Showing 15001 words to 18000 words out of 28317 words
Chapter 6 - Sai Na Auri Marubuci Nafseen Complete by Zulaihat.txt
kina gani anbarta ta kwana tun jiya yau kuma ta kai dare,maza rike hanun Sabeer ya rakaki ku rakata."
Nafeesa ta shagwabe fuska tana kokarin kuka, Mammah ta kara da, "Laa kar ki, kuskura Gobe ai da kwai makaranta kwa hadu acen amman yanzu kam Maryam na da bukatar komawa gida."
Ba ason ran Nafeesa ba haka ita da Sabeer suka raka Maryam ta hau nafe.
Tana komawa gida sallah tayi tana idarwa kuwa da zumudinta ta dauki wayarta tare da kunna data...
Urs Xayyeesherth
_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_
*NOBLE WRITERS ASSOCIATION*
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
_Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
https://www.facebook.com/106494781436168/
NA
XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH
27 feb 2021
10:5am
✨6STARS INDEED
_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_
PAGE-19
BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM
*Jinjina Gareka Haruna Birniwa👏ina godiya da goyon bayanka gareni tare da tallafamun wajen dauruwa a hanyar rubutu mafi inganci,Allah ya kara basira da haza❤️*
*Saudaukarwa gareku Deeymusah,tare da Walida Rano🥰ina yinku irin sosai dinnan*
*SAI NA AURI MARUBUCI FANS GROUP,Duk da kasancewar gajren fejine amman ina tsammanin ganin ruwan sharhi🤷♀️*
Messages ne suka fara shigo mata, zuba ido kawai ta fara yi tare da jiran sakon abincin ruhinta, da mamaki har sun gama shigowa amman ba ta ga nashi ba, sannan ko nuna alamar yana online ko ya zo online din ma babu.
Wata ajiyar zuciya Nafeesa ta sauke, ta dafa hannu a bangaren kanta, tsintar kanta da karanto INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJI'UN ta yi.
Nan take ta ji wani sanyi a ranta.
"Allah kenan!"
Abun da ta iya furtawa kenan, sannan ta kara riƙe wayar hannunta gam, group din marubuta ta leƙa, ai ko ban da zuba ba abun da marubutan ke yi kamar 'ya'yan kanya, hira cikin nishadi da barkwanci suke, wani sa'ilin su juya wa'azi ko wani bangaren na daban a cikin wannan group, kai duk tsegumin da kuke tunani to ya fi karfin hakan.
Murmushi ta sake a zahiri tare da fara bin hirar cikin group din, aranta tana sa ran cewa za ta iya gamo ko cin karo da hirar masoyin nata amman kash, har ta kai ga karshe ko alamar gilmawarsa ba ta gani ba.
Sallama ta yi cikin group din, cikin sa'a kuwa a amsa mata wajen mutane biyar a lokaci guda.
Cikin hirar da suke kawai ta tsinduma inda aka sa daya daga cikin marubutan a gaba da tsokana, SAIFULLAHI MUHAMMAD LAWAN duk da kasancewar yana da baki amman taron dangin da aka yo masa ya sanya shi yin tsit, ita kuwa Nafeesa abun nema ya samu tuni ta shige masa fadan tare da ba kowa amsa daidai da shi.
Dariya ya fara yana mai jin dadin ya samu 'yar team, tun dai ana gabzawa har da karshe fadan ya juye izuwa barkwanci da hira mai cike da nishadi da walwala, har ta rufe datarta kasancewar dare kuma gobe tana da skul, a zahirance bata da wata damuwa amman cikin zuciyarta damuwa ce fal domin tana da muradin jin lafiyar sahibinta, sai da ta yo alwala tare da sallah raka'ah biyu kan ta kwanta cike da yin addu'o'i kamar yadda ta saba kullum.
A bangaren NAFSEEN kuwa, gabadaya aiki ya yi masa yawa ba shi da lokacin wani abu ban da aikin da ke gabansa, a duk lokacin da aiki ya masa yawa irin haka bai samun damar hawa social media bare ya yi chatting sai tsakar dare yayin da komai ya lafa masa, mussaman in bai gaji da yawa ba.
Yau ma kamar kullum, karfe sha-biyun dare daidai ya kunna datar wayarsa domim duba sakonni yadda ya saba.
Abun mamaki da bai karewa dangane da Nafeesa Cikin barcinta hakan ya zo mata, abun da ke faruwa azahiri.
Daukan wayarta tai kamar yadda shi ma ya yi, messages din da yake tsammani gun abokan aikinsa ya fara dubawa tare da yi masu reply kan ya dawo kan 'yan uwa da abokan arziki.
Idon Nafeesa na kan Numbersa mussaman da ta ga yana yi mata typing gyara zama tai ji take tamkar ta kwato ta ji abun da yake rubutawa alokacin, ban da murmushi ba abun da ke bayyana a fuskarta.
"Iyee Antynwa? See dis rigima girl, an ki ace Antyn." Reply din NAFSEEN.
Cike da yanayi irin nata na shagwaba ta ce, "Ni ko? To ma ka daina kulani, kuma ba ruwana da kai, Uncle mai kan gwangwanni kawai."
Dariya maganarta ta ta ba shi har cikin ransa ya ce, "Sorry, dawo Momy Nafeesa ma ba Anty Nafeesa ba, shikenan ina mun shirya?"
"Yeess mu kulla tunda da mun kunce ne ma." Nafeesa ta yi masa reply cike da dariya tana mai jin dadi.
Ya ce, "Ok, to amman waye mai kan gwangwannin? Momy Nafeesa ce ko? dan ni dai na san Uncle ba ya da kan gwangwani."
"Umm... Umm... Ni dai yasin ba ni ba sai dai Uncle, shi ne mai katon kai irin na gwangwani."
Murmushi ya saki, har a zuciyarshi yana jin dadin yanda suke chat da yarinyar nan, ga barkwanci kamar 'yar mahauta, ga uwa-uba shegiyar shagwaba. Ya sake murmishi a karo na biyu kan ya tura mata da, "Byee Momy mai kan gwangwani aiki zan yi yanzu, kuma kin ga dare yayi sha biyu daidai, a yi barci kar Mama ta miki fada ko ki kasa ta shi sallah."
Ba ta so hakan ba ko kadan domin ji take zata iya kwana sannan ta yini in dai suna hira ne ba tare da ta taba gajiyawa ba, amman a yanzu ba yadda ta iya ko dan farincikinsa yadda ya bukata dole ta sauka.
"Nyt Bye, bye Uncle mai kan bera, kuma yasin ni ba na makara ni ke tashin limamin unguwarmu ma." ta rubuta ta tura masa, ji take rabuwa da shi tamkar rabuwa da numfashinta.
Batare da ta bare ta ga sakon da zai turo ba ta kulle data tare da gyara kwanciya, ta so kam ta ga amsarsa amma gudun kar ya fahimci tsananin kaunar da take a gare shi ya sa ta sauka, tana jin wani sashe na zuciyarta yana mata radar ta sake kunna datar amma ta basar saboda tsaro.
Duk hirar da Nafeesa tai kar ku ji mamaki in na ce maku a cikin barcinta ne batare da ta farka ba har yanzu, to shin da wa Nafseen ya yi chatting? Nafseen ce ko kuwa?
Al'amura boyayyu suna da yawa wanda muna bukatar saninsu.....
Kada ku gaji🥰ku biyoni a feji na gaba,love yhu oll❤️
Urs Xayyeesherth[3/16, 2:23 PM] Xayyeesherthul-humaerth: _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_
*NOBLE WRITERS ASSOCIATION*
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
_Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
https://www.facebook.com/106494781436168/
NA
XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH
✨6STARS INDEED
_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_
PAGE-20
BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM
🤗 *A YANZU NAFEESA XAYYEESHER AMMAN A KARSHE NAFEESA BA ZATA TABA ZAMA XAYYEESHER BA😁WANDA YA FAHIMTA YA FAHIMTA KAWAI👌*
*MRS MUBARAK,AISHATUL HUMAIRA,DEEYMUSAH,WALIDA RANO,LEEMAH,JASMINE,NAPHYSERT,FATIMA MUHAMMAD,INA YINKU IRIN TOTALLYN NAN ARADU😍KUNA SHARHI INA KWAMUSAN NISHADI😍*
***
Addu'ah tayi daga nan wani bacci mai dadi yayi gaba da ita tare da cigaban mafarkin Nafseen Wanda ya zame Mata jiki bata,kamar yadda taba tsallake ko da rana dayane ba tare da kallon Nafseen acikin mafarkinta ba,ba ta taba wani mafarki Wanda ba nashi ba Dan yadda har zanensa tanayi Wan da kawarta maryam take cewa ba iya soyayyan Nafseen bane a tare da Nafeesa zanen kaddaransu tamkar guda ne.
Cikin darannan yana ta faman aiki kwatsam sai ga Nafeesa ta fado masa arai ba tsammani murmushi ya sake tare da fadin, " My rigima girl hmmm ko ina take nasan she looks cutie." a zuciyarta sam ya san cewa ba son Yarinyar yake da wata manufar soyayya ba,abu daya yasani kawai dai tana birge shi duk da kasance ba wai ya taba ganinta ba amman yanayinta na nunin cewa yar gidan mutuncice,haka kuma duk da karancin shekaratun hakan bai hanata nuna kamun kai da sanin darajarta na 'Ya mace ba, abu guda Jameel yana da son mutane tare gudun wulakantasu koma ya suke, hakan ya sa in yana ba masoyansa lokaci wasu kan yi ma hakan wani kallo na daban.
Nafeesa kuwa tunda ta kwanta bacci bata farka ba sai da taji kiran sallah a kunnenta tashi ta yi ta shiga toilet tayi alwala tazo tayi nafila sannan tayi sallah ta jima tana addu'ah tare da rokon Allah ya cika mata burikanta tana wajen har gari ya para haske Qur'Ani nata ta dauka ta Karanta bayan ta kammala wayanta ta kalla tana murmushi ta nufi wayan tana son kallon reply din Uncle din ta.
Ta kai hannu kenan zata dauka wayan kenan taji muryan Mammah na kiranta " ki yi maza ki zo ki yi break zamu yi late fa."cewar Mammah
Dan turo baki Nafeesa ta yi cike da shagwaba ta ce, " to Bari nai wanka ina zuwa Mammahn Sabeer."
tana kallon wayan haka ta barta a wajen tayi wanka tazo tayi break suka wuce Mammah hospital ita da sabeer kuma skull.
Ana sauke Nafeesa tun a gate take zuba ido ko za ta ga habibty dinta Dan tayi missing nata.
Ji tayi an rufe Mata ido ta baya ta san ba Mai yin hakan sai Maryam ta juyo da farin cikin ta tana darjya ta ce , "habibaty Miss you ."
itama ta amsa mata da" Miss you more babyn Nafseen." Nafesa tayi wani fari da ido ta ce, " gaskiya yau kina son farin ciki ya hanani karatu." dariya suka sa sannan suka wuce sun rike hannun juna abin sha'awa.
Sun kusa department nasu kenan sai gasu ga su Mutansir zasu wuce shida yaransa suna hada ido da Nafesa yanayin sa ya canja kana kallon idon sa kasan ya gama storata Nafesa ta fahimci hakan, shi ko yana tuna abin da tayi masa a ranan sai zufa ta keto masa bare ya ganta.
Kawai nafeesa ta bata rai ta canja murya kaman Wanda ta jima bata hankainta ta ce , "kai zo nan." abokansa suka ce, " keeee lallai yau kina so ki koma gida a na kashe."
Duk da kasancewar suma atsorace suke gudun dai kar ya ci masu zarafine.
Mutansir ya ce, " ina ruwan Ku? Ku nace min dagani ku aka kira koni duk suka saki baki suna kallon sa,Aran su kuwa sun san dalili,tuni suka fara watsewa.
Nafeesa ta ce, "duk kace su dawo ayi komai a gaban su." Mutansir ya ce, "ku tsaya kowa ya dawo ta ce."maganar yake cike da tsoro.
Nafeesa ta gyara zaman glass dinta tare da gyaran murya ta ce, "kowa yazo ya dalla ma sa mari ."
suka fara zare ido.
Kallonsa kawai Nafeesa tayi ba tare da tace komai ba.
ya ce, "wai ba magana ake mu ku ba ne?"
nan da nan suka fara daya bayan daya suna wanke Mutansir da mari kafin kace me fuska ya kumbura dama duk abokan haushinsa suke ji yadda yake nuna musu isa da walakanci amman ba yadda suka iya tun da suna cin arziki.
sai da Nafeesa ta tabbata ya maku sannan ta ce, " dauki takalmanka a hanu ka bace min da gani ."
maryam me take idan ba dariya ba haka sauran students ma akko nan da nan mutansir ya sheka da gudu waje ba abin da kake ji sai dariya.
Maryam kan hadda su faduwa kasa Dan dariyar mugunta
Nafeesa ta ce, " tashi Wlh mu wuce hall nikan."
Taja Maryam suka wuce ban da tafi ba abun da ake yiwa Nafeesa ,domin tayi maganin wanda ya addabi dalibai har ma da daliban kowa na da cikin Mutansir.
suna shiga hall Maryam ta ce, "ke habibaty Wai meke faruwa ne dama tun a wancan ranan naga kaman akwai abin da ya faru ."
Nafeesa tayi dariya tare da fadin, " wallahi nima ban san komaj ba habibaty naga dai Kawai yana tsoron hada ido dani shiyasa Kawai na ma shi haka yau amma ni bansan meya faru ba."
Maryam ta ce, " aiko kin burgeni sosai wallahi kinyi maganin Dan iska,ashe ma ragone matsoraci." duka dariya sukayi tare da daukan handouts nasu su suna dubawa.
Mutansir ko kunya be barsa ya kasa zama a skull s motor shi ya shiga tare da nufan gida kawai Domin kuwa Allah ya sanya Mashi tsoron aljanu, afadarsa Nafeesa ba Mutum bace Aljan ce babu tantama yana tafiya yana jin takaici Wai yar talakawa ne Zata dizga shi duk yadda yake ji kansa dinnan,har yaransa su maresa shi ke nan raini ya shiga tsakani!
....bayan an gama lectures suka fito zasu wuce gida sun ci sa'a sun samu Nafe da wuri suka shiga kowa ya nufi gida kasancewar yau baza azo daukan Maryam ba.
Nafeesa na isa gida dai,dai kofar gidansu taci karo da bayan wanni sauri,bata gabansa ba amman ayadda tsarin bayan sa yake saurayine dogo madaidaici sanya da bluen shadda wadda tun daga nesa shekinta ke tashi,kamshi kuwa da ka dumfaro wajen kamshin zai maimaye hancinta.
Kasa magana tayi yayin da kamshin ke shiga cikinta abu daya ta iya furtawa , "Subhnallah!
Kalmar da ta furta ne ha sa saurin juyowa cike da kasaita,ban da murmushi ba abun da ke bayyana afuskarsa.........
"Subhannallah,"kalmar data kara furtawa kenan.
Urs Xayyeesherth
[3/16, 2:24 PM] Xayyeesherthul-humaerth: https://chat.whatsapp.com/Fogl4Tv2O7C8qEJRgUaLKG
_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_
*NOBLE WRITERS ASSOCIATION*
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
_Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
NA
XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH
✨6STARS INDEED
_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_
PAGE-21
BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM
_*Koda ke kadai mahaifiyarki ta Haifa kada ki taba sawa aranki cewa bakya da yan uwa, tabbas akwai yan uwa aduniya da suke kasancewa tamkar garkuwa garemu yayinda wata matsala ke kokarin kunno mana,Ina matukar alfahari tare da farincikin kasancewata da ke ANTYNA FARIDA MUSA (SWEERY) bana da kallaman godiya agareki domin sunyi karanci illa fatan alkairi😍*_
🙌😂 _*SAI NA AURI MARUBUCI FANS GROUP DA SAI NAGA MARUBUCI FANS GROUP ARADU INGA RUWAN SHARHI FIYE DA TAMBAYAR DA KUKEMUN KO IN TAFI HUTU😍*_
Kallonsa kawai ta tsayayi cike da Mamaki, Wanda ya bayyana karara afuskarta, ba kowa ta gani ba face NAFSEEN tsaye yana sake mata murmushi ba tare da ya ce ko mai ba.
Ta kasa tafiya kokarin fara Jan kafarta tai domin karasawa garesa, gabadaya ratansu ba zai wuce taku takwas Amman tafiya take ta kasa karasawa garesa, ga shi kusa da ita Amman Sam ta kasa iskansa, har yanzu ban da murmushi ba abun da yake sake mata, daga fuskarsa har kayan jikinsa ban da sheki ba abun da suke.
Daga hanunsa ya yi yana mata nunin cewa tazo hakan ya bata damar mika nata hanun kamar yadda ya bukata.
Ta mika kenan yana kokarin rikyewa karaf ,Mammah ta ce, "Nafeeesa Miye haka? Kina hankalinki kuwa."
Juyawan da zatai ba tare da ta ankare ba Ashe har ta shigo cikin gida, ba tare da taba Mammah amsa ba,saurin juyowa tai domin mika hannunta ga muradin ranta,Amman kash bata ga kowa ba.
Kuka ta fara tana fadin, "Mammah ya tafi,Mammah kin koreshi,Dan Allah ki ce ya dawo Mammah zan bisa, wallahi ina son shi."
Dafa kanta tai tare da kokarin faduwa da sauri Mammah ta karaso tare da tallefata, addu'ah ta fara karanto mata alokacin cikin sa'a kuwa Nafeesa ta fara dawowa, cikin raunanniyar murya take fadin, "Mammah zan kwanta ki kai ni daki."
Murmushi Mammah tai , "Ok Ammien Abhi Amman Please kada ki wannan barcin mai dadewa ban so kinji?"
Girgiza mata kai kawai tai.
Mammah ta kaita daki,ta kwantar da ita tare kunna mata karatu.
A bangaren Nutasir kuma tun da ya shiga mota yana tafiya ba abin da yake tunawa sai Nafeesa .
ba abun da yake tunawa illa ranar da ya fara ganin Nafeesa.
tun daga farkon kallon ta dayayi a makaranta zuwa abun da ta masa a yau , da wannan tunanin ya iso wani unguwa koda kallon unguwan kasan na masu arziki ne layin gidan su ya shigo daga farkon layin yake danna horn da karfinsa domin dabi'arsa kenan kowa yaji wannan horn din yasan Mutasir ne yadawo.
mai gadi ko tunda ya fara jin horn ya fito da gudu ya fara kokarin budewa Dan yasan idan Mutasir ya iso be bude ba yau shima yasan makomansa .
Yana isowa ya shiga da gudu domin baya driven a hankali bare ma yau dayake jinsa duk zuciyan shi ba dadi Talle mai gadi yana gaidashi Amma ko kallon sa beyiba nan da nan yasha jinin jikin sa.
Dan haduwa gidan su Mutansir ya hadu tunga wajen gidanma bare an shiga ciki .
apartment biyu ne a gidan na farkon ya nufa yana shiga Babban falon ya fara Momy" Momy" ya zauna akan kujera daya daga ciki ya kwantar da kansa tare da rufe idonsa wata matashiyar yar aiki ne ta fito ta ce, " tana sallah." Ransa ba dadi ya nufi apartment dinshi toilet ya shiga ya watsa ruwa ya dawo kan gado ya kwanta tareda Jan dogon numfashi.
Tabbas ya kamu da son Nafesa har yana jin idan har baj aureta ba komai zai iya faruwa .
yanzu taya zai tunkare ta gashi tsoron ta yake sosai da ace yasan zai so Nafeesa irin haka da bai mata abinda ya mata.
Ban da juyi ba abun da yake agadon domin ko idonsa ya rufe ita yake kallo yanayin ta da yadda take magana yana kara birgesa a gaskiya, Dady ya dawo asan abinda za,ayi .
Abun da yake ta sakawa acikin zuciyarsa kenan.
L
WAYE MUTASIR ?
Mutasir Dane ga Alhaji Abdallah Adam da hajiya balkis Ahmad tun bayan auren su suke son haihuwa Amma Allah bai basu ba sun jima a haka tun suna rai har suka cire Alhaji ba Irin abin da beyi ba amma shiru sai kawai ya fara tunanin aure Dan Kawai yasamu haihuwa Allah da ikonsa kuwa sai ga hajiya