta tasan
itama ta wanke shi. Suna t'saka da gaisawa
cikin nishad'i yaro yazo,wai tazo a waje inji
Ummi. Tuni ya sauya,dan yaga zuwan su
Muzammil. "Minti biyu kawai.. Kai ya k'ada mata
da dan yake. Tana fita suka ware gefe,tsakani da
Allah ta fad'a mishi yai hakuri. Baki sake yake
binta dashi har ta kule cikin gida. Amma Ja'afar
ya bala'in k'wada shi da kasa,dan haushi koh
isma'il bai jira ba yai gaba. Ita kam tana zuwa ta
bashi amsa gamshasshiya, wanda tasa fara'ar
Jafaririn ta dad'u ba shiri. Tad'i suke kamar ba
gobe, mot'si kad'an yace "kinyi k'yau..... Itama
cikin kunya tace yayi shima. ***************
************** "Naga sai zarmewa kike fa akan
Ja'afar salma,sam kinfi k'arfin shi kima ji da
wai,gaba ake son ci ba baya ba wallahi,d'uk da
ban san wacce iriyar amsa kika bawa Muzammil
ba... Da harara Salma ta bita, kan tai k'wafa, "ina
ruwan ki da sha'anina? Ke har kin isa ki fad'a
min wanda ya dace dani Ummi? Baki Ummin ta
ta6e, "ke dai kika sani,dama ni meye nawa? Ni
koh ana saurayi mey zanyi da Ja'afar mai shegen
dacin ran t'siya... "Wai ku baku zama inuwa
d'aya ne da juna Salma? Mey yasa baki iya daga
ma Ummi K'afa sai kin tanka mata kullum kuna
sa makota na jin ina daga murya.. Kasa Salma
tai da kai kawai,tasan yanzu in mama taji ta
kad'e.. Kamar k'wa wacce Ummi ta karanci
zuciyarta ta amshe.. "Wai fa mama daga
shawara ta tsaya min masifa,yau akan wannan
dan gidan Malam Kabiru mai shago ta kori
Muzammil,daga fad'a mata gaskiya ta hau ni da
masifa.. Dan Mama daga ganin yadda Muzammil
ya tafi rai 6ace nasan cewa tai bata son shi...
"Eh bana son shi,koh ana son dole?.. Ja'afar d'in
da kika rena ni shi ya min ki ji da wai.... "Kunga
ku min a hankali,koh yanzun nan na sa6awa
mutum... Shiru sukai,yayinda Salma taci ka tai
dam. "Ke ummi wani dan wajen Malam Kabirun
kike fad'a? Da harara Ummin ta k'allo Salma kan
tai ma Mama bayani,"yanzu haka mama Malamin
makaranta ne wallahi yana chan yana kokawa da
alli.. Jim Maman tayi kamar mai tunani,chan ta
nisa tace "Ikon Allah..anya yarinyar nan Salma
ba'a min misanye dake ba a layin jarirai a
haihuwa ba?... Mutum arziki na binshi yana
ki?...Ina laifin yaran nan?har kasa suka gaida
ni,ga mota ga boko..amma in banda abinki mey
na sama yaci bare ya bawa na kasa? Da shagon
uban zaku dogara koh da kud'in malami?.....
Shiru Maman tayi ganin yadda Salman ke
hawaye... "Au,au,Salma kuka? Daga fad'an
gaskiyar? Kai ta k'ada ma Maman. "A ni tawa
mai sauki ne Salma,ina d'ai hanga miki gaba ne
kawai... Amma banga abin kuka.... "Wa ke
kuka?... Assalamu Alaikum. Shiru sukai salman
na goge ido,sai Mama da ta amsa mishi sallama.
"Sannu da zuwa Abba. Kai ya daga musu kan ya
amsa. D'uk suka tashi sim-sim sukai d'aki. Sai da
Abban ya gama komai yasa Mama ta kira su.
Kowa tai ladab kai kasa suna saurarar Abba. "Ni
ke Ummi na ma kasa gane alkiblar da ki ka kama
sam,kullum da wanda za'a ga yazo gunki,sai
aukin shegen zance a titi ba wanda ya iya yazo
ya samu iyayen ki.. "Ga nan yayarki yau d'in nan
yaron nan na wajen Alhaji Kabiru yasa Baban shi
yazo muka zanta kan yana son Salma da
aure,kuma har sun sasanta da ita.. "Koh ba ai
haka ba Salma?... Kai duk'e cike da kunya ta
daga kai halamar anyi. "Haka shine musulunci, ta
haka kuma ake gane da'ar yaron da zai auri
y'arka... Shiru kake ji Ummi anyi lakwas. Nan ya
kara ja ma Ummi k'unne kan tara samari da
zancen waje,ya kuma ja mata k'unne kan ta
fidda na aure koh ya fiddawa mutum. ***** ***
Zancen aure dai ya kank'ama tsakanin Ya Ja'afar
da Salma. Itama Ummi Isma'il yace da gaske
yake.. Mat'sala d'aya tafi damun Salma,yadda
komai Ja'afar ya bata na alheri a rene yake gun
su Mama, barin Ummi. Dan ita fachaka isma'il
yake mata kamar ba gobe. Tun abin bai damunta
yau da gobe har ta fara ganin kamar Ja'afar
mammako yake mata. Zuciya bata kashi. By
Feenat Ja'afar. ?^NWA.
Like ? 2 ? Reply ? Report ? Jul 24
Feenat Ja'afar Novel's
*A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
14_Anyi bikin su Garba. Ana haka saurayin Ummi
ya d'allo mata wata sabuwar waya,ita kam tun
wata Zain da ya bata,nan habaici ya karu gun
Ummi. Biki ya kusa sukai shirin zuwa Borno
dangin Abban su. Sunyi sallama da Ja'afar ta
shigo gida rike da farar ambalan,d'uk suna zaune
t'sakar gida har Aunty A'i da yaronta. Hannunta
Ummi ta k'alla, kan cike da shakiyanci tace "ta
Ja'afar mey aka samu ne haka har a farar
takadda?.. Harara ta dan mata kan ta mikawa
Mama. Kai Maman ta k'ada, kan tace "a rabani
da kayan haushi,rike abinki kawai ki kirga...
Dariya Ummi ta sa,wanda tuni ta kara kular da
Salma. "Mama ba ma sai ta kirga ba,dan wallahi
ba kaffara nasan kud'in nan bai fi dubu biyu ba...
Kanta Salma ta yiwo a tunzure mama tai musu
iyaka. "Meye na jin haushi?.. K'yautar tashi tana
wuce nan ne?... Ba dai d'an d'an kasuwa zaki
aura ba? K'wafa tai,kan tace "baki fara ganin
komai ba ma Salma. Aunty A'i ce ta k'ar6a ta
kirga,ai kam sabbin hamsin hamsin ne ta dubu
biyu. Mama tace "Ahab,na sani ai. D'aki Salman
tai tana hawaye,sam bata kaunar abinda ake ma
Ja'afar,amma shima da laifin shi,dubu biyu ina
zata kaita? ****************************** Biki
kam yazo,gashi yau har anje jere, k'warai sunyi
mamakin gidan Ja'afar da gina kuma da kanshi.
D'uk da ba wani babba bane,dan koh t'sakar
gidan karama ce,babban _parlour_ ne sai _bed
room_ da band'aki aciki,ga _kitchen_ a ciki
karami,sai d'aki d'aya daban a waje, d'ai d'ai
zaman mutum d'aya de,rufin asiri dai ak'wai
shi,Alli da shago sunyi rana. Sa6anin Ummi mai
tafkeken gida da mai gate yasha alatu. Yanzu
lefe ake wat'sa ido aga na Ja'afar, dan tuni na
Ummi yazo san barka,sai zuzutawa ake. Salma in
ta tuno gabanta har fad'uwa yake,fatan ta Ya
Ja'afar ya fitar ta a magana. Dan tun a kud'in
anko taga tasku,dan isma'il ankon k'yauta yai ma
k'awayen Ummi da dubu ashirin nata na fitar
biki. Shikam sai hakuri yake bata,kan shi bai
d'aura ma kanshi abinda bazai iya ba,bare daga
baya ya dame shi. Kawai sai ta toshe k'unnenta
gun su mama,komai ta samu ta samu,wanda ta
rasa tasan bai da hali. Mamaki kam Ja'afar ya
bama su mama, dan ak'wati shidan nan y'ar yayi
sai da aka bat'se ta da kaya, ga uban
_cosmetics_ har a jakar Ghana must go. Aciki da
swiss d'aya, holland biyu,engla biyu,sai su code
dav'ior,sauran kam duk kana na ne su dangin
material. Salma baki har k'unne jin ba wanda ya
kushe a dangin sai d'ai ace na Ummi yafi t'sada.
Anyi biki lafiya kowa ya wat'se an bar amare da
halin su a gidan su. Kauna ziryarta taga gun
Ja'afar mai t'sayawa a rai,sosai sukai amarcin su
cikin kula da tarairayar juna,musamman ga
Ja'afar d'in. _kitchen_ tare,wanki tare,shara
tare,duk aiki in dai ba ya fita bane yana a makale
da Salman sa, d'uk wata kulawa tana ganinta a
gun Ja'afar,shi yasa sai abinda yace take
aiwatarwa matukar bai sa6a Shari'a ba. Yadda ta
fuskanta ma kamar bai kaunar tai nesa dashi,koh
dan ganin har wata biyu kenan da bikinsu amma
ba inda taje sai barkar Aunty A'i da makotansu
da taje tun tana sati daya da zuwa. Sai dai tai ta
jiyo shewar su ta katangar gidan halamar ana ta
_chapter_. *Farin Bacin komai* Yau tun tashinta
sallar asuba ta kasa komawa bacci,sakamakon
tun dare da yace yau ta shirya da wuri zata gida.
Dan farin ciki ji take kamar a wani garin zata je
musu. Waya tai da Ummi kan zata fito yau gida.
Gaban madubi take tana yi tana k'allon agogo
har sha d'aya saura. Karar _machine_ d'in Ya
Ja'afar taji a kofar gidan,sai ta cigaba da
shiryawa. Sallamar shi taji,daga d'akin ta amsa
tana fara'a. Yana shiga ya jingina da kofar d'akin
yana mata murmushi,ta mudubin ta mishi tana
d'auri. Kan ya tako gaban madubin ya t'saya ta
bayanta. "Sannu da dawo wa.. Kai ya daga
mata,sai kare mata k'allo yake, kayan sun mata
k'yau, "Kinyi k'yau... Tashi tai da jin dad'in
kalaman shi,sai ta dan ja mishi kumatu kan tace
"na gode... Muje koh?.. Ta fara nad'a lifaya. Sai
ya rike mata daya gefen tana nad'a dayan da
murmushi. Da kanshi ya yafa mata akai ya rufe
ko'ina ruf. "Ba dan kin nace sa abar nan ba da
hijab d'inki za ki sa zai fi min k'wanciyar
hankali.. Murmushi tayi kan ta lang'wa6e kai, "ai
ba g'yale bane Ya Ja'afar, Allah ina son lifaya.
Kai ya k'ada mata yana d'aukar mata jaka. "Toh
naji,amma ni banga maraba ba. Murmushi kawai
tai tana d'aukan mukulli. Machine d'in ya karkata
mata kirar lifan,a hankali take ko'k'arin hawa sai
ya dan girgiza machine din,da sauri k'wa ta dafa
kafad'arshi suna dariya. In kagansu g'wanin k'yau
suna ta nishad'i har suka zo gida. Tana g'yara
lifaya tace "bazaka shiga ba?.. Kai ya girgiza
mata da murmushi,"ki gaida su Mama, anjima in
nazo d'aukan ki zan shiga, yanzun makaranta zan
koma. Kai ta k'ada mishi,kan ta bashi hannu,sai
ya bata suka gaisa suna dariya. "Abincin ka yana
a kitchen a bisa faranti,na had'a komai, a dawo
lafiya... Kai ya daga yana mata murmushi,jin yaki
tafiya tace "kaje man.. Kafad'a ya make yana
nuna mata gefen fuskanshi, kai ta k'ada mishi
cikin kunya. "A layi muke fa... Shima sai ya kada
kan tukun ya tada sukai sallama. Har ya kule
tana daga mishi hannu,kan tai cikin gida. Da dan
gudunta ta shiga tana kiran Mama. D'uk suna
d'aki, Ummi an hakimce a kujera ana d'anna
waya. "Har kun rigani ashe d'uk saurin nan
nawa?.. K'allonta Ummi take ganin tana since
lifaya,ga flasks da jaka an ajiye. "A ina zaki zo
da wuri,ke dad'i miji ce ai.. Banza tai da ita tana
gaida Mama, itama Maman a dan ciki ta amsa
mata. D'uk sai taji ba dad'i, jikinta yai sanyi,da
murnar ta tazo amma sun dakushe mata. "Sai ya
barki ki waiwayo mu?.. Maman ta k'alla, kan tai
kasa da kai, "ai na zata irin ta y'an da zai
miki,sai kin shekara koh kin fito yawan arba'in....
Baki Ummi ta ta6e,kan tace "d'uk mai irin halin
Ja'afar ai dole yai k'ulle Mama,in banda haka
wata biyu wai sai yau za kizo gidan ku,ni nazo
yafi a girga,wallahi tun wuri ki mawa tufkar
hanci.. Dan in kika sabar mishi da haka zai mike.
Dagowa tai da niyar yi wa Ummi magana Mama
ta tari numfashinta. "Y'ar uwar ki ce,dole ta fad'a
miki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login