Showing 12001 words to 15000 words out of 125146 words

Chapter 5 - MIJIN MALAMA BOOK 1 Complete.txt

23 Nov 2024

9071

da Mahaukaci gabaɗaya ya juyo, kyakkyawar bugawa zuciyar Abu-turab ya yi in his whole life zai iya cewa bai taɓa ganin kamar shi ba, zubin idanunsa ma daban yake musamman yanzu da idanun suka sauya launi babu mai iya fassara abubuwan da suke nunawa, wanda ya yi masa mugun sani shi ne zai iya me yake ji ko me yake buƙata. Sosai yake da gashin gira a cunkushe, duk baƙin da yake da shi lips ɗinsa jajir yake. Ya lumshe idanu ya buɗe akan Abu-turab,bai ce komai ba ya ci gaba da ƙare masa kallo sai kawai ya ɗauke kansa.
"Ma ka ke buƙata?" Still bai magana ba. Sai a lokacin Hammad ya ƙara so wajan suka dinga kallon mahaukacin kafin P.a Hammad ya ce
"Hi crazy man, who are you, What do you need?"
Nan ma ya daɗe yana kallon su still bai ce komai ba, Hammad ya kalli Abu-turab ya ce
"Your Excellency Wallahi Mahaukaci ne"
Abu-turab ya jinjina kai yana ƙoƙarin juyawa cikin gidan ya ji saukar muryar mahaukacin ya ce "Hhhh kai... I want my Jee back, and my son" Hammad da His Excellency Abu-turab suka kalli juna kafin Hammad ya ce
"Who's Jee?" Yaƙi cewa komai sai ƙirjinsa dake ɗagawa. "Your Excellency na faɗa maka Mahaukaci ne, da alama ba a son ya hauro ta kadanga ba" Abu-turab ya yi jima kafin ya ce "Call securities" yana faɗin hakan ya juya zai koma cikin gida wajan Majeederh. Da sauri Mahaukacin ya sha gaban Abu-turab yana ƙare masa kallo idanunsa jajir kamar gauta cikin gurɓatacciyar Hausar shi ya ce
"Ina so Jee, i want my babe" "Are you mad? Kai ma haukaci ne?"
Shi dai babu abinda yake cewa sai "Ina so Jee, i want my Jee back babe na" His Excellency ya dubi sauran jami'an tsaron ya ce "Ku fita da shi" kafin su kama shi idanun Mahaukacin ya sauka akanta, tana riƙe da jajirin kamar kullum jikinta rufe da hijabi ya zaro dara daren idanunsa waje ya juya da sauri cikin ɗaga murya ya shiga faɗin "Jee, Jee!"
Tazarar dake tsakaninsu ya sa sam bata ji ba. Ya ƙara sauri kamar zai kifa, yana ƙoƙarin haure motar da ke parking lot aka cilla masa igiya ta ƙafa ya faɗo ƙasa, kafin ya yunƙura an sake cilla masa igiya ta harɗe hannayensa, maimakon ya yi ƙoƙarin dukan securities ɗin sai ya fara buga kansa da tarazon wajan yana faɗin
"Bebe, Jee, Malumana"
Ya dinga faɗa yana buga kansa cikin ƙaramin lokacin jini ya wanke masa fuska ya fara gani dishi dishi.
Majeederh na shirin ƙara sawa tsakiyar parking lot ta ji anyi saurin kama hannunta tare da janta baya, a tsora ce ta juya suka haɗa idanu da Abu-turab baki buɗe take kallonsa, daman shi ne? daman Gwamnan jihar su ne ya taimake ta? "Me ki ke?" Ya faɗa speaking calmly. Ta janye idanunta tare da kame kanta tana son ɓoye fuskarta ta tuna ai bata da wata sauran ƙima da daraja sai kawai ta ɗan ja baya ya tattausa murya ya ce
"Baki da lafiya Jiddo, kina son hutawa" ta juya ta kalli yadda Hammad ke kallon su haka kawai jikinta ya bata akwai wani abu ta ce
"Ni za a kashe?" Ta furta cikin kamilalliyyar muryarta. His Excellency ya buɗe ido ya ce
"No, wa zai kashe Jiddo, na samu baƙi ne da zamu yi meeting koma ciki ko?" Haka kurum ta ji ta yarda da shi kuma ta san waye shi yana kyakkyawar mu'amala ta juya shi kuma ya bi bayanta, tana ɗaga ƙafa zata shiga ƙofar ta ji an ce "Malumana" cak ta tsaya ƙirjinta na bugawa zuciyarta na harbawa a ranta ta ce "Little Son"
Zata juya ya yi saurin faɗin "Meke faruwa?"
Ta ɗan yi jam can ta ce
"Na ji murya" ya ce "A voice?" Bata saurare shi ba ta juya shi ma ya juya har ya sha gabanta ya ce "Akwai jama'a, mu koma ba wata murya, ba wanda ya san kina ciki" ya lallaɓata tayi cikin gidan tana shiga ya rufe ƙofar ya sanya securities a jikin door ɗin.
Yana komawa ya samu ana dambe da shi ya yi jina jina da jikinsa "Duk sanda ya ƙara zuwa shoot him, kuyi masa duka" shigowar wata mota ya sa suka tsaya wasu ma'aikatan asibiti suka fito da wani dattijo wanda yake sanye da ƙatuwar sarƙa mai zanan kurus. David ya haɗe hannu alamar apologies ya ce "Sorry" Abraham sosai ya gane David domin shi ne babban Pasto ya jinjina kai kawai. David ya ce "His name is Abraham Daniel David, My grandson ya samu depression har ya zama taɓin hankali, na yi mamakin yadda na'urar jikinsa ta nuna mana nan, duk yadda akai akwa abinda yake nema, baya zuwa waje babu dalili duk haukansa" Pasto David ya faɗa yana sawa a kunce Abraham tare da sanya shi a mota.
Faɗa akai sosai kafin daga ƙarshe aka danna masa Allura nan take ya fara barci.
Majeederh ta zubawa jaririn nata idanu tana son ƙara fahimtar kamanninsa amma abun ya kwanta mata gashi kullum ƙara juyewa yake kama da ita.
"Kin sanya masa suna ne?" Mama ta tambaya tana miƙawa Majeederh haɗin tea a cup ta lumshe idanu ta buɗe a hankali ta girgiza kai. "To ai yana da kyau ayi masa huɗu ba, wanne suna ki ke so?" A hankali ta ce
"Ibrahimul-khalil"
"Ikon Allah, Sarkin zuciya da faɗa kenan, ga ƙwazo shi kuma ba rago ba halin su ɗaya da Aliyu Haydar Allah ya raya mana Ibrahimul-khalil" Majeederh ta saci kallon Mama so take ta ɗan saba da ita amma yanzu gabaɗaya zuciyarta na gargaɗinta da ƙara yarda da wani, tunda Latifa Omar ta riga ta sanya mata tsoro ainun a zuciya ta gane babu Aminiyya, Abbu ya sama tabo na har abada wanda ya sa ta fahimci babu wani masoyin ƙwarai ko true love.
"A beautiful name, but why Ibrahimul-khalil?" Ba tayi masa magana ba ya zauna saman kujera kafin ya ce.
"P.a a shirya tsaro na musamman a gidan nan, a duba motsin kowa" Hammad ya rusuna ya ce "In sha Allah, Allah ya taimaki Your Excellency"
Fita su kayi gabaɗaya ya rage daga Mama sai Majeederh da Kalil dake barci.
Aaliyyah na zaune a parlour farin ciki ya kamata gobe za a ɗaura aurenta kamar yadda Uncle Isma'il da Uncle Bello su kayi al'ƙawari.
Abbu taga ya fito ɗauke da tarin takardun Majeederh na makaranta, da shaidar zamuwarta mace ta farko data fara lashe gasar musabaƙar Alkur'ani ta ƙasa da duk wasu ducoment da Award nata da tarin littafanta. Ta miƙe da sauri ta ce "Abbu me za ka yi da wannan?"
Ya yi mata banza tabi bayansa har zuwa tsakiyar compound gani tayi ya zuba musu fetur ta cilla Ashana ta zare Idanu ta ce.
"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un, me kayi haka Abbu" ya dubeta ya ce
"Har na koma ga mahaliccina ba zai taɓa daina yi wa Majeederh Allah ya isa ba, da haihuwarta gwara ɓarinta Allah ya sanya ta ƙarasa lalacewa har abada,ta ɗakko cutar ƙanjamau Hiv har tayi silar mutuwarta a wulaƙance" Aaliyyah kuka take sosai ta ce "Abbu kana sanya mini tsoro anya kai ka haifi Anti Jeederh?" Ya yi murmushi ya ce "Kowa zai yi zaton haka, wallahi wallahi ni ne uban Majeederh ni na haifeta amma yanzu kaf duniya ba Wacce na tsana sama da ita, a kullum idan na ce ta fito da mijin aure sai ta ce Allah bai kawo ba har cewa take ba wanda ya taɓa cewa yana sonta na zaɓa mata, na sha haɗata da maza daga ƙarshe su gudu ashe su sun riga sun halinta sun gane Fasiƙa ce, Mazinaciyya ce, la'ananniyya ce, Allah ya isa Allah ya isa Ubangiji ya tsine miki Albarka Majeederh" ya fashe da wani irin kuka Aaliyyah ma kukan take. Bar Aliyu Sufyan Alhassan yini ya yi yana neman Malama Majeederh amma ko mai kama da ita babu, yana dawowa gida zazzaɓi mai zafi ya rufesa...
Misalin 1:23 na dare tana zaune rungumeta da Ibrahimul-khalil da yaƙi barci yana ta rarraba Idanu gashi so Ma sha Allah sbd kyau daman ance shegu masu iya kyau ba. Sai ya zame mata abokin hira ta ce "Ina son ka Kalil, yadda na riƙe ƙa amana Ubangiji ya kawo sanadin da gaskiya za tayi halinta, ina jin kamar na shiga duniya na kama hotel....," Gilmawar inuwa ta gani kamar an shige ta ɗan kalli wajan ta juya ta duba lokaci taga ɗaya da rabi na dare saura kafin ta san abin yi an fara buga ƙofar bedroom ɗin da ƙarfi ana faɗin "Jee Jee Malumana...




Na kusa ending free pages. Contact to subscribe.... 08119237616 Whatsapp only.*🌈 MIJIN MALAMA🌈*


Nimcyluv Sarauta
*7.......*




_Complete story Arewabooks👇🏾_
https://arewabooks.com/chapter?id=6219d7896c0de838cd360960


Duk yadda Jeederh ta kai da son kamewa waje guda da riƙe kanta amma ka sawa tayi ta miƙe tsaye hannunta riƙe da Khalil, amma ta kasa motsawa sbd bata ƙara jin saukar sautin da kunnuwanta suka jiye mata ba. Shiru shiru sai kawai ta juya zata koma saman bed ta ƙara jin ance "Jee, Jee Malumana" a wannan karan muryar da aka kira sunan bata fita sosai kamar bai kiran yana cikin wani hali, ƙirjinta ya yi kyakkyawar bugawa, bugawar da sai data runtse Idanunta, me ya sa muryar ke yi mata tsananin kama data Little Son? Me ya sa hatta sunan ya zo ɗaya da wanda ya laƙaba mata sbd bashi da hausar da zai iya kiran complete sunanta Majeederh kamar yadda kowa ke faɗa, iya ƙoƙarinsa da faɗar sunan sai dai ya furta kalmar _Jee_ a sauƙaƙe?
"Yaa Allah" ta furta domin tasan har abada har gaban abada idan akwai he never comes to her, amma meke damunta har haka me ya sa muryar ke mata amsa kuwwa a kunne? "Jeeeee!!!" Ya sake furtawa muryarsa bata fita sosai kamar wacce aka tsikara tayi wajan ƙofa tare da sanya hannu ta murɗa handle, tsaye ta gashi yana zabga ƙamshi daga shi sai wata kyakkyawar Arabian jallabiya brown kallo wacce tayi masa kyau sosai, ya ɗan sakar mata kyakkyawan murmushi kafin ya ce
"Kina buƙatar wani abu ne?" Tayi masa kallo ta ɗauke kai ba tare data amsa shi ba, domin bata da yawon magana Majeederh nada matsanancin aji sosai, wanda kuma halittar ta ce hakan. Gani ya yi tana leƙa waje shi ma ya leƙa yana cewa "What are looking for? Me ki ke kallo?" A raunane wanda kuma ba kowa take son yaga raunin nata ba ta riƙe kanta sosai tana sake rufe jikinta da hijabi ta ce "Allow me to go"
"Where?" Ya amsata da sauri. "Ban son zaman nan, kuma ka bari na leƙa waje" Abu-turab ya ware idanu yana shafa sumar kansa ya ce.
"Me Jiddo zata yi a waje yanzu? 2 saura ok" tayi shiru ya ƙarasa shigowa cikin bedroom ɗin tayi saurin ƙanƙame jikinta waje guda lokacin Khalil ya fara kuka..
Sosai Abu-turab ya rufe ƙofar kana ya nemi waje nesa da ita ya zauna saman kujera ya harɗe ƙafa. Malama Majeederh hankalinta ya rabo wajan kashi uku, ɗaya na waje, ɗaya na kan Khalil dake kuka, ɗaya na kan Abu-turab daya sanyata a gaba tare da kafeta da idanu. Sai ta zama ira bata ƙaunar kallo yana takura ta ainun.
Abu-turab yana ƙoƙarin magana su ka ji an daki ƙofar ya miƙe tsaye tare da kallon Jeederh ya ce
"Sorry, na ce a kawo mini abin shur ina da azumi" bata ce komai ba ita dai.
Ya nufi ƙofa yana fita ya rufe ta, kokawa ake sosai da Abraham Daniel David wanda yake son ta ƙarfi sai ya ɓalle ƙofar, gadai securities da yawa amma sun kasa controlling nasa ya jiwa kansa ciwo amma yaƙi ya yi giving up, wani irin ƙarfi ke zuwar masa. "Abraham" Abu-turab ya kira shi,ya juya kalli Abu-turab.
"Me ka ke buƙata?" Da hannu ya nuna masa bedroom ɗin da Malama Majeederh ke ciki, kana ya nuna ƙirjinsa wajan zuciyarsa ya ce.
"Jeena, nan" Abu-turab ya fahimci Abraham na son shaida masa Jee na cikin zuciyarsa ita kuma yake nema. Cikin nutsuwa yana murmushi ya ce
"My friend zo ka ji" Abraham ya kafe waje guda domin babu na biyunsa a taurin kai. Cikin tattausa harshe ya ce "Ita Jee ɗin bata nan, amma ka dawo gobe zan kaita wajanta" ya faɗi hakan cikin harshen Ingilishi yadda Abraham zai fahimci mai yake nufi.
"Promise?" His Excellency ya ce "Promise" Abraham ya sanya hannu a tsakiyar rigarsa inda ya yage ya zaro wata kyakkyawar flowers sai ƙamshi take ya miƙawa Abraham yana wani irin buɗe ido ya ce "Malumana"
Ma'ana the flowers is for her. His Excellency ya amsa deep down na zuciyarsa cike da mamakina Abraham who is he to her?.
Securities ɗin za su kama shi ya girgiza musu kai tare da yin gaba yana ɗan tangaɗi yana yin gaba ya ji saukar muryar Khalil na kuka ya tsaya cak, sai ya juya kawai sai su kaga ya yi murmushi ya ce
"My pregnancy"
"An samu matsala" In ji Khamal. Abu-turab ya saka hannu ya tsige flower ɗin tare da zubar da ita ya ce
"Make sure baku sake sakaci ba, i hate noises"
"We're sorry Sir, Hakan ba zai sake faruwa ba, wallahi ta sama ya hauro mahaukaci ne daya kama hannun Captain sai da ya ƙarya shi,ya sha duka sosai wajanmu amma bashi da haƙuri yana da zuciya ban san wani abu giving up ba" His Excellency bai ƙara magana ba ya buɗe bedroom ɗin har yanzu tana zaune saɓanin ɗazo Madara take bawa Khalil, Abu-turab ya jima yana satar kallonta da tayi ƙoƙarin ɗago kai sai ya janye idanunsa ya basar
"Jiddo, we need to talk please" yadda ta ƙara nutsuwa ya san cewa ta bashi dama cikin nutsuwarsa ya ce
"Majeederh kina da hankali, ko ban girmeki ba zamu iya zuwa age mate don haka duk abinda zan faɗa miki ba zai zama cutarwa a gareki ba" ya sauke numfashi ya ɗora da "Don Allah kada ki ji zafinki akan hukuncin da ya yanke miki, iyaye ba a taɓa fushi da su ki ɗauki hakan matsayin jarrabawa kuma ƙaddara wacce babu yadda zaki iya dole sai ta kasance, ba zan miki nasiha akan yarda da ita ƙaddarar ba domin kusan kin fini sani, sai dai na nemi ta barraki a wajanki" ya ƙara yin shiru ya ce "I feel your pain, kafin na zama gwana na sha wahala,ina rayuwa da mahaifiyata after my father's died, dangin mahaifina they are so selfish sun ƙwace komai dana mallaka wajan Abbana, filaye, kadarori all the properties, mun fara yawo yawo a dangi kowa yana gudunmu sbd babu ran mahaifina sun manta alherin da ya yi musu, dangin Mamana basa kusa, na fara dako ina garuwa ban taɓa yarda ba zan iya ba, burina Mamana ta ji daɗi na zama wani abu" ya ɗan sauke numfashi kamar lokacin abin ke faruwa kafin ya zuba mata Idanu ya ce "I was thinking mene ya sa mutane suke manta alheri? Kuma da yawan mutane suke sawa ka zama mutumin banza, ko dana fito takarar House of assembly kin me ne ya faru?" Sai a lokacin ta ɗago kai ta kalle shi some seconds kafin ta janye ganinta daga gare shi, tana ɗan ɗauke numfashi sbd abubuwan da suka tukare mata bata san ranar faɗawar su ba. Abu-turab smile yana jan idanunsa zuwa sama kafin ya ce
"Cewa akai kada a sake a zaɓeni wai bani da uba, ba wannan ya daman ba familyna sune kan gaba wajan ganin na fasa kujerar da nake nema, kamar yadda suka so ban samu ba, gabaɗaya deligate suka juya mini baya, cikin ikon bayan an cinye tenuwa huɗu cif na sake fitowa takara i won the election, nayi shekara huɗu a lokacin ne na haɗu da ƙaddarata, wacce ta zame mini Dafi a zuciya, ta zame mini wani tabon da bana tunanin zai taɓa gogewa da jikin zuciyata sai dai idan zuciyar ce ta samu abinda take buƙata, Jiddo ban faɗa miki haka domin ki tausaya mini zuwa gaba ba, shi ya sa ma ba zan baki labarin cikakkiyar ƙaddara tawa ba, amma ki sani ko wanne mumini idan har amsa sunansa dole Ubangiji ya jarabce shi da jarrabawa, bafa don ya son mutum yake jarabtar shi ba, sau tarin wanda Ubangiji ya fi jarabta to ya fi samun kusanci da shi, kiyi haƙuri ki ɗauka haka zanen taki ƙaddarar yake, babu mamaki mahaifinki ya fiki jin zafin abun da ya faru kiyi masa uzuri, ki addu'a cikin sauƙi komai zai zama labari" ruwa ya ɗauka ya sha yana sauke numfashi.
"Thank you!" Ta furta cikin kamewarta da nutsuwarta a koda yaushe, da nuna cewa ita ɗin babba ce mai ƙiba da daraja wacce a yanzu ta rasa ko wanne daga ciki.
"It's my pleasure, an kawo Raguna na raɗin sunan baby" "ba buƙata"
"Akwai" ya furta cikin tsare gida.
"Kada ki zama mai son kan ki Jiddo, kada ki zama mai musu after all this am elder than you na je 42 ke kina 35, kin ga akwai respect na girman dana baki" shi kansa mamakin surutunsa yake a yanzu ya manta rabon da ya yi magana mai tsayi, lallai zuciya bata da aji ga abinda take muradi da kwaɗayin zama da shi..
"Khalil na godiya"
"Mamin Khalil fa?" Bata ce komai ba ya watsa hannu ya ce "Alright, i don't need your thanks"
Ganin yadda take kallo agogo ya sa ya fahimci tana son kwanciya ya miƙe tsaye yana shafa sumar kansa ya ce
"Ya Rabb! Good night"
Har ya je bakin ƙofa ya sake juyawa ya zuba mata idanunsa ya ce
"Lailatan sa'ida" ta bisa da kallo har ya fice.
Majeederh Yaronta Khalil ta zubawa idanu wanda yake barci cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, bata da sanya damuwa a rai, amma kunnuwanta sun kasa manta sautin Abbu da yake cewa
"Allah ya isa Majeederh"
Ta rufe ido da sauri ta buɗe data tuna kalmar "Tamkar gawa haka ki ke a waje na" "Fasiƙa!"
Ƙirjinta ya fara ɗagawa numfashinta na tsayawa ta fara kokawa da iskar dake kaiwa zuwa hunhunta ta miƙe da sauri tare da shigewa Bathroom tana daga tsaye ta sakarwa kanta ruwa mai sanyi shower ta dinga ratsa tsakiyar kanta jikinta ya jiƙe ta mance ciwonta sam, ita da ace ciwon zai zama sanadin tafiyarta lahira da wallahi sai tafi kowa murna da kan ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login