Showing 1 words to 3000 words out of 23100 words

Chapter 1 - HABIBI DAIMAN Compelet Hausa Novels BY AUFANA.doc

??ࡱ?>?? ?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F? WordDocument????J0Table????????
Data
???????????????????? P??]KSKS?J?+???????ppmmmm=Q?T?dm??????????$U?*pmm??mmmm?1?Q1?Q?1Q??mQ _*HABIBI DA'IMAN*_
_*BY~AUFANA*_
_wattpad@Aufana8183_
_*Intelligent writer's association*_
_*Page 1~2*_
_*Bismillahir rahmanir rahim*_
Kwance take akan makeken bed d'insu tana bacci, daga d'ayan gefenta na dama, yarane kamarta y'ammata kuma kyawawa masu kama daita guda biyu, saikuma d'ayan gefenta ma wata yarinya ce wacca bata wuce sa'arta ba a kwance,

Jiyo bugun k'ofar da'akeyi ne yasa suduka sukai saurin farkawa daga baccinda suke a razane kuma a kid'ime kuma a tsorace,.

D'aya daga cikinsu ce tace "ohh...!!! God momy, wai meyasa take mana haka ne dan Allah",.

Itakuwa a kid'ime tai saurin mik'ewa dasauri jikinta har kyarma yake saboda sanin ko wacece ke bugun k'ofar taje tabud'e k'ofar a tsorace,.

Wata matace nagani a tsaye taharde gabas da yamma, kudu da arewa, tasha kunu tasha mur tamkar bata tab'a sanin miye dry ba, sauran yaran suna ganinta suma suka sakko daga kan bed d'in cikin tsananin tsoro da fargaba,.

Itakuwa a tsorace tace "mom...momy dan....dan Allah kiyi hak'uri wallahi gajiyarda mukai jiyane yasa muka kasa tashi dawur....." kyakkyawan marinda ta sauke matane yahanata k'arisa maganar,.

Cikin zafin nama da d'agawar murya tareda zazzaro idanuwa da firfito dasu woje tace "zanci kutmar ubanki wallahi idan kika k'ara cewa tak awajen, shegiya wawoyar banza",.

Kallon sauran tai sannan tacigaba da fad'in "wato yarannan kun rainani ko dan ubanku watou dama banzo na tashekuba da babu lokacinda zaku tashi ko, to mekuke nufi ne da aikin gida, kuna nufin nice zanmaku shi bayan kunsan bawani wanda zai maku aikin sai ku, to wallahi bara kuji yau ba'inda zakuje harsai kun k'arisa aikin gidannan gaba d'aya, ina nufin hadda School",.

Tana gama fad'ar haka tajuya tafice fuu kamar zata tashi sama.

D'aya daga cikinsu ce tazo dasauri tarik'o hanunta cikin tsintsar tausayi tace,

"Sannu *HUDAYYA* dan Allah kiyi hak'uri kinji halin momy sai addu'ah kawai" wani irin murmushi HUDAYYA tai wanda yafi kuka ciwo tashare kwallanda suka zubomata tace,.

"Wallahi HAMIDA insha Allah sai Allah yasaka mana da cin zalinmu da momy keyi, nidai fatana Allah yatashi kafad'ar Ammin mu yakuma dawo da tinanin Abban mu da hankalinsa akanmu ko Allah zaisa mufita daga cikin wannan k'angin bautar damuke ciki",.

"Ameeeen"

Sauran yaran biyun dake bayansu sukace sannan d'ayar tace "ni wallahi Allah magaji da wannan bautar, haba wannan wace irin wohala ce, mu da gidan mahaifinmu amma munzama tamkar bayi",.

D'ayar ma cewa tai "wallahi nima nagaji kawai musami Abban mu mufad'amasa gsky amaido da y'an aikin nan sucigaba da aikinsu, amma ina zamu iya aikin wannan k'aton gidan",.

Itadai HUDAYYA shuru tai tana sauraronsu batareda tace uffan ba, hamida ce tace.

"kunga kutashi muyi sallah muyi brush muje mufara aikin nan" nan dai suduka suka tashi suna k'unk'uni sannan suka fara shirin yin sallah,.

Da d'addaya duka farayin alwala tareda yin brush sunayin sallah har suka gama, suna gyangyad'in rashin isasshen bacci suka fita daga bedroom d'insu suka nufi cikin gida,.

Kai tsaye bedroom d'in wacca suka kira da momy sukai, koda suka shiga tana kwance kan bed d'inta, cikin ladabi suka durk'usa sukamata barka da kwana,

Kamar bazata amsa ba kuma ta amsa tana zabga masu muguwar harara, ganin haka yasa suka tashi zasu fice,.

Dasauri tace "ke hamida zo nasakaki wani aiki" wacca takira da hamida taje gunta sukuma sauran suka fice abunsu.

Kitchen suka wuce kai tsaye d'aya daga cikinsu na fad'in "shine takira y'arta tafiddata acikinmu dan kar tai aiki tawohala, hm wai ta dauka bamu gane nufinta ba",.

HUDAYYA ce tai murmushi sannan tace "hmm wai aunty HUNAYYA dan Allah meyasa momy take cutar damu take wohalar damu haka? bayan Ammin mu tace itama uwa ce agaremu".

Wacca takira da hunayya tace "nima bansaniba HUDAYYA, kawai mudai muyita addu'ah Allah yasa Ammin mu taworke ta tashi Abban mu kuma yadaina wulak'antar da mu",

"ameen" suka amsa suduka sannan suka fara aikace aikacen,.


Breakfast suka fara had'awa iya yanda suka iya sukai sbd sam basuwani kware ba wajen girki sbd bakoda yaushe sukeyinsa ba a da.


Aikuwa break d'in idan kaganshi dik jagwal gwale ne baiwani dafu ba, wainar kwanda sukai ko soyuwa bataiba gashi HUDAYYA hadda yanke hanunta tai wajen yanka albasa, daka gansa dai kasan aikin yara ne,.

Albasarma sai bayan da suka gama girkin sannan HUMAIDA tatino da ba'afa saka albasa ba, to shine HUDAYYA tad'akko tana yankawa cikin rashin sa'a tayanke hanunta,

Aikuwa jini yace salamu alaikum, nanfa yafara zuba kamar anbude pampo, a rikice hunayya taje dagudu tafad'awa momy,.

A maimakon momyn tanuna damuwarta da b'acin ranta sai kawai tahauta da masifa tana fad'in "wai yarannan me kuke nufi ne, to bara kuji wallahi ko k'afarta tayanke saitayi aikinnan, wato kun rainani ko, hmm yamaku kyau dani kuke zancen maza wuce kibani woje sha-sha-shar banza y'ar iska".

Jiki a sanyaye kwallah nazubar mata tabaro d'akin tadawo kitchen gun y'an uwanta, suna ganin yanayinda tashigo dashi ya tabbatar masu da korota tai,.

Kama HUDAYYA sukai suka fita daita sai kuka take tana yarfarda hanu saboda zafinda takeji gakuma jini har yanzu zuba yake,.

Shikuma yaro kunsan idan yaju ciwo koda ciwon baimasa zafi matuk'ar yaga jini yana zuba to rikicewa yake yatsorace.


Pampon woje sukaje suka fara wanke hanun, a maimakon jinin ya tsaya sai yacigaba da zuba, dik rikicewa sukai suka rasa yanda zasuyi,

Can dabara tafad'owa humaida saita tashi dagudu tafice, kusan 5mnts tadawo d'auke da wani kyallen atamfa, tana zuwa saita kama hanun tadaure da kyallen,.

Hunayya tace "aunty humaida d'an kwalinkine kika yago ko?" tace "Eh".

Bayan sun d'aure hanun sannan suka kamata suka koma ciki daita,.


Wani d'aki naga sun nufa ba bedroom d'insu ba, cikin sallama suka shiga suna isa ciki sainaga wata yarinya sanye da kayan masu jinya na asibiti wato nurse zaune kusa da wata kyakkyawar mace dake a kwance tamkar mai bacci, matar kuma tana kama ssi da yaran, hakan ya tabbatar min da itace mahaifiyarsu,.

Yarinyar na ganinsu saitai murmushi sannan tace "a,a triples, y'an ukun Ammin su kenan, yanaganku har 9am amma bakuje school ba?",.

Basu iya cemata komaiba saima k'arisowa dasukai cikin yanayin tausayi fuskokinsu kamar zasuyi kuka sukazo kusa da kyakkyawar macenda ke kwance akan makeken bed sannan ahankali suka kwantarda kawunansu akan jikinta suna fad'in cikin muryar tausayi,.

"Ammin mu kitashi dan Allah kitashi adaina wohalar damu tamkar bayi wallahi muna shan wuya ana wahalardamu ana cin zalinmu sosai",.

Ahankali sukaga tabud'e idanuwanta saikuma sukaga kwallah na zirarowa daga idanuwanta, HUDAYYA da hunayya ne suka sakad'a hannayensu acikin nata suna zubda kwallah humaida kuma tazo kusa da kanta tana shafa sumarta cikin yanayin tausayi,.


Kallonsu kawai take da dara daran idanuwanta farare tas amma bata iya masu magana, HUDAYYA da hunayya kuka suke sosai tamkar ransu zai fita humaida ce kawai kedan yin ta maza tana share kwallah kawai,

Cikin muryar kuka HUDAYYA kefadin "Ammin mu kitashi, kitashi dan Allah, ya Allah kabama Ammin mu lafiy....a" tak'arisa tareda sauke nannauyan ajiyan zuciya saikuma kuka yabiyo baya,.

Itama Ammin kwallah kawai take zubarwa tana kallonsu, nurse d'inda ke tsaye tana kallonsu dik tausayinsu yacikata sai sharan kwallah take,.

Suna acikin wannan halin kwatsam saisukaji shigowar momyn su acikin d'akin, saiji sukai tace,

"Kan uban can, lallai yarannan wallahi kun rainani fiye da tinani na, wato bama aikinda nasakaku kukeyiba ko, dakyau dani kuke zancen",.

K'atuwar bulala sukaga tafitar cikin zafin nama tadamko HUDAYYA dan tafi kusa daita nan tafara zabga mata bulalar ajiki, gaba d'ayansu sai suka sakko dasauri suka durk'ushe agabanta cikin kuka suka fara bata hak'uri,.

Cigaba tai da dukanta tana ihun neman taimako nan tacigaba da dukan sauran suma, matar dake kwance wacca suka kira da Ammi tadinga d'aga yatsanta tana nuna momy idanuwanta na zubda kwallah bakinta na rawa kamar tai magana amma ina ba damar yin hakan,

Nurse d'in ce taje tadinga rok'onta tana bata hak'uri da magiya akan tabarsu haka tamasu hak'uri, dakyar da sud'an goshi takyalesu bayan dikta kukkumbura masu jiki da duka,.

Dikda wohalarda sukasha hakan baihanasu tashi dagudu suka fice ba saboda tsoron karta sake damk'arsu,.

Suna fita kowaccensu takama aikinta tafara, kasancewar su yara k'ananu ne yasa dole aikin bazaiyi kyauba kamar yanda ma'aikatan gidan keyi,.

Sai kusan 2pm sannan suka kammala komai da komai, bayan sungama sannan suka wuce bedroom d'insu,.

Zaune sukai acikin bedroom d'in nasu kowacce tai tagumi fuska narai narai kamar zatai kuka gwanin ban tausayi.

#/Vote
#/Share
#/Comment
#/AUFANA for life
_*HABIBI DA'IMAN*_

_*BY~AUFANA*_
_wattpad@Aufana8183_

_*Intelligent writer's association*_

_*Page 3~4*_

_*Bismillahir rahmanir rahim*_

HUDAYYA ce tace "wayyo Allah na katausaya mana kasaka mana da cin amanarmu da akeyi, anacin zalinmu, ya Allah kasaka mana" saita fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai karatu,.

Suma sauran kukan sukeyi sosai gwanin ban tausayi, hanun HUDAYYA har yanzu a d'aure yake kuma yanamata zafi amma ahaka dole tadaure taci uban aikinda koda kud'i aka bata bazata iyayinsaba amma sbd wohala dole tayisa yanzu,.


Ganin dai kuka bashine mafita agaresuba yasa suka tashi da d'addaya suka farayin wanka suka sauya kaya, bayan sungama sannan humaida taje domin dibo masu abinci dan saima yanzune zasuyi breakfast,.

Dikda su suka girka abincin amma basuda halin sakawa kansu saisun jira momyn tazo tasaka masu iya yanda taga dama koda kuwa bazai ishesu ba,.

Haka kuwa akayi datazo wanda taga dama shita saka masu dikda kuwa tasan bazai ishesuba, haka humaida tad'akko abincin tafito ranta namata k'una,.

HUDAYYA naganin abincin saitace "yanzu wannan abincin ina zai ishemu dan Allah, ni wollahi yunwa nakeji" saita fashe da kuka,.

Cikin tausayi hunayya tazo tarungumeta tana rarrashinta, haka suka zauna sukaci abincin sannan suka d'ora da ruwa ko zasuji dama dama, bayan sungama sannan sukai sallar azahar suka konta,.

Ko 30mnts basuyi ba da kwonciya saigata tazo tace dole saisuntashi zuwa aikin maraice da girkin dare, HUDAYYA na kuka gashi yankuwarda tai tasakar mata zazzab'i amma haka matar nan tai biris tace baruwanta,.

Cikin rashin tausayi da rashin imani matar nan tajibga masu uban aikinda yafi k'arfinsu suna kuka suna sharan majina haka sukai aikin,.

Aikuwa sune basu gama aikinba sai kusan 9:30pm lokacin kuwa gaba d'ayansu sun gaji ssi sbd wohala, dikda yunwarda sukeji amma haka suka kwonta bacci agajiye batareda sunci komaiba,.


*D'AN TSOKACI*

Alhj. Modibbo, MUHAMMAD MOALLAYID'I, dattijo mai halin dattako cikekken bafulatani d'an k'asar kebbi, jinin fulani Ard'on rugar modibbo,.

Muhammad moallayid'i cikekken bafulatani ne haifeffen k'asar kebbi, cikekken d'an kasuwane kuma manomi,.

Allah ya albarkaceshi da tarin dukiyar dabbobi da tarin kud'i wacca yagada agun iyayensa dasuka rasu suka barmasa kasancewar shikad'ai ne suka haifa, bayan rasuwar iyayensa ne yad'ibi shanunda aka barmasa yasiyar,.

Bayan yasiyar sannan ya tattara yabaro rugar modibbo yadawo babban birnin k'asar kebbi inda yafara gudanarda kasuwanci,
Cikin ikon Allah kuwa Allah yasanyawa kasuwancinsa albarka,.

Acikin lokaci k'ank'ane yai fice yazama hamshak'in d'an kasuwa ko'ina yakan shigo da kaya kuma yakan d'ibi abunda yakeda a ksarsa yakai zuwa wata k'asa da batada shi yasiyar masu,.

Yana cikin haka ganin yanada kud'i sosai sai kawai yakoma rugarsu yadebi ma'aika daga cikin fulanin rugar yabasu kud'i makudai suka fara masa noma,.

Shekararda yafara noma a shekarar yai aure inda ya auri wata kyakkyawar yarinya bafulatana y'ar boko mai suna khadija acikin rugarsu, y'ar wani malamin primary ce mai suna garso,.

Tana jss 3 aka cireta akamasu aure, watansu goma cif da aure khadija ta haifi santala santalan yaranta tagwaye mace da namiji, hmm murna agun moallayid'i ba'a magana,.

Bama shikad'ai ba hatta danginsa na uwa da uba sunyi matuk'ar farinciki sbd shikad'ai ne iyayensa suka haifa yanzu shikuma gashi yahaifa,.

Kud'i makudai yafitar yadinga narka har akai suna inda yara sukaci sunan iyayensa da suka rasu, macen Aisha suna kiranta da mami namijin kuma Aliyu Barkind'o.

Haka moallayid'i yadinga bama yaransa kulawa shi da mahaifiyarsu khadija, Alhmdllh kasuwancinsa kuma albarka sai shiga take acikinsa,

Y'an biyu nada shekara hud'u khadija tasake haifar d'a namiji aka saka masa suna Ahmad, lokacin ne kuma moallayid'i yasaka y'an biyu makarantar primary lokacin ne kuma aka bashi ard'on rugarsu,.

Bayan tahaifi Ahmad tasake haifar Abubakar daga nan kuma batasake haihuwa ba,.

Ahaka suka cigaba da rainon kyawawan yaransu fulani sak masu kama da kakanninsu, yanzukam dikya sakasu makaranta na boko dana Arabi,.

Lokacinda y'an biyu suka kammala secondary sai yayiwa mami Aysha aure dawani d'an amininsa mai suna doctor uthman, bayan angama shagalin bikin yasamarwa Aliyu barkind'o admission a Australia,.

Mami Aysha nada shekara d'aya da aure tahaifi santalelen yaronta mai kama da kakansa sak, aikuwa ranar suna yaro yaci sunan kakan nasa wato HISHAM,

Hisham nada shekara biyu tasake haifar twin's dika maza HANASH da HINASH, daga nan kuma batasake haihuwa ba,.

Bayan Ahmad shima yagama secondary School shima yasake turasa Australia lokacin kuma Barkind'o Aliyu yakammala degree dinsa na farko haryafara master's dinsa, abubakar kuma yabarsa anan kusa dashi yana karatu yana taimaka masa akan business d'insa inda shima yasama mashi admission a A.B.U zariya,.

Saida Barkind'o Aliyu yakwashe kusan 11yrs a australia sannan yadawo gida Nigeria, kimanin watansa uku da dawowa mahaifinsa yadorasa akan kasuwancinsa sbd shi yafara gajiyawa shekaru suntafi donhaka shi yacigaba da gudanarda kasuwancin,.

Badan yasoba kasancewarsa babba a gida yasa dole yakarb'i kasuwancin hanu bibbiyu kodan mahaifinsa yai alfahari dashi,

Sannu ahankali kuwa yafara gudanarda business d'in k'asashe k'asashe ko'ina yawo yake acikin Africa akan kasuwancinsu,.

Tofa Barkind'o yadawo gida har yai shekara d'aya da dawowa amma baya batun aure koma kawosa bayayi a gabansa gakuma shekarunsa na tafiya amma bashida iyali,.

Ganin haka yasa moallayid'i yakirasa yamasa magana akan batun aure idan akwai wacca yakeso yafada idan kuma bashida yanema inkuma bazai iya nemaba shi zai nemamasa dakansa,.

Dasauri yacemasa bashida wacca yakeso amma zai nema insha Allah yakawo nan bada jimawa ba,.

Kasancewar bashida wacca yake soyayya daita kokuma wacca yakeso sbd dika dika baiwani dade da dawowa k'asar ba gaba d'aya gashi ba zama yakeba bare haryaga wacca tamasa acikin y'ammatan garin,.

Ganin yarasa mafita yasa dole yanemi amininsa wanda sukai primary da secondary atare yafad'amasa matsalarsa,.

Acikin lokaci k'ank'ane Aminu yamagance masa matsalarsa inda yahad'asa da wata kyakkyawar yarinya bafulatana dan yace bayason kad'o,

Sunanta Farida kuma ita marainiya ce, su hud'u ne agun iyayensu ita da yayanninta mata biyu Fatima Firdausi sai k'aramin kanensu wanda mahaifiyarsu tarasa ranta lokacin haifarsa Faruk,.

Farida kyakkyawa ce son kowa k'in wanda yarasa, yarinya ce mai hankali, nutsuwa, ilimi, tarbiya, dakuma tsintsar kyau, iyayensu fulanin k'asar yola adamawa ne aikine yakawosu k'asar kebbi har sukai gidan kansu,.

Batareda sanin Barkind'o da y'an uwansa ba mahaifinsu moallayid'i yagina masu wani tamfatsetsen gida mai d'auke da part hud'u da estate na masu aiki, a can saman gate din gidan anrubuta WELCOME To MUALLAYID'IS FAMILY.

Sai bayanda akai engagement dinsa da farida sannan yanuna masa gidan, yai matuk'ar farinciki kuma yai murna sosai nan yaita gdy tareda kyakkyawar addu'ah wa mahaifin nasa,.

Cikin lokaci k'ank'ane soyayya da shak'uwa tashiga tsakanin Barkind'o da farida barkind'o yana matuk'ar k'aunar farida haka itama,

Barkind'o mutum ne maison gayu, gyai ne nagaske he's very handsome gyai bayason kazanta kokad'an yana kula da kansa ssi hakan yasa dik tarin shekarunda yakeda suka b'oye acikin yanayin yarintar jikinsa.

Batareda b'ata lokaci ba aka fara gudanarda shagalin bikinsu, hm zan iya cemaku a wannan bikin b'arin naira da dollar's akaita yi takoina b'angaren biyu, b'angaren amarya dana ango kasancewar itama amarya farida mahaifinta mai dukiya ne ssi hakama yayyenta,.

Ana cikin shagalin biki abba moallayid'i da matarsa umman Ahmad suka fara tarewa a sabon gida kasancewar part hud'u ne acikin gidan wato shi da yayansa, Umman ahmad kam tareda ma'aikatanta tazo sbd tanajin dad'in aikinsu ssi shys tace bazata iya canja su ba,.


Bayan angama shan shagalin biki amarya ta tare akatafaren gidanda aka gina dominta tareda sababbin ma'aikatanta,.

Watansu tara cif da aure farida tahaifi kyakkyawar y'arta, murna da farinciki agun barkind'o baya misaltuwa,.

Haka suka fitarda naira aka kasheta tamkar baasan zafinta ba, ranar suna yarinya taci suna HUMAIDA,

Humaida nada wata uku a duniya akai bikin kannen Barkind'o Ahmad da abubakar danhaka farida tasami abokan zama,.

Humaida nada shekara biyu a duniya farida tasake haifar y'a mace mai suna HUNAYYA, batafi kwana goma da haihuwa ba Rukayya matar Abubakar tahaihu tahaifi d'a namiji wanda yaci sunan abba moallayid'i kakansa wato Mohammad sai suka masa inkiya da Affan,.

Rukayya nada wata hud'u da haihuwa maryam matar Ahmad tahaifi y'an biyu mace da namiji, ranar suna macen taci sunan hajiyarsu barkind'o wato khadija namijin kuma Bashir sunan kakansa na uwa,.

Haka albarka tadinga shigowa acikin wannan ahalin, farida da k'annenta maryam da Rukayya suna zaman lfy da k'aunar juna, suna kuma bama yaransu tarbiya mai kyau wacca take cike da tsabta,.

Hunayya nada shekara d'aya da haihuwa Barkind'o Aliyu yasake aure inda ya auri wata yarinya mai suna Saudatu,.

Saudat y'a ce agun wani hatsabibin malamin tsibbo wanda yake zaune a garin Legos Nigeria, barkind'o yahad'u da saudat ne lokacinda yaraka abokin kasuwancinsa gun mahaifinta malam Haliru mai sittin tara,.

Sunje gunsa ne domin yataimaka masu akan kasuwancinsu kwatsam suna aharabar gida suna jiran fitowar malamin saiga saudat tashigo ita da K'awarta,
Tana d'ora idonta kan barkind'o saitaji ba namijinta takeso a duniya sai shi,.

Bayan sungama abunda suke gun mahaifinta saitaje tasami mahaifin nata tafad'amasa tanason barkind'o ita yamata shi takeso ta aura,.

Nantake kuwa yacemata ta kwantarda hankalinta tama k'addara ta auresa kawai,

Malam haliru mutum ne maison iyalinsa yana matuk'ar k'aunar yayansa zanma iya cemaku sune silar fara wannan mummunan aikin dayake na tsibbo sbd kawai suji dad'i suyi rayuwa tamkar sauran y'ayan masu gata waenda kuma iyayensu keda tarin dukiya,.

Ko gidansa da suke aciki kagansa zaka rantse da Allah kace nawani hamshak'in mai kud'i ne ko d'an kasuwa, upstairs ne hawa biyu sannan dika yayyen saudat mata biyu kowaccensu hamshak'in mai kud'i take aure yanzu ita kad'ai ce tarage wacca batayi aure ba dama su uku ne,.

Kuma kowacce daga cikin yayyen nata ita ke mulki acikin gidanta koda kuwa itace ta uku kota hud'u to zaka tadda itace ke fad'a aji a gidan,.

Acikin k'ank'anen lokaci malam haliru yai dik yanda zaiyi da tsafe

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login