Showing 15001 words to 18000 words out of 42609 words

Chapter 6 - A BAKIN AUREN KI Complete Writing by Feenah.doc

30 Aug 2025

1310

ya barta
ta fita toh. K'allonta yake,abu yai sauki yanzu
tana son dawo da hali? "Son ranki za'a bi yanzu
koh nawa Salma?... A gida na ban isa nace ga
abinda za ai ba sai ace a'a?.. Meye haka kike
son kawo wa kuma da ya wuce?.... Hawaye ta
fara mishi,tabbas yau in bata fita ba,toh gobe fa
sai dai ta toshe kunne. Haushi tai bala'in
bashi,akan wannan shine harda kuka?.. Sam bai
son abin da ya wuce a dawo dashi. Nan ta zaune
mishi tana mishi kukan gardamar sai ya batta.
Haka yanaji yana gani sai shi ya sauke ya barta
yace ta shirya su je. Da murnarta ta shirya suka
fita ya sauke ta. Sai dai shi sam baida walwala.
Haka tai ta fita har ran suyar nama,washegari
ma wai zata wanke gida,anan suka hau suka
fad'o.. Ya ja ta ja,harda fad'in dama ance
tsoronshi take ji. Ya rant'se da in har ta fita,toh
zai maimaita mata abin ranar,wato ta fita a bakin
aurenta. Tuni ta nut'su ta dawo hankalin ta. Tuni
ya kashe bakin t'sanya,har ya fice ya barta tana
kuka,harda dariyar mugunta... Ya k'wa gano lago
ai. By Feenat Ja'afar.
Like ? 2 ? Reply ? Report ? Jul 29
Feenat Ja'afar Novel's
*A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
21_Ranar ta fita a Napep ta layin su Ja'afar taga
wani kamar shi tare da wata, har zasu wuce ta
gane Bintu ce,da sauri tace mai Napep ya t'saya.
Sam a yadda suke ba kace ba masoya bane,dan
sai wani sunne kai take kasa halamar kunya.
Tuni zuciyarta ta hau tafasa,ba shiri tai wajen
gadan-gadan,dai dai suyi sallama harda dago
mishi hannu. Kan ta karasa har ya juyo itama ta
tafi... Ganin yanayinta shima ya dan
tsorata,amma sai ya maze. "A'a, har kin fito?..
Harara ta sakar mishi kan ta k'allo Bintun da har
tai mata nisa. "Ban sani ba... Ashe dama zance
ka fito shine kace na hau adaidata koh?.. Kuma
da Bintu?.. Har kana wani yage mata baki...
Hannu ya kai kan bakinshi halamar tai shiru yana
duba layin, "Haba Salma,a titi fa muke,kiyi hakuri
ba abinda ki ke zata bane ba... Harara ta kara
sakar mishi,kan ta farga har ido ya ciko da
hawaye. Tabbas yau ya tabo jaraba... Dan sarai
yasan Bintu kam sonshi take,kuma Salma ta
sani. Akan kishiya k'wa, yasan sai Salma taki c??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????i
taki sha. Tuni ya hau lallami harda rantse rantse
kamin ta yarda bayan anje gida. Wataran yakan
yi tunanin koh Salma na da Aljanu,in ta tashi
sauya hali tafard daya ne,sai dai in ya bud'e
mata wuta su shirya. ~~~~~~~~~~ "Shiru ake
jinki makociya,koh dan ziyarar yamman nan an
daina zuwar mana sai jefi-jefi, koh mutumin har
yau yana nan da kullen?... Baki ta dan ta6e,kan
ta bawa maman Ummi amsa. "Ai sai abinda yai
gaba, yanzu tunda akai abinnan na farko abu
kadan sai ya kafan sharad'i kan in na t'sallaka a
bakin aurena, ina gudun rabuwar mu,yanzu ma
minti goma ya ban na dawo. Baki Maman Ummin
ta ta6e, "lalle kina da aiki in dai mazan nan ne,
saf zasu mayarka marar y'anci in bakai ma
tufkar hanci ba,harda lokaci? Tab aiki.. Ga gobe
sunan _nurse_ din layin chan (Maman
Nuwaira),ke koh barka baki je ba, ke kinsan za'a
watsa karya kiyi kok'ari ya barki muje. Kai ta
k'ada, "Ai dole,dan wallahi baza ai bani ba,ko bai
bari ba naje koh minti ashirin ne a wat'sa
warishan nan dani. Hannu Maman Ummi ta bata
suka tafa harda shewar su,ana haka Ummi tai
sallama,kan tunda ta shiga Jafar yace tana nan
ta fito,wai sai had'a rai yake,shi yasa ta bar
mishi gidan, nan ta daura kan na Maman Ummi,
Zuwa chan Maman ummin tace "Kiyi kok'ari hudu
ki biyo min zuwa 5 dawo. Da wannan suka baje
har ta wuce ka'idar Ja'afar. *Washegari*. "Wai
dan Allah Salma na tambaye ki zaki ban amsa?
Y'atsine fuska tai kan tace "ina ji.. "Shin dad'i ki
ke ji in kin t'saya muna musayarya magana
dake?.. "Mey yasa in na ce ki bar abu sai dai nai
son ranki,amma ni ban isa ba? "Ita maijegon ta
ta6a tako kafarta cikin gidan nan da sunan tazo
gunki?.. Ki ban amsa? Baki ta saka,kan tace
"oho,kana nufin gyaiyar sod'i zani kenan?.. Tunda
ga areni muje biki koh?.. Kai ya kada, "Ke ki ka
kira kanki haka,ba Ja'afar ba,abu daya na sani,ko
na fita ba jimawa zanyi ba, saboda in ma kin
fita,toh kisan inda dare ya miki... "Mey ka ke
nufi? Kana nufin yau ma zaka ce a bakin auren
nawa Ja'afar?.. Da sauri ya kada kai,
"K'warai,tunda abinki naga na yanzu har so yake
yafi na da, in har kam kin fitan,toh kisani,kin fita
*A BAKIN AURENKI*... Sai ki zabi wanda ya fi
miki, aure? Koh gidan suna?... Kofar ya bugo
mata yai waje tare da barinta baki sake. "Eh lalle
yau zan nuna ma tabbas ba tsoron ka nake ba
Ja'afar... Wannan kurin bakin wallahi bazai
hanani fita sunan ba,daga yau kalmar nan ta *A
BAKIN AURENKI* tabar bakinka. Daki tai tana
balbalin masifa ita kadai kamar yana k'allonta.
Kaya ta fito dasu tana duba wanda zata sa,
_lace_ din sunan Ummi ta dakko wani karamin
_swiss_ da aka sashi siyanshi dan dole. Sunan na
manya ne, dan haka sai da kure adaka. Ba koh
shakku ta fice, yau tun dazu taji gidan su Maman
Ummi t'sit kamar ruwa ya shanye su,halamar mai
gidan yana nan kenan,amma tunda ta fara jiyo
hayaniya tasan yai waje. Gidan suna kam ya
kayatu, sun samu abinda ake so tuni aka baje a
faranti ana ci ana kora wa gulmar wata. Kan ta
farga har 5 da yan mintina. Haka kawai taji
gabanta na fad'uwa hankalinta yayi gida. Tashi
tai ana fad'in ta t'saya k'ulli ya kare a k'ulla
mata tana a bawa Maman Ummi. Sauri take ta
zubawa, dan da y'ar tazara a t'sakanin su.
Adu'ar ta daya,Allah sa Ja'afar bai dawo ganin
koh ta fitan ba. Ta rasa dalilin da ya sa
hankalinta ya tashi,bayan ita ta zabi hakan.
Lekawar da zatai shine taci ka'ro da Ja'afar suka
had'a ido. *WAIWAYE*... ***************
************** Haka yai ta juyi har kusan k'arfe
biyu. Washegari haka ta tashi sukuku, ga
fargabar Abba yau zai dawo,ga wani mugun
mak'on Ja'afar da yake taso mata. Kai in ma ba
wai bata kula bane gani take zazzabi ne a jikinta.
"Salma... Dagowa tayi ganin mama a kofa,da
mamaki fal fuska ta karaso ciki. "Wai har yau
kukan nan ki ke Salma?.. Mey yaron nan yai miki
ne haka?.. Hannu ta kai kan fuskrta,sam ba
tasan tana kuka ba, da sauri ta goge tana
k'ak'alo murmushin dole. "Mama ina k'wana.. Kai
kawai ta kada mata. "Haba Salma,kar fa ki rako
mata duniyar nan...kar ki zamo mace mai
kulafucin D'a namiji duk k'wa wulakancin da ya
mata man... Ashe ni ina chan jiya nai baccin
farin ciki da aka rabu lafiya ba rabo bare ya kawo
cikas a zawarci ashe ke kina nan kina kukan an
rabu? Haba Salma, karan nan ne fa ki ke da
dama ta biyu,tunda har ya sallame ki. "Maza
goge hawayenki ki biyoni daki yanzu. Kai ta
kada,a gaskiya ta fara mamakin irin kiyayyar
dasu mama suke ma Ja'afar, wato har ma godiya
ake ta rabu da alakakai?... Allah yaga tafi jin
haushin kanta sama da haushin Ja'afar, in ma
taji haushin shi toh bai wuce yadda ya k'ulle
mata gida ya kuma tafi koh ajikinshi. By Feenat
Ja'afar.
Like ? 1 ? Reply ? Report ? Jul 29
Feenat Ja'afar Novel's
*A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
22_"Toh wa ya jawo?... T'sam tai yayin da zuciya
ta tambaye ta, "Ni ce... Tabbas ni najawo, amma
ba laifi na bane. Kuka ta fashe dashi,tabbas anci
k'arfinta,ta ko'ina an mata dabaibayi da huduba
gur6atacciya. "Gashi na jawo wa kaina saki biyu
ba tare da na samo kan ba(kan Ja'afar).. "Oh ni
Salma.. Ina tunani na yake da har na aikata
wannan wautar?.. Ina son da nake ikirarin ina ma
Ja'afar?.. Ina ya je... "Salma... Mama ce ta
kat'se mata tunanin gaskiya da kira. Hannu tasa
ta share hawayen ta,ta daga kai tare da fitar da
iska dan daidaita nut'suwar ta. "Na'am.. Ta amsa
kan ta tashi tai waje. "Gani mama, Kan gado ta
nuna mata kan tazo ta zauna. Ba musu ta
karaso. Kafad'arta ta dafa kan ta numfasa, "Kina
ji koh Salma? Kai ta daga mata. "Baban ki yau
nasan zai dawo,tabbas ya rit'saki nasan zai cid'a
ki ne a banza. "Yanzu abinda nake so kiyi
shine,ki je gidan A'i,dan mijinta baya gari ya tafi
sari,ki barni in na gama lalla6a shi sai ki
dawo,dan karan nan kam sai dai ai wacce za ayi,
amma aure kin gama... G'wara a chanja
hannu,tunda wannan d'in ba fus, bare ass,sai dan
banzan dacin rai ba koh gidan kai... Hawaye ne
ya zubo mata,ba da ban suna matukar kama da
Mama ba,da tayi shakkun akan haihuwar ta...
Mama na da kamasho a ta6ar6arewar aurenta
kashi 70 acikin dari... Tabbas uwa uwa ce,
amma su kam tasu uwar sai g'yaran Allah..
"Au,au,kuka ki ke? Dan nace baida gidan
kanshi?.. Koh shi ya siya ya gina da gumin ajin?..
Yarinya ki duba yadda ake harka,y'an uwanki na
shiga ta alfarma amma ke kin zama y'ar k'allo..
Ki farka a bacci Salma,dan rayuwar nan ta zo mu
fafata ce. Kai ta k'ada tana goge ido,sai ta mike
tai hanyar waje, "Bari na shirya zuwa gidan
Aunty A'in, naga 10 tayi. Kai Maman ta daga
harda washe baki, "Yauwa,ko ke fa.. Maza aje a
shirya,ga nan abincinki a kitchen. Kai ta k'ada
kan tai waje, da kallo Maman ta bita, ba abinda
y'arta ya gaza a gareta,wa ma zai ce ta ta6a
aure in ta fito da ita gari?.. Dole kud'in da ba taci
ba da yanzu taci gun Salma. ***************
************** A k'wance take kan _3sittern_
Aunty A'i,in banda ciwan kai ba abinda take,
"Tashi ga maganin kisha... Kai ta dago,Aunty A'i
rike da kofi da _paracetamol_. Bayan tasha ta
g'yara zama,d'uk gidan bata jin da wanda bai
ta6a kushe mata Ja'afar ba sai Abba da Aunty
A'i. Hawaye ne ya zubo mata,kan kai duk'e tace
"ban san mey Ya Ja'afar ya t'sarewa su Mama
ba da sam basa kaunarshi... Yanzu ki duba Aunty
A'i Mama yau tace murna take an sake ni..
Harda fad'in g'wara da bamu samu rabo ba...
Kuka ne yaci k'arfinta,tuni ta hau yi ba
kakkautawa. Taso wa Aunty A'in tayi zuwa kusa
da ita ta hau lallashi,chan ta numfasa itama
harda hawaye ta fara fad'in "Kinyi wauta Salma
matuka,samun irin Ja'afar a yanzu wallahi sai kin
tona,irin halin da kika dinga karta mishi duk na
samu gun Abba,kinsan nima ba wai Mama nayi
dani bane sosai,dan ban fiya shiga irin shirgin
nan ba. "A gantali har gida sukutum ki ka kona
mishi Salma.. Naji ance ya kuma shiga cikin y'an
_missed call_..Bana tunanin har yau ya gama
tattare takaddun da ya rasa kuma duk a dalilinki
fa,amma dai dai da rana daya bai ta6a hanaki ci
koh sha ba?.. Duk da baki san ta ina yake samu
ba. "Maimakon ki zama mace ta gari mai
k'wantar mishi da hankali har ya manta bakin
cikin da yake ciki na rasa aikinshi,a'a sai ma
kara hura mishi wutar masifa ki ke a gida.
"Salma kina da ilimi fa,kinsan d'ukkan hukunci a
game da matar da take sa6a umarnin mijinta,
bare ke da kusan kullum cikin shi kike?.. Ina ki
ka bar islamiyar taki Salma?.. Da har kika bari
rudin su Ummi da chan wasu jahilan makotan
suke hure miki k'unne,wanda in zaki titsiye su ba
mai iya rashin mutuncin da ki ke Salma.. "Nayi
imani zaman cikin gidan ki ya fiye miki alkairi
sama da zaga makota yawan gulma da ki ke..
"Ya sanar ni shi sai a shafe wata nawa,baiga
makotan naki na zirya gidan ki ba sai dai aiken
bani taliya bani mai, shin sun fiki sanin ciwan
kansu ne Salma? "K'wanaki haka har gida na
samu yana fad'a kina fad'a, amma dana shiga nai
miki fad'a, sai kika nunan wai maza sai da wuta..
"Kan kiyi aure Salma ni nayi da shekara hudu, ba
zaki fad'an halin maza ba,amma a lokacin na biki
da murmushi ne kawai. "Ki dube ni nan Salma...
Dago tai ido jajir hawaye na zuba. "Wallahi tunda
nake akan fita unguwa ban ta6a sa'inasa da
Abban Aslam ba,kar kara in naja,ya ja,hakura
nake na barshi,wani sa'in sai kiga har ya
fita,amma sai ya dawo yace in shirya ya sauke
ni,ina fara'a za'a gama komai ba bacin rai, duk
wanda zai fad'a miki ana tank'wasa namiji ta
fad'a da bala'i wallahi karya yake miki,sai dai ma
kullum yai ta baud'e ga uwa uba sane mishi da ki
ke. "Zuciya nason d'ukkan mai k'yautata mata
Salma,sannan a kullum tana kara nisa ga wanda
ke munana mata... Ki gane wannan, tunda dama
taki,shine ya koma miki ta hagu, ki fita a bakin
aurenki Salma, tun da kuruciyar ki wai har kin
zama bazawarar k'arfi da yaji? Ranar da kanshi
Ja'afar din yazo gidan nan,akan irin yadda ba
k'ya jin maganarshi,nai mishi alkawarin zanje har
gida na miki fad'a sai gashi Allah ya kawo
wannan. Sosai tai mamakin Aunty A'i,da yau ta
zauna fed'e mata biri har wut'siya.. Tai imani duk
maganganunta ba wanda ba ita ke da laifi ba
tabbas. Wata muguwar nadama ce ta sakko
mata,kuka kam ba kama hannun yaro, har sai da
taji ba dad'i. Bataki koh yanzu ta nemi gafarar
Ja'afar ba kan ya maidata aurenshi,tai alkawarin
d'auwama acikin dakinta har sai yace Salma fito.
Aiya Salma, Ja'afar baya tataki,yanzu ta Bintu
yake.. By Feenat Ja'afar.
Like ? 1 ? Reply ? Report ? Jul 29
Feenat Ja'afar Novel's
*A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*.
23_Zazzabi harda amai take,duk zatan Aunty A'i
akan kukan da taki dainawa ne. Washegari ba
zato ba t'sammani Aunty A'i ta t'sinkayi sallamar
Abba a t'sakar gida. Lokacin dawowarta daga
band'aki kenan ta gama zuba ma Salma ruwa a
amai na tun jiya da yaki t'sayawa,sai dai tana jin
Abba ne ta mike tare da yin waje da sauri.
Hannu Aunty A'i ta d'aura aka,ganin zabga-
zabgan bulalin da Abban ya shigo dasu gidan,
fad'i yake "Ina take Aisha?.. Tuni idonta ya raina
fata,fatan ta Salma taji ta buya. Cikin in'ina tace
"Abba wa d'in?.. Hannu daya marar bulala ya
nunota dashi, "Kinci gidan ku... "Bani hanya na
wuce,yau mai rabani da Salma sai Allah a gidan
nan.. Da k'arfi Aunty A'i tace ta gudu,hayaniyar
ce ta fiddota a band'aki ta had'a uban zufa dan
azabar amai, har bata danji sosai, lekawa tai ta
labule jin an ambaci sunanta... Ido waje ta koma
da baya tana neman ma6oya,tuni ta ware tai
bayan kujera tana rufe baki da duk hannunta biyu
jin Abba a parlourn. "Dan Allah Abba kai
hakuri,wallahi bata da l... "Aisha,koh ki fito min
da ita koh bulalinnan su kare a kanki... Ido Salma
ta rint'se da sauri,kirjinta sai d'ukan tara tara
yake. Sai dai mey? Kamshi turaren kayan Abba
ne ta busu hancinta,take taji amai ya taho tai
kokarin ta mat'se sai dai ta kasa,tuni k'ak'arin
aman ya taho sai dai ciki ba komai. Bata zata ba
sai jin magiyar Aunty A'i tai tana dan Allah yai
hakuri... K'wak'waran mot'si batai ba taji saukar
bulali tai ajiki ta ko'ina. Ihu take da iya guntun
k'arfin daya rage mata tana Abba zan mutu,
ina,kawai lafta mata yake,da Aunty A'i ta rike sai
ya cika ya hau zuba mata wata. Makogaro ba
ruwa,duk ya tafi a amai,tuni har muryarta ta
dashe,sai k'ak'arin amai da take. Kamar an hullo
mama sai ganinta sukai a kid'ime,ganin yadda
yake jibgar Salman ta bala'in tsorata, da sauri tai
waje dan kara kiran yayanshi Ganin Abba zai
kisa,yasa da sauri Aunty A'i tai ma Salman rumfa
tana yai hakuri cikin kuka,ganan Salma koh
k'wakkaran mot'si batai,bai bi takanta ba ya hau
zuba musu tare, "Abba ciki ne da ita,wallahi zai
zube.... Chak ya t'saya da bulala a hannu sai
zufa yake, yai dai dai da shigar Mama tai katari
da zancen Aunty A'in. Bulala ya yarda yana
haki,tamkar yasa kuka dan bakin ciki,tunda yake
basshi da fadanshi amma bai ta6a sa hannu ya
dakesu ba sai akan Salma,wannan shine karo na
biyu gareta. So take tafi k'arfin kowa a ganin
shi,toh shi bazata fi karfinshi ba. "Ba mai fin
karfina a gidana ban maganin shi ba... Yau kin
t'sira a dalilin zancen A'i,da na lahira ya fiki jin
dad'i.. Duk da laifin nafi daura ma uwarku data
zuba ido kuna abinda kuke so... "Mun shiga
uku... Da sauri Maman tai kan Aunty A'i mai
magana. Jijjiga salman take tana kira. "Salma!...
Salma!!.. Mama bata mot'si wallahi... Tuni suka
hau jijjigata Aunty A'i na kuka. "Shikenan Malam
ka kashe min Y'a ka huta... Babu yadda banyi da
kai ba akan kai hakuri kar kazo,kar kaje,ga nan
irinta ka... "Ki rufe mana baki, koma meye ke
kika jawo, ruwan k'anin Aslam ya gani a jarka da
sauri kuma ya dakko wai su mat'sa agun,ido duk
hawaye suka mat'sa. A hankali ya dagota tare da
yayyafa mata, a hankali ta kawo numfashi sai dai
ido a rufe. "K'unnen k'ashi gare ki ne Salma,shi
yasa baza mu shirya ba sam sai kin g'yara hali.
Kuka ta fara kad'an kadan lokacin da suke
dagata, sosai ta lillisu,duk jiki ciwo. Wayar Aunty
A'i,da Ja'afar suke magana wai yaji Abban su
yace Mama ta bugo kan Abba zai kashe Salma...
Cikin kuka tace "Kazo gidana suna nan. Duk ya
kuma kid'ime, tabbas ba d'ukkan wasa yasan
Abba yake ma Salma ba,tunda Aunty A'i take
kuka. Garba ya kalla,"dan Allah kaini gidan Aisha
yayar Salma. Da mamaki yake K'allonshi, "amma
dai kasan yanzu _chairman_ zai zo yama signing
koh?.. "In bazaka kaini ba na fita na hau abin
hawa. Kafad'a ya daga, "a muje, ni meye nawa.
Mijin Aunty A'in ya kira koh yana gidan,yace su
shiga kawai,Abba ya sanarshi komai tun dazun.
Abba ya fita lokacin da suka zo,mama ta tafi
nemo abin hawa. Aunty A'in ce ta shiga
dasu,ganin bulalin wajen duk sun kakkarye ji yai
kamar yasa kuka,yanzu duk bulalin nan a jikin
Salman sa ta kare? Jiki a sanyaye suka je
parlourn,duk ta kudindina tana rawar sanyi,da
sauri ya karasa gunta yana kira,tana jinshi ta
kara rushewa da wani kukan. Hijabin ya yaye
mata,yana ko'k'arin cicci6ota ya tuna da sakin
dake t'sakanin su,sai ya zame hannu tare da
zama. Bai san wani irin so yake ma Salma
ba,wanda har yake rawar jiki akanta duk da
abinda ta mishi, gashi har taja jiya ya bada kai
gun Bintu bori ya hau. "Mey yasa Salma?.. Mey
yasa ki ka zabar mana irin rayuwar nan?.. Gashi
yanzu kin dasa min son kara aure koh na samu
maslaha aciki... A zabure ta tashi,duk da yadda
take jin jiki tana cije le6e dan azaba. "Mey kace
Ya Ja'afar?.. Aure?.. Da sauri ya k'allo ta,sam bai
tunanin zancen ba a ciki yai ba. Ganin bai bata
amsa ba yasa ta yarda da abinda taji,hannu tasa
duka biyu ta dafa kan ta zamo kasa tana cije
baki,g'wiwa biyu ta durkusa duk tai kalar tausayi.
"Ka rufamin asiri Ya Ja'afar dan Allah,wallahi, na
rantse bazan kara ba..Dan Allah kar kamin
kishiya.. Dan Allah, wallahi bana sonta.. Allah
zan g'yara..nai alkawari,.. Ido ya rint'se, had'i da
cije le6e,ba yau Salma ta fara mai magiya da
rantsuwa kan ta d'aina ba,amma ba abinda ya
sauya zani.. Yanzu komai ya kare musu,aure
gareshi ya zama dole. By Feenat Ja'afar.
Juma'@ Mubarak.
9/29/16, 9:07 AM - Queen Safiyyert???a: *A BAKIN AURANKI* *o Feenat Ja'afar*. 24-Kai
ya kada tare da mikewa, "kiyi hakuri Salma.. A
baya na baki d'ukkan wata dama taki kinyi watsi
da ita.. K'arfi da yaji so ki ke ki mayarni wani
iri,dame zanji Salma?.. Na fita waje na samo
6acin rai,sannan na shigo gida nan ma wani
6acin ran ne,maimakon a lallashe ni..A'a ni
kullum ni nake lallashi. "Kiyi hakuri,Allah ya baki
lafiya.. Garba ya k'allo yai mishi halamar su tafi.
A hankali ta mike tana jin wata irin hajijiya na
debarta. "Nasan ni na ja ma kaina komai Ya
Jaafar... Ja yai ya t'saya, jin taci gaba yasa ya
juyo. "Tabbas na chanchanci d'ukkan wani
hukunci da zaka min in dai zaka yafe min.. Kasa
tai da kai,tai matukar zama abin tausayi a
gunshi,sai dai kawai ya kasa gane nadamar
Salma a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login