Showing 105001 words to 108000 words out of 125146 words

Chapter 36 - MIJIN MALAMA BOOK 1 Complete.txt

23 Nov 2024

9066

yana da hankali sosai daga ƙauyen Rurum yake naga da ƴar sana'arsa daidai gwargwado domin har ɗan dako yake, na ce ko shi za a haɗa da Majeederh tunda Kinga al'amarin nata shiru babu mashin shi ni, sunansa Tasi'u" Ruma ta ce "Lallai da kin yi aikin lada sosai Raihana" Mami ta ce "Shi ɗan dakon kenan?" Raihana na kallon Abbu ta ce "Wlh ai irinsu babu ruwansu, musamman ga Majeederh fara tas wlh haukacewa zai ya samu mata ta keta raini bama zai duba taimakon da ya yi ba, nan nan zai dinga yi da ita kamar ya lashe" Cak Abbu ya ajjiye cup ɗin hannunsa da yake ƙoƙarin kawai baki zai sha ruwa, ya mayar ya ajjiye tare da miƙewa ya fice daga parlourn. Compound ya nufa Driver na ganinsa ya miƙe tsaye, Abbu ya nufi wajan mai gadi ya ce "Waya shigo cikin gidan nan jiya?" Mai gadi ya kama kame kame Abbu ya ce "Ohk haɗa baki ake da kai ana shigo mini gida? Ka tattara kayanka na sallameka kuɗinka zan tura maka ta acct" Mai gadin ya rikice sosai ya zube yana bawa Abbu haƙuri amma ina tuni ya shiga mota... Zuwanta gidan Maman Alpha kenan ta nufi part Innati tabar Latifa tare da Maman Alpha, bayan sun gaisa Innati ta ce
"Ina Kululu?" Majeed ta ce "Gani kusa" Innati ta ce "A to bana ganki ba kuma, ƙara tabbatarwa zan yi" Ta ƙara zama ta ce "Shikenan ku dangin mahaifiyarku basa ƙaunarku ne?" A sanyaye Majeederh ta ce "Me kika gani?" Innati ta yi mitsi mitsi da idanu ta ce "Ji wata wulaƙantacciyar tambaya?? To ke yanzu dan Allah wa kika sani a dangin Fulani?" Majeederh ta ce "I don't know anyone, I've never seen anyone from my mother's family" Innati ta saki baki ta ce "To banda kin so wulaƙanta ni a idanun jama'a meye zaki sauya raye, ni zakiwa turanci?" Ita dai Majeederh bata ce komai ba, domin jikinta duk ya mutu tana son yi wa Abbu maganar Mother's family ɗin su tana jin tsoro. Innati ta ce "Kawai ki rutsa mahaifinki shi ne nunafukin ki ce ya fito miki da dangin mahaifiyarki, ki ɗaga masa hankali sosai idan ma kidnaping ɗin su ya yi sai mu ji labari, tunda ba wani yarda nayi da zuciyar Audil azizu ba, sama taka mu kaga yayi arziƙi fa? Shi yasa yake ta wani fankama yana ɗaga kai, to ai mu munga ƙaruna ma" Majeederh ta yi shiru Innati ta ce.
"Allahu Akbar, ai ba zaki san ƙaruna ba, munga ikon rabbi a wajan bawan Allan nan, gashi dai ƙarshen shi bai wani kyau ba, ai wallahi wannan kyan na fuskarki da farar fatar nan kamar sadaka yalla to haka uwarki take, har ta ɗaraki a kyau mace mai sanyin hali da haƙuri, ta sha fama da talaucin Audil azizu sana'a kala-kala tayi fa? Ko Attajirin uban naku bai baku labari ba? Babu mamaki gadonku ya tattara ya siyar kwasha kwasha, domin har gwala-gwalai ne da ita" Majeederh idanunta ya cicciko da hawaye ta kasa cewa komai. Innati ta zabga sallati ta ce "Yanzu kamata Kululu ni zakiwa turanci? Ni zaki sauya harshe, yanzu fa muke Shira dake rumi rumi kawai sai kika sauyan raye ni ki kaiwa turanci" Majeederh ta miƙe ta ce "Kyaci kanki ke kaɗai" Ta yi waje abinta, Innati tayi ƙasa da murya ta ce "Tab, kaɗan ya rage ban saki fitsari ba yarinya kamar Aljana, zaki Albarka,zaki Albarka mijinki daban yake sananne ne shi tauraro ne, wanda duniya ta gama saninsa" Haka take something kamar wacce ake buɗewa idanu. Maman Alpha da kalli Majeederh ta ce "Majeederh Kinga ɗan uwanki har yanzu shiru? Ko yana raye ko ya jima da mutuwa? Ko a hankalinsa yake ko ciwon hauka ya same shi Allah kaɗai ya sani" Gently Majeederh ta kalli Maman Alpha ta ce "Ki yi haƙuri, addu'a za a yi" Murmushi kawai ta yi kafin ta ce "Ya maganarki kowa? An samu tsayayyen?" Kafin Majeederh ta yi magana Latifa Omar ta ce "Aliyu ya ce zai aureta, amma taƙi" Maman Alpha ta ce "Mijin naki?" Latifa ta ce "Eh" Da mamaki Ta ce "Son ta yake?" Latifa ta ce "Sosai, sbd ya ce na yi conversing ɗinta to marry him take gaba dani" Maman Alpha ta yi shiru for a second kana ta ce "Eh to gaskiya conversing Majeederh to marry ur husband Aliyu, kamar ki yi forcing nata ta cakawa kanta wuƙa a ciki ne, How do you think she can marry her Aminyya's husband? It is a difficult thing that the mind cannot handle. Honestly, even I do not support this useless thought, Majeederh tana buƙatar taimakonki,She needs your help, but not this way, think of something else besides this" Latifa ta marairaice ta ce "Ni wlh tallahi na amincewa Aliyu, ba zan taɓa kishi da Majeederh ba, zamu ci-gaba da zama kamar yadda muka sabaSocially there is sacrifice, I sacrifice my husband's love for Majeederh" Maman Alpha ta ce "Sacrifice?"
"Eh" Cewar Latifa Omar
Maman Alpha ta ce "Let me tell you something you don't know, ko da ƙanwarki da kuke ciki ɗaya aka haɗaki waje gudu wlh sai kin yi kishinta, balle Majeederh? Sanda zaki shige ɗaki kina ihu idan suka keɓe Allah kaɗai ya sani,We are dedicated to Love, it does not mean that we have stopped loving, in love there is jealousy, Think about that Latifa Omar" Kafin kowa ya yi magana Innati ta shigo tana kuka wiwi hannunta riƙe da sanda. Maman Alpha ta ce "Subuhanallah lafiya Innati?" Innati ta ce "Fatima wai ni Kululu zata juyawa yare ta yi mini turanci?" Maman Alpha ta ce "Allah gasky bata kyauta ba, turanci ana zaune lafiya?" Lafita ta dinga dariya sosai sun jima a gidan kafin su ta fi. A hanya Lafita ta nufi Tahir Quest Palace Majeederh ta dai kalleta ganin hakan ya sa ta ce "Abu zan karɓo kin san mu ƴan jarida, muna amfani da Opportunity da zarar ya samu"
5 days left. Tun ranar Majeederh bata ƙara jin motsin Abraham ba even on the phone, har numbersa ta kira ta ji a kashe. A hankali ta rufe Idanunta da sauri ta buɗe kuma tama rasa wanne kalar tunani za ta yi, tana zaune wayarta ya fara ringing dubawa ta yi taga new number sharewa ta yi, kuma ba a fasa kiran ba, tunaninta ya bata masu neman taimako ne ko wani abu ne ya tashi a Ngo ɗinta. Ta ɗaga kiran tare da cewa "Assalamu alaika/ki" Taj ya yi wa Salamon alama da ya yi shiru a ladabce ya ce "Good day Mami" Sosai Majeederh ta ɗauki muryar ta yi shiru, Taj ya ce "Sorry na kira without ur permission, am very sorry about that" Bata ce komai ba, a ransa yana mamakin girman kanta ya ce "Abraham, baya da lafiya kwana biyar kenan, baya ci baya sha sunanki kawai yake kira gashi Grandpa baya gari" Majeederh ta yi shiru a hankali ta ce "Bashi wayar" Taj ya ce "Dr ya duba shi yanzu bacci ya ɗauke shi, amma yana da kyau idan ya buɗe idanu ya ganki" Shortly and silently ta ce "Address" Ya ce "Ohk check ur Dm" Kashe kiran ya yi ba jimawa ya tura mata da Address ɗin gidan. Sosai ta dinga duba location ɗin tana mamakin unguwar. Shiryawa ta yi cikin mik ɗin Abaya mai kyau ta ɗauki hijab ta saka tare da liƙab, waya da key kawai ta ɗauka ta nufi waje. Mami na zaune Main parlour watching TV ta ce "Mami zan ɗan je dubiya" Mami ta ce "Subuhanallah wani ne bashi da lafiya?" Majeederh ta ce "Eh" Ta jinjina kai ta ce "Kada ki jima" Fita tayi ta nufi wajan baƙar motarta tare da buɗewa ta shiga bismillah ta yi tare da yin key tai reverse gatekeeper ya buɗe mata, tana fita motar Abbu na shigowa, Aliyu dake tsaye a bakin gate ya ji he need to follow her, ya ga where she's going to?....
Babban gida ne wanda kafin kaga irinsa sai an tona, tsayawa faɗin yadda gidan yake ɓata baki ne, ga wasu mahaukatan securities birjik, gidan ta ciki part part ne. Gang team ne zaune a wani haɗaɗɗan parlourn gidan wanda ya kasance mallakin Abraham shi ya zana gidan da kansa. John ya ce "Taj me ya sa ka yi mata ƙarya?" Taj ya ce "Kawai ta zo ta gansa" Salamon ya girgiza kai ya ce "Baka da kirki wlh" Dry ya yi sosai duk sun cika parlourn da hayaƙin Shisha ya ce "Na kusa barin country ɗin nan" kafin su yi magana sun ji ƙarar doorbell. Taj ya miƙe ya ce "Ta ƙarasu, ku ɓoye kayan drugs ɗin nan" Da sauri suka kwashe komai, ya buɗe mata ƙofa ya ce "Wlcm Mami" Bata kula su ba sai parlourn data shiga ƙarewa kallo ya ninnka na gidansu a komai, ta yatsuna fuska. Gabaɗaya suka miƙe kamar marasa gsky sbd kwarjini ta yi musu duk da fuskarta a rufe yake. Salamon dake ya fi kowa bin diddigi ya shiga ƙarewa yatsun ƙafar Majeederh har wani yellow suke don fari. Waya Taj ya ɗauka kira Abraham dake can cikin wani narkakken part. Majeederh ta kasa zama har wajan minti biyar kafin ta ji John ya ce "Gashi nan ma" Bata ɗago kai ba haka nan Moment ɗin su ya faɗo mata, da tunanin wanda aka ce bashi da lafiya me ya fito da shi?
"Hold on. Who is that girl standing next to him....??" Jin an ambaci yarinya ya sanya Majeederh ɗago da kanta da sauri, idanunta ya sauka akan wata siririyar yarinya chocolate colour tana da kyau daidai da ita, daga ita sai half vest da wando iya laps ɗinta, ga wani gashin doki sai mannewa Abraham take, Wanda ya haɗe rai kamar ya ce ya shigo uku, tun faruwar abun babu wanda ya sake kulawa sbd ransa ya ɓaci da abinda Taj ya yi masa, Kallonsa Majeederh ta dinga yi ganin ya rame sosai idanunsa ya faɗa, a hankali ta juya ta kalli budurwar sunan Debeka ya faɗo mata wato ita ce Shegiyar dake lalata mata yaro? Salamon ya ce "Ur mother is here" Da wani irin sauri Abraham ya kalli Doorway idanunsa ya sauka cikin nasa, ya miƙe tsaye tare da ƙare mata kallo yaga tana kallon Debeka wacce ta yi tsaye tana kallon Majeederh, Shi kuma ya juya ya kalli Taj irin me ya sa? Ganin Abraham ya kasa cewa komai ta juya zata bar parlourn murya ƙasa ya ce "Ma....mi.. Mami" Cak ta tsaya ba tare data juyowa ba, Abraham ya nufi inda take yana zuwa ya rungumeta ta baya yana sauke ajjiyar zuciya a hankali dadai kunnenta ya ce "Am sorry Mami" Ta juya ta kallesa ta kasa ce masa komai ya riƙe hannunta har zuwa tsakiyar Parlour ya ce "Wlcm come to my house Mami" flowers ta ji suna zubu mata aka daga ita har Abraham ɗin, Kafin ta yi magana ta ji Gang team ɗin sun saki ihu tare da yin tafi sun ce "It's ur day bad boy, happy Engagement" Mami ta kalli Debaka bandai da ita ya yi Engagement ɗin ba? Debaka kowa suman tsaye ta yi numfashinta ya shiga ɗaukewa, Abraham ya ɗan yi cute smile da jajeyen laɓɓansa ya ɗauki wata ƴar ƙaramar box ya buɗe wani ɗan ƙaramin Gold ring ya bayyana sai sheƙi yake, a hankali ya durƙoshe akan ƙafafuwanta ya kama hannun Majeederh cikin low voice da wani irin sound ya ce "Ƴar Madara Mamina, Will you marry me?" Bugawar da zuciyarta tayi ya sanya ta yi baya kamar zata faɗi sai kuma ta tsaya da kanta jikinta ya shiga rawar da bai taɓa yi ba. Abraham na durƙoshe ya ce "Zaka auren Mami? Ɗan ki zai zama mijinki" Taj ya ce "Wip wip Wip hureee, baka faɗa mata how much u love her ba, tell her" Ya ɗan langwaɓar da kai shi fa bai wani iya ɓata lokaci da wani i love you ba, a aikace yake komai ya kwaɓe fuska ya ce "I don't need all this, ta san ina sonta ai ko Mami?" Majeederh kamar wacce ƙwaƙwalwarta ta tsaya ta kasa magana tana ji ya zura mata ring ɗin a yatsarta, ya sumbaci wajan ya ce "You're Mine" Wani kalar Ihu Gang team sukai tare da cewa "Happy Engagement Bad boy, the leader team the richer young boy" Ya miƙe tsaye yana lumshe idanunsa wanda suka azabtu da rashin ganinta sosai, John ya ce "Remain kiss, First kiss" Shi kansa Abraham mmkin yadda Majeederh batai masa komai ba yake, ta yi accepting nasa as her husband? Bai san cewa brain ɗinta ce ta tsaya cak ba. Slowly ya nufi inda take da niyyar kissing nata, Debeka dake tsaye tunaninta ya gama bata Majeederh ita ce wacce Taj ya faɗa mata Abraham ya je wajanta jiya ya kwana, Gadan-gadan ta nufi kanta da plate zata kwaɗa mata Abraham ya yi saurin tare Majeederh ta hanyar rungumeta ya ce "Mami..." Plate ɗin ya sauka a kansa nan take jini ya shiga fita ƙarar plate ɗin ya sanya Majeederh sakin ajjiyar zuciya ya haddasa dawowarta cikin tunaninta, Abraham ya juya da saurin still holding onto her ya ce "Debeka stop" Hawaye kwance akan fuskar Debaka ta ce "Stop? Na bar iyayena, karatuna ina level na ƙarshe na zama cikakkiyar low na bar ƙasata na biyoka sbd kawai ina sonka? Shi ne zaka kawo wata tsohuwa wacce ta haifeka ka ce zaka aura? To bari naga ta yadda za a yi auren" Ta ƙara nufar su Abraham ya ɗauka Majeederh zata daka babu zato balle tsammani yaji saukar hannunta a mararsa ta damƙa tare da murɗewa ya fisga, wani masifaffan zafi ya ratsa kwanyar kansa numfashinsa ya tsaya cak domin inda ransa yake ta taɓa, a hargitse Majeederh ta ce "No!!!!!! Zaki nasaka shi" Debaka ta ƙara murɗewa da ƙarfi ta ce "Sai ayi auren muga" Baya Abraham ya yi Majeederh ta tare shi suka zube a ƙasa ya faɗa kanta babu numfashi........








Har yanzu a labari muke,sai mun koma asalin labari za kuga muhimmancin baku wannan labarin..... The story is going to be different In sha Allah🫰🏽💔 muna zuwa page 50 zamu gama labari a nan book 1 ya ƙare.*_Sai Mace ta turo wata yaƙunanniyyar ƴar dubu ɗayanta tana son MIJIN MALAMA, kuma sai ta dinga sharing gari gari har Aljanu duk su karanta akan guntuwar 1k? To Sannunku ku ta nadi kuɗinku idan mun dawo labari a book2 zan muku Discount kowa ya karanta Allah ne ya taɓa zuciyata wlh........ MIJIN MALAMA 08119237616_*




Wani irin jijjiga shi ta shiga yi bayan ta mirgina ta zame jikinta sai kanshi dake saman cinyarta. "Khalil? Ibrahim buɗe idanunka" Duk ta rikice ganin yadda ya sanƙame baya ko numfashi. Debeka dake tsaye jikinta ya ɗauki rawa, Allah yana gani bata yi don ta kashe shi ba, he so much loves him,She loves him very much, his jealousy makes her feel that she will never let him be with another woman other than her. Tsananin kishi ya rufe mata idanu ya sa ta kasa controlling kanta. Gang team ɗin kallon Debeka suke sun san ko da wasa suka taɓa ta sun shiga uku. Majeederh gently ta zame kan Abraham dake cinyarta tana zuwa bata tsaya jiran komai ba ta ɗauke Debaka da wani mahaukacin mari, sai da ta jera mata maruka guda biyar cif wanda suka nemi zautar mata da tunani. Tana pointing ɗinta da hannu ta ce.
"Baki da tarbiyyar da zaki iya haɗa inuwa da Khalil, mara tsafta irinki sam bata dace da shi ba" Debeka da kumatunta ya kumbura ta ce "Who are you? Waye ubanki a duniya bakiɗaya, da har kika mareni kike tunanin kin mari banza?" Ta cikin liƙab Majeederh ta watsa mata harara cike da tsana wacce bata taɓa yiwa kowa ba ta ce "Me? Forget about my father, ki tambayi wacece ni kaina, I Malama Majeederh Abdul'aziz Khan! Idan kin sani better, idan baki sani ba You can search on Google zasu gaya miki" Debeka ta girgiza kai sosai ta ce "Ok shi ne sbd abin kunya wata tsohuwa dake sbd kin rasa mijin aure kika liƙewa masa ko? Kinga sabon jini, daman ke ce wacce kika shiga tsakani kike masa yawo da zuciya har ya kasa accepting nawa matsayin budurwa balle ya kwanta dani? Kin fa haifeshi haba Mama" Sosai Majeederh ta ji zafin maganar jin ta kirata da tsohuwo hala bata san matsayinta a wajan Abraham ba. Ta juya ta kalli Abraham dake kwance su Taj na shafa masa ruwa ya riƙe mararsa gam zufa na yanko masa, ta dawo da ganinta kan Debeka ta ce "Me kika ce? To ina nan ina addu'a da izinin Ubangiji babu wata ƴar iska data isa ta ja hankalin Khalil sai matarsa da sunna wacce addini ya bashi ita duk wuya duk tsanani, ba zai taɓa aikata zina ba, naga kamar baki da cikakken hankali idan baki sanni ba su abokan nasa sun sanni, na raineshi da hannu na yi masa wanka da hannuna, na goyasa a bayan nan nawa, ya yi bacci a jikina akan ƙirjina tun yana 3yrs a duniya, Abraham is my son, ni nake da ikon zaɓa masa matar data dace da rayuwarsa wacce zata taimake shi ya ɗora shi akan tubalin zuwa aljanna, wacce zata ribaci ra'ayinsa ga taimakon al'umma, wacce zata dawo da shi akan hanya, mace mai tsafta da hankali nutsuwa kamala, mai addinin ba wacce ke bin gidan maza ba" She slowly heard him say "The woman you are praying for me to marry is none other than you" Debeka ta saki dariya ta ce "Kenan kanki kikewa fatauci ko? Sannu uwar guzuma kune hajiyoyin dake lalata ƙana nan yara kenan no wonder"
Abraham na jin su, maganganun Debeka kamar saukar mashi haka yake ji, amma ya yi shiru yana son Majeederh bakinta ya buɗe ta fara kwatarwa kanta ƴanci ba sai an shigar mata faɗa ba. Hakan ya sanya ya yi shiru yana mayar da numfashi yana jin yadda lokaci guda jikinsa ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login