Showing 21001 words to 24000 words out of 50778 words

Chapter 8 - KISWA Book Complete Document by Chuchujay.txt

29 Nov 2024

2572

saka hannunka jikina sai na baka mamaki mara misaltuwa,nuna Kiswa tayi da hannu tace"akan wanna ɗiyar karuwar zaka nemi ka raina mun wayau"Kafun yace wani abu ta bar gurin Farry ma ta tashi tana kuka ta mara mata baya,aje spoon Sageer yayi yace "Allah ya kyauta "yayin da Kiswa ta fashe da wani iri kuka mai cin rai,lallashinta Sameer ya fara yayin da Appa ya zauna ya ɗora hannunsa a fuskarsa yana mai jin wani irin yanayi na baccin rai a tattare dashi,tashi yayi bai ce musu komai ba ya bar gurin,kuka sosai Kiswa ta cigaba da yi tana mai jin kirjinta kamar zai faɗi Yayin da sameer ya cigaba da lallashinta yana mai bata hakuri har sai da tayi shiru kafun yayi mata magana masu kwatar da hankali Kafun ya rakata ɗakinsu.


Bangaren Mother kuwa tana shiga ɗaki kiran Mahaifiyar Haidar ya shigo mata,cikin zumuɗi kuwa ta dauka ta samu guri ta zauna tana mai saita kanta tace"Assalamu alaikum future sirikata barka da warhaka,daga ɗayan bangaren Ummi tace"barka dai dama ina ta san na kira ki amma Ban samu dama ba saboda jiya naga dare yayi,na kiraki ne da albishir mai daɗi,jiya na zauna da Haidar nayi masa magana kan diƴarki Faridha,so ya faɗa mun yana dating ,amma abunda yayi mun daɗi sosai yar uwar Faridha ɗin yake so daya yarinyar ki Kiswa,im Just happy da ya zamana either way zamu zama sirikai na bada dukkan goyan bayana musamman da ya zamana Haidar na mutuƙar san ita Kiswa ɗin Ko ya kikace? Ajiyar zuciya Mother ta sauke Kafun tayi wata ƴar dariya tace"Hajiya kenan,kicce sharriin Kiswa ya ziyarci Haidar kenan,kyau Babu kyan hali ake faɗa miki,to ni Kiswa ba yarinyata bace domin kuwa ina Allah wadai ace na dauki ciki kamar na Kiswa a jikina ban zubar ba wada da haihuwarta gwanda barinta,koda yake ai ba abun mamaki bane idan tazo duniya Ta hanyar uwarta domin kowa ita kanta uwar tata karuwace wadda ta samu cikinta ba da Aure ba kasancewar Mahafiyarta kanwar mijina ce ta saka ya daukota domin bata rayuwa mai kyau amma duk da haka bata bar komai ba a halayyar uwarta,kinga hajiya ba wai san zuciya ba Ko wani abun ba amma Kiswa bata dace da shiga zuriar ku ba domin kuwa Kiswa Wake ɗaya ce mai bata miya.


Shiru Ummi tayi tana mai jin maganar kamar dukan guduma,sai da Mother ta sake cewa "Hello Hajiya"Kafun Ummi ta dawo daga shock ɗin da ta shiga,ajiyar zuuciya tayi tace"zan nemeki Hajiya i need to digest this".tana kashe waya Mother ta saka dariya tana mai faɗin"indai nice wallahi muzuba mu gani domin kuwa nafi karfin bataliya guda",zama Farry da mamaki Ya kusa kashewa tayi tace "mother mai yasa kike yin haka wai don't you think Bai kamata ba sannan ni dake munsan Kiswa is decent kuma da Aure aka sameta mai yasa zakice yar karuwa ce,beside ni mai yasa kike san haɗa ni da Haidar?.


Wani irin Kallo mother ta bita dashi kafun ta kamo hannun Farry tace "kalli Nan Faridha,kowa da kike gani kansa ya sani sannan a maganar da na faɗa ai ba duka ne karya ba cos Zubaida Na da reputation ,but ba wannan ba ,ki saurareni da kyau,duk duniya babu mai sanku sama dani ,ina san ki sani Kiswah ba sanki take ba,da zataga abunda zai cutar dake bazata taba faɗa miki ba ,iyakaci ma ta tura ki,ni Na tabbata idan kika kuskura kina gidan nan ta Auri mai kuɗi kamar Haidar to kisa a ranki wulakanci da sharri a gurinta sai ya baki mutukar mamaki,She's Just using you a gidannan domin zuwa wani matsayi mai girma,and gradually zata kai dan tunda Appanku ya fara wannan Abun wata rana zakiji ya tsigeki daga Kujerar ki ya bata.


da sauri Farry tace"God forbid Mother kar ki mun baki mana"ajiyar zuciya mother tayi tace "abunda nake nufi kenan kuma zai faru idan baki bani Haɗin kai ba zaki sha mamaki dan haka dole ki kwace Haidar a hannunta,a hankali cikin karfin Zancen uwa ga ɗanta Mother ta wankewa Farry kwakwalwarta tass inda ta fara disgusting tunanin marasa kyau kan Kiswa ,


Kai tsaye bayan ta gama da Mother ta nufi ɗakinsu da zummar korar Kiswa daga dakin ,tana shiga ta tarar da Kiswa kwance ta rumtse idanunta Ta lullube da bargo, kanta tayi kai tsaye ta yaye bargon wanda yasa Kiswa buɗe idanunta amma bata tashi ba,fahimtar idanunta biyu ya saka Farry cewa"bai dameni ba ki tashi Ko kar ki tashi amma Nasan kunnuwanki suna saurarena,to kiji nan you're selfish,san kanki yayi miki yawa ,idan ba haka ba mai zakiyi da maza biyu indai ba zalama ba tunda kinsan mutum ɗaya zaki Aura and maganar Saleek kuma ai kinsan i appreciate Handsome guys idan da na ganshi bazan taba cewa bana sanshi ba sannan bazan taba kirkirar masa halayyar banza da na lissafa ba,da Kin bani hint bayan dawowarki yarda yake da yanzu komai ya dai dai ta tsakanin mu"


Tashi zaune Kiswa tayi tace "madam Hold on ,kina nufin duk abunda kika faɗa mun kan Saleek karya kike?"murguɗa baki Farry tayi tace and so?after all kuɗi kike yiwa cos ina baki baki taba so mun abu mai kyau ba a rayuwa,you're always this greedy ga san nuna ke mai gaskiya ce bayan cewa mamanki ma dake bauchi reputation gareta...wani irin tashi Kiswa tayi inda Kafun Farry ta ankara a dauke mata fuska da mari mai kyau Kafun tace"wallahi tallahi idan kina haukanki da aka doraki akai kika zo inda nake kina ƙokarin faɗan abu mara kyau kan mamana to baki ɗaya garin nan yamana kaɗan,sannan magana da kike akn kuɗi ko mene ke kinsani abunda nake dashi baya mun kaɗan sannan a kullum ina godewa Allah da abunda ya bani and kuɗinki idan har ba daƙiƙiyace ke ba kinsan ban taba roƙonki ba sannan in faɗa miki idan baki sani ba duk da ban taba kawowa zaki mun gori ba amma ban taba kashe su ba suna nan a account and i will send Your fucking shit back,sannan maganar Saleek da kika hada kika saka nayi making fool of myself shima zan baki mamaki ,sha sha sha kawai wadda bata san inda yake mata ciwo ba".


Cike da fitina Farry ke riƙe da kuncinta hawaye na mata reto a fuska,cije lebe tayi tace "ni kika mara Kiswah?"kaɗa kai Kiswah tayi tace ki rama mana sai naga adadin haukanki,ai Kafun kace ƙwabo faɗa ya kece a tsakaninsu ,hayaniyarsu Mother ta fara ji,dakin tayi kai tsaye dan ganin maike faruwa,ganin yarda suka chakume gashin Juna ya saka Mother shiga da gudu tana fadin"wanne irin hauka kenan"ganin yarda Kiswa ke neman fin karfin Farry yasa Mother shiga ta kama Kiswa a rike kam tace ma Farry "oya zo ki yamutsa mun fuskarta da mari,aikuwa kamar Farry na jira ta fara haɗawa fuskar Kiswa mari,tana ƙokarin yin na huɗu Appa ya Sameer da sagir suka shigo,cikin zafin Nama samer ya shiga ya dauke Farry da wani irin mari da saida ta tuntsura,kafin ya farga Mother ta rama mata tana mai faɗin"'dan baka da hankali kasan mai tayi mata da zaka rama mata."wani irin fushi ke daukar Appa dangane da Mother wadda idan ya biye ta yau bazata kwana gidan sa ba ,a hankali ya saita kansa yace kai Sageer je ka riƙeta kamar yarda Mother ta riƙe Kiswa,Babu musu sageer ya riƙeta ba tare da ya saurari mai Mother ke faɗi ba,kallan Kiswa da fuskarta ya tashi yayi yace"idan har na isa dake ina so yanzu ki rama adadin Marin da tayi miki "aikuwa ba abune mai sabuwa ba"mother ta faɗa hannunta a kugu".


"Idan kuwa kika kuskura kika matsa daga inda kike da zummar hanata to a bakin Aurenki,na miki alƙawari".






TBC


Chuchujay


08130229878
[5/13, 9:28 PM] Chuchujay✍️: https://chat.whatsapp.com/DgTUlodRcp2AHM4rmfKTqK
💥KISWAH💥


(Surrogacy was the cause)


Na


Chuchujay ✍️


Book1⃣


Page1⃣1⃣


Da mutuƙar mamaki Mother ta juyo tana kallan Appa Wanda ya haɗe rai iya mutuƙar haɗewa,kanta ta nuna da yatsa idanunta sun kawo ruwa tace"ni zaka faɗawa abakin Aurena akan yarinyar da zubaida ta haifa ?"


Cikin nuna mata rashin wasa a maganarsa yace "ƙwarai kuwa idan kuma kina ganin bazan iya ba dan Allah ki ƙara taku daya daga inda kike kiga cikakken mamaki,magana da kika akan yarinyar da zubaida ta haifa Eh ita ɗin sannan ina so ki sani zan iya chanza ki amma bazan taba chanza Zubaida da Kiswa ba"maida hankalinsa yayi ga Kiswa yace"oya fara rama marukanki"Babu musu Kiswa ta matsa ga Farry wadda ke fuzgewa ta fara shatata mata mari har saida tayi mata huɗu masu kyau Kafun ta saka kuka jin yarda Farry ke kuka,har ga Allah rana ta yau ba ƙaramun muni gareta ba a gurinta dan ita mutum ce mai bawa family ɗinta muhimmanci ,bata san abunda zai taba mata su ,yau sai gashi irin sabanin da suka samu bashi da daɗin ji,kallan Farry dake faɗin wallahi bazata yarda ba Appa yayi yace "to dan Allah Faridha ki dauki mataki ni kuma zan baki mamakin da tunda nake matsayin Mahaifinki ban taba baki ba."


Sanin Halin sa idan yayi fushi yasa Mother da tayi tsit cewa"kija bakinki ki yi mana shiru anan Farry"wani irin kallo Appa ya bata yace "better da kina faɗa mata tuntuni da rana irin wannan bata zo ba"'dan shiru yayi yana nazari Kafun yace"Its better ku raba ɗaki, dama ai Faridha ɗin ta nace tun yarinta a haɗa su ,so dole yanzu tunda shashanci ya fara shiga tsakani kowa ya zauna ɗakin sa"


Yana kai karshen maganarsa ya bar ɗakin,kwafa Mother tayi itama ta fita,faɗa sosai Sameer ya fara yi musu inda Sagir yace "Just kallesu akan namiji wanda kilan ma yaudarace a zuciyar sa suke wannan faɗan kamar zasu kashe kan su"tsaki yayi ya fita a ɗakin yayin da Sameer ya yi musu Nasiha wadda Kiswa kawai ke gamsuwa dashi Amma banda Farry.daren Ranar Kiswa guest room ta kwana kafun washe gari tayi aikin parking to koma ɗakinta wanda yake da komai gyarawa kawai zatayi saboda Babu mai kwana cikin sa,washe gari bata iya fita aiki ba saboda ciwan kai dake damunta amma Farry kam karfin hali tayi ta fita dan da zaman gidan gwara ta fita ɗin koda ba office zata ba kuwa,Babu wani breakfast kowa ya kama gaban sa ban da Sameer wanda ya tsaya dan ganin mai Kiswa ke buƙata a saban ɗakinta ya taimaka mata.


•••••••••• •••••••••• ••••••••••


TUKUR BULA'S MANSION


"Son wait we need to talk like right now"mahaifiyar haidar ta shigo ɗakinsa tana mai zama kan couch kamar an koro ta,


Haidar dake tsaye yana gyara tie ɗin sa ne ya juyo yana mai cewa"Ummi hope im safe dai"kafarta ta ɗora kan ɗaya tace"trust me muddin kana tare da yarinyar nan Kiswa to bazaka taba zama lafiya ba,Ko kasan cewa ba yar ALIJUA bace sannan ɗiyar karuwa ce and bada Aure aka sameta ba,no bazan taba yarda da mace irin wannan ba cikin zuri'a ta".


Cike da confusion ya zauna yace"well rashin zama ƴar sa abune da na sani niece ɗin sa ce da Maman ta dashi uwa ɗaya uba ɗaya and ya ɗauko ta ne daga garin su bauchi bayan rasuwar mahaifinta ,a zallar sanina da kuma gaskiyar magana ita ba wadda aka haifa bace wajen Aure, da mahaifinta dangin sa kuma suna cikin garin Bauchi though sunyi abandoning ɗinsu,yanzu haka mahaifiyarta tana cikin garin Bauchi tayi Aure da yaranta biyu Khalel da Ra'abiatu ,Bansan Wake feeding ɗinki waccan maganar ba amma Ko wanne maƙiyin Kiswa ne and dole zan suing ɗinsa for defamation of character ki bani suna kawai Ummi.


Shiru ummi tayi tana nazari yayin da Abubuwa suka fara dawo mata daga zuwan Mother office ɗinta tayi mata tallan Farry har izuwa kiran da tayi mata jiya da daddare .kallansa Ummi tayi tace "ya zaman takewarta da Barrister juwairiyyah?"


'dan shiru Haidar yayi yana san ya fahimta dan a iya zamansa da Kiswa bata taba nuna masa koda da wasa ba tana fuskantar matsala a gidansu ba ,sannan a iya saninsa tsakaninta da yan gidan Babu wani matsala tana san su suna santa ,dan haka yace"Gaskiya Ummi i dont know about Mother tunda ba hirarta ta cika yi mun ba amma ga dukkan alama tsakaninsu ba matsala duba da yanayi na yarda mu'amalar Kiswa take da yaran gidan".shiru Ummi tayi tana kallan fuskarsa da yarda baya so ace akwai Matsala a rayuwar Kiswan sa,ajiyar zuciya tayi tace"i need to see that girl cos na tabbata akwai wani abu a rayuwarta wanda take boyewa,sannan a wannan gidan na Alijua na tabbata akwai bangaren da bata jin daɗi saboda Barrister juwairiyyah jiya take fada mun maganganun nan da daddare bayan na kirata,but my instinct is telling me otherwise duk da Kafun naji ta bakin ka hankalina ya yarda da maganarta amma da nayi magana da kai yanzu hankali na ya kwanta akan cewa ta haɗa labari ne saboda tana san ƴarta ta Auren ka ba Kiswa ba,koma dai yaya ne zamu san gaskiya Just bring the girl to my Boutique.


Tashi tayi ta fita tabar Haidar da jimami yana san sanin mai yasa tayi ma Ummi ƙarya sannan wacce irin rayuwa ma Kiswa ke yi a gidan ,yakamata yaje ya sameta,wayarsa ya ciro ya fara kiran layinta akashe dan haka kai tsaye da ya fita ya nufi office ɗinta, yana ƙokarin shiga Elevator ɗin da zai sadashi da floor ɗin office ɗinta Saleek ya na ƙokarin shiga,dakata masa Haidar yayi ya shiga kafin yabi bayan sa,kallo ɗaya Saleek yayi masa ya gane sa yayin da Haidar bai ma sanshi ba ,ba tare da Saleek ya kallesa ba yace "You're a doctor right"?


Kallansa Haidar yayi yana mai tabbatar dashi yake magana Ko a'a,murmushi Saleek yayi yace"i hope you made it out of Your relationship Alivee"kafun Haidar yace wani abu lifter ɗin ya tsaya a Floor ɗin da zasu sauka,Saleek ya Fara fita kafun Haidar yabi bayan sa yana mai Juya maganar da ya faɗa masa Na Allah yasa ya fita a relationship dinsa a raye wanda baya ce ga mai yake nufi ba,jan kunne ne Ko barazana,ƙaramun tsaki yayi ya nufi hanyar da zata sadaka da ofishin Kiswa , yana isa Amira ta taresa tana mai faɗin "barka da zuwa yallabai ,unfortunately yau Madam Kiswa bata shigo ba and Batayi reporting ba ina ta ƙoƙarin kiranta amma akashe,"dauko wayarsa yayi yana mai sake dialing ɗin wayarsa Kafun ya ɗagawa Amira Hannu ya fita a gurin dan zuwa gidan su Kiswa ,gudu kawai yake a titi dan a yanzu He's worried beyond expectation,koda yaje bakin gidan su cigaba da kiran wayarta yayi amma a kashe ,fitowa yayi a motarsa ya taka zuwa bakin gate ɗin gida ya Fara knocking cikin nutsuwa,yayi wajen knocking uku zaiyi na huɗun Aka buɗe ƙofar gate ɗin,sauke hannunsa da yayi ƙokarin knocking yayi yana kallan wanda 'ya fito,'ya sameer ne tsaye,Takowa yayi fuskarsa babu yabo Babu fallasa ya miƙa masa hannu yana mai faɗin "Assalamu alaikum"


Karba Haidar yayi yana mai amsa masa sallamarsa Kafun kuma yayi shiru bayan sun raba hannun su ,kallan sa ya sameer yayi da Kyau kafun yace "wa kake nema naga kana knocking hala kazo gurin Sageer ne"murmushi Haidar yayi yace "yaya Sameer right"?


Kallansa sameer yayi musamman da yaga yarda yake sinnewa ga kuma kiransa da yayi yaya wanda a ƙalla zasu iya yin sa'ani,ganin kallan da yake masane ya saka Haidar cewa"sunana Haidar and nazo gurin Kiswa ne dan ina ta kiran wayarta a kashe sannan naje gurin Aikinta an tabbatar mun bata zo ba shine nace bari nazo gida naga Ko lafiya".


Cike da Fara'a Sameer yace "kace mun wanda yayi wuff da zuciyar ƙanwata ya hanata sukuni"ƙasa Haidar yayi da kansa yana mai murmusawa kafun Sameer yayi masa jagora suka shiga yana mai dan jan sa da hira mai kama da tambayoyi har ya ajjesa falon da aka tanada domin baƙi Kafun ya shiga ciki domin yiwa Kiswa magana,ya jima yana ƙwanƙwasa mata ƙofa Kafun ta bashi izini ya shigo,da mamaki ya kalleta yace"har kin bani tsoro danaji baki amsani,ya jikin naki"?


Murmushi tayi tace"jiki da sauki yaya Sameer but my heart is still bleeding na rasa abunda yake Mun daɗi baki ɗaya na".


Murmushi yayi yace"well ina tunanin maganin matsalarki yazo ,kinyi baƙo a kasa,bazan kuma tsaya ja miki rai ba mai kiranki ba kowa bane face Haidar ɗinki,"wani irin daɗi taji ya ziyarce inda lokaci guda ta nemi damuwarta ta rasa, hijab ɗinta da tayi sallah dashi ta ɗauko ta saka taɗan gyara fuskarta kaɗan Kafun ta fita dan zuwa gurinsa ranta fari tas,da sallama a bakinta ta shiga falon tana mai faɗaɗa fara'arta ,tasowa yayi cike da damuwa da kulawa yace"Baby mai ya faru,mai ya same ki?are you sick?mai yasa kika kashe wayarki sannan mai yasa bakije aiki ba?you got me worried".


Ajiyar zuciya ta sauke tana mai sauke idanunta akansa ganin yarda ya wani ruɗe ,murmushi tayi tace "calm down masoyina wannan tambayoyin naka wanne kake so na Amsa,?Nasan duka ne dan haka bari na amsa maka su duka,Bana jin daɗi ne shi yasa ban bar wayata a kunne ba cos i was very sick to talk and bana yanayin da zan iya waya kuma shine dalilin da banje office ba,kaga na amsa tambayoyin ka baki daya.


Cike da damuwar da tafi ta farko yace"baki da lafiya shine baki karani ba ,mene amfanin zamana Likita rayuwata bata da lafiya "?


Takawa tayi dan zuwa ta zauna kafun tace"calm down nawan baka ga na fito gareka ba kasan idan na saka ka cikin idona Ko wacce irin damuwata da ciwo na daukewa suke ,ka kwantar da hankalin ka ciwan Kai ne kuma na warke Alhamdulillah .


Zuwa yayi ya zauna inda take yace"ina fatan ba faɗa kike ba kawai dan naji daɗi,kinsan lafiyarki tafi mun komai a rayuwa"murmushi tayi tace "hayatee calm down im okay wallahi,and maimakon kabari sai ka tashi a aiki kazo amma kabar aikin ka Just to see me".


Kaɗa kan sa yayi yace "yarinya kenan baki san

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login